Sponsored Links
Hausa NovelsUncle Datti Hausa Novel

Uncle Datti 45-46

Sponsored Links

4️⃣5️⃣—4️⃣6️⃣
Washe gari da safe kamar yanda ta kuddura a ranta hakan kuwa ta kasancewa bayan sun gama breakfast ta nufi d”akin Alhaji ta tarar da iyayen nata maza a ciki, har k’asa ta tsugunna tana gaishe su suka amsa mata kana ta nemi guri a gefe ta zauna tana jiran ya sallame su kafin nan na ta fad’a mishi dalilin zuwan ta d’akin.
Kallon ta yayi yace” ke Aina matso nan ki zauna maganar da kika kawo min ita muke so mu tattauna da iyayen naki.
Ba tare da musu ba ta taso ta zauna a gefen baba K’arami ta kwantar da kai tana kallon kasa lokaci guda tana wasa da yatsun hannun ta.
Alhaji ne yayi gyaran murya kana ya hau kallon  y’ay’an nashi d’aya bayan d’aya,” Aina’u ta zo min da wata magana ni kaina maganar ta tab’a min zuciya, ba wani bukata ta zo min da ita ba illa cewa tayi tana neman a ba wa Datti auren Nana”.
“Whattttt cewar baba Babba kenan a fusace ya dubi Aina da ta d’ago kai ganin sun had’a ido da shi tayi saurin maidawa k’asa tana ci gaba da wasa da yatsun hannun ta.
” Ashe ban san baki da haunkali ba sai yau, ko kad’an baki san ciwon kanki ba….., idan har ma Datti kike nema a ba shi Auren Nana ki sani abunda kike nema ba zaki samu ba sakarai kawai shashasha, ya kare maganar tare da jan tsaki mai k’arfi, har ga Allah ranshi ya matuk’ar baci sosai.
Jikin ta ne yayi matuk’ar sanyi sosai cikin dakiyar zuciya tace” yi hakuri baba ba wai dan na b’ata muku bane ya sa na fad’a hakan, duba nayi da yanda matsalar Datti yake yanzu baba idan ba’a aura mishi ita ba wa kuke tunanin za’a zai aura  yayi zaman aure da ita wacce zai samu nutsuwa da  kwanciyar a tattare da ita?
“Babaaaaa” ta fad’a cikin sanyin murya tare da jan sunan kana ta cigaba da cewa” ba laifin shi kad’ai zaku duba ba lalurar ce kuma na tabbata wasu abubuwan ba yin kanshi bane……., ya yi dan nemar ma kanshi mafita yake yi”.
“Murmushin yake baba babba yayi” Aina lalura bata ce ayi zalunci ba, Dattin nan fa kema ya cutar da ke tunda yayi taraiya da y’ar uwar ki kuma a cikin gidan ki, bayan haka idan aka aura mishi Nana ba’a mata adalci ba”.
“Ehhh haka ne amma ban k’i naku ba amma mafita d’aya ne shine ayi k’ok’arin samo shi daga cikin matsalar da yake ciki idan aka yi hakan hankalin mu zai kwanta shima zai koma kamar ko wani namiji magidanci”.
” Shi kuma Fu’ad d’in da ya taimaka mata yaya kike son ayi da shi?”, sannan kuma idan aka yi mishi haka kina tunanin an kyauta mishi? cewar Alhaji kenan yayin da yake gyara zama.
“Rashin kyautawa ba’a mishi ba amma wani bukatan yana danne wani bukatan, alfarma ne nake nema, kun min auren had’i da Datti kuna sane da matsalar shi amma haka nayi muku biyayya na zauna da shi bil hakki,  ina so ku min alfarmar biyayyar da nayi muku ku aura mishi Nana………, baba nima fa kun cutar da ni da kuka had’a ni aure da wanda ba lafiyayyen namiji ba kuma na zauna da shi…….., idan har nayi muku biyayyar nan ya kamata ku dubi lamarina……..mafita ne nake samar mana baki d’aya ta yanda kowa ba zai cutu ba”.
Shiru suka yi duk jikin su yayi sanyi, baba karami kam rasa abun fad’a yayi cuz bai san ta yanda zai fara ba.
