Sponsored Links
Hausa NovelsKurkukun Kaddara Hausa Novel

Kurkukun Kaddara 48-49

Sponsored Links

*💋KURKUKUN ƘADDARA💋*

*Daga alƙalamin Boss Bature✍️*

*Dedicated to Aunty kubra❤*

*Gargarɗi!!!*

_Ban amince wani ko wata ya yi amfani da wani sashe na book din nan ba ta kowace siga, ko a karanta mini shi a Youtube, ba tare da an nemi izni a wurina ba. Ko a haɗa mini document, idan kunne ya ji jiki ya tsira, ko da Allah na bar mutun zai bi mini haƙƙina!_

E48-49 free pages

💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫

*_ALBISHINKU MATAN AFRICA DA KEWAYE, SHAHARARRA KUMA K’ASAITACIYAR MAI SAIDA KAYAN MATAN NAN WATO DR MAMAN YUSUF LIKITAR MATA SOKOTO TANA FARINCIKIN SANAR DAKU CEWA ZAKU IYA SAMUN KAYANTA ADUK INDA KUKE A FADIN NIGERIA DA NIGER HARMA DA WASU K’ASASHEN BAKI DAYA, KU SANI A DADE ANAYI SAI GASKIYA KUMA MACE MAI GYARA KANTA BATA BORANCI , INA MARABA DA MASU SIYAN DAYA KO SARI_* .http://wa.me/+2347069711327

*_munada zafafan kaya kamar haka ,_*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻

*Hadin amarya budurwa ko zawara*

*Hadin uwar gida Mai taken (Maida tsohuwa yarinya)*

*Maijego package (virgin gain)* 📦

*Hadin sabon budurci ga yarinyar data rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar da namiji*

*Sahihin maganin sanyi na Maza Dana Mata Wanda yake fatattakar sanyi cikin Dan lokaci*

*Maganin gyaran nono Wanda zai gyara maki nononki cikin Dan lokaci komai lalacewarsa*

*Maganin hips Wanda zaisa shape dinki ya fita kiyi kyau kema ki shiga jerin Mata masu aji*

*Maganin kiba Wanda zaisa ki ciko kiyi kiba yar dai dai misali kema adinga binki da kallo Idan kin juya Sam rama batayi ba yar uwa*

*Hadin mallaka ba boka ba malam , akwai taimakon da muke bayarwa ga Mai butsarin namiji Wanda cikin ruwan sanyi Zaki dinga juya abunki , haka akwai Hadi na musamman Wanda komai rowar namiji sai kin samu alkhairin a wajanshi,*

*Muna da kalolin gumbuna masu Saka ni’ima sha’awa da dandano*
*Kalolin garrika mash gyara gaban mace da jimawa ajiki*
*Kalolin Zuma masu saukar da ni’ima Nan take da gamsar da maigida*
*Kalolin tsumi Wanda cikin sauki zasu Baki ni’ima da dandano irin wadda akeso*
*Kalolin matsi Wanda suke ciko da gaban mace matse gaban mace da bata Wani irin dadi da dadano*
*Akwai set kala kala Wanda yawansh ya wuce na zayyanasu anan ga Mai bukatar kayana zata iya mun magana Kai tsaye ta hanyar danna wannan blue rubutun* 👉🏻 http://wa.me/+2347069711327

*Muna dahuwar zabo ,dahuwar kaza ,dahuwar kifi ,dahuwar zuciya ,dahuwar Yan shila ,dahuwar tsoka Tara ,dahuwar Kwan mallaka, dambun nama ko na kaza Wanda yake saukar da ni’ima da jimawa sosai ajikin mace*

*Idan nace zan rubuta komai da komai to wannan page din ba zai isheni ba ,Amma ga masu sha’awar siyan kayana Zaku iya mun magana Kai tsaye ta wannan number, haka masu sha’awa su dinga ganin kalolin kayana a status sumin magana ta wannan number sai nayi seving numbers dinki ta hakan ne Zaku dinga ganin kalolin kayana idan na daura*
http://wa.me/+2347069711327

*Ina maraba da Mai siyan Daya ko sari Dr maman Yusuf likitar mata sokoto*

*❤❤❤PRISONERS❤❤❤*

 

 

Ruwan na sauka saman fuskarta, awani irin firgice ta farfaɗo ta zabura zata miƙe, ga6o6in jikinta suka ƙi bata haɗin kai, wani irin raɗaɗin azaba taji a jikin ta, ba arziƙi Ta koma ta kwanta, Cikin shessheƙar ku ka take ambaton sunan daddynta bakomai idanuwanta su ke hango mata ba face waɗannan halittun da ta gani suna cuzgar naman Jikin daddayn, abun ya tsaya mata aranta, daƙyar ma sautin muryar ke fita saboda raunatar da la66anta suka yi, ga maƙoshinta dake abushe ƙamas tana cikin buƙatar ruwan sha, jikinta sai kerma yakeyi, a hankali danish ya ajiye bottle water ɗin daga ƙasa gadon, rumfa ya yi mata da ƙirjinshi yana jiran ta ƙarasa dawowa cikin hayyacinta, yana ganin ta fara ƙoƙarin buɗe idanuwanta, ya yi saurin sanya tafin hannun shi ya toshe mata ƙaramin bakinta, saboda gudun tsiwarta, yasan muddin ta haɗa ido dashi sai ta zazzaga mishi masifa, jin hannun mutun saman fuskarta yasa ta ƙara firgita, da ƙarfi ta buɗe idanuwanta tana faman zazzare su, launin gray ɗinsu ya ciza, eye lashes ɗin sun cukurkuɗe Cikin juna, kaitsaye eye balls ɗinta suka sauka akan fuskar danish, biji biji take iya ganin shi,

