Sponsored Links
Dabi'ar Zuciya Hausa NovelHausa Novels

Dabi’ar Zuciya 52

Sponsored Links

52
D/Z

Tunda ta tunkaro wajen ya gaza dauke ganinsa daga kanta,karon farko daya soma ganinta cikin shiga irin wannan.

Abaya ce a jikinta baby pink mai sulbi mai kuma hawa biyu,wadda ta wadata da adon baqaqen duwatsu masu wani irin walwali da sheqi,duk da cewa shiya siyo kayan,amma ba tsammaci zasu karbeta har haka ba.

Yayi tayi rolling mayafin ya baiwa gaban gashinta mai santsi damar fitowa,idan ka kalleta zakayi tsammanin irin kyawawan Ethiopians din nan ne,saboda yadda kalar fatarta ya sake fes kamar bata shiga rana.

Igiyar da akayi daga tsakiyar ciki don daure rigar ta zauna daidai jikin me ita,ta taimaka wajen fitar da surar albarkar qirjin da Allah ya bata,wanda sam batasan hakan ya faru ba,saboda ko madubi bata tsaya kalla ba,idanunta sun sake shanyewa saboda rashin wadataccen baccin da bata samu ba a daren jiya,babu koma a fuskarta banda wata powder da jawahir ta siya mata ta masu kalae fatarta, powder din kuwa ba qaramin kyau takewa fatarta ba,sai labbanta daketa qyallin man lebe daya qarawa leban nata taushi da kyau.

Baisan ajiyar zuciya ya saki ba,saida ya tsinci zuciyarsa tana tuhumarsa da yadda ya qure kaltum din da kallo har ta kamashi yana kallon nata,abinda ya sanyata jin kunya,ta saka hannu a hankali ta bude gidan gaba ta zura jikinta kafin qafafunta da suka sha hill shoes su biyo baya,abinda ya qarawa adon nata kyau,budurcinta daya fara bayyana ya sake fitowa fili muraran.

“Ina yini” ta gaidashi a ladabce tana dora purse dinta saman cinyarta

“Lafiya lau” ya amsa mata yana kallon yadda garin ya fara hada hadari,ba kasafai yakeson tuqi da damina ba saboda ruwa,yaso tafiya ne a jirgi,so amma duka yau babu jirgin da zai tashi daga kano zuwa bauchi,don haka ya maida tafiyar kawai a mota,saboda lokaci ya riga ya qure,gobe ne daurin aure,a haka ma yayi missing events masu yawa,ya kuma sha mita da qorafi wajen amiru,amma duka ya shareshi,don dama shi ba kasafai ya fiya shiga irin wadan nan shagulgulan ba sai wadanda suka zama dole.

Yana qoqarin tayar da motar qamshinta nason dagula masa lissafi,sai zai murza key din sai yaji kamar bazai iya ba,kamar wanda aka zarewa dukka lakar jikinsa,har taji shurun yayi yawa,ta daga kanta daga murza yatsun hannunta da take tare da wassafa yadda xasuyi tafiya tare dashi ta awanni masu tsaho daga ita saishi.

Kallon datayi masa akayi katari shima ita yake kalla,a hankali ya motsa labbansa,idanunsa kan dan qaramin bakinta

“Wannan rigar…..” Sai kuma yayi shuru ba tare daya qarasa ba,ya cire hannunsa daga kan motar a hankali ya nufo inda take zaune,numfashinta ta dauke gaba daya ganin ya nufo da hannunsa qasan qirjinta.

Yatsa daya ya saka ya kunce igiyar data daure tsakiyar rigar da ita,take rigar ta ware,ta batar da duk wani shape nata daya fito.

Sake qamewa tayi tare da runtse idonta ganin ya matso da jikinsa gaba daya inda take,qwayar idanunsa cikin nata,cikin second biyu qamshin turarensa,da hucin numfashinsa da dumin jikinsa gaba daya suka mamayeta.