” Shikenan jeki Aina’u”, ta mik’e tayi musu sallama ta tafi.
Bayan fitan ta suka ci gaba da tattaunawa a tsakanin su kowa na kawo nashi dalilai da hujjoji daga k’arshe suka yanke hukuncin su tuntub’e Nana da maganar su ji ta bakin ta.
B’angaren Aina bayan ta bar wajen main patlour ta nufa ta tarar da Nana na zaune a parlour ta jingina kanta da jikin kujerar tanta na kallon sama ta lula duniyar tunani.
Kafad’an ta Aina ta dafa a sanyaye ta k’afa mata ido har ranta tana jin tausayin Nana a ranta” rau-rau tayi da fuska kamar zata yi kuka”Aunty don Allah ki daina zargina wallahi ban yi abunda kuke tsammani ba hasalima ma raping d’ina yayi niyar yi fa”.
“Libs Aina ta cije tana mai jin zafi a ranta, she have no choice than ta sadauk’ar ma y’ar uwar ta mijin ta ko da kuwa zai zama ajalin ta tunda Uncle Datti jikin Nana kad’ai yake so yayi rayuwa da ita”.
” Hakan ne kad’ai zai saka ta cece Datti da Nana daga sharrin fad’awa halaka a k’aro na biyu, sanin kanta ne ko da ace Fu’ad ya aure Nana babu abunda zai canja zani domin hakan ba zai hana Datti ya fasa neman Nanar ba, kenan rayuwar ta yana cikin hatsari babba”.
Idanuwan ta ne suka fara kad’aya suna neman turning read, tana breathing kamar zai yanke tace” Na san abunda zan fad’a zai miki zafi ko kiyi tunanin bana tausaya miki…..wallahi Nana ina matuk’ar tausayin ki hasalima shi ya sa kika ta nayi hakan……..shiru tayi tana kallon Nana cike da fargabar abunda zata fad’a mata, sai taji gaban ta ya fad’i ta hau jujjuyar maganar Auntyn tata a kasan zuciyar ta.
“Nana ki amince ki aure Datti shine kad’ai abunda zai saka na daina zargin ki, idan baki min hakan ba baki da wani hujjan da zaki kare kanki daga zargin da nake miki, bayan haka idan kika bijire ma bukatata zan fad’awa wa su baba su san cewa kina kai kanki ma Datti kuna aikata abunda kuka saba………., saurin toshe kunnuwan ta tayi tare da runtse idanuwan ta cuz bata jin zata iya jure maganganun ta.
Mamaki ne ya cika ta karara, a matsayin ta na y’ar uwar ta bata tausayin ta take cewa ta aure mijin ta……….., ko ta manta ne har yanzu da auren Datti a kanta………., ko tafi son ta faranta ma Dattin fiye da ranta………., a gaskiya Aunty Aina ta jefa ta a tsananin rud’ewa ta jefa ta a ramin da baza ta iya kubuta ba……..yaya take son tayi da Fu’ad wanda yake sonta da gaskiya kuma itama ta koya ma zuciyan ta son shi”.
” A wani matsayi zata karb’e bukatar y’ar uwar ta?
Tana cikin tunanin taji muryar Aina tana magana da kakkausan murya” Idan kika ki bin abunda da na fad’a miki kin san me? ta ja kwafa ta girgiza kai kana ta d’ora da cewa”zumuncin mu da ke har abada babu ita……zan saka almakaci na datse komai.
Da sauri nana ta kafa mata ido tana ruwan hawaye……ganin haka Aina ta sa kai ta bar wajen cikin sauri ta nufi d’akin ta ta fad’a saman wani uncontrollable kuka ya kwace mata ta hau rerawa.
“Anya idan ta had’a Datti da Nana tayi ma kanta adalci kenan? Anya zata iya rayuwa babu Datti? Matsanancin kuka ta fashe da shi tana cewa” why!!! why!!!!! me yasa baka son jikina sai na yar’uwata after all zaman da muka d’eba da kai kana cikin lalura nake rokar maka Allah ya yaye maka ita mu more zaman auren mu?
Ashe dama har abada jikin ka ba zai zama mamora a gare ni ba?
*”JIKIN KA NAKE SO KAI KUMA JIKIN TA KAKE SO?”* ashe ba zan tab’a mallakar jikin ka ba?