Muryarshi na ɗan rawa ya fara yi mata magana

“Angel…..ki natsu ba ki da ƙoshin lafiya” a dabarbarce yayi maganar ganin irin kallon da take watsa mishi, wanda ke nuni da tsantsar ƙiyayyarshi da take ji,
Sassauta muryar shi yai batare da ya zame tafin hannun shi daga saman fuskarta ba, yaci gaba da cewa”Nasan yanzu bani da sauran mutunci a wurin ki, kin gaya mini cewa kin tsane ni, baki son gani na, Angel Ni mai laifi ne a wurinki, duk yadda xanyi maki bayani ba lallai ne ki fahimce ni ba, Amma bazan takura maki ba, idan har da akwai abunda za ki yi mini wanda zaisa ki huce haushinki a kaina, Ni na amince ki yi mini shi, amma kada kice xaki ƙaurace mini, zuciyata zata iya bugawa……..” bai kai ga ƙarasa yin maganar ba, Sakamakon damƙar hannun shi da angel tayi, Cikin fushi ta janye shi daga saman bakinta, batare da ta tanka mishi ba, da yasan yadda take jin tsanar shi a halin yanzu da bai wahalar da kanshi ba wurin neman yafiya agare ta, ji take kamar ta shaƙe wuyanshi ta jijjiga shi ta buga kanshi jikin bango har sai ya sheƙe tukunna ta ƙyale shi, Ba don Allah yasa jikin nata ba isasshen lafiyace dashi ba, da ba abunda zai hana yau ta Illata shi,

Tuni yasha jinin jikinshi, domin kuwa yana ji a jikin shi irin tsanar shi da take Ji, wasu irin zafafan hawaye ne suka cika idanuwan shi, muryar shi tamkar zai fashe da kuka yace”Ki bani dama ta ƙarshe xan gyara kuskure na,” lumshe idanuwanta ta yi, Yayin da maƙoshinta ke motsi tamkar tana haɗiyar wani abu, sam bata jin zata Iya tanka mishi gani take kamar in yaji muryarta zai ji sanyi acikin zuciyarshi, that’s the reason why taƙi yi mishi magana, tafi son Yaji a jikin shi irin halin da ya jefasu, har abada baxata ta6a mantawa da abunda ya faru Jiya ba, duk irin alƙawarin da ta ɗaukar wa batul akan zata taimaki rayuwarta, bazata ta6a bari a cutar da ita ba. Yanzu ya tashi abanza kenan? taya hankalin ta zai kwanta? Bayan batasan awani hali batool take aciki ba, tana can hannun waɗannan azzaluman mutanan da deeja ta bata labarin ta gansu akanta, suna Cutar da rayuwarta, Sai ta dinga imagining ga batul can itama sun danneta tana ta kuka tana buge buge.

Lokaci ɗaya angel ta fashe da kuka mai sautin gaske, Hankalin danish ya tashi matuƙa, duk yabi ya ruɗe, yana so ya lallashe ta, Sai dai yana jin shakkar ta6ata,

“Am sorry angel….ni ne silar komai, pls stop crying it’s hurting my heart, bazan juri ganin ki, cikin wannan Yanayin ba……” Wani irin matsiyacin kallo ta jefa mishi, idanuwanta sunyi jawur gwanin ban tsoro, dama tunda ta farfaɗo daga suman da ta yi fuskarta take a kumbure, cheeks ɗinta sunyi ja, La66anta sunyi luhu luhu ,

Duk da irin kallon da take wurga mishi hakan baisa shi ya dakata da yin maganar shi ba,

“Angel, nima bada son raina ba, Na miƙa batul ba, bana tunanin akwai wanda yakai ni ƙaunarta acikin ku, Batul tamkar jinin dake yawo ajikina take, Na rayu da ita tun ban mallaki hankali ba, mun shaƙu da juna, kusan komai atare da ita muke yi, a duk lokacin da lalurata ta tashi ta rashin son hayaniya, ita ce take jana ajikinta, ta rungume ni har sai taji na samu natsuwa tukunna take saki na, Meyasa ba zaku fahimce ni ba? Ku yi tunani mana, Ni har raina zan iya sadaukarwa akanta….” daƙyar ya ƙarasa magnar tare da kifa kanshi saman katifar gadonta, da alama kuka yake yi,

Gaba ɗayan su kuka suke yi babu mai lallashin wani acikin su, duk wannan budurin da ake yi ƴan uwansu dake ta sharar bacci babu wanda Ya motsa acikinsu, kamar matattu, idan har ba danish Yaje ya tashe su ba, zaiyi wuya su farka da kansu, In ba wani iko na Allah ba, saboda baccin nasu bana Allah da annabi bane, shi kaɗai yasan mai ya yi musu da har suka kama yin shi, duk da yai hakan ne don ya kawar musu da damuwar dake acikin zuciyarsu,

a hankali ya ɗago da kanshi daga saman mattress ɗin, idanuwanshi sunyi jawur dasu, launinsu ya ciza sosai, fuskarshi tayi jawur da ita, Cikin sanyin murya yace”dame xanji? Idan har kuka juya mini baya zan shiga damuwa, Ni bazan hana Ku tsane ni ba, idan ma takama ku buge ni son ranku, but please don’t say that you’ll cutt me off from u, abun zaiyi mini yawa, ga rashin batool ga kuma rashin ƴan uwana,”

