Sponsored Links
Arubuce Ta Ke Hausa NovelHausa Novels

Arubuce Ta Ke 91

Sponsored Links

Page 91

Sassanyan qamshi parlor din yake fitarwa baya ga wani kwantaccen yanayi da duk wanda ya shigo ciki sai ya burgeshi,awa guda kenan da gama dukka aikinta,ta kuma shirya kanta cikin wata gown ta yadin chiffon mai qaramin hannu,plain ne black babu digo ko adon komai a jiki,ta matse gashinta da jiyan abbas ya kaita da yammaci aka gyara mata shi,yana daya daga cikin abinda yakeso,shi yasa shima yake bashi kulawa har fiye da yadda ita ke kula da sumartata,duk sanda take kwance a jikinsa zaka samu hannunsa saman kanta yana yamutsa sumartata mai tsaho da santsi,abinda yake yawan haifar mata da kasala,saita lafe a jikinsa.

Hankalinta ya dauku ga wayarta sosai,tana karanta wani hausa novel mai suna HANGEN DALA,labarin ya tafi sosai da hankalinta,ya kuma fara ankarar da ita matsayin hafsat a wajenta.

Ya dauki mintuna kusan uku tsaye a bakin qofar yana qare mata kallo ba tare data sani ba,hancinsa kuma yana shaqar daddadar iskar da parlor din yake fitarwa.

Tayi masa wani mugu mugun kyau,cikin kwanakin gaba daya wani kyau take qarawa,ga wani irin fari data sakeyi kamar ka sanya hannu jini ya fito,ta kuma qara qibar data sakata murjewa,alamun hankali da girma sun fara nunawa a jikinta,qibar tayi mata wani irin kyau dake dimauta masa tunani,shi kansa wani lokaci yakan tuhumi kansa

“Abbas anya baka zauce akan yarinyar nan ba?” Bai sani ba ko zaucewar yayi,amma shi kansa yasan yana mata wani irin so da bazai misaltu ba,baya gajiya da kallonta,baya gajiya da ganin shirmenta,baya gajiya da sauraren hirarta,ko ba komai zai samu nishadi irin wanda duk duniya idan ba wajenta ba babu wajen wanda yake samunsa.

Yaga alamun hankalinta yayi nisa sosai,don haka ya sanya qafarsa cikin tattausar muryarsa yayi mata sallama,suna hada ido ta miqe da sauri bayan ta watsar da wayar gefe,ta kuma tako da sassarfa yadda ta saba yi masa ta dane shi,ya sanya dukka hannayensa ya tarbeta,ya kuma dauke abarsa cak ya aza a jikinsa yana aika mata kisses ta ko ina,laushin fatarta da qamshinta kamar zai zautashi.

Kamar ko yaushe ta sunne kanta tana jin kunyarsa,ya saki qawataccen murmushi yana shiga cikin falon sosai da ita hadi da cewa

“Gayamin…..me zanyi na qarasa cire kunyar nan baby……tana qwarata wani lokacin fa” ya fada murya qasa qasa kamar su da wani ne a falon,saita sakar masa murmushi tana shigewa jikinsa.

A hakan yana dauke da ita suka shige bedroom dinsa tana masa sannu da zuwa

“Yau anyi zafi,wanka zan fara yi baby,ba wani abinci yau” dariya ta sakar masa,sannan ta wantsalo daga hannuwansa zuwa qasa,ya tareta da sauri yana cewa

“Yi a hankali,wai bakiga kin fara zama ‘yar lukuta ba?,inajin na kusa fara kasa daukarki” baya taja tana bata fuska

“Ka kusa daina daukata kuma uncle?” Ta fadi tana bubbuga qafa a shagwabe,yasan yanzun zai ballowa kansa ruwa,sai yayi saurin yin kwana

“Wasa nake miki fa babyn uncle…..amma fa wait…. seriously kin fara zama ‘yar lukuta,ban yarda ba akwai abinda yake faruwa,me kike ci bakya sanmin?” Siririyar dariya ta saki

“Uncle ka fini ci fa,saidai wanda nake ci da daddare kana bacci” kai ya gyada yana dariya

“Harda rabona kike ci ai,kuma ban bayar ba,saina fanshe abuna,zo nan” ya fada yana takawa gabanta idanunsa a narke a kanta,ta saki dariya taa fadawa toilet da gudu.