Haka ta ci gaba da kukan nata tana surutai kamar zautacciya ita kad’ai.
B’angaren Fu’ad kuwa duk yanda ya so ya cire zargin Nana a zuciyan shi abu yaci tura yana tsananin kishin ta fiye da tsammani, idan ya ganta ko a hanya sai abun ya fad’o mishi a rai yayi ta jin haushin ta gani yake ita ta kaimi kanta dama tuni suke shirya plan d’in su suyi ta abubuwan su.
Cikin lokaci kankani har ya fara rama watarana suna zaune da Kamal yace” me yake faruwa ne two days ina ganin ka cikin damuwa baka da aiki sai na tunanin……kamar wanda aka ce za’a raba ka da amanar ka?
“Doguwar ajiyar zuciya ya ja ya sauke a hankali kana ya d’ago jajayen idanuwan shi ya sauke kan Kamal da shi d’in ma shi yake kallo” Wallahi Kamal auren nan duk ya fitan min a rai…….idan na tuna da abunda Nana tayi min sai na ji na tsane ta……..ka san kuwa Nana Datti take so ba ni ba?
“Whattttt ka san abunda kake fad’a kuwa? Na tabbata kai take so ba shi ba domin kuwa fuskar ta kad’a mutum zai kalla ya gano hakan”.
” Hmmmmm”, ya fad’a cikin kunan rai tare da fuzar da iska mai zafi ya dora da cewa” da nayi tsammanin hakan amma yanzu na gano cewa ba ni d’in take so ba, hasalima taumakon da nake yi mata ne shi yasa take kokarin b’oye son da take mishi dan ta kyautata min.
“Bana tunanin haka Fu’ad domin kuwa na san halin ku d’aya da Nana baku iya b’oye so ba sannan baku iya kin abu ba idan kun tashi yi da zuciyan ku kuke yi”.
” Ina baka shawara ka bi komai a sannu kar ka bari kishi ya rufa maka ido ka tafka kuskuren da zaka yi dana sanin aikata shi.
“Hmmmmm kawai yace daga nan suka kawo hirar duniya suna yi.

B’angaren Datti kammm a nashi b’angaren wani irin dad’i yake ji sosai ya san Fu’ad sarai ya san halin shi mutum ne wanda bai iya saka abu a ranshi ba shi yasa yake jin a ranshi cewa dole Fu’ad d’in zai hakura ya bar mishi Nana.
Da ace ya san zai zo da sai dai ya tarar da shi yana danna mata dick tana k’arb’a ko da abun sab’ulewa zai yi a yayin da yake sexxx da ita sai yayi duk dan kawai Fu’ad yaji haushi.
Kwance yake a saman kujerar da ke parlour ya d’ora Sadeeq a kan faffad’a k’irjin shi yana bubbuga bayan shi a hankali.
Shafa gemun shi yayi tare da  sakin shu’umin murmushi kamar yaron na jin shi yace” mamar ka taki bari ta samar maka kani gashi daddy na so, daddy d’inka na son duminta”.
Mitsi-mitsi da k’afa Sadeeq yake yi yana wasa, Datti ya shafa tafin k’afan shi tare da lumshe ido” yaron na da soft skin irin na uwar shi, gashi yana da kyau sosai, sau tari dad’i yake ji a ranshi a duk sanda ya kalle Sadeeq ko ba komai shima ya ajiye d’a, Sadeeq d’an shi gudan jinin shi kuma yana son shi.
Iska ya hura ma yaron a kunne sai ya lumshe ido yana murmushi dimples din shi suka bayya hakan ya dad’a fiddo mishi da kyaun shi.
“Yanzu duk wannan kyaun na Sadeeq amma ace anyi ma rayuwar shi illah ta hanyar kawo shi duniya ba ta hanyar aure ba?
” Ina ma ace Nana matar shi ce ta sunnah Sadeeq kuma na shege bane da yayi alfahari da shi amma duk da hakan ma zai bashi kulawar da ya kama ta………., shine gatan Sadeeq….., kakanin shi sun raba shi da mahaifiyar shi……ita kuma bata nuna tausayin ta a gare shi ba ta guje shi………
Rungumar yaron yayi so tide a jikin shi yana fidda wani irin numfashi da kyarrr a sakamakon zogin da zuciyar shi ke mishi yana harbawa fatttt fattttt kamar zai fita.