Seat belt ya zaro a hankali ya zagayo da ita ta saman cikinta,wanda garin hakan yadan shafi qirjinta da bayan hannunsa,al’amarin daya sanyashi jin wani shock tun daga yatsun qafarsa zuwa kwanyarsa,ya sauke numfashi me nauyi sanda ya gama saka mata ya maida bayansa ya jigina da kujera yana qoqarin maintaining nutsuwarsa.

Har zuwa sanda ya bude nashi idanun,ya murxa key din ya tashi motar yana karanta addu’ar matafiya a fili amma qasa qasa.

Tata addu’ar itama ta fara karantawa sanda suka ficewa daga gidan,wanda basuyi wata doguwar tafiya ba ya sanya karatun daya daga cikin shahararrun malamai kuma bayin Allahn da ubangiji yayi mana kyautarsu wato mlm dr umar sani fage.

Karatun kusan shine ya janye hankalin kowannensu,karatu ne cike da tarin hikima da kuma maganganu na fasaha,tare da tunkuda bawa zuwa kusanta kai da Allah matuqar kusantuwa,tun tana iya jin abinda malamin ke fada tana kokawa da bashin baccin data ci jiya,har yayi nasarar yin awon gaba da ita ta daina jin komai.

Tafiyar awa uku da rabi suka shiga garin azare,kai tsaye suka nufa cikin garin,zuwa lokacin garin azare ya fara duhu saboa hadarin da ya yiwa sama rumfa,saidai mutane da yawa basu kawo zubarshi ba,saboda wannan kusan shine hadarin farko tun bayan sanya ran shigowar damina.

Idanunta biyu a sannan,sabida sun tsaya sunyi salla,ya siya musu take away duk da itadin bata iya ci a gabansa ba.

Ringing wayarsa tayi,yana tuqi a hankali da hannu daya,yasa daya hannun ya daga wayar ya sanyata a kunne idanunsa na bisa titi.

Magana suke da amiru,ya shaida masa akwai dinner din mr and mrs da za’a gabatar takwas na dare,amma saboda ganin hadari yasa an maidota nan da awa biyu

“This is none of my business…..meye amfanin gayamin?,kai kanka ba zaka samu shiga ba tunda tuzurun banza ne,har gwara gwara ni” dariya sosai amiru ya qyalqyale da ita,bazai biye masa suyi abinda suka saba ba,don so yake yallaboshi yazo kodon saboda kada angon ya fassara wani abu daban,saboda yarinyar da zai aura din tadan so samir

“Wai tula ne zaiwa audi gori……gwara kai ame?,tuxurantaka?,meye marabar dambe da fada,ni dakai ai duk d same,amma dai afuwa master,na yadda da kai,yanzu abinda za’ayi,kada ka wuce gida,ka tsaya dai dai Round about din nan da zaka shiga titin gidan ya dikko,kafin ka shiga titin ka tsaya,am on my way” katse wayar kawai yayi ba tare daya amsawa amirun ba,sai ya koma tuqi a hankali yana duban hanya.

Tun kafin su qarasa ya hangi samir din jingine da wata sabuwar baqar mota,dai dai sanda motar take fakawa,daidai lokacin yaga ya cusa kanshi ta window din motar,da alama magana yake da wasu,sai samir din ya kashe motar kawai yaci gaba da xama cikin motar ba tare daya fita ba,ganin haka amirun ya tunakarosu,kanshi tsaya ya tsaya side din kaltum,ya bude murfin motar yana cewa

“Sannu da hanya madam,ga mota can shiga ta ciki” duban samir tayi suka hada idanu kana ta dauki jakarta ta fice daga motar,wanta tashinta ya sanya wani abu fadowa daga jikinta,hannu ya miqa yana qoqarin dauko takardar,saiya kula hotone,ya juya hoton a hankali,take idanunsa sukayi arba da fuskar dake jikin hoton,abinda ya sanyashi bin baya kaltum da amiru dake tafiya zuwa wancan motar da kallo,mamaki na mamayarsa na inda ta samo hoton,saiya bude locker din motar ya saka hoton ya rufe yana juya tambayar inda ta samo din cikin ransa.