Tun da ya soma yin maganar, ta tsagaita da yin kukan idanuwanta na fuskantar ceilling, Haƙiƙa kalaman danish sun kashe mata jiki, sun so suyi tasiri akanta, Sai dai a duk lokacin da ta tuna da irin yadda ya damƙo hannun batul Ya rabata da ita, Yaje ya miƙa ma Giant, Sai ta ji tsanarshi Ta ƙara ninkuwa acikin zuciyarta,

Ɗauke eyes ɗinta tayi daga kallon ceilling da take Yi, ta tsayar dasu akan fuskarshi, bakomai take gani ba acikin idanuwanshi face tsantsar nadama.

Sun ɗauki tsawon lokaci suna kallon juna batare da wani daga Cikin su Ya ƙyafta idanuwan shi ba, Kowa Da abunda zuciyarshi take raya mishi, ganin ta fara motsa la66anta alamar za ta yi magana, sai yaji sanyi acikin ranshi, yayi tsammanin zata yafe mishi ne, amma sai yaji tace”inaso ka yi mini alƙawari…” a ƙagare yake kallonta cike da son jin wani alƙawari ne takeso Ya ɗaukar mata, Don a shirye yake daya bi umarninta.

Muryarta adisashe taci gaba da cewa”idan ka yi mini wannan alƙawarin zanyi farin Ciki, kuma zan tabbatar da cewa Kai ɗin mai ƙaunata ne,” aɗan ruɗe yake kallonta, shi dai fatan shi Kada tasa yayi mata alƙawarin da ba zai Iya cika mata shi ba.

Calmly ya furta”Ki faɗa mini menene kike son in ɗaukar miki alƙawari akanshi? Girgixa kai ta ɗanyi, Still hawaye na bin kuncin tace”Ka fara ɗaukar alƙawarin kafin na faɗa maka akan menene”

Hawaye wasu nabin wasu akan fuskarshi Yace”I can’t, saboda nasan ba alkhairi xaki faɗa mini ba,” Saukowa yai daga saman gadonta, Ya zuƙunna saman gwiwowinsa, a ƙoƙarinsa naya nemi yafiyarta, don shi har ga Allah baison tayi fushi dashi, Yana matuƙar Jin ƙaunar angel acikin zuciyarshi,

“Nasan idan nace ka dawo mini da batool bazaka Iya ba, Haka zalika idan nace Ka faɗa mini wanene kai? Still amsa ɗaya zaka bani shi ne baka sani ba, kaga kuwa baka da amfanin da zaka Iya mini….” bai bari ta karasa maganar ba, yai saurin katse mata hanzarinta da cewa”I know bani da amfani awurinki, amma ki tuna abunda ya faru jiya, may be kin manta, ni ne naje na ceci rayuwarki, na faɗa miki ne badan Ina tunƙaho da hakan ba, sai dan kisan cewa ni ɗin mai ƙaunarki ne kuma ina da amfani awurinki,” awahalce yai maganar, daga shi har ita babu mai ƙoshin lafiya acikinsu, Daƙyar suke magana kamar anyi musu dole, kayan jikinsu ba ƙaramin tsami suke yi ba, hada ƙarnin jininta da yai bleeding jiya,

Fuskarta a yamutse tace”danish, ban damu da duk wani abu da zaka faɗa mini ba, alƙawarin da nake so ka ɗaukar mini shi ne, Ka nesanta kan ka dani! Ras! Yaji gabanshi ya faɗi, tun kafin ma yaji ƙarshen xancen nata, Ya soma girgiza kai alamar bazai Iya ba,

“Bana son ka ƙara kusanto ni, balle ma har kayi tunanin zuwa wurina, koda gigin wasa kada ka kuskura ka bari mu haɗa ido da juna, ya zamar maka dole ka janye jikinka daga nawa, idan har kana son zaman lafiya acikin kurkukun nan…….”

Bawan Allah ya rasa ina zai tsoma ranshi yaji dadi, ya riga dayasan Halinta, tana da wuyar sha’ani, ga kafiya idan ta furta magana zai yi wuya ta canza ta, duk da wani lokacin tana da saurin sauka idan tayi fushi sai dai wannan karan babu sassauci akan fuskarta,

“Har tsawon wani lokaci kike so in janye jikina daga naki”? Idanuwanshi cike tab da kwalla yayi mata maganar,”

“Har zuwa lokacin da za’a dawo da batool, Idan tace ta yafe maka shikenan nima zan yafe maka mu cigaba da yin rayuwar mu kamar yarda muka saba, idan kuma har ba’a dawo da ita ba, hmmmmm…..” ta ambaci hakan saboda tagaza idasa maganar, sai faman taunar la66anta take yi, har sun ɗan ƙara fashewa dama abushe suke.