Mugun feelings yaji na neman kama shi da ya tuna irin azabar da yake sha a duk sanda ya tuna ta, dan gudun kar ya b’aro ma kanshi aiki yayi saurin kawar da ranshi yana mai tursasa wa zuciyar shi cusa wani tunani da na da ban.
Da taimakon Allah yaji abun ya fita a ran shi dick d’in shi ma ta daina azalzalar shi da son shigan ramin Nana da ya haka dai-dai da shigan shi.
Da taimakon Allah ya samu ya fara jin nutsuwa na shigar shi har ya dawo cikin hayyacin shi sai ya ji da shi cikin wandon shi yayi murmushi kawai cuz ya san sperm ya fitar ko ba komai ya rage ruwa.
Lokaci na dad’a tafiya biki na dad’a matsowa yau ta kama saura kwana biyu a d’aura aure, duk yanda su Umma suka so su hana Datti shigowa gidan abu ya fasakara, ya gigice ya d’aga musu hankali ba zai tab’a bari Nana ta aure Fu’ad ba shi ya fara sanin ta kuma shi zai aure ta……, Aina ma ta dage akan a taimaka a ba ma Datti Nana su samar musu da mafita.
Suma a nasu b’angaren abubuwa sun cunkud’e musu ba su san wa zasu bada auren ba su hana wani…….idan suka ba ma Datti Nana sun yi butulci ma Fu’ad, idan suka ba ma Fu’ad Nana sun cutar da Datti da ta zam magani a gare shi.
Duk yanda Umma ta kai ga jin zafin Datti zuciyar ta ya karaya sosai…..idan ya shigo yana tisiye su a gaba da kuka wani sa’in har kwalla take fitarwa da tana da ikon yaye mishi lalurar da tuni ta yi domin ta sama mishi lafiya.”
Kamar yanda su baba babba suka yanke shawarar tun-tubar ta suji  daga bakin ta hakan kuwa aka yi suka kira family meeting ciki harda Datti,suka tambaye ta tsakanin Fu’ad da Datti wa take so a aurar mata.
Rasa abun fad’a tayi bata san sanda ta fashe  da kuka ba har ta matuk’ar basu tausayi sosai, ganin yanda take ta aikin kuka kamar zata amayo da hanjin cikin ta cike da tausayawa Alhaji yace” Nana kar ki sake ki cutar da kanki…….ki fito ki fad’a mana gaskiya ba za mu tursasa miki ba wanda kike so shi zamu baki”.
“D’ago idanuwan ta tayi wanda suka cika da hawaye zata yi magana kenan suka had’a ido Aunty Aina ta ga tana gargad’in ta da ido cewa karta manta da maganar su ta kwanakin baya sai tunanin maganar ya fad’o mata a rai…….kenan idan ta zab’e Fu’ad ta yanke zumunci da y’ar uwar ta tilo?
Bata jin zata iya fifita namiji akan y’ar uwar ta kuma bata jin zata iya furta k’armar k’i ma Fu’ad ta butulce ma shi.
” Uncle Datti jikin ta yake so wanda shine ya zam magani a gare ta, Fu’ad masoyin ta ne na hakika wa zata Lab’a a tsakanin su?
Shin zata amince da bukatar y’ar uwar ta ne ta butulce ma masoyin ta ko kuma zata zab’a masoyin ta ne akan bukatar y’ar uwar ta?
Kawar da kai tayi tana kallon Aunty Aina ta ga tana gargad’in ta da ido cewa karta manta da maganar su ta kwanakin baya.
Saurin d’auke kanta tayi ta ga Fu’ad shima ya tsare ta da ido a matuk’ar tsorace yana kallon ta da ido……., a tare zuciyoyin su suka fara harbawa da k’arfi, sai taji numfashin ta na neman d’aukewa tayi saurin d’auke idanuwan ta daga gare shi tana mai jin tsananin zafi na ratsa zuciyar ta………, Datti ta kalla wanda yayi ma Sadeeq masauki da cinyar shi yana barci sun rame mata sosai fun fita a hayyacin su hakan ya tabbatar mata cewa shi kan shi Sadeeq yana tsananin bukatarta a kusa da shi, hakan yana nufin Datti a matsayin mutum biyu yake a gare ta shi kuma Fu’ad mutum d’aya. To wa zata zab’a?