Ruqunqumeta jawahir tayi sanda suka shiga cikin motar,kamar xata koka cikin kaltum din,jtakam dariya kawai kaltume din ke mata,har zuwa sanda amiru da yaga basu da niyyar rufe motar ya rufe musu ya koma wajen samir.

*********kayan da amirun ya miqe masa ya kalla

“Am telling you fa,babu inda zanje,ina buqatar na huta malam” kicin kicin amiru ya masa,yasan idan baiyi da gasken ba ba zaya je ba

“Wallahi koda wannan shine last thing da xakayi a azare sai kaje” gira ya dage ma amirun dukka biyun yana dubanshi

“Really?” Harara ya watsa mana,saiya fincika kayan daga hannunsa ya watsa gado ya bisu ya kwanta kawai a kai,qyaleshi amiru yayi,tunda yayi hakan yasan zayaje din koda baiso ba.

Kanta ta karkatar ta dubi jawahir

“Don Allah ki shiga na jiraki anan mana” kaltum ta fada tana kwabe fuska,tun daga sanda akayi.mata kwalliyar dake fuskarta har zuwa yanzu duk a takure take,sanda taga fuskarta a madubi sai data tsorata,irin kyan da tayi bata taba zata ko tsammatar ganinsa a fuskarta ba,dukka jama’ar dake wajen sai da suka tsaya suna kallonta,saboda yadda kwalliyar tayi masifar bin lafiyayyar chocolate colour din fatarta ta kwanta sosai.

Idanu jawahir ta fitar

“Wa?,ai wallahi saikin shiga,nima setup mukayi da ya amiru a matsayin miji da mata zamu shiga,kema haka zaki haquri kizo mu shiga…..kinga ma yana kirana,hala ya iso” jawahir ta fada tana daga wayarta tana duban me kiran,sai kawai taga ta balle murfin motar ta fita tana duba ta inda suke.

Ta bangaren da take ta leqo ta mata alamar ta fito,a hankali ta janyo jikinta ta zuro qafafunta daga motar.

Yana tsaye ya basu baya kadan,hannayensa zube a aljihun wandonsa yana duban wajen,ranshi baiso zuwa wajen ba,kawai dai yayine saboda ya faranta ran amirun daya dage.

“Oya….muje already ma an fara event din” amiru ya fada,abinda ya sanya samir juyowa kenan.

A hankali idanunsa suka sauka kanta,tana tsaye dab dashi,sai yaji wuta ta dauke masa na wucin gadi,baisan sanda ya bita da kallo tun daga sama zuwa qasa ba,wani kyau na musamman da bai taba tsammatarsa ba tayi masa,komai ya fito perfect,duk wata baiwa tata ta fito,ta zama cikakkiyar budurwar me tashen shekaru da zata iya jan hankalin kowanne namiji da zai dora idanunsa a kanta.

Wani abu da yaji ya tsaya masa a wuya ya hadiye,ya dauke idonsa daga kanta ya maida kan amiru,saiya miqa hannu ya fincikeshi gefe

“How dare you zaka sata tayi irin wannan kwalliyar amiru?” Idanu amiru ya fitar

“Mene aibu to?”

“Ka manta matar aur…….” Maganar ta maqale masa ba tare data gama fita gaba daya ba,saboda rashin sanin ma’anar yin maganar.

Dariyar da amirun ke boyewa tadan fito kadan

“Bari na qarasa maka tunda kunyar qarasawa kake,na manta matar samir ce?,ko?,karka damu,ni kadai na sani fa,amma yau kowa a hakan zai kalleta……muje please muna sake makara” amirun ya fada yana yin gaba da sauri,ya jera shida jawahir itama daketa boye dariyarta,duk da batasan alaqar dake tsakani ba amma cewa take

“Wallahi ya Aamir sunyi kyau sosai,sun dace da juna Allah yadda kasan miji da mata,dama zaiso kaltum, she’s cute wlh,duk da bayason baqar mace amma kaltum ta dace dashi,yau ka yima ya samir shigar sauri” murmushi shima yayi ya waiwaya yana satar dubansu sanda suke gab da shigewa hall din.