Ba ta yi tsammanin zai ɗaukar mata alƙawarin ba, sai ji tayi yace”I promised u angel, bazan sake koda kallon ki ba, ballantana har inyi miki magana, Inaso in tabbatar maki da cewa ni mai ƙaunarki ne, Kuma inason farin Cikin ki,…….” dakatawa ya ɗanyi da yin maganar, yana bin fuskarta da kallo, tun yanzu ya fara jin kewarta a tare da shi, wahalallan murmushi ya sakar mata har dimples ɗinshi suka lotsa sosai, da sauri ta kawar da fuskarta gefe ɗaya, saboda wani irin shock da taji, Kyanshi na ƙoƙarin jan hankalinta, idan har taci gaba da kallonshi zata fara danasanin janye jiki dashi,

“Angel zan tafi, Amma kafin nan, ina neman alfarma a wurinki, ina fata zaki yi mini abunda nakeso a ƙaro na karshe, Muryarta ƙasa ƙasa tace”menene”?

“Ki kula mini da kanki, sannan an kawo mana breakfast ɗin mu, kada damuwa ta sanya ki gaza cin abinci nasan kina jin yunwa, ki samu wanda zai taimaka miki acikinsu wurin yin tafiya saboda ƙafafuwanki sun raunata sosai, ba zaki Iya taka su ba, bayan haka Jiya na same ki acikin mawuyacin hali kina ambaton sunan daddynki, zai iya yiyuwa kinyi ƴan gane gane da suka shafi mahaifinki, wanda ba gaskiya bane, inaso ki kwantar da hankalin ki, akan wannan, after that, akwai taimakon da zan Iya yi maki, ta yadda zaki gane cewa, mahaifinki da batool awani hali suke ciki, idan har kin amince mini zan nuna maki,” wani irin kallo angel take binshi dashi na rainin wayau, sai kace wani malamin duba, da alama yana ƙoƙarin yi mata wasa da hankaline,

“Nasan zaiyi wuya ki yarda dani, but pls Ki bani dama”muryarshi ce ta katse mata zancen zucinta da take Yi, shiru ta ɗanyi tana was wasin kalaman shi acikin zuciyarta, kafin ta ɗan yamutsa fuska tace”its ok, ka nuna mini ta wace hanya zan iya gane a wani hali suke Ciki,”

Ba ƙaramin daɗi yaji ba, da sauri ya Juya mata bayan shi tare da cewa”Ki hau in goya ki,” fuskarta a ɗaure tace”Ina zaka kaini”? Ya bata amsa da cewa”Cikin toilet ɗin mu,” ba don taso ba, ta yunƙura daƙyar ta miƙe xaune tana faman cizon la66anta, ta sanya hannayenta biyu ta ruƙoshi, Ta hau saman bayan shi, ya miƙe ya nufi sashen toilet ɗinsu ɗauke da ita a bayan shi, Sam bata lura da sabbin gadajen da aka kawo musu acikin ɗakinsu ba, Saboda ta lumshe idanuwanta, yayin da yake wucewa da ita cikin toilet ɗin, Bayan ya shiga cikin makewayin nasu, wanda keda glass window ɗin nan, Yayi mamakin ganin Kayan amfanin da aka zuba musu sababbi acikin toilet ɗin su, An gyara shi tsaf komai a tsaftace, An ajiye musu trash can mai girma, Daga can sama Jikin bango inda cabinet dinsu Yake, Care product ne a jere tun daga kan hair gel, shower gel, conditioner, komai ma aka tarkata musu hada Toothbrushes da aka ajiye musu acikin holder dinsu, tare da toothpaste, Kuma kowani product yana ɗauke da sunan kurkukun ƙaddara, hakan na nufin ma’aikatan Prison ɗinne suka haɗa su, Ya yi farin Cikin ganin sabbin kayan amfanin da aka sanya musu acikin toilet, ta wani 6angaren kuma sam Bai ji sun kwanta mishi a ranshi ba, tun da ba dawwama zasu yi cikin farin ba,

Jin yaƙi cigaba da tafiya yasa ta ɗan ɗago da kanta daga saman kafaɗar shi, Ta cunkuli fatar cikinshi da hannunta, Har saida ya ɗan ciji la66ansa saboda zafin daya ji, Muryarta a kausasace tace”Idan ba zaka nuna mini ba, ka sauke ni in koma ɗaki,” Muryarshi a sanyaye ya furta mata am sorry, Taja tsoki, tafiya yaci gaba da yi cikin toilet ɗin ya nufi ƙatuwar tukunyar fulawar nan dake a killace Jikin bango, Anan ya ɗan zuƙunna ya sauke Angel, ta xauna a ƙasa tana faman lumshe idanuwanta, ta ko’ina raɗaɗi take ji ajikinta, sai lokacin ta lura da sabbin kayan dake a cikin toilet dinsu, da mamaki akan fuskarta take binsu da kallon ƙurulla, Sai ta dinga gani kamar ba gaskiya idanuwanta suke nuna mata ba,

“Lokacin da kuna bacci, Giants suka shigo da su, hada new metal beds da boxes guda biyu, ina expecting din sabbin prisoners xa’a kawo mana” Danish ne ya kora mata bayani, Ganin yadda take bin ko’ina na toilet din da kallo yasan dole ta buƙaci jin daga ina aka same su,

