Sponsored Links
Hausa NovelsKurkukun Kaddara Hausa Novel

Kurkukun Kaddara 74

Sponsored Links

*💋KURKUKUN ƘADDARA💋*

قصة خائفة ومتعاطفة للسجناء💔🥺

*Daga alƙalamin Hafsat Boss Bature✍️*

Dedicated to Aunty kubra💘🌹

74

*Gargarɗi!!!*

_Ban amince wani ko wata ya yi amfani da wani sashe na book din nan ba ta kowace siga, ko a karanta mini shi a Youtube, ba tare da an nemi izni a wurina ba. Ko a haɗa mini document, idan kunne ya ji jiki ya tsira, ko da Allah na bar mutun zai bi mini haƙƙina_

💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫

*_ALBISHINKU MATAN AFRICA DA KEWAYE, SHAHARARRA KUMA K’ASAITACIYAR MAI SAIDA KAYAN MATAN NAN WATO DR MAMAN YUSUF LIKITAR MATA SOKOTO TANA FARINCIKIN SANAR DAKU CEWA ZAKU IYA SAMUN KAYANTA ADUK INDA KUKE A FADIN NIGERIA DA NIGER HARMA DA WASU K’ASASHEN BAKI DAYA, KU SANI A DADE ANAYI SAI GASKIYA KUMA MACE MAI GYARA KANTA BATA BORANCI , INA MARABA DA MASU SIYAN DAYA KO SARI_* 08133079957

*_munada zafafan kaya kamar haka ,_*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻

*Hadin amarya budurwa ko zawara*

*Hadin uwar gida Mai taken (Maida tsohuwa yarinya)*

*Maijego package (virgin gain)* 📦

*Hadin sabon budurci ga yarinyar data rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar da namiji*

*Sahihin maganin sanyi na Maza Dana Mata Wanda yake fatattakar sanyi cikin Dan lokaci*

*Maganin gyaran nono Wanda zai gyara maki nononki cikin Dan lokaci komai lalacewarsa*

*Maganin hips Wanda zaisa shape dinki ya fita kiyi kyau kema ki shiga jerin Mata masu aji*

*Maganin kiba Wanda zaisa ki ciko kiyi kiba yar dai dai misali kema adinga binki da kallo Idan kin juya Sam rama batayi ba yar uwa*

*Hadin mallaka ba boka ba malam , akwai taimakon da muke bayarwa ga Mai butsarin namiji Wanda cikin ruwan sanyi Zaki dinga juya abunki , haka akwai Hadi na musamman Wanda komai rowar namiji sai kin samu alkhairin a wajanshi,*

*Muna da kalolin gumbuna masu Saka ni’ima sha’awa da dandano*
*Kalolin garrika mash gyara gaban mace da jimawa ajiki*
*Kalolin Zuma masu saukar da ni’ima Nan take da gamsar da maigida*
*Kalolin tsumi Wanda cikin sauki zasu Baki ni’ima da dandano irin wadda akeso*
*Kalolin matsi Wanda suke ciko da gaban mace matse gaban mace da bata Wani irin dadi da dadano*
*Akwai set kala kala Wanda yawansh ya wuce na zayyanasu anan ga Mai bukatar kayana zata iya mun magana Kai tsaye ta hanyar Kiran ko Kuma Whatsapp* 👉🏻 08133079957

*Muna dahuwar zabo ,dahuwar kaza ,dahuwar kifi ,dahuwar zuciya ,dahuwar Yan shila ,dahuwar tsoka Tara ,dahuwar Kwan mallaka, dambun nama ko na kaza Wanda yake saukar da ni’ima da jimawa sosai ajikin mace*

*Idan nace zan rubuta komai da komai to wannan page din ba zai isheni ba ,Amma ga masu sha’awar siyan kayana Zaku iya mun magana Kai tsaye ta wannan number, haka masu sha’awa su dinga ganin kalolin kayana a status sumin magana ta wannan number sai nayi seving numbers dinki ta hakan ne Zaku dinga ganin kalolin kayana idan na daura* 08133079957

*Ina maraba da Mai siyan Daya ko sari Dr maman Yusuf likitar mata sokoto*

💋PRISONERS💋

“Ita mu ke jira ta fito daga wanka, Ki koma ɗaki ki kwanta, Yanzu zamu shigo Ciki” Hibba ce ta bata amsar tambayar ta, juyawa jamimah ta yi zuwa cikin ɗakin su ta koma saman gado ta haye tare da kwantawa.

“yanzu haka zamu zauna muna ta jiranta? Shiru duk irin bugun ƙofar da mu ka yi babu alamun zata buɗe mana, Anya kuwa lafiya? Ni tsoro na kada ace wani abun ne ya same ta,” a cewar Deeja, hankalin su duk ba a kwance ya ke ba.

“In sha Allah ma ba abun da ya same ta, Zai iya yiwuwa bacci ne ya ɗauke ta a cikin toilet ɗin ko kuma zurfin tunani ta shiga…..” tunkan Batul ta rufe baki Sarah tace “wani irin bacci ne wannan mai nauyin gaske da har za’a dinga bugun ƙofa mutun bai farka ba? In kuma zurfin tunani ta shiga ai yaci ace bugun da muke ya dawo da ita hayyacin ta, Gaskiya bana tunanin haka sai dai wani abun ne na daban,” kowa na tofa albarkacin bakinsa,

“Yunwa nake ji, ƙwara ku zo mu haɗu Mu ci ganyen nan idan mu ka kammala sai mu ƙara jaraba Bugun ƙofar” A cewar Parveen, Atare su ka matso kusa da kwandon, Kamar akuyoyi haka suka dinga kwaso Ganyen Suna Cunkusa shi Cikin bakunan su, a tsiyace su ke taunar shi, Zuciyoyin su duk ba daɗi, damuwar rashin Angel ta hana su sakat.