Matsancin kuka ne ya kwace tana jin zuciyar ta na mata zafi yana tafarfasa kamar tururin wuta.
Ganin haka baba babba ya gyara murya ya kalle y’ay’an shi d’aya bayan d’aya duk sun matuk’ar bashi tausayi sosai amma sai ya dake yace” Cikin ku akwai wanda zai iya hak’ura ya bar ma d’an uwan shi?
“Baba na fishi bukatar Nana ba don ni ba ko dan Sadeeq ba zai taso cikin tsana da kyara ba muddin ta zamo mata ta”.
” K’arya yake baba ni nafi dacewa da Nana ni na san zafin ta da darajar ta ba shi ba, Nana rayuwa ta ce ba iya jikin ta kad’ai nake so ba……., Fu’ad ya fad’a yayin da wadu silent tears na rolling a saman fuskar shi.
“Muryar Alhaji suka ji yana cewa” shikenan ku tashi ku tafi mun baku kwana d’aya idan kun gama yanke hukunci sai ku fad’a mana idan kuma har lokacin kuna nan akan bakan ku sai mu san abun da zamu yi”.
Da haka taro ya watse ko wannen su na cikin tashin hankali.
Datti da Fu’ad tun a hanya suke jefa ma junan su maganganu kamar yanda suka saba,,
Yauma haka Datti yake ce ma Fu’ad” Nana hannun shi ce shi ya bud’e ramin ta shi yafi ko wani namiji sanin darajar ta”.
Fitowan Nana kenan ita da Mardiya suka ji yana fad’a, tayi ta matso hawaye mai uban d’umi maganar yayi mata zafi sosai, ina ma ace Datti bai tab’a sanin ta ba balle yayi gadarar shi ya k’arb’a budurcin ta, gani tayi Fu’ad”  yayi Murmushin tare da zira hannun shi a aljihun wandon shi yace” A kullum ina godiya ma Allah da ban kasance mai cin amana ba……ban zamo sanadiyar lalata tarbiyar yarinya ba balle na ajiye abunda har abada zai dinga damuna.
Rassss taji gaban ta ya fad’i ko kad’an bata ji dad’in abunda ya fad’a ba…..Sadeeq d’anta ne dole taji zafin goranta mishi asalin da yayi amma da ta tuno abunda Datti ya fad’a mishi sai ta d’auki hakan a matsayin ramawa yayi shima.
Wannan k’almar da Fu’ad ya fad’a sai ya zamanto weak point na Datti, ma’ana ya ajiye shege kenan shima ya rama maganar da ya cab’a mishi………., fuuuuu ya tashi kamar zai dake shi Fu’ad ya jacking d’in shi dukan su suna huci kamar zasu had’iye juna d’anye, Sadeeq kam har ya tsorata ya fara kuka ganin haka Nana ta shigo tsakanin su da gudu ta tsaya” ku kashe ni kawai ku huta nima na huta da rikicin duniyar da nake fuskan ta.
“Me yasa a kullum nice tsilar zama matsala a tsakanin ku………to she bakin ta tayi a sakamakon gunjin kukan da taji ya zo bata, sai duk jikin su yayi sanyi suka saki juna suna kallon ta cikin wani irin yanayi.
“Magana Fu’ad yayi cikin wata dishashshiyar murya” Nana tsananin kishin ki da nake yi shi ya sanya bana son wani namiji ya rab’e ki hatta d’an uwana……ban tab’a tsammanin a lokacin ina tsananin k’aunar ki ba sai daga baya naji zuciyana na bijiro min da son ki kamar zai fasa k’irjina……., idan zaki lura a da ina nuna miki tsana sosai wallahi tsabar son ki ne yake d’awainiya da ni kuma na fahimci cewa Datti ma na son ki, sai dai na kasa fassara ko wani irin so yake miki kasancewar Aunty Aina a matsayin matar shi……
“Karya yake wallahi ni ke son ki da gaskiya tun kina tsumma har kika girma na raine ki da soyayya na a zuciyar ki…….bak’ar k’addara ne ya sa na cutar da ke cuz duk da cewar na san ke ce kad’ai maganina amma babu yanda banyi ba na cire sha’awar ki a raina amma na kasa.
