Sponsored Links
Hausa NovelsHausa Novels and Love StoriesZafin Kai Hausa Novel

Zafin Kai 49

Sponsored Links

49
Daqyar sallamarta ta fito daga maqoshinta lokacinda ta shigo tsakiyar gidan sbd tsoron da zuciyarta take ciki.

Duk da ba Wani sosai ta saka tirare ba Amma tsadansa ya sakashi sauya iskan tsakan gidan ahankali da sanyin qamshi hande dake daki bataji sallamar ba qamshin taji iska ya Dan kado mata shi daga waje take ta fito sbd tasan dole baqine suka shigo gidan.

Anne kuwa zaune take tsakar gidan tana Yanke farcenta da wata tsohuwar Reza wadda da benazir dince ta Saba Yanke mata farcen

Har cikin tsakiyan zuciyarta sallamar benazir din ta ratsa sbd take tasan Bena dinta ce Dan haka ahankali ta dago jikinta na sanyi da mutuwa wasu hawaye masu zafi suka ciko idanuwanta dake bushe tana kokarin maidasu kada Benazir ta gani.

Benazir kuwa ganin Annenta kadai tsakar gidan ya sanyata qarasowa da wuri ta nufeta qafafunta na rawa Basu tsaya janye Amnah a tsakaninsu ba Benazir ta rungume mahaifiyarta tana Jin dukkanin qarfin zuciyarta na karyewa.

Hande data fito salati me qarfi ta sake ganin su a Hakan Wanda ya saka Ababa Dayake shirin fitowa fitowan da sauri Yana cewa hande saita kashesa wata Rana da wainnan salatin nata masu daga hankali.

Yana fitowa idanuwansa akan Anne ya fara sauka Saida ya duba dakyau ya tantance Benazir ce
Gyaran murya yayi suka saki juna ahankali suna tsayawa gefen juna kan benazir qasa tana hadiye yawun zuciyarta dake bugawa da karfi.

Da sanyin murya me taushin data fara samu na nutsuwan rayuwar data fara samu ta Bude baki muryarta na Dan rawa ta gaidasa.

Bai amsa ba ya Tako ya qaraso gabansu ya tsaya cikin sake tsuke fuska ya miqa hannu ta miqo masa Amnah dake bacci ya karbeta.

Kallan babyn yake Yana Jin farin cikin  ganinta,
Bai taba kaunar ko nasa ‘yayan ba Amma ita cikin ransa yake jinta sbd ta zama silar arzikinsa da ‘yayansa suka kasa zama sanadin.

Dagowa yayi ya kalli Benazir murya a zafafe ya tambayeta metazo Yi

Shiru tayi kanta a qasa

Cikin zafi ya sake cewa

“Me na fada Miki?
“Babu ziyara matiqar ba nine na buqata zuwan naki ba Kuma ba yanzu zan buqata Hakan ba sai kin zaunu cikin Kaantes kin jiqu yanda ya yakamata,
Annenki zata biya duk Wani hukuncin laifin ki wlh sbd bansan hakuri ko asara ba.

Rufe idanuwanta tayi ahankali kanta na sake Yin qasa hannuwanta na Dan tsananta rawa.

Ahankali ta Bude baki ta sanar dashi Abinda akace tazo dauka makaranta zata.

Gyara tsayuwa yayi cikin Jin Wani lissafin na Hawa Kansa Jin anfara considering dinta as kaante itama tinda aka ware mata mota da drivern kanta.

Hana farin cikin fara samun Abinda yake Neman yayi ya Dan daure murya yace taje ta dauko ta fice daga gidan.

Juyawa tayi qafafunta na Dan rawa da  sanyin jiki ta nufi dakinsu ta shige Anne na bayanta.

Suna shiga ta dakata tareda juyowa ta Kalli Annenta da itama ita take Kallo zuciyarta na wadata da sanyin ganinta tareda farin cikin ganin dd babba ya dauko hanyar inganta rayuwar Bena dinta kaman yanda yayi mata alqawari Dan haka itama zata qara juriya da hakurin kowace irin ukuba da wahalar gidan har lokacin da dd babba zai gama bincikensa akan rasuwar su sumayyah tukuna ya dauki mataki akan Ababan da dalili.

Hannuwanta ta daga ahankali ta zaunar da Anne qasan tsakiyar dakin da tini aka dauke katifar ciki.

Rezan sake hannun Annen ta karba ta durqusa ta Yanke mata duka farcenta cikin kulawa da sauri.