Tsayawa yayi ya bita da kallo har ta shige,qugunta ya bude sosai,qirjinta ya fara cika irin yadda yakeso,abinda yake sake dimautar dashi a kanta koda yaushe,saidai har yau ‘yar shagwabar tasa kukan amarci takeyi bata daina ba,hakan baya damunsa,hakan ma burgeshi yakeyi,ya zauna ya lallashi kayarsa.

Gaban mudubi ya taka ya zuge jakar daya shigo da ita yana duba takaddun daya shigo dasu,ya sake sakin murmushi yana tunanin irin yadda zataji idan ya gaya mata komai na tafiyar ta saudiyya ya kammala,yana tsaka da dubawar kuwa ta fito tana goge ruwan hannunta da qaramin towel

“Uncle ka shiga na hada” ajjiye su yayi,ya matsa zuwa gabanta,a tausashe ya kamo qugunta ya hade da nashi yana duban qwayar idanunta,itama shi take kallo,tana samun kanta cikin wani irin yanayi a duk sanda irin hakan zata faru,tana ji da ganin wani abu na musamamn cikin idanuwansa

“Amma dai na gaya miki,indai kina yin wankanki bakya jirana,zaki dinga wanka biyu ko?” Fuska ta narke masa sannan ta turo masa dan qaramin bakinta

“Uncle saina zauna ka dawo kaga qazantata?” Bin siraram lips dinta daketa qyallin lip gloss yayi da kallo tsigar jikinsa na zubawa,sannan ya dauke ya maidasu cikin manya kuma fararen idanuwanta,har cikin zuciya da ruhinsa yana yaba mata,yadda bata qaunar ya ganta ba wanka,naturally haka take,sometimes kafin ya dawo daga salla tayi wankanta

“Okay,tunda haka ne zaki biya ladan qin jin maganar uncle” bai barta ta samu damar cewa komai ba ya hade bakinsu waje daya ya shiga aika mata da wani zazzafan kiss da ya sanya taji kwanyarta tana yamutsawa,cikin lokaci kadan ya sauke mata wani saqo mai nauyi daya sanya jikinta saki gaba daya,yayin da ilahirin nashi jikin ya dauki rawa gaba daya,kusan ta saba da wannan yanayin nasa,tun tana tsoro harta saba gani,ta saba ganin wannan romance din mai zafi daga wajensa,fice mata a hayyacinsa yakeyi cikin lokaci qalilan,wannan yake rudata itakuma tayita masa kula,kukan da baya samun damar lallashinta sai bayan komai.ya kammala.

Yau dinma daga bata ladar rashin jin magana ya zarme,shi kamsa baisan me yakeyi ba,illa dai zuciyarsa da qwaqwalwarsa yaji sun kasa jurewa,bai kuma barta ba sai daya isa ga muradinsa duniyarsa qarshen farincikinsa.

Tana a jikinsa tana masa ‘yan koke koken data saba,hannunsa cikin sumarta yana yamutsata,idanunsa a rufe,lips dinsa kawai ke motsawa suna fidda sautin wasu kalmomi masu zaqi da kwantar da rai,yayin da zuciyarsa tayi nisa wajen son gano iya matakin matsayin da widad ta tsaya a ransa,ko yaushe yana jin kamar a ranar ya fara saninta,tana da wata irin baiwa da bai taba tsammanin za’a sameta jikin kowacce diya mace ba,a duk sanda ya kasance da ita burinsa na sake kasancewa da ita baya raguwa saidai ya qara hauhawa

“Uncle wayo” ta fada a shagwabe da siririyar muryarta, murmushi ya kubce masa,hakan take yawan gaya masa duk sanda irin hakan ta faru

“Kiyi haquri dani babyn uncle,na jarabtu dake har bansan iyaka ba,am sorry….but I have something special for you,muje muyi wanka ki gani”.

Tare sukayi wankan duk da tana dan zuzzulle masa,suka shirya ta gabatar masa da abinci yaci cikin nutsuwa da kwanciyar rai,best taste for ever a wajensa.