” Na tabbata duk namijin da ya tsinci kan shi a halin da nake ciki sai ya aikata fiye da abunda na aikata…….
Shiru suka yi suna kallon ta ko wannen su na hawaye……….., Mardiya ce tayi k’arfin halin janta suka shige d’aki tana jin kukan Sadeeq amma ta kasa kwacewa daga rikon da tayi mata balle ta kawo mishi d’auki…….., suna isowa Mardiya ta datsa ma kofar key ta dukusa da gwiwan ta ta rushe da kuka” kiyi ma Allah ko yi ma Annabi ki zaba wanda kike karki so a tsakanin su, kar ki bari gabar su na baya ya dawo sabuwa……kar kiyi sanadiyan dasa gaba mai tsanani a zuciyoyin su”.
“Itama Nana kukan take sosai kamar ranta zai fita” wayyo Allah Mardiya ina zan jefa kaina na samu Sa’eedan radad’in da nake ji…….ban san wanda zan zab’a ba……..ban san wanda zan d’,auka na bar wani ba……..
Ita kuka Muardiya kuka aka rasa mai lallashin d’an uwan shi, da kyat suka tsagaita kukan daga nan Mardiya tayi mata sallama ta koma b’angaren Umman ta.
Bayan fitan ta ne Fu’ad ya ritsa Nana a gaba yana cewa” me yasa bats fad’a ma su alhaji cewa shi take so shine zab’in ta? Anya kuwa ta na son shi? Ta mishi adalci da zata k’i bayyana ma mutane cewa shine zab’in ta? Shi hawayen ita hawayen har ya kare surutan shi ya fita ya koma d’aki yana jin pains a k’ahon zuciyan shi.
Da daddare kusan kwana zaune mutanen gidan suka yi musamman mutane ukun nan.
Washe gari kuwa iyayen nasu suka sake k’iran meeting bayan an gama hallara baba babba yace ya maganar su ta jiya ta kwana? Shin an samu wanda zai yi sacrifice ya janye ma d’an uwan shi?
Duka su biyun suka yi shiru ganin haka sai iyayen nasu suka fahimci dai cewa kowa na kan bakan shi na auren ta.
Kan kace me sai gasu sun had’a zufa tafffff hatta tsohuwa ma bini-bini take sharar hawaye tace” ja’irai kawai kun jefa mu cikin damuwa wallahi ko barci bama iyawa……..da ku mayuwa kuna kama mutum tuni zaku cinye shi., tana yi tana sharar kwalla.
Alhaji ne yayi gyaran murya sai da ya natsa kafin nan ya dubi Nana da ta sadda kanta ta kasa d’agawa tana wasa da yatsun hannun ta, da zaka binciki kasan zuciyar ta damuwa ne yayi mata yawa shi ya sa ta yin hakan.
B’angaren ki fa akwai wa da kika zab’a ko kuma har yanzu babu mafita?
Sai ta girgiza mishi kai alamar a’a babu”.
Numfashi ya ja mai nauyin gaske ya sauk’e a hankali sai yayi jimmm kad’an yana nazari can kuma yace” Tunda dukan an rasa wanda zai sadaukar ma d’an uwan shi, kema Nana kin ki zab’ar wanda kike so ina so ki bani zab’i kuma ina fata duk wanda na zabar miki zaki aminta da shi.
Mugun bugu zuciyoyin su su ukun suka yi a tare ko wanne na tsoron kar d’an uwan shi za’a bawa a hana shi.
Kai ta gyad’a mishi tare da sharo hawayen alamar ta amince.
“Shikenan ku tashi ku tafi, Datti da Fu’ad ina so duk wanda ya rasa ya d’auki komai a matsayin k’addara Allah zai yi mishi zab’i da mafi alkhairi……., ba wai dan mun fi son wanda muka zabar mata bane ya sa muka yi hakan dukan ku matsayin ku guda ne baza mu so wani mu k’i wani ba, ko Datti da kwanaki muka yi maka hukunci dan mu natsar da kai muka yi ba wai dan mun ki ka ba dan haka duk sunan da kuka ji an ambata a wajen d’aurin auren d’ayan ku yayi hak’uri”.