Tana gamawa suka miqe tare Anne da kanta ta dauko mata id card dinta inda yake ta kama hannunta ta saka mata cikin murya Mai bayyanarda jarumta da kauna tace

“Karki sake dawowa Nan ki zauna gidanki kiyi ingantacciyar rayuwa,
Ki nutsu kiyi karatunki ki inganta kanki ki samu Daman Gina taki rayuwar da Zaki samu Daman samun ‘yancinki,
Inshallah zanyi dauriya nayi juriya Zamu tsira da yardar Allah,
A baya Banda qarfin zuciyan fatan rayuwa me nutsuwa Amma a yanzu inadashi sbd ke Bena Dan haka kije na yafe karki dawo Nan din saikin Gina rayuwarki me kyau Allah ya sadaki da dukkanin Alkhairi da farin cikin gidan ki.

Duk Wani gabar jikin benazir Saida yayi sanyi ya sake da maganar Annenta hawaye ya ciko idanuwanta Amma ya kasa saukowa sbd Wani irin sanyin jiki Dana zuciya da zantikan suka sakar mata tare Kuma da qwarin gwiwa.

Sake rungume Annenta batareda ta iya cewa komaiba sbd zasu iya fashewa da kuka su dukan idan ta Bude baki Dan haka ita kadai ta fito Anne tayi zamanta daki.

Hande na daki tana jiran shigowar benazir din dakin har ta fice bata saniba a waje ta tadda Ababa Yana lissafin motar da aka bawa benazir din zata fi miliyan Dari.

Tana fitowa driver ya Bude mata motar ta shige ya rufe.

Ababa da Kansa ya Kwantar da Amnah gefen benazir ya rife kofar motar Yana Jin zuciyarsa fal haske da lissafi.

Suna barin kofar gidan Benazir ta lumshe idanuwanta ahankali hawayen Datake riqewa suka gangaro mata ta Ciro handkerchief me taushi daga Jakarta ta share fuskarta ahankali tana Jin zuciyarta na sanyaya da rabata da mahaifiyarta da Akai Wanda takejin zatayi karatu inshallah tuquri ta inganta rayuwarta ba iya zaman kaantes ba tana buqatan yiwa kanta nata sunan bayan na kaantes Dan samun iKon karban mahaifiyarta,
Zatai karatun da zata Tara arzikin da zata Siya mahaifiyarta daga mahaifinta ko nawa ne inshallah.
Sake share hawayenta tayi tana sauke numfashi Mai zafi da ajiyar zuciya.

Kai tsaye jamia suka Isa hankalinta na kwantawa daga tinanin duk Wanda zai ganta da baby,
Basa muamala da mutane ko a baya Dan haka babu damuwanta ga duk Wanda zai ganta da babynta.

Parking driver yayi Bata Jira ya Bude mata ba ta Bude ta fito rungume da Amnah ta wuce Nafisat na bayanta suka nufi inda zata samo tabbacin komai na hutun da aka dawo su timetable da lectures da Akai da sauransu.

Cikin sa’a yau din sunata lectures in the next 20 min masu zuwa Dan haka taje duba results dinta na last semester data San ba lallai ma taci ko Daya.

A sa’arta taci courses uku ta fadi sauran 5 Dan haka Bata Wani damu ba tinda tasan yanzune zata dage tayi karatun Kaiwa matsayawa.

Da zasu shiga lectures Nafisat ta goyawa Amnah bayan ta Bata Madara Tasha Takoma bacci.

Mota Nafisat suka koma sbd babu inda driver ya tafi Yana Nan saita gama idan dare zata Kai zai Jira tinda aikinsa kawai shikuma na ta ne.

Suna fitowa 12 to 2 kai tsaye mota ta nufo tana Isa wayarta dake jaka kira ya shigo
Cikin Wani irin sanyi ta Ciro wayar sbd bayan Su Anne babu Wanda take magana dashi a wayar.

Sunan Umme tagani ahankali ta sauke ajiyan zuciya sbd wannan shine Karo na farko data fito kaantes tin kaita shiyasa ummen duk ta Dan damu sbd Amnah da Bata fita Rana.

Daukan wayar tayi cikin nutsuwa da sanyin murya tace

“Umme Ina wuni”

Ajiyan zuciya ummen ta sauke daga can bangaren tana cewa

“Bena Yaya makarantan?
Akwai Rana da yawo ko?
Ga Amnah tanata rigima Kila ko?

Ajiyan zuciya Bena ta sauke tana lumshe fararen idanuwanta zuciyarta na na’am da kaunar Umme akansu Dari bisa dari Dan haka tayi kokarin gwada Sakin murmushi me sauti tace

“Amnah a mota na barsu tin dazu Nima yanzu na fito daga lectures din Amma zamu sake shiga 2 zuwa 4.”

Ajiyan zuciya ummen ta saki tana cewa “ok ki kula da kanki da Amnah akwai Rana sosai,saikin dawo.”

