Sponsored Links
Amatulmaleek Hausa NovelHausa Novels

Amatulmaleek 18

Sponsored Links

Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

18
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs๐Ÿ’ฏ๐Ÿ”ฅ๐Ÿ‘
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku๐Ÿ’ฏ๐Ÿ‘*

MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI’IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER

08142800199
07068558096

************
Shiru kawai Faisal turaki yayi Dan kuwa shi a tsarinsa shine yake karantar abinda yakeda raayi akansa da kansa Baya daukan bayani ko yabawar Wani Dan haka duka bayananta Babu Wanda ya damesa hakama Babu Wanda zai qara masa Sonta ko Rage masa Dan haka shiru kawai yayi harya gama ya fita ya wuce tinani da yawa ne akansa.

AmatulMaleek da bama zatace Ta Kalli fuskarsaba bare riqe kamanninsa tini ta manta da Wani baqon da Akai ta kama alamuran gabanta.

Shikuwa kwana biyu ya sake zuwa gidan dayake Shima yasan maamah wannan Karan da ita yayi fira sosai har Amatun ma Saida suka gaisa ya Dan jata fira gameda karatunta sbd law take karanta itama.

Yanda ya ringa fahimtar da ita wasu abubuwan gameda course din ya sata Dan sakin jiki tana fahimtarsa Wanda har dare Yana gidan Saida yayi dinner tareda jamaar gidan kafin ya tafi.

Dayake me saukin Kaine shi da sanyin hali kaman Amatu tini suka fara fahimtar juna Yana Bude mata sani akan karatunta da Daman tana Neman me zaunawa da ita suyi karatun yanda ya kamata sbd a school Batada qawaye.

Karatuta dayazo Daya da nata shine ya Basu Daman fara kusanci da juna da yawan waya batareda tasan Menene abinda yake zuciyarsa akanta ba,

Maamah data fara fahimtar sosai son Amatun Faisal turakin keyi sai Hakan ya Bata nutsuwa sbd Bata taba sanin Husnah Faisal dinne a ranta ba sbdz Bata taba fada mata ba su mum Aisha ne kawai suka sani da sauran dangin Abeeda.

Dan haka ita idan har Amatun zata auri Faisal turaki hankalinta zai kwanta da yanzu yake a Dan tashe da lura da Naufal ma Amatu yakeso.

Hutunsa Amatu ya qare Dan haka su Husnah Basu dawoba a satin sai kusan bayan sati biyu sbd basa qasar suna Greece tareda Dad dinsu gurin Madame Abeeda.

Amatu tayi mamakin ganin Faisal turaki a university dinsu Ashe Nan ya dawo da aiki sosai tayi farin cikin Hakan Dan kuwa ba qaramin taimaka mata Hakan zeyiba.

Shi kansa yayi mamakin farin cikinta shiyasa ma Bai fada mata ba tin Farko,
Sabuwar shaquwa suka sake samu ta Hakan Dan wasu lokutan shine yake dawo da ita gida.

A satin dasu Husnah suka zasu dawo a satin ya sanar da AmatulMaleek son da yake mata tareda Neman damanta na Neman aurenta idan sun sake fahimtar juna.

Da farko mamakinsa tayi sbd Kai tsayensa daya sata Jin nauyinsa tinda baa taba furta mata ana Sonta ba bayan Haydar da kullum yake fada mata yana sonsa sosai takuma San shi nasa wasa da Kuma kaunar Dake tsakaninsu ne.

Kunya ta hanata amsa masa Amma Shima yaga alamar ya samu karbuwan Dan haka sai hankalinsa ya kwanta sosai ya tashi daga matsayin Dan uwa dayake ya koma na masoyi Kuma mijinta inshallah.

Bata fadawa maamah ba saida suka kwana biyu maamah taga yanayinsa ya sauya daga yanda yake gaidata da sauran abubuwan.

Itama mum Aisha data fahimci a sosai Faisal din ya mutu akan Amatu cikin qanqanin lokaci tini tafara Jin nutsuwa tareda fatan ASH na dawowa zata fada masa ayi auren ba Bata lokaci Amatu tabar gidan.

Mum Aisha nata gaggawar kusan baifi na maamah ba data fita son Amatu tayi aure ta tafiyarta batareda matsalar komaiba itama ASH din take Jira ta sanar masa da kanta.

*****Su Husnah sun dawo sun tarar da wannan mummunan labarin Daya kusan tayarda ciwon Husnah na qwaqwalwa Dan kuwa shock Mai tsananin gaske ta shiga Jin Faisal da AmatulMaleek suna tare har ana maganar afadawa Dad dinta maganar aurensu.