Suna tsaka da Cin Ganyen kunnuwan su suka soma Jiyo masu motsin buɗe ƙofar ɗakin su, A firgice su ka ɗago Suna kallon Junan su! Zuciyar su cike da fargabar Motsin buɗe ƙofan da su ke Ji, Tun da sun riga sun san An kawo masu Abinci, shiru su ka yi an rasa mai ƙwaƙƙwaran motsi A cikin su, hatta ganyen da suka cusa a Cikin bakunan su sun dakata da taunar su, babban abunda suke jima fargaba kada ace Tsohuwa Zafreen ce ta kawo masu ziyara, Tuni kowannan su Yasha Jinin Jikin shi.

Garam! Su ka ji an datse ƙofar alamar wanda Ya shigo Ya fita, nauyayyiyar Ajiyar zuciya kowaccen su ta sauke, Kafin wani yai yunƙurin motsa La66ansa Muryar Jamimah ta karaɗe kunnuwan su.

Wata irin razananniyar ƙara ta fasa Mai kuwar gaske, Hankulan su A tashe su ka mimmiƙe da gudun gaske suka faɗo Cikin ɗakin a sukwane Suka ci uban burki Suna faman Haki, A tsakiyar ɗakin su ka ganta Ɗaure da bargo a jikinta Sai tsalle ta ke yi, babu wanda Ya lura da me ta ke Yima Murna, Rai a6ace Parveen tace”Wannan wani irin rashin Hankali ne jamimah? Salon kawai ki kara tada mana hankulan mu shine kika fasa Ihu kamar mai ta6in Hankali”? Jin muryar Parveen Yasa ta juyo tana kallon su fuskarta ɗauke da murmushin Farin Ciki,.

“An dawo mana dasu Ƴan uwan mu dole in yi farin Ciki…..” Tun kan ta ƙarasa maganar Kusan atare Suka kai idanuwan su akan benan Ɗakin su! Wani irin bugu zuciyoyin su suka yi atare, Abu ne da basu Yi tsammanin shi ba, Tamkar A mafarki Haka suke ganin su, sun kasa Yarda da abunda idanuwan su suke nuna masu!

A tsaye su ke cirko cirko saman Matakalar benan, su biyar babu Danish Daga ganin su babu ƙoshin Lafiya atattare dasu, Fatar Jikin su Ta yi haske Hatta Haris da ya ke da duhu fatar shi ta canza, Sun rame sun bushe kamar babu Jini a jikin su, ƙafafuwan su kansu ba adai dai su ke ba, musamman ƙafar Mubeen da ta javed rawa su ke Yi kamar zasu kasa, Sumar kansu Kuwa Duk a hargitse Dama Allah yayi su da tarin sumar kai, Ba kamar Javed Da Gabriel sai Naufal, yanayin yadda suka yi tsayuwar Ya nuna sam babu kuzari a jikin su Kamar waɗanda Aka ɗebi Naman Jikin su, Sun faɗa sun zabge……..”

Muryar Deeja Na rawa ta furta sunan HARIS! Mamaki ne ƙarara akan Fuskokin su, Lamarin Ya yi matuƙar ɗaure Masu Kai, Cikin karyayyiyar Murya Parveen Ta furta Sunan NAUFAL! Hannun Batul dafe da saitin Zuciyar ta ta furta Sunan JAVED!! Muryar Hannah A disashe ta ambaci Sunan MUBEEN! Cikin shessheƙar Kuka Azeeza Ta ambaci Sunan GABRIEL! kamar a mafarki haka suke ganin su, Jikin su ba ƙaramin sanyi yayi ba, zuciyoyin su sun karaya sosai, Ganin yadda ƴan uwan nasu Suka Ƙi motsawa, Bakomai ya ɗaga masu hankali ba face Ganin Yadda Haris daya fi su ƙiba Ya koma Ramamme uwa su Javed, Sun fita hayyacinsu, Daga ganin idanuwan su ba ƙaramar izaya suka sha ba, Allah kaɗai yasan Azabtarwar da su ka yi masu na tsawon watannin da su ka yi a hannun su.

Tuni idanuwansu Deeja sun Cicciko tab da ƙwalla, Parveen tana kuka tace”Wlh kamar basu ba! Kamar an canza mana ƴan uwanmu! Ku kalli yadda suka rame ko magana ma basu Iya yi, Ni ina tsoron kada ace irin na unaiza su ka yi masu……..” daƙyar ta ƙarasa maganar saboda kukan daya ciyota, Cikin rauni na murya Deeja Tace”Haris kaine ka koma haka? Ina Jikin ka ya ke? Javed Mubeen Naufal baku Iya magana? Meyasa ku ke kallon mu kamar Ba ku gane mu ba”?

“Ba kallon su Ya kamata mu tsaya muna yi ba, Yakamata muje gare su, wata’ƙil Sun kasa yin tafiyar ne” A hankali su ke tafiya suna tunkarar su kamar sunga abun tsoro, Koda su ka ƙaraso gaban benen Atare suka dakata da yin tafiyar suna kallon su, Gwanin ban tausayi farar fatar wuyan su harda jajayen ta66una na yakushi, Wurin yayi jawur La66an su duk sun faffashe sun bushe, Gabriel hada busasshen jini saman Ƙaramin lower lip ɗinsa daya ciza launin shi pink, Fatar idanuwan su sun yi ja alamar sun yi kukan mutuwa Sakamakon wata azabtarwar da aka yi masu.