Ahankali ta iya Bude bakinta dayayi nauyi sbd mutuwar jikinta ta furta “Nagode Umme Allah ya saka da Alkhairi.”

Murmush kawai ummen tayi tareda kashe wayar daidai shigowan DD palonta Yana amsa wayan Safnah da kusan kullum take kiransa ahankali,ita wannan dake gabansa baimayi noticing nata ba hakama Bai taba tambayar ta ba sbd baisan Tayaya zai fara kulawa ko Neman matan yayansa daya rasu tinda dai Amnah dinsa zai ringa ganin babynsa Hakan ma is ok.

Sallah Bena tayi a mosque na mata
Ta bawa Amnah Madara ta canja mata diaper da kaya zuwa Versace overall marasa nauyi da qamshi kafin suka koma ta shiga lectures suka zauna mota.

Sai 4 har da Rabi suka baro makarantan suka nufi gida.

Suna Isa driver yayi mata Saida safe ta wuce Nafisat na biye da ita gajiye duk da Bata ciki yunwa sbd akwai biscuits da drink da Umme ta sako musu cikin jakar kayan Amnah.

A gajiye suke sbd sabon da suka fara samu daga ita har Nafisat me aikin nata na zama guri Daya cikin hutu.

Babu kowa a palon Dan haka Kai tsaye dakinta ta wuce ta tube ta fada toilet Saida tayiwa Amnah wankan tayi tayo alwala ta fito ta shirya cikin Riga da straight skirt na atampar super wainda kusan duka atampopinta babu qarama bare laces da baa maganar kudadensu.

Sallah tafara Yi kafin ta shirya Amnah cikin guntayen overall blue da safa Mai taushi itama suka fito zuwa dakin Umme Dan gaidata.

Suna zuwa tayi knocking ahankali ta Bude ta shiga ahankali ummen na zaune tana amsa waya cikin nutsuwa.

Tana ganinsu ta sake fuskarta da farin ciki tana miqa hannu ta karbi Amnah din tana ci gaba da wayarta.

Bena kuwa ficewa tayi ta nufi dakin Zeenah batanan Dan haka ta fito ta nufi kitchen acan taci Brown spaghetti da aka dafa Dan ita kawai da yamman.

Sama sama taci ta koshi sbd Sam batada cin abinci sosai hanjinsu sun Dade da tsukewa daga Horan da Akai musu tin tasowansu.

Ruwan sanyi Tasha kadan kafin ta kamawa su Madam beba aikin abincin dasuke Yi na dare.

Tuwon semovita sukai da Miya kala biyu sbd banbancin raayi kowa yaci wadda yakeso.

Ita tayi miyan fresh veggies da Alayyahu sai uban Naman Kazan da babu qashi da nikakken nama
Madam beba kuwa miyan yauqi sukai da kifi da Naman rago.

Suna gamawa Zeenah na dawowa ta Kalli benazir din tana tambayarta me takeyi a kitchen.

Murmush kawai tayi ta sanar da ita Aiki sukai na abinci.

Sallar magrib tayi Bata fito ba sai bayan datai ishai dinta ta miqe ta fito.

Tana saka qafarta tsakiyar palon hancinta ya shaqar mata qamshin Daya sakata dakatawa sbd sanin Yana kusa kokuma Yana cikin palon Dan haka ta silale Takoma daki.

Koda aka Aiko kiranta cin abinci cewa tayi ta Kasho Bata Dade da cin spaghetti ba.

Kyaleta sukai sukaci abincinsu batasan DD baya part din ba shigowa yayi Kuma ya fita da Amnah.

Saida ta tabbatarda sun gama cin abinci ta fito Zeenah ta Rakata gurin dd babba gaidasa da masa godian komawarta makaranta.

Sun shiga Zeenah ko qarasawa batayiba ta juya sbd Kiran Daya shigo wayarta Dan haka ita kadai qafafunta na Dan rawa ta qararasa cikin palon da sallama a natse cikin siririyan muryanta me sanyi kanta a qasa.

Kallan Dawood da Bai dagoba dd babba yafara Yi kafin ya amsa sallamarta tareda Kiran sunanta

“BENAZIR? Qaraso ki zauna kinji.

Sunan da dd babba ya ambata ya saka DD dakatawa daga kallan datakewa Amnah cikin nutsuwa da tsananin kauna Amma Bai dagoba duk da sunan ya tabbatar masa da Mummyn Amnah dince ake nufi.

Itama Bata dago ba bare ta iya kallansu batama San waye da waye a palon ba Dan haka kanta a qasa ta zauna natse kaman yanda dd babba ya umarceta.
##MAMUH#
#LOVE
#HOT
#DBENA
#BABY MAMAH

*_Arewabooks@Mamuhgee_*

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button