Shuru ya biyo baya a wajen,tana tsaye a inda take kanta aqasa tana wasa da yatsun hannunta,saboda gaba daya jinta take a takure,yayin da yake tsaye,har yanzu hannayensa zube a aljihunsa yana ci gaba da qare mata kallo,a hankali ya tako zuwa inda take,ya zare hannunsa daya dake aljihunsa ya kama nata hannun,gaba dayansu wani abune yabi ta jijiyarsu ya aikama qwaqwalensu saqo,saiya fara takawa a nutse tana biye dashi,wanda kafin sukai ga shigewa ciki yayyafi mai qarfi ya fara sauka.

Suna shigowa wajen idanun jawahir na kansu,baki ta bude tana mamaki,yau yayansu ne da kama hannun wata?,kasa daurewa tayi sai data tabo amiru.

Daga can baya ya zabar musu sit,tunda suka shiga wajen bai motsa ba kamar yadda itama bai barta ta motsa ko nan da can ba,bayaga ango da yaje ya yiwa Allah ya sanya alkhairi,abinda ke bashi haushi da mamaki shine duk wanda zai wuce ta wajen saiya kallesu yakuma juyowa,wayarsa na hannunsa yana amsa saqonnin da baiyi niyyar dubawa bama,lokaci lokaci yakan saki tsaki ya kuma jewa amiru harara.

Sanda aka fara rabon abubuwan motsa baki jawahir ta matso gurin ganin bata taso ba

“Kaltum….bakwa sha’awar komai ne?” Ta fadi tana ajjiye wani paper plate dake hannunta

“Get out malamarsu” samir din yadan fada a kausashe,da alama akwai abinda ya taba rashi,ba zata iya tuna yaushe ne na qarshe daya mata hakan ba,don haka ta dauke plate dinta tana boye fuskarta tabar wajen.

Da kadan da kadan ake raguwa awajen,duk da ruwan saman daya fara sauka bai hana mutane tafiya ba,saboda kusan kowa da motarsa yazo shida iyalinsa,wajen ya qayatar sosai,babu hauka babu baragada,kowa da matarsa yake,masu setup irinsu jawahir kadanne,sai zuwa sannan ya daga kanshi yana maida wayarsa aljihu yana kuma dora kansa a kan kaltum.

Kwalliyarta na nan kamar sannan aka yita,dan qaramin bakinta da yasha jambaki yana motsawa kadan kadan,baisan me take fada ba,daya tsura mata idanu sanda aka yi tsawa sai ya lura addu’ar tsawa take,ta dan rufe idanunta kadan,wanda hakan ya fito da zara zaran gashin idanunta da zaka tsammaci sa mata akayi,saidai mascaran da aka sanya musu ya sake fitar da kyau da tsahonsu,ya fuskanci tsoron tsawa take sosai,saiya miqe a hankali ya miqa mata hannunshi.

Jin tsaiwarsa saman kanta yasa ta bude idanuwanta,suka sauka akan lallausan tafin hannunsa da yake miqa mata,karo na biyu kenan daya taba bata wannan damar,tana jin kunya tana kuma jin nauyi,yana kuma sanyata shiga wani yanayi,amma haka ta dora masa nata hannun a hankali ya rumtse cikin nasa ya kuma jirayi tashinta kana suka nufi hanyar fita.

Dukka akan idanun jawahir,mamaki yana sake kamata,bata taba ganin haka daga yayan nata ba,hannunsa cikin na wata?,me aikin gidansu?,kuma ba muharramarsa ba,shida kullum maganarsa itace su kare mutuncin kansu,kada su yarda koda wasa su hada jiki da wani da namiji?,binsu tayi da idanu har suka fice daga hall din.