Ko kaɗan bata yi farin Ciki da ganinsu ba, Ita fa a halin yanzu komai na kurkukun ta tsane shi, abu ɗaya ne idan aka daina Yi musu xata so shi harma ta haƙura ta rungumi ƙaddararta, su cigaba da yin rayuwarsu Har Illah masha Allahu, shine a daina ɗaukar ƴan uwansu ana lalata rayuwarsu, sai dai tasan abune mai wuya, wannan dalilin ne ma yasa zata cigaba da neman hanyar da zata ku6utar dasu, domin kuwa babu fashi, Shiga Cikin kurkuku yanzu ta fara, Babu gudu babu ja da baya! ba’a halicce ta don ta zama raguwa ba, ita ɗin Jinin jarumai ce, masu dakakkiyar zuciya, waɗanda suka Yi imani da Allah batare da was wasi ba! duk da abunda ya faru da ita jiya, hakan baisa zuciyarta ta karaya ba, Sai ma taji kamar ana ƙara encouraging ɗinta akan taci gaba da bibiyarsu, a mutu ko ae rai, Kuma taci alwashin daga rana irin ta yau bazata ƙara sakin baki tayi bacci ba, Zata dinga raba dare biyu, kodan ta dinga kai kukanta wurin Allah, akan halin da suke aciki da kuma ƴar uwarsu batool!……..” Ya jima yana kallonta ganin yadda numfashinta ke fita, ta ciccije la66anta, bakomai yajawo hakan ba face zancen zucin da take Yi, daga cikin zuciyarta,

“Angel!!” Firgigit tayi Jin muryarshi acikin kunnuwanta, wani irin kallo ta jefa mishi, da sauri yace”Ki ɗan jira ni, Yanzu xan dawo” Bata amsa mishi ba, dama bai sanya ran zata tanka mishi ba, don ya lura yau mulki take ji.

Miƙewa Yayi da sauri Ya juya ya fuce daga Cikin toilet ɗin, badajimawa ba sai gashi Ya shigo ciki hannun shi ruƙe da robar ruwan daya yayyafa mata afuskarta ɗazu Cikin ɗaki, Bin shi da kallo tayi har ya ƙarasa gaban fanfo. ya zuƙunna Ya kunna shi, ruwa ya shiga kwararowa ya tarba robar, saida taci ka tukunna ya miƙe da azama ya dawo inda take zaune jikin bango, Ya zuƙunna agaban tukunyar fulawar,

ya ɗan saci kallonta ta wutsiyar idanuwanshi, harara yaga tana jefa mishi, ƙayataccen murmushi ya saki tare da cewa”Idanuwanki basu gajiya da yin harara”? Murguɗa mashi ƙaramin bakinta ta yi, tana faman hura hanci tace

“Bai shafe ka ba” Yace “its ok am sorry, abunda zan nuna maki ayanzu, sharaɗin shine, Koda ace zuciyarki ta ƙaryata hakan to kada ki amince just ki yarda kawai da duk wani abu da zan faɗi batare da kokwanto ba,” bata amsa mishi ba, sai ma ta juya mishi ƙeya,

Bai damu ba, yaci gaba da cewa”yanzu inaso ki rufe idanuwanki”, rai a6ace tace”saboda me xan rufe idanuwana”? Yatsina fuska yayi don tafara hayaƙa shi da tsiwarta,

“Kiyi kawai abunda nace miki, asannu zaki fahimce ni” Sai da taja guntun tsoki mai sauti, kafin ta runtse idanuwa nta, tana faman murga baki,

Bai san ya akai ya tsinci kanshi da kallon kyakkyawar fuskarta ba, sai yaga tafi yi mishi kyau a haka, duk da raunin dake akan fuskarta, sai ma suka ƙara mata kyau especially heart shaped lips ɗinta da suke abushe sun faffashe, kamar ta shafa musu jan baki pink, bakomai ya ƙara ƙawata fuskarta ba face gashin jagirarta masu tsayi dark brown dasu.

Jin shiru Danish baice ta buɗe idanuwanta ba, yasa ta harzuƙa ta yunƙuro zata wage baki ta zazzaga mishi masifa, Yai saurin cewa”Saura kaɗan” ajiyar zuciya ta ɗan sauke Cikin ƙagara da son jin me zai ce next,

“Ki buɗe idanuwanki a hankali,” mutsu mutsu ta soma yi cikin wani irin yanayi ta ɗan waresu ta ƙara buɗesu kafin ta zarosu tana ƙarewa tukunyar fulawar kallo, abun mamaki abun al’ajabi, yauƙanannun fulawowin dake acikinta waɗanda sun jima da bushewa duk sun yagalgale sun lafe cikin ƙasar dake acikinta, ɗaya daga Cikinsu tagani ta miƙe ta bubbuɗe ganyayyakin jikinta sun wawware tayi matuƙar ɗaukar hankalinta, musamman launin Jikinta Ja da ya ciza, tsabar mamaki ya hana ta rufe bakinta, Idan ta kalli furan sai kuma ta kalli fuskar Danish,

Har dai tagaza jurewa tace”taya akai kayi hakan? Kamar a mafarki,”

“Ba shi yakamata ki tambayeni ba, wannan furen da kika gani ki ɗauka cewa ran mutun ne mai numfashi a jikin shi ” Ya ƙarasa maganar tare dakai hannu ya shafa ganyen shi tare da cewa”Batool ɗinki ce, Our lovely sister, idan kika kalli furan da kyau, zaki ga yana da cikakkiyar lafiya ajikinshi, Launin shi ya ciza, hakan na nufin batul aduk inda take a yanzu tana acikin ƙoshin lafiya, Idan kuma ki gaka ganyen jikin furan Yana fitar da ruwa kamar zufa batare da an yayyafa mashi ruwa ba, that mean batool kuka take yi tana kewan ƴan uwanta, idan kuma ganyen ya kwanta jikin ƙasar dake acikin fulawar, to batool bacci take yi……..” tunda ya soma kora bata jawabi, take kallonshi babu wasa a fuskarshi, Yadda kasan irin malamin duban nan, sai da yakai ƙarshen maganarshi tukunna tace”to idan furan ya mutu fa me hakan yake nufi? Maimakon ya bata amsa sai ya sadda kanshi ƙasa, tuni ta gane me hakan ke nufi wato mamallakin furan ya mutu kenan,