Fashewa su ka yi da kuka tamkar ransu zai fita Yayin da su ke cigaba da bin ƴan uwan nasu da kallo mai nuni da tsantsar Tausayin su da su ke ji.

Azeeza Ce tai Ƙoƙarin matsawa ta haura saman matakalar farko har takai ga inda Gabriel Ya ke atsaye, Faɗawa ta yi saman jikin shi tana cigaba da yin kuka, Ganin ta ta6a shi bai nuna yaji zafi ba yasa Deeja matsawa Ta rungume Haris a jikinta, Da sauri batul ta hau benan ta Ruƙo Javed ta kwantar da kanshi saman kafaɗarta, Parveen ta nufi Naufal ta janyoshi ta rungume shi sosai tana cigaba da yin kuka, Hanna ce ta ruƙo Mubeen ta haɗa shi da jikin ta, Yadda suka ƙanƙame su A jikin su suna yin kuka tamkar ran su zai fita, Sun yi kewar ƴan uwan su sosai.

Matsawa saman benen Yasmin da su rubina su ka yi, A bayan su Batul dake rungume da ƴan uwansu maza suka ɗaura kawunan su, Gaba ɗaya sautin shessheƙar kukan su ce ta karaɗe Ɗakin nasu, Jamimah da sarah ne kaɗai su ka rage a tsaye bakin benan suna kallon su Idanuwan su cike tab da ƙwalla.

Batul da ke ruƙe da javed taji Jikin shi ya saki gaba ɗaya ya tafi zai sulale ƙasa da sauri ta daddafe shi a haka suka Zauna saman Matakalar benen, ta tallabo fuskar shi da Hannayenta biyu “Javed! Pls ka yi mini magana Inaso insan a wani hali ku ke ciki” Daƙyar ya ke iya kallon fuskar ta, saboda raunin da idanuwan shi su ka yi mashi kamar zasu lumshe, hatta numfashin su da hucin zafi Ya ke fita.

“Haris Ɗina ne ya koma haka? Inna lillahi Wa’inna ilaihirraji’un! Wlh ba zamu ta6a yafe masu ba, Allah ya isa tsakanin mu dasu Mugaye Azzalumai, Duk sun canza masu Halittarsu, ko magana ma ba su iya yi” cikin jin Ƙunar rai Deeja ta yi maganar, har lokacin bata janye haris daga jikinta ba, Kamar zata maida shi Cikinta,

“Dan Allah Naufal ka buɗe baki Ka yi magana, Hankalin mu ba a kwance ya ke ba, Muna so Muji koda muryoyin ku don mu tabbatar da cewa kuna da Lafiya” parveen ce ta yi maganar, fuskar ta sharkaf da hawaye yayin da ta ɗago da kan Naufal daga saman kafaɗar ta, Bawan Allah sai bin su da ido Ya ke yi, fuskar shi Ta yi jawur saboda hasken da ke gare shi, Dama duk Cikin mazan In ka cire Danish a wurin haske sai Naufal mutun na gaba Javed ne Duk da shi ba fari bane sosai amma Baya a cikin jerin baƙaƙe Launin fatar shi Chocolate ce, Yana da tarin sumar kai, iya kafaɗar shi ta tsaya, Bayan shi sai Gabriel Kalar fatar su Kusan ɗaya Da Javed babu bambanci, Kamar za suyi hauka wurin yi masu magiya akan su yi masu magana ko sun ji sanyi acikin ran su, Gaba ɗaya sun manta da zancen Angel tun da su ka yi tozali da Ƴan uwan nasu.

“Jikin su ba ƙwari, Muna ƙara masu ciwon nasu, Mun ishe su da surutu, Mu taimaka masu Su shiga cikin ɗaki su kwanta,” Hibba ce ta yi maganar, Ruƙo hannun haris Deeja tayi a cikin nata, Ba ta yi tsammanin zai motsa ba sai ji ta yi ya sanya hannu ya dafa kafaɗarta, Hakan ba ƙaramin kwantar mata da hankalin ta Yayi ba, A hankali su ke yin tafiya suna tunkarar cikin ɗakin, Ruƙo hannun Naufal Parveen tayi da taimakon ta ya dinga ɗyangyasa ƙafar shi suka nufi gadon shi, Yayin da Batul ta ruƙo javed ya kwantar da kanshi saman kafaɗarta a haka suka nufi cikin daki, Ita kuma Hannah ta taimaka ma Mubeen, Ya rage saura Gabriel da Azeeza ke a rungume dashi, ta rasa ya za ta yi ta taimaka mashi su shiga ɗakin, Gaba ɗaya su Hibba sun bar bakin benen babu wanda Ya lura da Gabriel da su ka bari saboda babu shaƙuwa mai ƙarfi a tsakaninsu dashi, Sunfi Jinsu Javed shiyasa Hankalin su yafi karkata akansu.

Tana so ta taimaka mashi sai dai bazata Iya ba, Saboda tsayin dake gare shi Ga ƙirar Jiki, tsawonta daƙyar Ya kai waist ɗin shi, ruƙo hannun shi ta yi a cikin nata tare da jan shi don su shiga ciki ko motsi wannan baiyi ba, hakan yasa ta fashe da kuka tare da ɗaga murya tana yi ma su batul magana “Wai bazaku zo ku taimaka mashi ba? Kun barshi shi kaɗai a tsaye” babu wanda Ya juyo ya kalle ta Hankalin su ba akanta ya ke ba, Tsagaitawa tayi da yin kukan tare da kallon fuskar shi wata irin zufa ce ke tsastsafo mashi, Ya galabaita sosai, Cikin shessheƙar kuka ta ambaci sunan shi, bai amsa mata kiran da ta yi mashi ba, Sai dai taga Ya zuƙunna saman matakalar benan Yana faman Fitar da numfashi mai ɗumi.