Dakatawa yayi da tafiyar yana kallon ruwan,ya soma qarfi sosai,wanda mutane da yawa dake ciki basusan da hakan ba,waiwayawa yayi kadan ya dubeta,sai yaga ruwan ta zubawa idanu itama,da alama tana wasafta ta yadda zata shiga cikinsa.

Yana riqe da hannunta a hankali suka fara taka cikin ruwan suna dosar motarsu,idanuwanta ta runtse sanda sanyin ruwan yake ratsa jikinta,saukarsa ta farko ji tayi kaman numfashinta zaya dauke,tunda can ita me tsoron ruwa ce,shi yasa kaf rayuwarta bata taba shiga rafi wanka ba,saidai tayi rakiya wa su wasila,tana tsaye kuma har suyi su gama.

Qarfin ruwan ya sanya kafin su isa motar ta jiqe,duk da bame yawa ba amma tana jin sayin har cikin qashinta.

Takurewa tayi sosai a sit dinta,tana kallon singalilin hannunsa da ruwa ya jiqa yana kashe ac ya maidata zuwa heater,sumar gargasarsa itama tayi luf,ta rufe idanunta sanda akayi wata walqiya,ta tabbatar tsawa ce zata biyo baya don haka ta sake curewa guri guda.

Binta yayi da kallo,saiya saka hannunsa ga seat din baya,ya dauko hiramin daya siya dazun a store din da sukaje siyayya shida amiru,ya farke ledar ya wareshi ya soma rufa mata,abinda ya sakata bude ido,idanunsu ya shiga cikin na juna,eye lashes dinta sun jiqe sosai sunyi wara wara,sai tayi qas da kanta tana jin dadin rufetan da yayi

“Na gode” ta samu kanta da fada,ya tada motar yana amsa mata da

“You are welcome”.

Tun basuyi nisa ba ruwan yayi wani irin qarfi naban mamaki,tituna suka fara cika saboda rashin kyakkyawar magudanar ruwa,tsaki samir din yaja yana kallon yadda titi ya shafe da ruwa,ya rasa aikin me gwamnati keyi?,ruwa a saman titi kamar layukan unguwanni?” Baka bambace titi da kwata?,yana daya daga cikin abinda yasa ya tsani siyasa iyaka kenan,babu komai cikinta sai yaudara da daukan alqawuran dako kusa ko alama basa iya cika koda kaso daya cikin ukunsu.

Ji yayi bazai iya ci gaba da tuqin ba,don baisan yadda zai tadda unguwarsu ya dikkon ba,bugu da qari ma ya tabbatar idan yaje zaiyi horn ne ya taso me gadin da a yanzu yake cikin dakinsa ya samawa kansa mafaka daga dukan ruwan saman,wannan tunanin yasa ya gangara a hankali hannun da yake tuqi qofar wani katafaren guest in,ba tare daya tuna inda zai ajjiye kaltum din ba.

Umarnin fitowa yayi mata bayan ya bude mata murfin motar,ta fito a hankali tana sake hade jikinta waje guda,saiya saka hannunsa saman daya kafadartata ya janyota zuwa jikinsa,abinda ya rage mata dukan ruwan,saidai kuma hakan da yayi mata tamkar ya sake jefa abun fashewa ne cikin zuciyarta,ta dinga sauke qaramar ajiyar zuciya a hankali.

Da tarba ta mutunci receptionist din ya karbeshi,ya buqaci daki biyu

“Saidai kayi haquri yallabai idan babu damuwa kuyi squatting a daki daya,babu dakuna sai wannan da ka karba yanzu guda biyun da suke ba kowa a ciki gyara ake musu,babu damar iya zama a ciki”

“Ba matsala” ya fada a hankali.

Sai daya bude mata dakin ta shiga sannan taga ya sake fita ya dawo bada jimawa ba,hannunsa dauke da wani irin akwati dan qarami me dauke da tambarin wani store,wanda manyan customers dinsu da sukayi siyaya da yawa ko me manyan kudi suke zubawa kaya a ciki.

Tana daga zaunen ya kunna heater din dakin,ya rage haske qwayayen,sannan kuma ya kunna water heater ta bandaki ya shige bayan ya tara ruwa me zafi sosai.