Ba dan ransu ya so ba suka fita suna tunanin anya zasu d’auki k’addarar rashin ta kuwa?
Daren ranar ya kasance rana mafi muni a gare su gaba ki d’aya family d’in cuz ranar ta zamar musu cike da fargaba, tsananin rud’ani…., rikici mai tsananin gaske….. tsarkakiya……ranar da kowa zuciyar shi ke cike tsoron tunkarar wucewan ta.
Da ace Datti da Fu’ad na da ikon hana wucewan wannan dare da sun jima da yi saboda tsoron abunda za su bud’e ido su tarar da  shi.
Washe gari da safe mutanne har sun fara hallara a cikin gidan ana shirye-shiryen d’aurin aure…….Fu’ad tun kafin gari ya gama wayewa ya shiga d’akin Nana ya ta ita a a kwance cikin bargo duk eyes d’in ta sunyi luhu-luhu sun dafe alamar taci kuka sosai d’in nan har zazzab’i ya fara kama ta.
K’amshin turaren shi taji ta bud’e ido a hankali ta zabura ta mik’e da saurin” Ya Fu’ad na shiga uku za’a aura min miji ban san ko wanene aka zabar min ba…….., kaine mafita a lokacin da duhu ya bayyana a gare ni kaine kake yaye min…….., kaine Ammintacce na mai tsamo ni a cikin dukka wani bala’in da ya kunno min kaiiiiii,
Kamar yanda ka zamar min Amintaccen nan na baya wanda ya cece ni, ya taimaka min da iyakacin iyawar shi…….don Allah ya Fu’ad ka zamar min Amintacce a yanzu ka fidda ni daga cikin matsalar da nake ciki………,ina tsananin fargabar wanda za’a bani a matsayin mijina.
Runtse idanuwa yayi ya bud’e a hankali har ranshi yake jin kukan nata na ratsa shi………muryar shi na cracking yace” kiyi hak’iri na zo muyi bankwana ne……., ki sani ba lallai ne na dawwama a matsayin Amintacce ki ba……….wannan k’aron abu ya juya salo yanzu bani da k’arfin da zan baki kariya…….kiyi hakuri da duk zab’in da kika ga an miki har abada ba zan daina son ki ba……….yana gama fad’a ya mik’e ya fita yana sharar kwalla, tana ji tana gani Fu’ad ya tafi, tafiyan da ta san ba lallai ne su had’u a matsayin masoya ba…….
Fu’ad na barin ta d’akin shi nufa ya d’auko car key d’in shi ya fito ya ya kashe wayan shi saboda kar ma a kira shi balle yaji abunda zai d’aga mishi hankali haka ya bar gidan cuz ba zai jure ganin an d’aura auren Nana da wani ba balle ace akaita gidan wani ba, gudu yake ta zafgawa a titin kamar zai tashi sama duk inda ya gifta a motan sai ya bad’a wa mutane k’ura…….., da haka har ya kawo wajen da yake so ya je ya nemi guri a gefen  titi ya parking ya fito ya zauna a saman motar shi, yayin da sanyin huturun da ke kad’awa a hankali ya ratsa jikin shi.
“Yanzu Nana ba lallai ne ta zamu nashi ba? ” Idan ya rasa ta ya zai yi da rayuwan shi bayan ya d’auki son duniya ya d’ora mata?
“Shi dai ya cire rai da samun Nana domin ya tabbata ba lallai ne a bashi ba.
B’angaren Datti ma tun safe ya d’auki Sadeeq suka bar gidan ya kashe wayan shi, Usman yayi mishi fad’a sosai da hakan ya tursasa shi lallai lallai sai sun tafi amma sai ya k’afe yace babu inda zai je, haka Usman ya halacci gurin d’aurin aure yana ma abokin nashi fatan samun nasara.