“Ka tashi mu shiga ciki, Inaso na taimaka maka” A hankali yake bin ta da kallo fararen idanuwan shi sun canza launi zuwa ja, daga gani ba ƙaramin jin jiki ya ke yi ba, azeeza sarkin tausayi hada sanya Ƙasar rigarta saman fuskar shi tana share mashi gumin da ke tsastsafowa, acikin zuciyarta ba ta ji dadin yarda su Batul suka manta da zancen shi ba, Shi kaɗai suka ware, marairaice mashi fuska tayi “Pls ka tashi mu je ka kwanta, baka da lafiya fa, Nasan baka jin dadin Jikin ka,……” tunkan ta ƙarasa maganar Gabriel ya yunƙura ya miƙe, Daurewa kawai ya ke yi don ba ƙaramin jiri yake gani acikin idanuwan shi, ƙoƙarin Yin tafiya yayi Ƙafarshi ta Hagu taƙi bashi haɗin kai, Gaba ɗaya Ya tafi zai kife ƙasa, Azeeza ta fasa uwar ƙara haɗi da ambaton sunan shi, hakan ne ya jawo hankalin su Parveen ga kallonta A lokacin har sun taimakama su Haris sun kwanta saman gadan su, Da gudun gaske suka nufi Gabriel dake ƙoƙarin faɗuwa, Da ya ke Namiji ne Allah yayi shi da ƙarfi bai bari Ya faɗi ƙasa ba, Handrail ɗin benan Ya dafe da hannun shi, Sai faman Huci ya ke fitarwa, Nannaɗaɗar sumar gaban goshin sa duk ta rufe idon shi, Koda su parveen suka ƙaraso ganin ya dafe Hannun benan yasa suka sauke ajiyar zuciya, Azeeza kamar jira ta ke yi su ƙaraso ta dinga surfa masu bala’e akan sun tafi sun bar ta da shi, bayan sun san ita ƙarama ce, da ace ya faɗi kasa kanshi ya bugu me suke tunanin zai biyo baya, Faɗa sosai ta rufe su dashi, ta inda take shiga bata nan take fita ba, sai faman tada jijiyoyin wuyanta take yi duk akan Gabriel.

“Allah ya huci zuciyarki Azeeza bada son ranmu muka ƙyale shi ba, Hankalin mu ba a kwance Ya ke ba, Amma yanzu kiyi haƙuri, zamu shiga dashi Ciki” Fuskar Yasmin a hautsine tayi mata maganar, ɗaure fuska azeeza tayi hada ruƙe qugu tana binsu da kallo.

Parveen da Yasmin ne suka taimaka wurin ruƙo Gabriel Suka nufi Cikin ɗakin dashi, agaban gadon shi suka sake shi ya hau ya kwanta, Daga gefen shi Azeeza ta hau ta kwanta tana ƙare mashi kallo mai nuni da tsantsar ƙaunar shi kewar shi da Tausayin shi.

a 6angaren Haris Deeja ce zaune saman gadon shi, Eve da yasmin suna zazzaune gefen gadon shi, Sai sannu su ke yi mashi, Sam ya kasa amsa masu, Sai dai yabi su da ido,

Javed Yana a kwance saman gadon shi, Batul da Sarah ne Zaune gefe da gefen mattress ɗinshi, Ji su ke kamar su ɗauke masu ciwon Jikin su saboda tsabar tausayinsu da su ke Ji,

Idan muka koma 6angaren Naufal Shima Yana kwance Ya lumshe idanuwan shi, Parveen da Hibba suna a zaune saman gadon nashi, suna yi mashi sannu.

A yayin da Hannah da Rubina suke akan gadon Mubeen, hakan ba ƙaramin sanyaya zuciyoyin ƴan uwan nasu yayi ba, Ganin yadda suka nuna damuwa akan su,

“Yanzu ya zamuyi? Ko abinci babu da zamu Iya basu nasan dole suna jin yunwa,” parveen ce ta yi maganar,

“Ko ruwa ne mu fara basu Mu ga idan zasu sha” a cewar Batul, Jin suna maganar ruwa yasa Jamimah ta nufi ƙarƙashin gadon batul ta lalubo robobin ruwa taje ta miƙa ma Deeja, Bayan ta kar6a taje ta miƙa ma parveen kafin ta nufi Batul ta bata ɗaya” da sauri ta koma ta ɗauko sauran robobin ruwan guda biyu Ta kaima Hanna ɗaya, sannan ta nufi gadon Gabriel Ta miƙa ma Azeeza, Hannu tasa ta kar6i robar ruwan tare da miƙewa zaune ta cire murfin kallon shi tayi, Still idanuwan shi Na akan fuskarta,

“Ruwa ne ka tashi ka sha” tayi maganar tana nuna mashi robar ruwan, Da ƙyar ya yunƙura Ya tada kanshi saman pillow, Yatsun hannun shi sai kerma suke Yi ya gaza iya ruƙe robar, hakan yasa ta kafa mashi ita saitin bakin shi ya soma kur6ar ruwan Yana bi ta makoshinsa, A tsanake Azeeza ta ke kallon fuskarshi Ya canza sosai, kamar ba Gabriel ɗin da ta sani ba.