Har sanda ya murda qofar toilet din ya fito tana zaune a wajen jikinta a hade,duk da dumi ya fara ratsata,saidai hankalinta ya rabu biyu,ta yaya zasu kwana a dakin nan daga ita saishi?,me zata cewa jawahir idan ta tambayeta ina sukaje?,zatace mata ne sun kwana tare bayan babu wanda yasan alaqarsu?.

“Ki cire wadan nan kayan kafin sanyi ya kamaki,ki shiga toilet ki dumama jikinki da ruwan zafi” ya fada sanda yake fitowa daga toilet din sanye da sabuwar rigar wanka ta towel har qasa me budadden qirji,abinda ya bayyana tarin sumar dake kwance a qirjinsa baqa sosai mai kuma santsi.

Numfashinta ta dauke gaba daya tana sake qanqame jikinta,ruwan da yayi wanka ya sanya kowacce suma ta jikinsa kwanciya,hatta da qawataccen sajen fuskarsa mai kama da qasumba,saidai baikai qasumba fadi da cika ba.

Wani abu ta hadiye,cikin dakiya tace

“Da zaka qarasa dani gida….saboda su jawahir…..” Kasa qarasawa tayi saboda ji da tayi a jikinta ita ya zubawa ido,ilai kuwa haka ne,har baisan sanda murmushi ya subuce masa ba,yana da tabbacin batasan waye samir ba,wannan rayuwar ba irin waddanya fasaltawa kansa ko yake sha’awarta bace,inda tazo masa a matsayin matar aurensa da suka fahimci juna,duniya tasan da aurensu da ba wannan zancan ake ba a yanzu,kwata kwata wannan ba irin rayuwar auren daya tanadarwa kansa bace,saidai akwai wani qwaqqwaran bond da yakejin yana son gilmawa a tsakani,duk da haka aure duka aure ne,zai tunasar da ita abinda takeson mantawa,duk da cewa baison ya wuce gona da iri,saboda yanajin cewa gaba kadan xai bata dukkanin zabi ne.

Batasan ya tsaya a gabanta ba sai da idanunta suka dauka kam xara zaran yatsun qafarsa da gashin ke kan kowanne dan yatsa ke akwance shima,kafin tayi wani motsi ya kama dukka kafadunta ya dagata,sai ya saka hannu ya zare hiraminsa ya aje gefe,jawota yayi jikinsa ya mata sasssuqar runguma,abinda ya kusa sanyata daukewar numfashinta kenan saboda jikinta daya gogi nashi,shi dinma yaji,amma ya dake,yanason ya mata tuni ne kan abinda ta manta,saiya kama zip din rigarta ya saukeshi qasa gaba daya,duk da cewa a iya nata qarfin fa cukuikuye rigar a jikinta amma hakan bai hanashi sabule mata ita ba ya hada harda bra dinta,adalci daya yayi mata tana jikinsa bazai iya kallonta ba saidai duk wata fata ta jikinta da hannunsa ya taba yana jin aiken saqo zuwa kowanne sashe na jikinsa,sai ya dauko hiramin ya rufa mata,ta kamashi kuwa tsam ta riqe tana sake lullube jikinta,ko ina na jikin nata yana rawa,qafafunta kamar ba zasu iya daukarta ba

“Akwai ruwa me zafi kije kiyi wanka kixo ki kwanta,idan sun tambayeki gobe,kina iya gaya musu mijinki kika biyo,naki da zunubi ko dis a wajen Allah” ya fada yana juya mata baya yana takawa zuwa gaban madubin dake fuskantosu,saidai yana iya hangenta ta madubin sanda take takawa da sauri kamar zata fadi ta durfafi bandaki.

Ta dade a tsaye tana haki tare da sauke numfashi,gaba daya ya aza mata wani irin nauyi da tsoro,bata taba kawo haka a tsakaninsu ba,duk da cewa tana jin abubuwa masu yawa dangane dashi cikin zuciyarta…….