“Baka amsa mini tambayata ba,” ɗagowa yai da kanshi ya ɗaura idanuwanshi akan fuskarta yace”idan ganyen dake ajikin furan Ya bushe ƙamas Ya tsotse ko ya fiffige, Hakan yana nufin mamallakinsa yana acikin mawuyacin hali, Idan kuma ganyen furan ya mutu, ko ansa mishi ruwa bazai tashi ba, ma’anar hakan mamallakinsa ya mutu baya araye” duk da bata gasgata maganarshi ba, amma sai da taji gabanta ya faɗi ras, muryarta na ɗan rawa tace”Shi…shi fa daddyna? Ina nashi furan yake? Taya za’ae in iya gane cewa yana a raye ko ya mutu?” aruɗe take jera mashi tambayoyin,

Kwantar mata da hankali yayi, “Ki natsu yanzu xan duba maki na daddyn ki amma kafin nan Kiyi mini alƙawarin cewa komai ki ka gani ba zaki yi kuka ba, idan kuma muka yi nasarar ganin furan daddynki Cikin ƙoshin lafiya, zaki bani abinci abaki. Nima in baki, a karo na ƙarshe kafin mu ƙauracewa juna,”

da yake a ƙagare take da son gani, da sauri tace mashi eh ta amince, yace to ta rufe idanuwanta, Bayan ta rufe su, Na ɗan wani lokaci, Yace ta buɗesu a hankali, Kamar wata sakarya haka take bin umarninshi, tunkafin ta ƙarasa buɗe idanuwanta ta soma hango fure Launin Kore, a gaggauce ta zare eyes ɗinta akan furan har zata fara Farin ciki sai kuma ta lura da naƙasar dake a ƙasan furen ya ɗan lanƙwashe alamar ba lafiya atattare da shi.

Wasu irin zafafan hawayene suka wanke fuskarta, Har wani zazza6i taji ajikinta, muryarta adabarbarce take faɗin” Danish Ya mutu ko? Naga ganyen kamar ya karye, Dan Allah ka faɗa mini, zuciyata zata Iya bugawa….” tsananin tausayinta ne ya kama shi ganin yadda tabi ta ruɗe, bakomai yake tunani ba face Iyayen shi, Shi da bai rayu dasu ba, kuma ba shi da tabbacin Suna araye ko sun mutu, shin dagaske sune suka sadaukar dashi? Anya kuwa shima yana da iyaye kamar kowa? A lokacin baya kafin zuwan angel bai ta6a tunanin wasu iyaye ba, gani suke Yi kamar tsohuwa itace komai na rayuwarsu, zuwan angel ne yasa suka fara tunanin suma ina iyayen su suke? Idan tana basu labarin irin ƙaunar da daddynta yake yi mata sai suji inama ace suma sunyi rayuwa da nasu Iyayen………”

Sautin kukan angel daya ƙaru ne yasa shi Barin yin zancen zucin nashi ya ɗago ya kalleta, ta wage baki sai kuka take Yi, baisan time daya saki murmushi ba, bai ta6a ganin ƙuruciyarta ba sai yau, da ta gasgata abunda shi kanshi baida tabbaci akanshi, kawai yana nuna mata ne don ya samu ya kwantar mata da hankalinta,

Ahankali ya sanya hannayenshi biyu Ya tallabo fuskarta, Yana ƙare mata kallo, hawaye ta ko’ina, Cikin sanyin murya yace”kin manta bayanin da nayi maki? Idan har furan bai bushe ba ko ya fiffige ya mutu, to mamallakinsa yana araye,” Cikin shessheƙar kuka tace”Am…amma ae ya naƙasa, kai ba ka ga Ciwo a jikin iccen shi ba” Da lumsassun idanuwanshi ya ɗan kalli furan kafin yace”na gani, sai dai ba hakan yana nufin mamallakinsa ya mutu ba, sai dai ko karyewa ƙafarshi tayi sakamakon wani rauni daya ji, ko kuma wani ciwonne na daban ya same shi a ƙafar shi, kinji ma’anar raunin dake ajikin furen” hannu tasa tana share hawayenta hankalinta har ya ɗan kwanta,

“Kuma Allah idan har na gane cewa ƙarya kake Yi mini, to ka sani har bada babu ni babu kai, kuma kullum xan dinga zuwa ina duba furennin ina basu ruwa akai akai. Kodan kada su mutu, hakan kuma ba yana nufin na yarda da maganganun ka bane kawai dai zanyi amfani dasu ne” ƙiris ya rage ya saki dariya, jin wautarta, Ta wani 6angaren kuma yaji daɗi sosai, koba komai yasanyata farin Ciki, ya kuma bata aikin yi, duk da shima yana jin fargabar ranar da zata gane cewa ƙarya yake yi mata,

Taso ta tambaye shi furan aunty aneelerh kodan tasan awani hali take aciki, amma sai ta fasa don ta gaji da zama Acikin toilet ɗin, Gashi tana buƙatar Yin wanka sai dai tasan bazata Iya ba saboda ga6o6in jikinta dake yi mata ciwo,