Bayan kowannan su Yasha ruwan, Jamimah ta tattara robobin ta maida su ƙarƙashin gado ta killace su,
Har yanzu babu wanda Ya tuna da Angel a cikin su, bacci ne ya fara ɗaukar su Javed, cikin ƙanƙanin lokaci baccin yai awon gaba dasu, ganin sun samu bacci yasa hankalin su Batul ya ƙara kwanciya. Kamar sun samu tv haka suka tasa su agaba suna kallon su yayin da su ke yin bacci,

Farin Cikin su ragagge ne, Abu Biyu ya tsaya masu aransu, Na farko Meyasa ba a dawo da Danish ba, Bayan An riga tafiya dashi? Na biyu me aka yi masu na tsawon watannin nan? basu da amsar tambayoyinsu.

“Allah sarki Danish ɗinmu shi ba’a dawo mana dashi ba, Na yi tsammanin dukan su zamu gansu” Batul ce tayi maganar, Deeja tace”saboda mugun nufin su akan shi sunƙi dawo mana da ɗan uwanmu, Nafi damuwa dashi saboda halin da aka tafi dashi, ”

Da alama ransu ya 6aci sosai na rashin dawo masu da Danish, tsawon Awanni Sunyi zugudum babu mai Magana a cikinsu, Wuraren marece Mubeen Ya farka daga bacci, A matuƙar firgice ya zabura ya miƙe zaune Yana haki Gaba ɗaya idanuwan su akan fuskar shi, Kafin su yi yunƙurin tunkarar shi Ya duro daga saman gadon shi kafar shi kamar zata 6alle A haka ya dinga janta ya nufi Sashen toilet ɗinsu, Da gudu Hannah dasu Yasmin suka bi bayan shi, A cikin toilet suka tarar dashi Ya zuƙunna gaban fanfo Yana kwara amai, Wani irin Farin abu mai yauƙi yauƙi ya ke fitowa daga bakin shi har ta hancin shi ya dinga gangarowa, Wa’iya zubillahi! Zuciyoyin su sun karaya da ganin yadda Mubeen ke kwara aman fargabar su kada ya mutu kamar yadda unaiza ta tafi tabarsu, Tuna wannan yasa hawaye wanke fuskokinsu, A gaban shi suka zuƙunna suna kallon fuskar shi, Sai nishi yake yi Yana jan numfashi a wahalce,

“Mubeen dan Allah ka jure, bamu so wani abu ya same ka, Kaga Muna ƙaunar ka sosai” a hankali ya ɗago da idon shi kan fuskar Parveen da tayi maganar, Girgiza kanshi ya yi yana faman cizon la66an shi ya soma magana “Kada ku tada hankalin ku akaina, lafiyata qalou,” tun daga kan yarda yai maganar zai ƙara tabbatar maka da Babu lafiya a jikin shi, ya faɗi hakan ne kawai don ya kwantar masu hankalin su,

“Wlh baka da lafiya Mubeen, Kalli yadda idanuwan ka suka canza launi, kamar ba mubeen ɗin mu ba”, murmushi ya ƙakalo akan fuskar shi Yayin da ya ke kallon Hanna da ta yi maganar,

“Nifa lafiyata qalou, Nagode da kulawar ku agare ni, nayi missing ɗinku sosai,” Cikin sanyin murya ya furta hakan, A hanzarce Batul ta miƙa hannu ta kunna fanfo ruwa ya soma zubowa, tarba tafin hannayen ta tayi Ruwa ya taru a cikinsu ta wanke mashi fuskar shi tare da zuba mashi ruwan a bakin shi Ya kuskure shi, Bayan ta kammala ta ruƙo hannun shi “Mu koma ɗaki Mubeen” Sai da suka taimaka mashi tukunna Ya iya miƙewa, fitowa su ka yi daga Cikin toilet zuwa ɗaki, A saman gadon Shi Ya kwanta Yana faman sauke ajiyar zuciya, kewaye da gadon shi suka tsaya suna tottafa mashi addu’o’i, hakan ba ƙaramin daɗi ya yi mashi ba, bayan sun samu komai ya lafa suna shirin komawa su zauna Kwatsam Gabriel Ya farka Hananyen shi biyu daddafe da kanshi Ya fasa wata irin gigitacciyar ƙara da ta janyo hankulan su Gare shi, Jikin shi sai kerma yake yi musamman la66ansa, Sambatu ya ke yi na fitar hayyaci, A hankali Su ka soma tafiya suna tunkarar gadon shi, A kewaye da gadon shi suka ja burki suna ambaton sunan shi Muryoyin su a tsorace

“Gabriel! Meke damun ka? Faɗa mana ina ke yi maka ciwo,” Shiru bai tanka masu ba, Hankalin Azeeza duk yafi tashi don tuni tafara sharar ƙwalla, tsananin tausayin shi ne ya kama su, musamman da ya daddafe kanshi sai ya tuna masu da Danish, duk idan ciwon shi ya tashi haka ya ke yi masu ya dinga fasa ƙara,

“Gabriel are u okey? Kan ka yana maka ciwo ne”? Azeeza ce ta ke tambayar shi, Deeja tace “Ku ɗan jira in jaraba yi mashi Karatu kamar yarda Angel ta ta6a Yima Danish wata’ƙil shima yaji sauƙi, ta ƙarasa maganar tare da hawa saman gadon ta matsa kusa dashi ta tallabo kanshi da yatsun hannayenta tare da ɗago dashi, Saitin kunnan shi na dama ta kai bakinta, Kafin a tsanake ta soma Yi mashi karatun qur’ani, surorin da ta haddace akanta, fatiha, iklas, Falak da nasi, da wasu ayoyi irinsu Ayatul kursiyyu, Amanar rasulu da sauransu, A nutse Deeja take karanta mashi su cikin kunnan shi, su Parveen duk suna a tsaye bakin gadon suna kallon shi azeeza tana zaune daga gefen shi, ga dukkan alamu natsuwa ta fara shigar shi, don tun da ta fara Jikin shi ya daina kakarwa, natsuwa ta fara shigar shi, A hankali ta zame Hannayenta daga saman kanshi,