*_A WANNAN DAREN_*

Su biyu ne rak zaune cikin dakin,duk da suna saka ran shigowar mutum na uku wato najwa.

A hankali hajiya jidda ke qarewa dakin kallo,tana qiyasta yawan dukiyar da aka sake narkawa dakin,kafin maganar hajiya shuwa ta shiga kunnenta

“Idan bakiyi wasa ba hajiya jidda kwabarki tana dab da tayi ruwa,dava tafiyata ace babu wani ci gaba da aka samu?,saima tarin koma baya dani na hango?,me yasa ba zaki kawo qarshen komai kowa ya huta ba kema ki huta?,tun kafin akai lokacin da zaki dora hannunki aka?” Murmushi mummy ta saki tana duban hajiya shuwa

“Akwai abinda nake jira da dako,banason garin sauri naje na aikata kuskuren da kika kusa aikatawa” murmushi hajiya shuwa ta saki

“Iya gidan nan kadai amma ya isheki amsa ko?” Maida mata murmushinta mummy tayi

“Eh qwarai,saidai akwai banbanci,banajin zan iya qarasawa bigiren da kike kai a yanzu” dariya sosai hajiya shuwa ta saki

“Kijimin mata…..da wanda yaci alade,da kuma wanda yaci mushe meye bambancinsu?”kai mummy ta girgiza

“Banbanci me tarin yawa kuwa,tunda ko banza shi mushe ai yankan Allah ne……”.

A hankali najwa taja da baya hannunta riqe da cup din tea data hado da niyyar sha,ta taka kuma zuwa dakin da aka sauketa cikin gidan hajiya shuwa tun bayan zuwansu garin azare,wanda sukaqi zama gidan ya dikko.

Katafaren dakin da sai ka zaci dakin wata hamshsqiyar ne,ranta a bace take duban tvn dake aiki a dakin,duk da cewa bata tvn take ba,hirarsu mummy ke dawo mata,ko daya bataji sun tattauna kan matsalarta ba.

shedan ke dake zafafa mata zuciya,ta fuskanci mummy tana slow ne kan abubuwa da dama,to itakam a yanzu tanajin qarfinta ya kawo,zata shiga nata yaqin,zata aiwatar da abubuwan da mummy ta kasa aiwatarwa,bata jin xata yarda ta amince….tasha dukka wata wahalar karatu saboda cikar buri da muradinta,sannan a qarshe daddy yace taje tayi aiki da kamfanin saraki a qarqashin sarakin?ba zata iya ba,kuma da sake.

Miqewa mummyn tayi tana tattaki gaban hajiya shuwa,maganganun da suka sakeyi suna mata yawo akai,hajiya shuwan kuma na binta da kallo.

Tsayin wasu mintuna mummyn ta dawo gabanta ta tsaya

“Na gamsu da dukka bayanai da hujjojinki,kuma a wannan karon ina ji a jikina zan aiwatar da tunaninki,muga kalar naki takun” kalaman da suka sanya fitar murmushi daga fuskarta hajiya shuwa,ta daga hannu tana jinjinawa mummy.

.

“Ya na ganki ke kadai?,Ina kaltum din?” Hajiya qarama ta tambayi jawahir wadda take fidda kayan jikinta da suka jiqe da ruwan sama.

Tsaiwa tayi da cire kayan,ta ta waiwayo ta dubi hajiya qarama

“Sun rigamu fitowa fa,basu iso ba kenan?”

“Nidai babu wanda na gani a cikinsu”

“Ok,bari na gama na kira ya sarakin” ta fadi tana dauko kayan da zata sauya din masu dan kauri saboda sanyin ruwan da ya ratsata,sai data gama shiryawa sannan ta zauna ta soma kiransa.

Tana shiga amma ba’a dagawa,already ya sanyata a silent ne,kaltum dake duqunqune cikin bargo tana sheqar lallausan qamshin turarensa daya kama kayansa tana iya hango hasken wayar saboda a saman kanta take a ajjiiye,saidai batason yin magana kwata kwata,tafison ya dauka tayi baccin ne kamar yadda ga zata,tun sanda ya bata rigarsa ta sanya kunya da nauyi suka cikata,saboda barin nata kayan da yayi cikin mota.

