Sponsored Links
Hausa NovelsMy Little Sister

My Little Sister 1-2

Sponsored Links

Page 1&2

 

_____________Wani kyakkyawan matashin saurayine dabaze wuce shekaru 27 ba aduniya kwance yake akan makeken gadonsa Yana bacci cikin kwanciyar hankali duk yakanannad’e jikinshi da blanket daganin yadda yake baccin kasan cewa hankalinshi kwance yakeyinsa Kuma bakaramin dad’in baccin yakejiba,,,asukwane tashigo d’akin tana famar surfa uban ihu tareda fad’awa kan bed d’in tana fad’ar wayyo Allah na sweet bro katashi bera ad’akin ado megadi wayyyo tashi kaganta,,, Y’ar k’aramar yarinya ce keta wannan uban ihu tana tana tada wannan saurayin.

Cikin bacci yabud’e Dara daran udanuwansa Yana watsa matasu hakan yasa taja baya dasauri tana sauka tareda rik’e bakinta da duka hannayenta biyu tana waro Ido domin Sam ita batayi tinanin bedroom d’in big bro d’insu ne tashigoba tad’auka bedroom d’in sweet bro d’inta ne wato sultan.

Shiko kallanta kawai yakeyi ko kiftawa Babu yakasa cemata komai,,,cikin tsoro Takoma dabaya tareda kwasa aguje tafita Aiko bakin k’ofar fita part d’in nasu taci karoda sultan d’in cikin sauri yatarota ganin tana gudu jikinta se rawa takeyi.

“Ke lpy my sweet sis Miyake faruwane kidawaye? Yatambaya Yana d’aukarta dudda cewa tawuce d’auka Amma sultan kamar jinjira hakan yake jinta,,,akunne tace bedroom d’in big bro naje natadashi daga bacci nad’auka Kaine domin banduba d’akin da kyauba.

Dariya sosai sultan yayi kamun yace yy miki kyau kinje kinjawo magana Kuma kinajin tsoro kindai San waye big bro too inkika jawa kanki duka ruwanki,,,aa ma baze dakeniba tafad’a cikin shagwab’a kamun tace sweet bro bera ne ad’akin ado megadi zumoje kaganta katuwa mukoreta karta shigo mana

“To shikenan muje mugantato,,hanyar fita daga part d’in suka nufa yanadaukeda ita suna saukowa sukaga anty asabe aperlo tana shara cikin sauri tace anty asabe kihad’amun sobo kafin mukori b’eta,,,to shikenan autar mom za,ahad’a.

Ad’akin ado megadi kuwa ba b’era bace irin k’aton burgunnanne Wanda yakusa girman kaza wani gidan akakoroshi yafad’a d’akin ado megadi Kuma yarasa hanyar fita shiyasa yake ta hauka ad’akin shikanshi ado megadi yakashiga domin damutin yashiga zasu fara Dara dashi,,,,suna zuwa Basu tsaya komaiba suka fad’a d’akin cikin sauri tamayarda k’ofar tarufe gamm Aiko burgu najin k’arar rofe kofa yashiga gudun neman ceto,,,Ido sultan yawaro ganin abunda sweet sis d’inshi kekirada b’era kamun yayi wani yunk’urin tuni burgun yayi kansu danneman hanya hakan yasa suka saki ihu atare suma suka shiga tsere dashi uhu sukeyi burgun nakarayi cikinsu..ganin hakan yasa ado megadi kwasa aguje yanufi cikin gidan Yana gayawa mom da fitowarta kenan daga kitchen taji wannan shirmen zatayi magana kenan wannan saurayin yafito cikin sauri tace “yawwa *AHZAD* Dan Allah kujeda ado waigasu sultan da *HUZDA* burgu yarutsasu.

“Cikin sweet voice d’inshi yace “mom wani irin burgu Kuma Shi sultand’inne keyiwa burgu wannan shirmen? “Ah to kaimadai kafad’a kuje Dan Allah Ni kad’aukomun autata karta firgita shiko shiyasani,,,bek’ara cewa komaiba suka nufi d’akin ado d’in Koda sukaje suka bud’e k’ofar tuni HUZDA tasuma sultan kuwa yasamu yadoke buegun aka dawani sandar k’arfe dayagani ad’akin da kyar bayan sunci uwar danbe domin yayi Masa cizo ukku biyu ak’afa d’aya ahannu dukkansu ukku agalabaice yasamesu,,cikin ko inkula yasa hannu yad’auke HUZDA kana yakwadawa sultan harara yafice,,,cikin k’arfin hali yatashi yabi bayanshi suka koma cikin gidan shiko ado megadi yad’aure bakin burgun yafitada can karshen layi yabawa almajirai.

Yana shiga mom dake zaune tataso tana fad’ar subahanallah miyasameta ne? Shidai bece Mata komaiba yanufi bedroom d’inta da HUZDA yakwantarda ita se alokacin yad’ago Jin mom Bata tambayar sa Wai Mike faruwa ne domin taga sultan d’in ma yashigo ahargitse.

,,Sumane tayi fa mom inaga tatsoratane,,Yana gama fad’ar hakan bejira cewartaba yanufi bedroom d’inshi cikin k’ank’anin lokaci yadawo da kayanahi na aiki atake yashiga Bata temakon gaggawa cikin sa,a kuwa tafarka tana ihun fad’ar b’era ze cinyeta wayyo Allah sweet brooo,,cikin sauri mom tace “ke ya,Isa autan dady kinji Babu wani b’era yayanki yakoreshi,,,se alokacin tayi shuru tana k’walalo Ido tareda kallon AHZAD dake yiwa sultan d’in dressing fuska amurtuk’e,,,shiko ko kallon inda take beyiba Sund’an jima ahakan kamun tazabura kamar wadda aka tsikara tana fad’ar anty azabeeeee Ina sobonaa? Tafad’a tareda kwasa aguje tabar d’akin,, murmushi mom da sultan sukayi suna fad’ar auta kayan Allah,,shiko AHZAD kamar ma besan abunda akeyiba,

Tana fita perlon tacikaroda anty asabe takawo Mata sobon cikeda cup,,takarb’a tana murmushin tareda d’auko cake d’aya Akan dining tajuya zata koma bedroom d’in mom cikin saurinta tana tafe tana Shan abunta batama kallon gabanta bazataso ba tsammani kawai taji tayi kaurada mutin gabaki d’aya sobon hannunta yawanke mishi jiki duka fararen kayansa sunyi fyanti,,,Ido HUZDA tawaro tana Jada baya cikin tsoro da fargabar abunda ze biyi baya..!

 

Daga alk’alamin Autar alheri ✍️

Yanzu akafara kabcen kowayaya Kuma wannan salon zetafi🤔

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button