Bayan ya kammala ya jingina bayansa da kujera qafafunsa a miqe harde wajen guda,yatsun hannunsa ma a hade yana dubanta,kamar cin abincinta yadan ragu,tun ranar nan ya gani,amma kuma bai sakashi damuwa sosai ba,ganin bata canza ba,saima murjewa da jikinta yakeyi,hannu ya miqa mata alamun ta taho,saita maqale kafada

“Uncle wayo” ta fada tana dariya,bai shirya ba dole shima dariya ta kubce masa,a baya yakan jima baiyi dariya irin haka ba,amma a yanzu.widad ta maidata abu mai sauqi a wajensa idan yana tare da ita,dukka tsare gida shan kunun nan da kamewa sun koma office da sauran guraren aiki

“Kizl ki karba albishir din naki,ba wayo bane yanzu” matsawa jikin nasa tayi,ya kuwa riqeta gam yana fidda takaddun ya fara mata bayani.

Ruqunqumeshi tayi da kyau cikin farincikin da batasan yawansa ba tana sake tambayarsa

“Uncle da gaske?”

“Na taba yi miki qarya?” Kai ta girgiza

“Baka taba uncle” ta fada hawayen farinciki yana sauko mata,saiya bata fuska kadan

“Kuka?,noo baby,don’t cry mana” ya fada yana janta jikinsa hadi da dan bubbuga bayanta alamun lallashi.

Irin godiyar data dinga masa sai daya ji qwalla ta sauko masa,godiya ce da bai taba jin irinta daga bakin hafsat ba,duk kuwa da ya kaita gurin da yanzun widad din zata je a qalla sau uku kenan,sai ya saka hannuwansa yana sake lullubeta cikin jikinsa da kyau,yana sake jinta tana shiga rayuwarsa da gasken gaske.

A ranar ta dinga kira waya tana shaidawa kowa,ummunta mommynta da abbanta sune farko,sannan uncle muhsin anty madeena anty deena dasu hajja,kowa yaji dadi ya kuma yi farinciki da wannan labari,ya kuma tayata murna qwarai, uncle muhsin ya kirashi yayi masa godiya,kai kawai ya girgiza

“Bakasan wacece widad a wajena bane muhsin,she meant alort to me,bansan ya zan fasalta maka ba” yayi furucin tun daga qasan zuciyarsa.

Murmushin jin dadi uncle muhsin ya saki,amma a fili sai yace

“Easy sir…..surukinka nake fa kaketa fallasamin sirrin zuciyarka” sai suka sanya dariya a tare.

Cikin satin yace ta shirya zasu wuce bauchi,batajin son zuwa bauchin sam,amma tana son ganin hajiya dasu mimi,don ta kwana biyu bata je ba,bata nuna masa komai ba,cikin karsashi ta shirya musu dukka jakankunansu,ta kuma siyawa su mimi da hajia tsaraba,bayan tace ya turo rose ko samuel su kaita kasuwa,sai gashi ya kashe aikinsa da kansa yazo ya kaita ta siya duk abinda takeso,don yanzun ba kasafai yake bari wani ya kaita wani waje ba,idanma ta kama to saidai ya turo mace.

**********Tunda sale ya bude gate din gidan ta gane motarsa ce,amma data fahimci bashi kadai yazo ba saita ci gaba da zamanta saman plastic chair din da take zaune a kai,ta jibge kayan da take siyarwa tana faman lissafi,gefenta su mimi ke wasa kamar ko yaushe futu futu abinsu,kai bakace akwai interlock cikin gidan ba.

Widad dake bacci abinta cikin motar ko shigowarsu cikin gidan bata san dashi ba,ya waiwaya yana mamakin nauyin baccin da takeyi a ‘yan kwanakin nan,fuskarta tayi wani mugun fresh hasken fatarta ya kashe masa idanu,ya daga hannu da nufin tashinta,saidai mimi da nawwara sun rage masa aiki,don tuni suka fara kiran sunanshi suna rige rigen isowa,muryarsu ta sakata bude idanunta a hankali,ta saki murmushi tana kallon yaran har suka iso garesu.

Ita dashi aketa rige rigen tarbarsu,tayi nasarar riqe mimi shi kuma ya dauki nawwara,daga inda hafsat din take kamar zuciyarta zata fado,ta janye idanunta tana jin kamar zuciyarta xata fashe,ta gaji da jiran da anty ummee tace tayi,sai take gani kawai ta soma gajiya da lamuranta,tunda ta nemi aron dubu dari biyu bata bata ba.
[3/20, 8:54 PM] +234 813 343 4840: *H U G U M A*

*_A RUBUCE TAKE_*
(K’addarata)
*Arewabooks:Huguma*

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button