Sponsored Links
Hausa NovelsKurkukun Kaddara Hausa Novel

Kurkukun Kaddara 44-45

Sponsored Links

*💋KURKUKUN ƘADDARA💋*

*Daga alƙalamin Boss Bature✍️*

*Dedicated to Aunty kubra❤*

*Gargarɗi!!!*

_Ban amince wani ko wata ya yi amfani da wani sashe na book din nan ba ta kowace siga, ko a karanta mini shi a Youtube, ba tare da an nemi izni a wurina ba. Ko a haɗa mini document, idan kunne ya ji jiki ya tsira, ko da Allah na bar mutun zai bi mini haƙƙina!_

E44-45 (Last Free pages of Takun farko, Saura kaɗan)

💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫

*_ALBISHINKU MATAN AFRICA DA KEWAYE, SHAHARARRA KUMA K’ASAITACIYAR MAI SAIDA KAYAN MATAN NAN WATO DR MAMAN YUSUF LIKITAR MATA SOKOTO TANA FARINCIKIN SANAR DAKU CEWA ZAKU IYA SAMUN KAYANTA ADUK INDA KUKE A FADIN NIGERIA DA NIGER HARMA DA WASU K’ASASHEN BAKI DAYA, KU SANI A DADE ANAYI SAI GASKIYA KUMA MACE MAI GYARA KANTA BATA BORANCI , INA MARABA DA MASU SIYAN DAYA KO SARI_* .http://wa.me/+2347069711327

*_munada zafafan kaya kamar haka ,_*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻

*Hadin amarya budurwa ko zawara*

*Hadin uwar gida Mai taken (Maida tsohuwa yarinya)*

*Maijego package (virgin gain)* 📦

*Hadin sabon budurci ga yarinyar data rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar da namiji*

*Sahihin maganin sanyi na Maza Dana Mata Wanda yake fatattakar sanyi cikin Dan lokaci*

*Maganin gyaran nono Wanda zai gyara maki nononki cikin Dan lokaci komai lalacewarsa*

*Maganin hips Wanda zaisa shape dinki ya fita kiyi kyau kema ki shiga jerin Mata masu aji*

*Maganin kiba Wanda zaisa ki ciko kiyi kiba yar dai dai misali kema adinga binki da kallo Idan kin juya Sam rama batayi ba yar uwa*

*Hadin mallaka ba boka ba malam , akwai taimakon da muke bayarwa ga Mai butsarin namiji Wanda cikin ruwan sanyi Zaki dinga juya abunki , haka akwai Hadi na musamman Wanda komai rowar namiji sai kin samu alkhairin a wajanshi,*

*Muna da kalolin gumbuna masu Saka ni’ima sha’awa da dandano*
*Kalolin garrika mash gyara gaban mace da jimawa ajiki*
*Kalolin Zuma masu saukar da ni’ima Nan take da gamsar da maigida*
*Kalolin tsumi Wanda cikin sauki zasu Baki ni’ima da dandano irin wadda akeso*
*Kalolin matsi Wanda suke ciko da gaban mace matse gaban mace da bata Wani irin dadi da dadano*
*Akwai set kala kala Wanda yawansh ya wuce na zayyanasu anan ga Mai bukatar kayana zata iya mun magana Kai tsaye ta hanyar danna wannan blue rubutun* 👉🏻 http://wa.me/+2347069711327

*Muna dahuwar zabo ,dahuwar kaza ,dahuwar kifi ,dahuwar zuciya ,dahuwar Yan shila ,dahuwar tsoka Tara ,dahuwar Kwan mallaka, dambun nama ko na kaza Wanda yake saukar da ni’ima da jimawa sosai ajikin mace*

*Idan nace zan rubuta komai da komai to wannan page din ba zai isheni ba ,Amma ga masu sha’awar siyan kayana Zaku iya mun magana Kai tsaye ta wannan number, haka masu sha’awa su dinga ganin kalolin kayana a status sumin magana ta wannan number sai nayi seving numbers dinki ta hakan ne Zaku dinga ganin kalolin kayana idan na daura*
http://wa.me/+2347069711327

*Ina maraba da Mai siyan Daya ko sari Dr maman Yusuf likitar mata sokoto*

*❤❤❤PRISONERS❤❤❤*

 

 

Saboda tsabar firgicin da azeeza ta shiga nan take ta saki fitsarin da take ji ya soma gangarowa ta cikin wandonta, an rasa me lallashin wani acikin su, kowa sai kuka yake yi, Kuma har lokacin Batool bata saki wuyan rigar azeeza da ta shaƙe ba, bayin Allah su kaɗai suka san Fargabar da suke aciki, babban abunda suke jima tsoro shi ne azo araba su da ƴan uwansu, Basu da tabbacin za’a dawo dasu ko baza a dawo dasu ba,

Cikin shessheƙar kuka ta wanda ya galabaita azeeza ta kware maki tana faɗin”Wayyo Allah na, Na shiga uku, batool kin shaƙe min wuyan rigata, Ki sake Ni, inji da abunda ke damu na…..”daƙyar ta kai ƙarshen maganar, tana kiciniyar ƙwace wuyan rigarta da ga ruƙon da batool tayi mata, wata irin zufa ce ta wanke fuskokin su, Sun yi jawur, idanuwansu sun kumbura luhu luhu saboda tsabar tashin hankalin da suke aciki.