Gudun kar Usman d’in yaje ya jiyo mishi mugun abu yayi zumburrr mik’e ya d’au d’an shi suka bar gidan ba tare da kowa ya san inda suke ba……ya saka Sadeeq a gaba yana kuka wi-wi da hawayen shi yana surutai kala-kala” mamanar ka zata yi mana nisan da har abada baza mu cimma ta ba……., shi kenan mun yi loosing d’in ta”.
“Nana ta zame min magani amma kaddara ta k’i had’a mu ban san ko sai na koma ga mahaliccina ba kafin nan mu had’u a matsayin ma’aurata da ita. Haka yaci gaba da kukan shi yaron na kallon shi kamar zai taya uban kuka.
Mutanen gida sai faman k’iran layin su ake yi dukkkk a kashe, tun ana saka ran ganin su abu yaci tura har mutane suka gaji da zaman jira wani aminin Alhaji ya lek’a  me ake jira ba’a fito ba an shanya mutane a waje, a sannan ne suka fiffiito aka fara gudanar da daurin aure.
Kamal da Usman sun yi cirko cirko ko wannen shi na so abokin shi ne jarumin da zai mallake Nana sai aikin harara suke sakar ma junan kamar idanuwan su zai tsiyayo, kowannen su sai shan k’amshi yake a matsayin shi na abokin ango suna cika suna batsewa kamar y’ay’an sarakuna.
Ana cikin haka Alhaji ya tarar da su yake tambayar su ko sun san inda abokan nasu suke, Usman yace Datti na gidan shi yayi yayi da shi ya fito su tafi amma ya k’i yayin da shi kuma Kamal yace tun d’azu yake k’iran layin Fu’ad baya shiga.
Alhajin yace yace suje da baba babba su tusa k’eyan shi ya zo gurin d’aurin auren nan, baza su iya da sakarcin su ace ana sure a gidan su dukan su sunk’i hakarta?
Babu b’ata lokaci suka tafi ga mamakin su basu tarar da shi a gidan ba haka suka dawo suka fad’a ma Alhaji.
Cikin narasa aka d’aura har aka gama mutane suka fara neman ango domin su taya shi murna ba ango, sai su Alhaji ne suke ta bada hannu ana musabaha har jama’a suka watsewa.
Gida suka shige su Umma suka hau tambayar da wa aka d’aura baba Karami ya fad’a musu……..,fatan Allah ya sanya alkhairi suka musu, Alhaji yace kar ayi saurin fad’a musu maganar auren tunda har yanzu babu ango, bayan hakan ba su san wani hali zata k’arb’a zab’in na su ba.”
Hakan kuwa aka yi har aka gama budurin buki dare nayi aka d’auki amarya aka kaita gidan ta da ke unguwar Federal lowcost, tamfatsetsen gida ne wanda Alhaji ya gida a sirrance shine aka kai amarya ciki aka yi mata jera rasssss gidan yayi kayatu sosai, daga nan aka barta daga ita sai Mardiya.
Tun Mardiya na ra ran ganin ango har ta gaji ta mata sallama zata tafi Nana take tambayar ta da wa aka d’aura auren tace itama bata sani ba su baba basu fad’a mata ba.
Shiru tayi har Mardiya ta tafi ta barta kana ta koma tayi lamo a ranta tana fargabar had’a ido da wanda zata gani a matsayin mijin ta wanda zata yi rayuwar aure da shi, to ko ma waye ta d’auki zaman ta da shi a matsayin k’addara cuz iyayen ta baza su tab’a zabar mata abunda zai cutar da ita, kuka taji ya zo mata ba ta hau sheshshek’awa……….

*eedatou*

 

*💫SHINNING STARS WRITERS ASSOCIATION*

“`The more we shine bright the more we educate and enlighten our readers.“`

https://m.facebook.com/110896360504039/photos/a.110896457170696/110898470503828/?type=3&source=45

🍇🍇🍇 *UNCLE DATTI*🍇🍇🍇.
“`JIKINA YAKE SO!“`

©
*eedatou✍🏻*
“`Follow and ✅ote me on Wattpad“`: *eedatou*

~Today na today, yaune ranar losers da winners wanda aka kada jarumin shi yayi hak’uri kamar yanda na fad’a haka na tsara littafina tun daga farko har k’arshe…..ku rungumi komai yanda yake……., tsarin labari na da rubutu na ne ya zo da hakan~

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button