“Muje mu ci abinci, Ko xaki yi wanka in taimaka maki”? Sakin baki tayi tana kallon shi jin abunda yace,

“Yanzu idan nace ka taimaka min inyi wanka? Kuma saika amince”? Fuskarta a ɗaure tayi mishi maganar, baisan sadda ya furta”ae naga komai jiya so ba wani abu bane, nima ae kin ta6a gani na naked, bai kamata ki damu ba, har wankan ma sai mu yi atare,”

ras taji gabanta Ya faɗi, Ta zazzare gray eyes dinta tana kallonshi, Da sauri ya sanya tafin hannayenshi biyu ya toshe kunnuwanshi, saboda gudun tsiwar da zatayi mashi, shi kanshi baisan Ya furta maganar ba, su6ul da baka yai,

sosai ta runtse idanuwanta, tana ƙoƙarin tariyo abunda ya faru jiya, saboda lokacin data dura tagar nan, batasan cewa Ya zame wandon jikinta ba, Ita dai kawai tasan ta dura ta miƙi hanya, sai yanzu da ya yi wannan maganar ya tuna mata da komai, aikuwa ta daddage ta fasa wata irin gigitacciyar ƙara, Jikinshi ya kama rawa, saboda sautin daya fita hatta masu bacci na Cikin ɗaki saida suka farka, Kusan atare suka yaye bargunansu, agaggauce suka dudduro daga saman gadajensu, da gudun gaske suka nufi sashen toilets dinsu hada masu Yin tuntu6e garin sauri, Haris ne agaba su Hanna na abiye dashi, kamar wasu sabbin mahaukata haka suka faɗo Cikin toilet ɗin, Gaba ɗayansu ne suka shugo ciki, Sai faman haki suke yi, a matuƙar ruɗe suke kallon angel da danish, ta runtse idanuwanta jikinta har wani jijjiga yake yi kamar mai iskokai, muryarsu da alamun baccin bai ishe su ba, suka shiga tambayarsu lafiya, azeeza tuni ta nufi angel ita da parveen suka zukunna suna shafa fuskarta tare da tambayarta lafiya meya faru da ita? Meyasa take kuka, Hanna dasu rubina suka karasa suma suka zuƙunna agabanta, Mazan da suka rage a tsaye sai aika mishi da harara suke Yi, gani suke kamar wani mugun abun yayi mata, dama tun Juya suke zargin shine yayi mata bugun tsiya da har ta raunata,

Haris yana huci yace”wato saboda kaga muna bacci shine ka ɗaukota daga saman gadonta ka kawo ta cikin toilet ka naɗe hannun rigarka ka nannausheta saboda bugun da ka yi mata jiya bai ishe ka ba, Wai danish me kake so ka zama ne? Slowly Ya xame hands dinshi daga saman ears ɗin shi daya toshe, hawaye ne kwance acikin fararen idanuwanshi, Tsawar angel tayi matuƙar ta6a kanshi ta tsokano mishi da lalurarshi, shiyasa jikinshi ya kama kakarwa,

Javed yace”Ae bazai ta6a buɗe baki ya bamu amsa ba, mugu kawai, yanzu xamu ji komai abakinta tunda ta farfaɗo, serious idan har tace kaine ka dake ta, zaka ji a jikinka ne,”

Mubeen dai bai ce komai ba, Ya jingina bayanshi Jikin bango yana kallonsu, Gaba ɗayansu babu wanda Ya lura da sabbin kayan da aka sanya musu acikin toilet ɗinsu, saboda hankalin su ba a kwance yake ba,

Su Deeja sai faman lallashinta suke Yi, Ganin yadda take ta kuka, Tana faɗin Wlh ka cuce ni, Na tsane ka Danish, ashe kai ɗan iska ne ban sani ba, Allah ya isa bazan ta6a yafe maka ba, tun da ka gane min budurci na…..” muryarta ashaƙe ta ƙarasa maganar, ita kanta batasan menene ma’anar budurci ba, tadai san kalmar acikin kanta, azeeza ta janyota ajikinta ta rungumeta tare da zagayo da hannayenta saman bayanta, tana ɗan bubbugashi, Hankalinsu Haris yai matukar tashi jin abunda tace har suna haɗa baki wurin maimaita kalmar budurci, basu ta6a ji ba sai abakinta, Amma sai suka ɗauka cewa wurin bugunta ne Ya ta6a wani organ na jikinta, Shi take kira da budurci, nan fa suka harzuƙu, Naufal Ya shaƙo wuyan rigar Danish Ya ɗago dashi Yana huci yace”ka faɗa mana uban me kayi mata? Taya akai ka gane mata budurcinta? Saboda baƙin hali irin naka”! bawan Allah ya rasa ya zaiyi, hayaniyar su ba ƙaramin tafasa zuciyarshi take yi ba, Ga wani irin zafi da jikinshi ya ɗauka, haris ne ya lura da yadda yake lumshe idanuwanshi, Da sauri ya ƙarasa gabansu Ya ruƙo hannun naufal ya janye shi daga jikinshi, wani irin jiri ne ya kwashi danish Ya tafi xai faɗi ƙasa sai dai bai kaiga ƙarasawa ba, haris Ya tallaboshi da hannu biyu, ya ruƙo shi zuwa saman jikinshi, Ya rungume shi sosai, yana ambaton sunanshi, duk da ƙarnin Jinin da ke a jikinshi hakan baisa haris Ya guji ta6a shi ba, kallonsu mubben yai tare da cewa”Pls ku taimaka mini, mu kai shi daki” Turo baki Javed, Naufal kuma ya juya mishi ƙeya, mubeen Ya ɗaga kai ya kalli ceilling ɗin toilet, alamar bazasu ta6a shi ba,