Haydar ma kusan shock din ya shiga sbd baitaba kawo Amatu ma zatai saurayi a yanzu kafin shi ba hakama da Wanda ‘yar uwarsa ke tsakanin so tin Bata gama zama cikakkiyar budurwa bama.

Kai tsaye Haydar ya soke zancen akan Bai yarda ba tareda tada rigima wadda tasa maamah da kowa ma shiga mamaki me girman gaske Dan har lokacin dauka sukeyi wasa yakeyi kamar dai yanda suke dauka a bayan wasa yakeyi idan Yana cewa Yana son Amatun.

Ita kanta Amatun kasa yarda tayi har lokacin da gaske yake Dan haka ta sharesa sai dai Kuma ga mamakinsu da tashin hankalinsu da gaske yakeyi Sonta yakeyi Kuma wlh bazai yarda ta auri kowa ba.

Naufal ma da sai alokacin yake samun zancen tashi hankalinsa yayi Dan bazai yarda Shima ya gama hadiye mata yawu Wani yazo ya aureta yabarsu da raba ido Amma dai Shima hauka yake daukan zancen Haydar.

Mum Aisha dataga wannan sabuwar masifar gargadin Naufal tayi akan karya yarda ya fidda nasa zancen akan Amatu Koda wasa.

Faisal ma mamaki da kishi me tsananin gaske ne ya fara cinsa sbd dai anbuga an raya Haydar da gaske yake ya daga hankalin jamaar gidan akan Amatu bazatai aureba.

Tashin hankalin Daya Saka mutane ya Hana a fahimci halinda Husnah take ciki itama ga ASH Baya Nan Saida kusan komai ya lalace yayi girma ya sani cikeda mamaki me girman gaske ya dawo Dan yakasa fahimtar Haydar din duka duka nawa yake yanzu ne yake jamiaa shekarar farko zaice Babu Wanda zai auri Yarinyar sai shi.

AmatulMaleek hankalinta tashi yayi a lokaci Daya kuma tareda sanyin jiki sbd har cikin zuciyarta batason ganin Haydar a halinda ya shiga na wannan tashin hankalin Dan haka take Neman shiga Wani hali na matsanancin damuwa,
Hakama maamah damuwa ta shiga sbd su duk sun dauka acan Baya wasa yekeyi da tini a andakatar da abin yanzu gashi komai na Neman zama babba.

Ranar da ASH ya dawo qasar Babu Wanda yayi magana dashi sai washe gari Bai nema kowa ba sai maamah wadda suka jima suna magana ya Sakata tayi magana da AmatulMaleek idan tanason Faisal din.

Daga maamah har Amatu Babu Wanda yake farin ciki da halinda Haydar ya Saka kansa Dan haka kamar ta fasa auren haka Amatun ta ringa ji to Amma zuciyarta ba qaramin so takewa Faisal ba shikuma hakama Shima acan nasa familyn anata rikicin nasu aminta da aurensa da Amatun ba da Husnah sukeso sai alokacin ASH TALBA yasan wannan sabuwar damuwar.

Rasa abin yi yayi sbd Shima bazai iya aurawa Husnah namijin da Baya Sonta ba bazata taba Jin dadi ba Dan haka ya Yanke hukuncin bawa iyayen Faisal turaki din dama su Turo zai aikawa dangin mahaifin AmatulMaleek din ko mutum biyu suzo.

*****Wannan hukuncin ya gigita kowa Banda mum Aisha datake Jin hankalinta na sake tashi matiqar Amatu Bata bar gidan ba batasan waye Kuma zai sake cewa Yana sontaba tinda kowa ya mutu akanta ana Neman shiga yaqi duk akanta sbd ko acan familyn Faisal din anata samun tashin hankali da matsala wasu basason ya aureta wasu Kuma Husnah sukeso hakama wasu na son ya hakura yabarwa Haydar Amma duk yaqi Dan haka aketa tashin hankali da Neman rarrabewan Kai.

Anan gidan ASH ma matsalarce Tako Ina Dan kuwa Haydar ya sake haukace musu,
Husnah kuwa Saida ta tabbatarda ta cirewa maamah so da shaawan auren Faisal din da AmatulMaleek dan haka takejin hankalinta na rabuwa biyu tsakanin Amatun da Husnah gameda auren.

Babban tashin hankalin da suka wayi gari dashi shine rantsuwar mahaifiyar Faisal akan Bata yarda ya auri Amatu ba idan ba Husnah ba.

Wanna shine karshen tashin hankalin da kowa ya shiga Daman Kuma dad dinsa ya rasu ummansa ce kawai.

Fasa auren shine babban bacin Rai da ASH ya samu a Dan lokacin Dan haka Shima ya Hana musu auren tasa ‘yar yakuma kashe maganar yabar qasar.

Faisal, AmatulMaleek, Husnah, maamah, Mum Aysha harma da Haydar Babu Wanda wannan hukuncin ba yiwa mummunan girgiza ba.

Lamarin yazo ne ya tafi tareda Bata kusan komai da wasu alaqar gidan Dan kuwa kusan kowa a cikin damuwa yake yanzu musamman Amatu da Faisal
Hakama Husnah da datasan tinda Dad dinta yace aa to tabbas bazaiyiba hakama itama idan ba Faisal dinba wlh bazata aura kowa ba.

Haydar kuwa Dad dinsa ya Yanke hukuncin ze bar gidan ya fasa barinsa qasar yayi karatu waje zai turasa bazai taba dawowaba sai ya kammala.

Wannan hukuncin ya sake jefe kowa cikin sanyin jiki da damuwa ga Faisal ya kasa rabuwa da AmatulMaleek Dan kuwa Shima bayajin zai iya auren a yanzu idan ba Amatun ba.

Haydar fadan nasa tashin hankalin bama zai yiyuba sbd Bai taba tinanin tafiya wata qasar karatu ba Kuma babu ranar dawowa a kusa Dan haka ya rikice ya ringa rokon Dad dinsa Amma Sam Babu ko sassauci daga Dad din.

*****
AmatulMaleek gaba Daya tayi sanyi sosai Takoma rayuwarta ta Baya ta kadaicewa da kame Kai sosai Sam idan ba makaranta zata ba bata ma fitowa sai gashi sunyi Hutu ma Bata zuwa koina
Faisal dinma ganin yanda Husnah take tsananin son nasa da gaske saita danne nata son ta hakura sbd a kwanakin ma Husnah din jinya takeyi sosai Bata Jin dadi rashin mahaifiyarta ya dawo mata sabo Dan kuwa da mahaifiyarsu na Nan zasu samu sauki da mafitar wannan hukuncin na Dad ga Haydar shima acikin mummunan hali bayason tafiya koina musamman jin bazai taba dawowa ba yanzu.

Ita kanta maamah Jin tayi komai ya fita kanta kaman ta kwashe nata ‘yayan takeji su koma inda suka fito sbd wannan fitinar ba lallai a Denataba idan ba tafiyar sukaiba,
Ba lallai Amatu ta samu Wani mijin a qanqanin lokacin Nan ba Tayi aure hakama ga Naufal bangare daya dasuke tsoron abinda zaije ya dawo.

***Ana saura kwana biyu Haydar ya tafi a ranar jikin Husnah din ya tsananta sosai Dan haka maamah a gurinta ta wuni hakama dole zata kwana tareda ita shiyasa yau Amatu tana sallan ishai taje ta sake dubota ta dawo a natse ta koma dakinsu.

Ko data shiga dakin sake gyarasa tayi kafin ta kashe wuta ta tube ta shiga toilet wanka.

Bata jima ba Dan Koda Rana tayi Wani wankan yanzu dinma tayi ne sbd batajin karfin jikinta itama zazzabi ne yake damunta.

Bayan fitowarta kofar dakin tafara zuwa ta Saka key ta rufe tareda shafa Mai sama sama ta Dan fesa spray kadan a armpit nata ta dauko duguwar Rigar bacci me Dan tsayi da kauri ta Saka tareda socks me laushi.

Wayarta Dake caji ta kalla batareda ta daukoba ta hau gado ahankali tareda rufe Rabin jikinta da abin rufa ta rife idanuwanta ahankali tareda karanto addua tana sake rufe ido Jin kanta dayake mata nauyi.
Babu jimawa bacci ya dauketa me nauyi sbd ciwon kan datake fama dashi.

Karfe 2 da mintina na dare taji Wani irin sanyi na ratsa wuyanta zuwa cikin rigarta,
Motsawa tayi ahankali tareda kokarin juyawa Amma Hakan Bai samuba sakamakon Jin mutum a bayanta kwance matse da ita sosai.

Wani irin mummunan faduwa gabanta yayi baccin idanuwanta na sakinta take ta yunkura da karfin gaske zata Tashi sedai Hakan Bai samuba sakamakon mirginowa da yayi ya danneta gabaki dayanta tareda Sakar mata nauyinsa.
#MAMUH#

 

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at๐Ÿ‘‡
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button