“Da sauƙi jikin naka”? Tayi maganar tana kallon fuskar shi, sai faman lumshe idanuwan shi ya ke yi, daƙyar ya iya buɗe baki Ya amsa mata da cewa “Am ok, Ina fata mun same ku lafiya,” har suna haɗa baki wurin furta mashi “Muna Lafiya” parveen tace “faɗa mana su wanene mu, don ni ban yarda ka dawo dai dai ba,” A hankali ya ke kallon fuskokin su ɗaya bayan ɗaya Ya soma faɗa masu sunayen su

Hannah Hibba Deeja, Parveen, Eve, Yasmin, Batool, Rubina, Aziza, Sarah, Jamima…….” tunkan ya rufe baki yaga suna ta murna ganin ya dawo dai dai, haƙiƙa Yaji daɗin kulawar su gare shi, Sai dai abu ɗaya daya faɗar mashi da gaba rashin mutun ɗaya acikin su, Yarinyar da ya ƙwallafa rai akan son ganinta, don su dasa daga inda su ka tsaya

“Where’s ANGEL”? Ras gabansu Ya faɗi Jin tambayar da ya yi masu, Nan fa suka fara kallon kallon a tsakanin su fuskokinsu ɗauke da matsananciyar damuwa

“Inna lillahi..! Mun manta da Angel! Tun ɗazu da safe ta shiga toilet ta datse, Ba irin bugun da bamuyi ma ƙofar ba amma ta ƙi buɗewa, bamusan me ta ke yi a ciki ba”

Muryar Haris ce ya janyo hankalin su ga kallon shi, Farkawar shi kenan daga bacci Yana ji suna zancen Babu Angel, Jikin shi A raunane Ya yunƙura Ya miƙe zaune, Da sauri Deeja ta nufi gadon shi ta haye sama ta zauna tana kallon shi,

“Haris Sannu Ya jikin Naka? Ina fata ba inda ke yi maka ciwo” murmushi ya sakar mata yayin da ya ke bin ta da kallo, daga gani ba ƙaramar kewar ta yayi ba,

“Deeja lafiyata qalou, Jiki na da sauƙi, Naji ana zancen babu Angel me ya faru da ita? Ko sun zo sun ɗauke ta ne”?

Girgiza mashi kai tayi alamar a’a “Ɗazu da safe ta shiga toilet yin wanka, bamusan meya faru da ita ba, mun jira ta buɗe mana ƙofa amma shiru, mun yi iyakar bakin ƙoƙarin mu wurin ganin mun 6alle ƙofar amma taƙi buɗuwa,’ deeja na kai ƙarshen maganar ta, Batul ta jefa masu tambaya “Haris Ina Danish ɗinmu”! Ɗago wa yai da idon shi tare da kallonta, Mamaki ne ya bayyana akan fuskar shi

“Kamar batul nake gani! Yaushe aka dawo da ke?” Murmushi ta sakar mashi tare da cewa “Tuntuni na dawo, Na yi kewar ku sosai,” Jinjina kan shi ya yi kafin yaci gaba da magana “Bansan inda Danish ya ke ba, saboda ba’a tare mu ke dashi ba, tsawon lokacin nan bamu ta6a Yin tozali da shi ba,” Idon Gabriel akan Batul Sai yanzu da ya dawo hayyacin shi ya gane ta, Yasan cewa ƴar uwar su ce da suke ta nema, kuma itace Yarinyar da ya gani a kwanakin baya saman Third floor Tana gudun ceton Rai! Baisan ya akai ta dawo ba, Sai dai yaji daɗin ganin ta da ranta da lafiyarta.

“Ƴar uwar mu ce Batul, nasan baka santa ba” Azeeza ce tayi mashi magana ganin yana kallonta, Numfasawa ya yi tare da saukowa daga saman gadon kamar zai kife kasa saboda rashin ƙwarin Jikin shi

“Ina zaka je”? Atare su Hibba su ka haɗa baki wurin yi mashi magana

“Inason ganin Angel, ku nuna mini ƙopar toilet ɗin da ta shiga, zan yi ƙoƙari in 6alle ta”

“Kana fama da kanka Gabriel taya zaka iya 6alle ƙofa, tafiyar ma daƙyar ka ke yinta, Pls Ka koma ka zauna bazamu bari ka Ƙara raunata kan ka ba, ” Hannah ce tayi maganar tare da ruƙo hannun shi, ba don ya so ba ya koma ya zauna daga gefen gadon shi.

Hankalinsu Ba ƙaramin tashi yai ba, sun gama murnar dawowar su Haris damuwar rashin Angel ta hana su sakat ga dare har ya gabato amma babu ita, Jamimah sai kuka take yi masu akan Su Je su buɗe ƙofa su ɗauko Mata Genie ɗinta Idan suna son zaman Lafiya, Sun saba atare su ke kwaciya bacci, kwanakin nan ita ke yi masu shimfiɗa a saman floor.

Komawa Cikin sashen toilet ɗin su ka yi, Don su ƙara jaraba ƙarfi ko sun samu ƙofar ta buɗe masu, Gabriel da haris sun so su taimaka masu Wurin buɗe ƙofar sai dai sun hanasu yin hakan saboda babu ƙoshin lafiya a jikin su.

Kukan Jamimah Ya karaɗe Cikin ɗakin su, Hatta Javed da Naufal sai da su ka farka daga bacci saboda sautin kukanta daya cika kunnuwan su, Taƙi samun wuri ta zauna, Ga uban bargon data zumbula a jikinta, Angel ta rufe mata uniform a cikin toilet shiyasa take ta yin zarya da bargo, Kanta har ya fara sara mata, Gabriel ne ya miƙa mata hannu tare da ambaton sunanta, Kamar jira ta ke yi da gudu ta nufi gadon shi ya ɗauketa saman jikin shi yana lallashinta, cikin shesshesƙar kuka take ce mashi “Dan Allah kaje ka ɗauko mini Genie ɗita, tun ɗazu tana a cikin toilet, ƙofa ta rufe da ita sunƙi su taimaka mata, Uniform ɗina ma suna a ciki itace ta yi mini wanka tace zata Wanke mani su, in sun bushe sai in saka su a jiki na….” duk ta cika shi da surutun ta, shi kanshi hankalin shi ba a kwance ya ke ba, Kowa da abunda yake saƙawa a ranshi dangane da rashin Angel gani su ke kamar fa an ɗauke ta shiyasa taƙi buɗe ƙofar, saboda babu alamun mutun acikin toilet ɗin, Ko motsi wannan baka Ji.

Ina Angel ta shiga meya faru da ita?

abunda ya faru Lokacin da Angel ta zuƙunna a gaban tukunyar fulawar nan, Hankalinta ba’a kwance ya ke ba, tun da ta fahimci Furen Danish, Azalzalar da zuciyarta ke yi mata akan taje ta nemo shi taga a wani hali ya ke ciki shi yaja hankalinta, miƙewa tayi a fujajen ta nufi glass window ɗin nan ta sanya Hannu ta sauke glass ɗin ta dire shi ƙasa Jikin bango, duk da irin tsoron da take ji hakan baisa ta fasa ƙudirinta ba, Bayan ta janyo bokiti ta haye sama sai da ta fara Ambaton Bismillahi da kyakkyawar niyya tare da wasu addu’o’in neman tsari masu ƙarfi Kafin ta daddage ta haura tagar ta duro ta bayanta, tsananin tsoro ne ya kamata da firgici Amma a haka ta daure ta cije saboda idanuwan ta a makance suke bata ji bata gani burinta Kawai ta gano inda Danish ɗinta Ya ke, Cike da ƙwarin gwiwa ta miƙi doguwar hanyar nan wadda zata sada ta da ground floor ɗin Gidan kurkukun, Tana tafiya tana ambaton sunan Allah, Duk addu’ar da tazo mata a cikin bakin ta karanta ta take yi, hada ɗan gudu gudun ta wurin yin tafiyar, lokacin da ta kawo ƙarshen hanyar ta faɗo ta cikin babban Filin dake a kewaye da waɗannan Dogayen benayen, Ras taji gabanta ya faɗi tunawa da abunda ya faru da ita a rana ta farko da ta fara zuwa wurin, ba zata ta6a manta irin baƙar wahalar da tasha ba, A tsananin tsoroce take ƙare ma benayen kallo don ta ga ko zasu motsa kamar yarda su ka yi mata aranar farko, ganin sunƙi Motsawa yasa ta soma tafiya Cikin sanɗa tana tunkarar su, shiru baka jin hayaniyar komai, ita kaɗai kwallin ƙwal kamar ba mutane A gidan Kurkukun.

Har ta kai bakin benan ta soma Jin sautin Wata shaƙaƙƙiyar murya tana ambaton sunanta, A gigice ta juya tana kallon bayanta don taga wanene Sai dai bata ga komai ba, Sautin dariya mai kama da haniniyar Doki ta dinga Ji a cikin kunnuwan ta, Tuni zufa ta wanke fuskarta sharkaf, Can kuma ta dinga jin kukan jarirai Enyaaa enyeeh, Da sauri ta toshe kunnuwan ta da tafin hannuwan ta, bugun zuciyar ta na ci gaba da hauhawa, Jikin ta ya hau rawa, Saboda taurin kai irin nata a haka ta soma hawa benen la66anta na kerma wurin ambaton sunan Allah, ba zato ba tsammani taji Matattakalar Benan ta soma Motsawa, hakan ya sa ta daddage ta watsa da gudu tana haura matattakalar Yayin da benan ke mayar da ita baya har tuntu6e take yi ta kife Ƙasa, Staircases ɗin suka dinga janyeta suna mayar da ita baya kamar zasu saukar da ita daga saman gadon, Cikin zafin nama ta ɗago da kanta tare da miƙewa ta dinga gudu zufa na bin jikinta har sai da Allah ya bata nasarar kaiwa ga Second Floor, Ta ƙarfi ta buga tsalle ta haye sama tana faman Haki, sumar kanta duk ta rufe fuskarta, Ƴan hanjin Cikinta sai kaɗawa su ke Yi, A hankali ta yunƙura ta miƙe tsaye tare da juyawa tana kallon benan, Wani abun mamaki Gaba ɗaya ya daina motsawa sauke ajiyar zuciya ta yi, Angel da kasada taci gaba da tafiya Saman hawa na biyu, Sai faman baza ido ta ke yi tana ƙarewa ginin kallo, tsarin shi yadda kasan Ƴan hanjin Cikin mutun saboda kwana kwanar da ke gare shi, A dai dai Bakin wani corridor taci burki tana leƙa Ciki, Ɗakuna ta hango A jere Kusan guda Huɗu biyu suna fuskantar biyu, Ƙofofin su a rufe su ke sai dai bata da tabbacin Ko an sanya masu Kuba.

“Ya Allah ka tsare ni daga sharrin duk wani abun cutarwa, Ya Allah ka haɗa ni da abunda nazo nemo Cikin sauƙi ba tare da nasha wahala ba,” acikin zuciyar ta take ambaton hakan, ɗaga kafarta tayi tare da nufar Ƙofofin, Hannu ta kai ta ɗan ta6a Jikin ƙofar farko ba zato ba tsammani taji ƙofar tana lilo alamar a buɗe ta ke, Sai da ta fara karanta addu’ar neman tsari ba tare da Jin tsoro ba, ta faɗa Ɗaya daga Cikin ƙofofin, wurga ƙafar ta ke da wuya wani uban wari ya daki hancin ta, Idanuwan ta a zazzare ta ke ƙare ma Ɗakin Kallo, tamkar Igiyar Shanya ce kewaye A cikin shi ta kowane 6angare, babban abunda yayi mugun ɗaga mata hankali Gangar Jikin Matasan Ƴan mata ta gani da maza Wanda basu haura shekarun su Batul ba, zindir babu kaya a jikin su, An ɗaure wuyan su sagale Jikin Igiyoyin nan kamar kayan wanki da alama Sun gama amfani dasu, wasu An cire nonuwan su,wasu kuma an cire gaban su,Wasu Idanuwan su aka kwalkwale Yayin da wasu kayan Cikin su aka wawake, Innalillahi wa’inna ilaihirraji’un!!

Wata irin narkakkiyar zufa ce ta wanke ko’ina na jikinta da ke ta yin kerma kamar wadda ake kada ma mazari, duk ta bi ta furgice ganin komai ta ke yi tamkar a mafarki, Hannayen ta daddafe da kanta cikin fitar hayyaci ta fito daga Cikin ɗakin, Maimakon tayi reverse ta koma Inda ta fito sai ta ƙara gaba saboda gushewar da hankalin ta yayi, A gigice Ta fito daga ɗakin Wani irin jiri take gani a cikin idanuwan ta, Hannunta dafe da ƙirjinta Zuciyar ta sai tashi take yi ga wani irin zazza6i da ya lullu6eta.

A bakin Ƙofar ɗaki na biyu ta faɗa tana faman haki, Karaf idanuwan ta suka sauka Akan Giants da ke gudanar da aikin su na Theatre, gadaje ne sunfi talatin Cikin Ɗakin mai faɗin gaske, kowani gado Yana ɗauke da mutun kwance saman shi, Sun fafe cikin su suna ɗibar kayan cikin nasu tare da ɗaura su saman table ɗin da ke a gefen su, A matuƙar razane ta juya tana neman hanyar da zata bi ta Fitar da ita daga Cikin Corridor ɗin, Allah Yaso basu lura da ita ba babu wanda Ya ganta don gaba daya hankulan su na akan aikin da suke kuma basu zaton wata matsala , Watsawa ta yi da gudu Ita kanta batasan inda take tunkara ba Sunan Allah kaɗai ta ke iya ambato a cikin bakinta, adaidai saitin wata ƙopa ta soma jin Wata kakkausar murya tana magana da wani irin gur6ataccen yare mara daɗin ji, A hautsine takai idonta Ƙofar Dogon labule ne launin Ja ya rufe ta, Yatsun hannunta na kerma ta ɗan yaye labulan.

Babban ɗaki ne mai girman gaske kamar palour, komai Na cikin shi Red & black Colour ne, bangon ɗakin Zanunnukan kan ƙwarangwal ne dana kunama, da na wasu halittu masu dogon harshe Da zaƙo zaƙon akaifu irin na shaiɗanu, Zanen su ne ta ko’ina gwanin ban tsoro, Mutane ta gani a jere sunkai su Talatin Kowannan su na sanye Cikin Jajayen dogayen riguna masu huluna, hannuwan su ruƙe da ƙoƙuna masu ɗauke da jini, daga tsakiyar su wasu tiƙa tiƙan mutane ne kusan su Shidda, Yadda kasan Irin malaman Majami’u na ƙasar India, Tumbur babu Kaya ajikin su, Sae dai wani ƙaramin Jan ƙyalle da su ka ɗaure ƙugunan su dashi, ga wani uban tumbi da suka tara, Jikin su bulbul ansha Jini An ƙoshi, Jan fentin da ke saman fuskokin su Ya rufe ainihin Suffar su sun koma kamar dodonni, Sun kewaye wani Dodon tsafi dake a zaune saman armchair, Wata irin halitta mai matuk’ar muni miyau sai zalalowa yake yi daga bakin shi, Zir Jikin shi babu kaya sai uwar yanar da ta nannaɗe gangar Jikin shi tayi mashi tamkar sutura.

A kowace kusurwa ta cikin ɗakin jajayen ƙwaryoyi ne a jere an rufe su da faifai, Ga wasu ƙananun Yara da basu haura 7 years ba mata zuƙunne saman gwiwowin su babu kaya a jikin su, gabansu ca6a ca6a da jini, daga gani amfani aka yi dasu.

Wani ikon Allah duk tashin hankalin da idanuwanta su ka yi tozali dashi baisa ta kurma ihu ba saida taga waɗannan yaran ƙananu tukunna sautin muryar ta ya dawo har ta ƙware Baki zata Kurma Ihu ba zato ba tsammani taji saukar hannun mutun saman bakinta, sosai Ya toshe mata baki! Batasan wanene ba hakan yasa ta zazzare idanuwan ta waɗanda su ka kaɗa su ka yi jawur dasu, tsoro da firgici ne acikin ƙwayar idonta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button