“Ka bani mamaki haris, Kafi kowa nuna 6acin rai akan abunda Danish yayi mana, amma sai gashi yanzu nema ka ke yi ka taimake shi” Rai a6ace naufal yai maganar,

Fuskar haris ɗauke da matsananciyar damuwa yace”bazan iya jure ganin shi acikin mawuyacin hali ba, Shi ɗan uwanmu ne, tabbas yayi mana kuskure amma abunda nake so ku fahimta, koda ace danish Bai miƙa ma giant batool ba, to xasu ɗaukota ne da kansu, don su tafi da ita, baida za6ine,”

Sunyi mamakin canzawar da haris yai lokaci ɗaya, duk dan sunsan irin ƙaunar dake a tsakanin shi da Danish, dole yaji tausayin shi a halin dayake ciki,

Ganin sunƙi taimaka shi yasa shi yin fushi, Yaja danish shi kaɗai ya shiga dashi cikin ɗaki ya kwantar dashi saman gadon shi, idonshi biyu sai dai jikin nashi ne ba ƙwari,

Shigowa cikin ɗakin Hanna da deeja su kayi angel tana a goye bayan hannah, Ta rurruƙeta da hannu biyu. A saman gadonta hanna ta kwantar da ita, sai faman sauke ajiyar zuciya take yi, a can ƙasan zuciyarta wani irin ƙunci ne ya cunkushe mata, danish yaga tsiraicinta, Babu sauran kwanciyar hankali, yanzu shikenan zai dinga ganinta tsirara koda ace da kaya ajikinta, tuna wannan yasa ta ƙara fashewa da wani sabon kukan, gaba ɗaya hankalinsu Ya dawo kanta, baiwar Allah bakinta duk ciwo amma ahaka take riskar kuka,

“Dan Allah angel ki daina kuka, Kiyi haƙuri, Ki faɗa mana me danish yayi maki? Hibbe ce tai mata magana, duk sun shiga damuwa, Azeeza tace”ina matuƙar jin tausayin angel, taji jiki ba kaɗan ba, danish bai kyauta mana ba Allah,” Kowa yana tofa albarkacin bakinsa, danish dai duk yana sauraronsu ya lumshe idanuwanshi yayin da hannayen shi biyu ya rungume pillow dasu,

sai da Angel ta gama shan kukanta mai isarta, tukunna tace musu ita fa bashi bane Yayi silar halin da tashiga ba, hasalima taimakon ta yayi a jiyan nan, a dole ta ƙirƙiro ƙarya ta fada musu cewa, Ta fita hayyacinta ne Saboda ɗauke batool da akayi shine ta fada toilet ta ɗauki bokitin nan na ƙarfe ta bubbuge jikinta dashi, da ta galabaita shine ta faɗi ta sume cikin toilet ɗin, ta faɗa musu hakan ne badan tana so ta kare shi ba, face don ta kwantar musu da hankalinsu,

Gaba ɗaya sunyi amanna da abunda ta fada musu, har suka ɗanyi danasanin maganganun da suka gaya mishi duk da haushin sa da suke ji, Duk wannan abunda dake faruwa babu wanda ya ankara da sabbin gadajen da aka sanya musu acikin dakinsu, Har sai da suka fara Jin yunwa, Parveen tana hamma tare da kai hannu ta shafa cikinta ta soma ambaton Yunwa take ji,

Tana rufe baki Danish yace “An kawo mana breakfast tun ɗazu da safe, time da kuna bacci,” batare daya buɗe idanuwanshi ba, yayi maganar,

Atare suka Juya baya don suka ga In dagaske ne an kawo musu abinci, duk da sun cewa danish baya ƙarya…..

*Idan Allah yakaimu na Kammala Free pages of Takun farko, zan ɗauki hutu, kafin acigaba da middle step,Ga masu son cigaba da Karanta Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne kacal, Labarin yanzu nake Cikin rubuta shi babu Complete sai dai ka biya asanyaka agroup inda zaka dinga samun update akai akai, Inka biya za’ayi adding naka a paid group kuma za’a sanyaka a comment section, Sa’annan Ba’a share Ko yin forwarding duk wanda yayi gigin fitar da littafin, akwai ta inda zamu ga sunan shi da alamar yayi forwarding to zamu cire shi a group ne👌 Kuma yaja ma kanshi zamu ɗauki mataki👌*

*Littafin Kurkukun ƙaddara 3 part ne, Yanzu muna gab da ending na Takun farko free kenan, Sai kuma Takun tsakiya wanda ya kasance na kuɗi ne, da takun karshe duk akan 500 zaku karanta shi*

*Ga wanda ya shirya Yin payment, ga details nan, Idan ka tura kuɗin zaka bamu shaida, Bamu kar6ar kati, Ta bank ake turawa ko ta pos, In yaso saika ɗauko hoton reciept ka tura mana*

*3196407426*
Bature Hafsat Muhammad
First bank

*Zaka tura da shaidar Biyanka ta wannan Numbers ɗin (0816985 6268) ko kuma ta (08103884440)*

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button