Sponsored Links
Gidan Aunty Book 1Hausa Novels

Gidan Aunty Book 1 Page 70

Sponsored Links

BOOK 1

Page 70

Lallashinta yayi har tayi shiru bayan ya gama dressing din kwalbar da ya shigar mata kafa, wayansa ya dauka da niyar kiran Ammeey tayi saurin dakatar dashi ,bata san lokacin da bakinta ya furta me zaka mata, d’an kallanta yayi shima na ‘yan second kafun ya furta yaja hancinta kad’an “ wani kunun ayar zansa a kawo mana”, ita kanta bata san lokacin da take wani abun ba “ No kabari gobe zanyi maka wani kajiii babyn? Ynxu bari na fara temaka maka kayi wanka sai kaji abinci ,okay? Kanshi ya d’aga mata alamar toh kafun ya kuma cewa “ but bari na saka a kawo mana wani kunun aya , Kema ai naga kina san kunun Ammeey” no kaji ka fara yin wanka already na hada maka another juice please ni yunwa mukeji nida babyn ka fa “,cikin ya ta’ba kafun ya saki wani ajiyar zuciya “ toh ayiwa dady hakuri yanxu zakuci abinci” yana kai karshen maganar sa yashi ya nufi kofar da zata sadashi da ban dakinsu, ajiyar zuciya Tahee ta sauke cikin zuciyar ta kuwa cewa take “ Allah ya tsare na karacin abincin shaid’aniyar iblisarcan, Wanda naci a baya ma a rashin sani ne , muguwa me kama da kwarkwata, ta Allah ba taki ba “, gudun karya sakko ya tarar da abun kunun yasa tayi saurin fita daga d’akin, Daidai inda kunun ayar yake ta nufa , a bun mamaki amaimakon ta samu kunun ayar sai wani ‘bakin ruwa da ta samu, addua ta soma yi cikin xuciyarta, kafun taje ta dakko Mopper ma gabaki d’aya ruwan kunun ayar ya kuma komawa ba’ki , karfin adduarta ta soma tun tana yi a zuci haka ta cigaba dayii ita kanta bazatace ga adduar da take karantawa ba, da Bismillah ta fara goge ba’kin ruwan harta kammala, tare da kunna karatun alkurani yanda bazai damesu ba , tana cikin Kimtsa falon ya sakko ‘kasa shima cikin shigar kayan bacci blue colour masu Taushin gaske , serving Dinsu abincin tayi atare suke feeding din junansu har suka kammala , a kan 3sitter ya zauna ita kuma ta kwanta akan cinyarsa tana wasa da sajanshi “ babyn” ta kira sunansa a hankali kamar me rad’a , kallanta yayi alamar na’am duk da ne bud’e baki yayi magana ba “ wacece Ammey a wajan ka “ wani lallausan murmushi ne ya bayyana akan fuskarsa da ya kara kawata kyawun fuskarsa har hakan yaso bata mamaki, mi’kar da ita yayi zaune tare da kamo hannunta Suka nufi d’akinsa ta lipter , zaunar da ita yayi akan sofa kafun ya bar d’akin , mintuna kad’an kuma ya dawo hannunsa d’auke da wani karamin white box’s,budewa yayi take a wajan wasu hotunan Suka bayyana duk da darewarsu amma babu abunda ya samesu,” sorry laifina ne da har yanxu baki gama sanin Tarihin mijinki ba,nasan kinsan full name dina , amma still zan kara fad’a TAHNOON ZAYED AL_NAHYAN, mumu 4 ummey ta haifa Akheee moha shine babba Allah ya masa rasuwa ,sai ukhtiii next tomorrow itama zaki ganta , sai ni sai kuma auta zoya , tun ina ‘karami na nake ‘bangaran Ammey sabida yanda take nunamun soyayya da wata shakuwa ta musamman komai ta samu ni zata fara bawa kafin ta bawa kowa na gidan har hakan ya kara sha’kuwa a tsakaninmu, soyayyar da take munne yasa sau da dama mutane sai su dunga d’aukar cewa ita tahaifeni sabida wani irin shakuwa da yake tsakanina da ita, part d’in ammeey na dawo cikin abinci, komai nawa a part din Ammeey nakeyinsa, hatta kwana a part d’in ammeey nake yi har lokacin tafiyata waje karatu, acan turkey na kammala karatun likitancina, har na kammala at time moment…” sai kuma yayi shiru yana runtsu idanuwansa , itama kallansa tayi sabida wani irin tausayinsa da ya mamayeta, tabbas ba karamin cutar dashi Ammeey tayi ba , hannunta d’aya ya dam’ke cikin nasa ,” At That moment, mukayi accident da Akhi , and at the same time motar da muke ciki ta kama da wuta , duk yanda nayi kokarin cecensa na kasa , ina jin zafin hakan every single day idan na tuna na kasa cetan best brother , I can’t save him, na kasa cetansa , agaban idona wuta ta ‘konashi” ya karasa zancansa kamar nunfashinsa zai d’auke , rungumeshi Tahee tayi tana fashewa da wani irin kukan tausayinsa , tabbas idan Ammeey zata iya ‘kona mutum da ransa toh tabbas zata iya yin kome tace ,a zuciyar ta kuwa fad’i take “Ammey kin cuci rayuwar mu, kin rusa mana farincikin , tana zan iya sanar Dashi kece kika kashe masa d’an uwa, kika rabasa da mahaifiyarsa”, shafa bayanta yake a hankali cikin rad’a rad’a ya furta “ banasan kukan nan naki idan ba so kike Nima nayi ba , duminki kawai nakeso,zuciyata ba dad’i inasan farin cikin matata “, ya karasa kalmar matata Tahee ta had’e bakinsu waje d’aya, duk yanda taso tsayar da hawayen fuskarta ta kasa , wani irin deep French kiss take basa, gabaki d’aya ta mantar dashi abunda ke damunsa, light din dakin king ya kashe kafun yaja bargo ya lullu’besu sabida sanyin da yake busosu…..