Waɗan da ke acikin ɗaki basu san meke faruwa ba, babu alamun zasu farka daga bacci, Wata irin gigitacciyar ƙara batool ta saki sakamakon Cizon da Azeeza ta gartsa mata a hannunta, kaitsaye sautin ƙarar ya daki dodon kunnuwan su, Aikuwa a firgice kowannan su Ya farka, at same time suka ya ye bargunansu tare da yin wurgi dasu, Kowa yana faman zazzare ido, fuskokin su da alamun ruɗani, lokacin da suka ankara daga inda sautin ke fitowa, Jiki Na rawa kowannan su Ya sauko daga saman gadonshi, da gudun gaske suka nufi sashen toilet ɗinsu, kamar an jeho su suka faɗo Ciki, Kowa yana faman baza na muzurinsa, Angel ce farko sai Hanna da hibba, kaf matan da mazansu hada danish da haris,

Hankalin su yai matuƙar tashi, ganin Jinin dake ɗigowa daga hannun batool sai yarfa shi take Yi, ta runtse idanuwanta sai kuka take yi kamar ranta zai fita, Tun da suke a rayuwar su basu ta6a ganin batool tana kuka mai sauti ba irin na yau, saboda tsabar hakurinta da juriyarta, Ita kanta azeeza data gartsa mata Cizon, duk tabi ta ruɗe jikinta sai kerma yake yi, ta manne jikin bango, Sai zazzare idanuwanta take yi fuskarta sharkaf da hawaye,

“Innallallahi wa’inna ilaihirraji’un! Batool meya faru dake? Me kuke yi anan keda azeeza? Badai faɗa kuke yi ba”? Angel ce ta jefa musu tambayar, a yayin da take matsawa kusa da batool, takai hannunta tare da ruƙo hannun batool dake bleeding, Hanna tace”ashe dama kune kuke faɗa? Tun ina bacci nake ta jin hayaniya cikin kunne na, amma kun bani mamaki, yanzu batool ki rasa da wa za ki yi faɗa sai azeeza”? Hannah na rufe baki haris yace”Ku faɗa mana meya haɗa ku da har kuke ƙokarin illata junan ku, wannan wani irin abun kunya ne, ” Lamarin duk bai yi musu daɗi ba, sai tambayar su suke yi akan su faɗa musu dalilin yin faɗan na su amma sun kasa tanka musu, saboda kukan da suke yi.

“Hannunta yana zubar da jini, Ya zamu yi? Ko dai muje mu faɗa ma tsohuwa”? Mubeen ne yai maganar, muryar danish da alamun bacci bai ishe shi ba yace”Basai an faɗa mata ba,” ya ƙarasa maganar tare da matsawa ya tsaya gefen angel dake a tsaye gaban batool, ya miƙa hannu ɗaya ya damƙo hannun batool dake zubar da jini, tare da kaishi saitin bakinshi tamkar zai gartsa mata cizo, ya kama wurin, kamar yana tsotsar jinin, duk suna kallon shi, Musamman angel da mamaki ya kamata ganin wani sabon salon treatment da bata ta6a gani ba,

Sosai batool ta runtse idanuwanta, tana faman cizon brownish lips ɗinta, a hankali danish ya zame bakinsa daga saman hannun batool, wani iko na Allah jinin ya tsaya da zuba, sai dai a bunda ya ɗaure ma angel kai, ganin bai zubar da jinin daya sha ƙasa ba, A ruɗe take bin fuskarshi da kallo batare daya lura da ita ba, Sauran ƴan uwan babu wanda Ya kawo komai aranshi sai ita data ankara da abunda ya yi, zuciyarta ta shiga ruɗanin, taya akai ya ke iya swallowing ɗin jini!?

Muryar azeeza cikin shessheƙar kuka tace”Dan Allah batool ki yafe ni wlh bada son raina na gartsa maki cizo ba, ke ce kika shaƙe mini wuyan rigata har naji zafi na cije ki,” wani irin jiri batool take gani acikin idanuwanta, biji biji take bin kowannan su da kallo, Angel tace”Batool meke damunki? Wai baza ku faɗa mana me ya haɗa ku ba? Meyasa ku ke yin kuka? Ga zufa duk ta wanke jikin ku,” matsawa batool ta yi kusa da angel ta kwantar da kanta saman kafaɗarta, da sauri angel ta sanya hannayenta biyu ta rungumeta sosai ajikinta, cikin muryar kuka batool ta zayyane musu abunda ke faruwa, Hankalinsu yayi matuƙar tashi, deeja dake a gefen haris ta fashe da kuka tana faɗin”mun shiga uku, abunda nake gudu sai da ya faru, wannan wace irin masiface? Fuskarta a yamutse takai kai ƙarshen maganar, haris yace”gaskiya bazaiyiyuwa ba, nidai bazan bari atafi da wani daga Cikin ku ba, sai dai a haɗa dani,” cigaba da magana deeja tayi yayin da hawaye ke bin fuskarta tace”Dan Allah mu hada kanmu, wannan karan kada mu bari atafi da ƴan uwan mu, ina matuƙar tausayin azeeza da batool, bazan so su ɗanɗani irin raɗaɗin azabar da muka sha ba, musamman azeeza zamu iya rasata,” maganar deeja ba ƙaramin tsorata azeeza ta yi ba, jikinta ya hau 6ari, haƙoranta har kakarwa suke yi kamar wadda sanyi ya kamata, da sauri javed ya janyota jikinshi, kamar jira take yi dama ta ƙanