Sponsored Links
Dabi'ar Zuciya Hausa NovelHausa Novels

Dabi’ar Zuciya 38

Sponsored Links

38

Dauke da babban faranti mutumin dake sanye da uniform irin na ma’aikatan cikin kamfanin ya shigo,ya qaraso cikin girmamawa ya ajjiye zazzafan coffe din,ya juya ya fita dai dai sanda saraki ya fara kai cup din coffee din bakinsa,yana sake kiran waya da wayar landline din dake gabansa

“What are you waiting for?…… file na office dinsa kawai nake jira fa,u r wasting my time” ya fada cikin fushi,dan jim yayi,da alama yana sauraren abinda ake fada daga daya bangaren ne,ba tare da yace komai ba ya sauke wayar

“Kai da waye?” Ya tsinci muryar amiru dake shigowa office din kansa tsaye,wanda kusan shi kadai keda wannan ikon,sai ya waiwayo yana riqe da cup din yana dubansa

“Fawwaz…..already na gaya masa ya tattara dukkan wasu bayanai dake offices din dakw qarqashinsa na qarshen shekara,kusan na karbi ko wasu bayanai amma nashi ya gagara zuwa?”.

Baice komai ba,sai daya ajjiye file din daya shigo dashi kan sauran dake wajen,yaja kujera ya zauna sannan yace

“Not surprisingly” cira kai samir yayi ya dubeshi,yana nazarin fuskar amirun na wasu sakanni,shima amirun shi yake kalla,kafin daga bisani ya dage masa gira,sannan ya tashi ya zauna sosai yana fadin

“Aje wannan a gefe……ya kukayi da daddy?” Kujerarsa ya koma ya zauna,ya hade hannayensa duka waye daya,sannan ya fara gayama amirun yadda ake ciki.

Shuru ne ya biyo baya na wasu sakanni kafin amiru yace

“Yanzu….what next?…..tunda kaqi yarda da shawarar mayar da ita?” Bayansa ya mayar ya jingina da fuskar kujerar

“Ko wajen hajiya qarama zata koma?” Amiru ya sake fada kafin yaji amsar samir.

Kansa ya kada

“A nan din dai zata zauna tare damu,duk da sabanin ra’ayi da muke yawan samu…..kusan nafi kowa karanta da sanin waye daddy,so i wil do my best naga nayi duk abinda nasan cewa zai hanashi sauya komai” kai amir ya kada,shi kansa tsayin shekaru har yau ya kasa sabawa da wasu abubuwan dake gudana a tsakanin samir din da daddy,hajiya qarama tasha gaya masa cewa, professor rashid nason samir fiye da duk wata halitta dake doron qasa,saidai kuma ayyukansa sun qaryata hakan,wannan abun ya sanya shakku a zuciyar shi kansa amir kan sahihancin maganar.

Neman izini da kuma shigowar fawwaz ita taja hankulansu dukka su biyun,babu wanda ya cewa komai a cikinsu,ya qarasa gaban table din saraki ya sakar maaa file din yana daga tsaye,sannan ya juya yana gyara suit dinsa zai fice,amiru yayi motsi da niyyar maida martani,samir ya masa nuni da hannu kan kada ya tanka

“Why….me yasa kake qyale gayen nan ne saraki?,wayeshi?,meye taqamarsa?,mommy jidda ko kuwa?” Wani qaramin murmushi samir ya saki yadan daki kafadar amiru

“Cool down…..” Ya fada alamun ranshi bai baci ba,hakanan hankalinsa a kwance yake

“Ba dole bane saiya nuna akwai sanayya tsakaninmu,aikine ya kawoshi shi kuma ya hadamu,hakanan shi xaiyi,abu daya na sani,bai isa ya taka koya karyamin dokar aikina ba….yafi kowa sanin me zai biyo baya idan hakan ta faru…..so please karka damu da wannan” ya fada yana tura masa coffee gabansa

“Mu tattauna abinda ya kawoka”

*********Kyawawan fararen dawakai ne guda uku a daure,sai wani mai ratsin fari da baqi,sunci sun qoshi sai harbin iska kawai da sukeyi,duk wanda ya kallesu saiya kuma kallonsu,saboda cika qoshi da alamun cikikakkiyar lafiya da tsafta dake tattare dasu.

A hankali samir ke zagayawa cikinsu shi da wanda ya ware musamman saboda kula dasu,ya gama duba lafiyarsu,suka danyi magana da mutumin da yake kira da wakili,sannan ya soma takawa yana barin sashen da dawakan suke,yana zaro wayarsa da aljihun wandonshi,karo na farko tun wayewar garin yau,wanda gaba daya wunin yau ya yishi a gida ne.

Number jawahir ya nema,bugu daya ta daga tana gaidashi

“Ki kawomin abun sha bamai sanyi sosai ba,ina ta wajen barga”

“To yaya”

“Wait…..ki tahomin da baquwar nan”

“Kaltume yaya?” Ta tambayeshi

“Yes” ya amsa mata yana mamakin yadda tayi caraf da sunan cikin kwanakin da basufi bakwai ba.

Qarasawa yayi a hankali inda yasa aka zuba masa kujeru,yana daura da inda dawakan suke,ta yadda duk wanda ke zaune zai iya hangosu,a wadansu lokutan suna daya daga cikin abinda ke debe masa kewa.

Da sauri ta dago daga durqushen da tayi daga can bayan kitchen din tana wanke ‘yan tsumman kayanta,tuntuni takeson wankewar,amma ta rasa a inama zatayi wanki cikin gidan,don ta fuskanci komai nasu a tsare yake,hakan ya sanya ta samu roba ta tari ruwa ta cikin famfon kitchen take fita ta baya take wankewa.

Murmushi jawahir ta sakar mata,ta lura kusan koda yaushe a tsorace take,har yanzun taqi sakin jikinta kwata kwata

“Wanki kike ne?,inata nemanki ai ban ganki ba” murmushin itama ta maida mata tana gyada kai

“Akwai washing machine ai,da baki wahalar da kanki ba” ta bata amsa tana qarasowa ciki,idanunta kan kayan da take wankewar,wanda ita a wajenta basu da maraba da tsumma,duk sanda zata ganta cikin kayan binta take da kallo,tanataso ta bata wasu kayan,saidai kwata kwata cikin satin bata samu sukunin zama ba bare ta fidda mata

“Muje yaya yana kiranki” fararen idanuwata da suka haska baqar fuskarta ta daga ta dubi jawahir,don bata gane wa take nufi ba,amma saita saki zanin hannunta ya koma cikin ruwan,ta janyo sudaddun takalmanta tana sanyawa,jawahir ta bisu da kallo kana ta juya,kaltumen ta soma binta a baya

“Wai bakya magana ne kaltume?” Murmushi tadan saki

“Kinga ki saki jikinki,mu gidan nan kowa yana da ‘yancinsa,matuqar kawai zaka bi dokar mummy to ita ba ruwanta da kai,ki saki jiki kiyi walwalarki kamar kowa” da kadan da kadan take janta da hira har suka isa inda samir ke zaune.

“Gata yaya” jawahir ta fada tana ajjiye masa abinda ya buqaci ta kawo masan

“Good auta,kije zan kiraki” ya fada yana murmushi,saita dan tsaya tana murmushi

“Amma yaya….” Murmushin shima ya saki,kaltume ta dan bishi da kallo

“I will call you when I’m done”

“Tom”ta fada tana juyawa ta soma barin wajen,kaltume ta bita da kallo tana jin kamar tabi bayanta,ita kadai a cikin gidan baya ga biba da take dan jin sukuni da ‘yar nutsuwa idan suna tare,barinta datayi a wajen sai takejinta wani iri gaba daya,gabanta na wani irin faduwa

“Bismillah….zauna” tattausar muryarsa ta ratsa kunnenta,saita waiwayo a hankali ta dubeshi da farare qal din idanunta,ta samu ya kafeta da ido yana duban black face dinta,sauke idanunta tayi a hankali,kana ta sulale zuwa qasa tana gaidashi

“Lafiya lau,tashi ki zauna” ya sake maimaita mata,duban kujerar tayi ta dauke kai,ba zata iya zama saman kujera ba yana kai,bata taba ganin ummanta ta yiwa babanta hakan ba,don haka ta girgiza kanta alamun a’ah

“Ta yaya kenan zamuyi magana a haka?,tashi ki zauna”ya furta yana gyara kujerar,tasan musu kusan haramunne,don shine abu na qarshe da bazata iya tuna sau nawa taga ya faru a gidansu ba,don haka ta miqe a darare ta nufi kujerar tana damqe da nannadadde mayafinta data yafa,tunda ta wanke hijabinta.

Idanunsa ya dauke zuwa wani sashe na daban yana boye murmushin daya taso masa,shi kadai yaji cikin ransa abun ya bashi dariya idan zuciyarsa ta raya masa cewa matarsa ce kenan.

Gyaran murya yayi kadan yana kwatanta ya yadda zai mata maganar da zafa fahimta dai dai da hankalinta,don yana ganin kamar tayi qanqanta da duk abinda zaya gaya mata

“Kinsan matsayina a wajenki?” Sai data dubeshi sannan tace

“Eh,miji…..” Kalmar tayi mata nauyi,ta kasa qarasawa,qaramin murmushi ya saki

“Haka” gyara zamanshi yayi sosai

“Inason daga yau ki dinga kallona a matsayin yaya ba miji ba kin fahimta?” Maganar tasa ta bata mamaki,ta sake dubansa ta dauke kai

“Eh,ki daukeni a matsayin yayanki,kinga yadda yanayin abun yazo,babu wanda yasan matatace ke,akwai lokacin da zan gaya musu da kaina,so karki damu da sai kin gayawa kowa,kinsan sunana?” Ya tambayeta,saita kada kai

“Muhammad samir,nan gidanmu ne gidan mahaifina,nasan kinga mahaifiyata,wadda ta rakoki qanwata ce,akwai yayarta nasan itama kin santa,kin fahimta?” Kai ta sake gyadawa tana saurarenshi

“Zaki ci gaba da zama tare damu har zuwa wani lokaci,yanzu ajinki nawa a makaranta?,kin gama junior secondary school ne?”

“Banyi karatu ba” shuru yayi cike da mamaki,ya dauka da bilal baiyi karatu ba ita din tayi,kasancewar ta girmeshi,amma kuma daya tuna yanayin society din data fito daga ciki sai mamakin nasa ha ragu,saidai kuma tabbas akwai aiki kenan a gaba?.

Sauya akalarshi yayi zuwa ga fannin addini,anan din alhamdulillah saiya samu babu laifi tana da sani sosai ta wannan fannin,hakan yasa yaji sauqin fargabarshi akan ta ina zai fara.

“Kina sha’awar karatun boko?” Ya jefa mata tambayar data sanya take fuskarta fadada da fara’a,da sauri ta gyada masa kanta,babban burinta kuma mafarkinta kenan a rayuwa

“Is ok,but ki saki jiki,ki daukeni tamkar yayanki kinji ko?” Kai ta kuma gyadawa

“Bakya magana?” Ya tambayeta yana murmushi,sanda ya tuna masoyanta da qauye irinsu haladu,qanqantar shekarunta na fita muraran,amma a hakan ake fada a kanta kamar wata cikakkiyar mace?.

“Inayi” ta amsa da siririyar muryarta wadda alamun farinciki ya bayyana ta cikinta

“Ku nawa ne a gidanku?” Ya jefa mata tambayar,sai yaga annurin daya bayyana dazu a fuskarta yana raguwa,sannu a hankali yanayin fuskarta ya sauya,da alama akwai abinda ya taba ranta yanzun

“Ni habiba……sai bilalu” ta qarashe fada muryarta na rawa,kansa ya gyada

“Allah ya gafarta masa”
“Amin”ta amsa tana duban tafin hannunta,tunanin ummanta da kullum take kwana dashi take tashi dashi ya bijiro mata

“Wa zai kula da ummanmu?” Tambayar ta subuto ta fito daga bakinta,har yanzu idanunta na cikin tafin hannunta.

Idanu ya zuba mata,sai yaji wani abu ya taba ransa

“Uwa” kalmar data sauka tsakiyar zuciyarsa kenan har sai daya lumshe idanunsa,ta wannan fannin rayuwarsa a hagunce take,ina tashi uwar?,tana da rai ko babu?,ida tana da rai wake kula da ita?,sune tambayar da suka hadu suka tsaye masa a rai

“Akwai wani abu da zai iya?” Tambayar daya yiwa kansan kenan,saidai tunanin nasa ya katse sanda ya fara jiyo alamun kukanta,haka kawai tausayinta ya saukar masa

“Habiba zata kula da ita,haka ne?” Ya samu kansa da fada,saita ji wani sassauci na saukar mata,qaramar ajiyar zuciya ta subuce ta fito daga bakinta,ta kuma daga fararen idanuwanta tana gyada masa kai alamun eh

“Good” ya fada yana bata qwarin gwiwa,yasan cewa akwai cakwakiya sosai cikin rayuwarsu,kusan shi ganau ne ba jiyau ba,amma akwai abubuwa da yawa da yasan cewa baisan dasu ba,bayason kuma shiga rayuwar data shafeta.

Shuru ya ratsa wajen sanda yake ciro wayarsa ya kira jawahir,ba’a jima ba sai gata,taja kujera daya ta zauna tana cewa

“Yaya da baquwarsa,ina fatan ba zata qwacemin fadata ba” qawataccen murmushin nan nasa ya sake ba tare daya bata amsa ba,saiya tashi sosai ya zauna yana dubanta

“Zaki iya squeezing time dinki ki dinga yima qanwarki lesson?” Ya tambaya jawahir din,tana murmushi ta daga gira

“Me zai hana yaya?,ka manta koyarwa yana daga cikin favorite dina,har ya najwa na ganin sakarcina?”

“Yes….i remember that,so daga yau ta zama dalibarki,zaku fara from the beginning ne,ayimin list na komai da komai da ake buqata zan siya”

“Tom yaya,amma yaya…..she need some items haka” ta fada tana jujjuya hannunta,ya fahimci bayani takeson masa,don hakaya bata hankalinsa

“Like?”

“Clothes”

“Ok,ba matsala”

“Thank you”

“You are welcome” ya amsa mata,sannan ya basu umarnin tafiya.

β˜€οΈπŸ”΄β˜€οΈπŸŸ β˜€οΈπŸ”΄β˜€οΈπŸŸ β˜€οΈπŸ”΄β˜€οΈπŸŸ β˜€οΈπŸ”΄β˜€οΈπŸŸ β˜€οΈπŸ”΄β˜€οΈπŸŸ β˜€οΈπŸ”΄β˜€οΈπŸŸ 
*_K’AMSHI,K’AMSHI RAHAMA NE MATAN DA SUKA AMSA SUNANSU MATA SU SUKA SAN MUHIMMANCIN DA K’AMSHI YAKE DASHI MUSAMMAN A WAJAN MAI GIDA ,_*πŸ’ƒπŸ»πŸ’ƒπŸ»
*_Zafafan turarruka masu zazzafan k’amshi hade da wasu irin manyan sirrika na mallaka cikin sauki ba boka ba malam hajiya , Zaki jefe tsuntsu biyu da dutse d’aya , domin zamowa star azuciyar mijinki_*🌟🌟πŸ”₯

*_nasan dai kunada labarin mashahuriyar Mai Saida kayan k’amshin Nan Wanda akafi sani da *HUMKAM GIDAN K’AMSHI* *_a wannan karon ma ta sake kawo maku da sabbin kayanta masu abun al’ajabi Wanda da kud’i k’alilan zaku more zafafan turarruka Kuma ki shiga jerin Mata masu aji_*

 

*IDAN SARI KIKE BUKATA INA BADAWA SANNAN INAGYARAN JIKI CIKI DA WAJE SHIN KINA FAMA DA INFECTION INA HADA MAGANIN SA DA IZININ ALLAH KISHA KI WARKE*
*Kadan daga cikin kayan da muke dasu*πŸ‘‡πŸ»πŸ‘‡πŸ»πŸ‘‡πŸ»πŸ‘‡πŸ»πŸ‘‡πŸ»

*BLACK KAJII*
shin kina bukatar turaren da Zaki turara gidanki ya dauke maki warin sanyi ya kwana biyu Yana k’amshi ,?ki saye black kajiji Zaki Gane banbancinsa da sauran wannan ba k’amshi kawai yake ba idan kina turara. Jiki dashi Yana maki maganin kala kala ciki kuwa har da na sanyi , nemi naki Kar ayi Babu keβ˜€οΈπŸŸ’β˜€οΈπŸŸ πŸŒŸ08132506044 HUMKAMINCENSE

*ANA WA HABIBY* Wannan harkan na oza room ne special turare Dan matan aure kadai yana dauke da abubuwa Wanda bazan fadesu anan ba sannan bashi kadai bane akwai Crazy powder da na ke hadawa dashi zakisha garin sannan kishafa turaren hmm

 

*SUDANESE HUMRA* Turare dake dauke da sirrika Mai DAUKAR hankali kamshin ya banbanta da sauran turare Hajiya babbar sirrine Wannan hadin manyan Mata 08132506044 HUMKAMINCENSE

*GLOWING OIL*
Wannan yasha bam bam da irin Wanda kuka Saba gani ,Yana kashe kuraje Yana cire tabo Yana maganin kezbi da duk wani matsalan fata ,stretch marks duk Yana ciresu ….

*MOWAR MACE*
turaren mowar mace turare ne da larabawa suke amfani dashi Wanda da yawa mutanenmu Basu San da wannan iccen ba Mai dauke da magani k’amshi da sauran abubuwan masu matukar amfani ga fata ba
Shi wannan iccen yanasa hasken fata yanasa fata tayi laushi da santsi sannan d’an alk’awari ne matuk’ar kina amfani dashi zai tsirga maki cikin fata ta yadda ko Bakiyi amfani dashi ba zakiji k’amshin shi na fita ta cikin fatar ki ,ke amfanin iccen mowar mace yanada yawa jaraba ko don gyaran fatarki , πŸ’ƒπŸ»πŸ’ƒπŸ»πŸ’ƒπŸ»πŸ’ƒπŸ»πŸ’ƒπŸ»

Muna gyaran jiki na amarya da uwargida zakizo har gida ayi maki gyaran jiki irin na Mata masu aji zakiyi kyau kiyi fresh ga kamshin da zai Kama jikinkiπŸ’ƒπŸ»πŸ’ƒπŸ»πŸ’ƒπŸ»

Munada πŸ‘‡πŸ»πŸ‘‡πŸ»πŸ‘‡πŸ»πŸ‘‡πŸ»
*JAS OUD* (hatsabibin turare kenan )

*AL’AJAB* ( Mai abun mamaki kenan )AL’AJAB Turaren tsuguno mai abubuwan Al’ajabi Yana maganin sanyi (infection) Yana matse HQ (Tightening)sosai 08132506044 yasa HQ dumi yasa jikinki da hq kamshi lokacin da kike AMFANI dashi idan Yana shiga gabanki zakiji wani Dadi na ratsaki Yana k’ara Dadi da Yana ciko gaba ya rikita ogaπŸ™ˆ

*FIRST LADY* na Mata masu aji turaren Kaya Dana daki
HAWII
KAJIJI
HALUT
πŸ‘ΈπŸ» *_PRINCESS_*
_Sabon turare Dana hada na shafawa ajiki da gashi *PRINCESS* Yana da Dadi cool kamshi gare shi babu hayaniya na fad’a muku sabbin turaruka na Nan tafe princess na daya daga ciki kisayi *PRINCESS* kiji sabon Hadi me sanyin kamshi babu kosarwa da ace zan iya zabi tabbas zan zabi princess a matsayin turaren gashina zan dauki princess ya zama shi zan farawa shafawa jikina idan zan kwanta zan dauki *PRINCESS* sbd yara na Dan kamshi bamai hayaniya bane musamman zan rika yi musu amfani dashi *PRINCESS* salon na daban kamshin daban dadin na daban *PRINCESS* Zabin ku ne Zabin Humkam shine farin cikin ku Masoya *PRINCESS* gidan kowa_

Duk wad’an Nan turarruka ne hatsabibai masu rikita mazaje masu wani irin k’amshi Mai shiga zuciyar masoya πŸ’ƒπŸ»πŸ’ƒπŸ»πŸ’ƒπŸ»

*SHU’UMAR HUMRA*
ke daga jin sunan kinsan ta dabance mashahuriyar humra ce ta tayi shuhura wajan birkita tunanin Yan maza , humra ce da indai namiji yajita a jikinki to komai muskilancinshi sai ya susuce maki tana tado da sha’awa shauk’i sirrin mallaka, cikin kankanin lokaci ki rikita maigidanki da daddadan k’amshin ki😍😍😍πŸ₯°

 

*HUMKAM GIDAN K’AMSHI INA NAN ZAUNE A KANO GA MASU BUK’ATAR ZAFAFAN KAYANA INA AIKAWA KOWANE GARI DAKE NIGERIA HAR MA DA K’ASASHEN K’ETARE , KARKU MANTA A DADE ANAYI SAI GASKIYA* πŸ’ƒπŸ»πŸ’ƒπŸ»πŸ’ƒπŸ»πŸ’ƒπŸ»πŸ’ƒπŸ»

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button