After 2 hours kwance take a jikinsa gabaki d’aya taki yarda su hada ido, “ a ina kika samo wannan karatun, I like it please kunyarnan ta tafi haka tana cutana fa “bugun kirjinsa tayi a hankali amma dukda haka saida yace ouuuush, yana kara rungumeta a jikinsa , lumshe idanuwanta tayi kamar me jin bacci Amma sam ba baccin take ba , tunanin yadda zata tona wa Ammey asiri kawai take a cikin ranta, tana cikin tunanin bacci ya d’auketa, forehead d’inta ya sumbata kafun ya ‘kara rungumeta a jikinsa, abubuwanda Suka faru tsawan shekarune suka dawo yawo akansa, babu inda ya fi tsaya masa arai kamar mutuwar d’an uwansa, ganin yanda jijiyoyinkansa suke ‘ko’karin ta shine yasa ya soma adduar tsari cikin zuciyarsa , ya d’ad’d’e yana addua kafun yayi nafila akan rokan Allah ya sassauta masa abun da yake ransa kafun shima ya kwanta yana kara rungumota a jikinsa.

********
✨✨✨✨✨

WASHE GARI king yana tafiya masallaci itama Tahee ta Tashi tayi sallarta, bacci take ji sosai shiyasa ta koma zata kwanta, a side d’in hagun da king ya fi kwanciya a gefen ta kwanta , hannunta d’aya ta zura ta karka shin pillow sa yanda zataji dad’in kwanciya sai taji abu kamar yana tokararta, gyara kwanciyar ta tayi yanda zata fi jin dad’in baccin nata amma still tanaji kamar abu na sukarta, ni’kewa zaune tahee tayi tare da yunkurin canza pillows din, hannunta ne ya sauka akan tsakiyar pillow d’in hannunta , da Sauri ta janye hannunta tana karantar addua, wajan ta kara ta’bawa amma still tanajin kamar akwai abu a wajan, cikin rashin tsoro ta kara kai hannunta wajan still har yanxu tana jin abinda takeji, rigar pillow d’in ta yi saurin zazzagewa kafun ta kara taba wajan, still dai abun na Wajan, cikin Sauri ta dauki pillow d’in ta nufi d’akin ta dashi, reza ta fara nema cikin sa’a kuwa ta samota, bakin pillown ta farka duka kafun ta zazzage abinda yake ciki, ‘karamar kwabace ba’ka ta bayyana a cikin abin cushion d’in, bakinta d’auke da Bismillah ta bud’e kwalbar, wani haya’kine ya fito daga cikin kwalbar ba’ki’kirin da shi ,Addua Tahee ta fara da ‘karfi cikin ‘kan’kanin lokacin kuwa haya’kin ya bace gabaki d’aya . A Daidai lokacin da wannan kwalbar ta fad’o a daidai lokacin kan king yayi mugun sara masa , ga wani jiri jiri da ya soma d’aukarsa, part d’in ammey zaishi amma ya fasa ya nufi nashi part d’in, yana shiga cikin falon sa ya fad’i kasaaaaa..

#MANAGE
GIDAN AUNTY
07041879581
MSS LEE 💖

MAI BUKATAR KARANTA GIDAN AUNTY HAR KARSHE YA TUNTUBENI TA NUMBER TA .

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button