Shafa addu’arsa yayi a hankali,sannan yaja bargon daya dora saman dogayen qafafunsa ya dawo zuwa qugunsa,sannan ya zame a hankali ya kwanta a hannunsa na dama.

A hankali ya lumshe idanunsa kana ya budesu,idanunsa suka sauka a bayanta,duk da cewa baya iya hango komai na jikinta sai bargon data duqunquna har kanta da shi.

Wani numfashi mai nauyi ya sauke,yanayi irin wannan yana saukar masa da feelings sosai tun ba yanzu ba,qamshin qasa hade da sassanyar iskar damina ta dare,saiya sanya hannayensa tsakiyar gwiwoyinsa kamar maijin sanyi,haka kawai kasancewarta kusa dashi ke neman dagula lissafinsa,tsahon rayuwarsa wannan shine karo na farko daya taba hada makwanci da diya mace,yaso ya barta ta kwana a qasa kamar yadda ta zaba,saidai kuma yaga hakan bai dace ba,duba da sanyin ruwan dake sauka,ga kuma tiles da ya yiwa dakin qawanya.

Hasken wayar ya hango,wanda ya bayyana bayan walqawar walqiya a sararin samaniya,walqiyar data sanya kaltum runtse ido sosai da kuma curewa waje guda tana addu’a qasan ranta,kan Allah yasa ba tsawa za’a saki ba.

Hannu ya miqa ta saman kanta zai janyo wayar,dai dai sanda qarar tartsatsin walqiya mai qarfi ya baje a fadin duniya ya sauka zuwa kunnen kowanne abu me rai dake sararin subhana.

“Alhamdulillahil lazi yusabbihur ra’adu bi hamdih,wal mala’ikatu min khifatihi” saraki ya fada a hankali yana dan runtse ido saboda qarar tsawar,sannan ya bude idanun nasa a hankali ya sauke a kanta.

Baiyi tsammanin cewa batayi bacci ba saida aka saki tsawar yaji yanda ta firgita,har kuma bayan shudewr tsawar yana iya jin yadda ta sake tattarewa waje daya,bai fasa dauko wayar ba,ya budeta ya shiga app din karatun qur’ani,qira’ar shaik abdur rahmani assudais,ya kunna suratul baqra,ya sanya volume dinta saisa saisa (indai har zaki iya kwana da waya saman kanki bayan kin gama danne dannenki,to yana da kyau ki koyi sanya karatun qur’ani cikin dakinki sanda zaki kwanta bacci,cikin qaramin volume ba mai yawa ba,hakan yana taimakawa wajen yin bacci me dadi mai kuma cike da nutsuwa,uwa uba ga tsaro da zaya baki daga dukkan sharri,koda bunu chargy indai akwai wuta,jonata a socket,ki kunna qur’anin,yana playing tana chargy,zaki mamakin yadda wayarki zata cika da wuri,ga kuma qur’anin yana yi har safiya,koda chargynki ya kusa qarewa kika kunna,wani hukuncin Allah wayar bata mutuwa,tana kaiwa har safiya yanayi,Allah ya bamu albarkacin qur’ani mai girma,alfarmar shugaba S A W👏🏽👏🏽).

Saman kansu ya sanya wayar,ya raba a hankali zuwa bayanta ya kwantar da jikinsa,idanunta ta lumshe gaba daya zuciyarta ta soma gudu yadda ta saba a duk sanda ya rabota….lokacin data jishi cikin bargon da take,hannunsa saman ruwan cikinta,muryarsa can qasa kamar meyin rada yana cewa

“You are safe….. good night” cikin son yin aiki da maganarsa ta rufe idonta a hankali tana sauke numfashi,dumin kowanne na ratsa dan uwansa yana haifar masa da wani yanayi na daban………

_to sai ince asuba ta gari kalsam_

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button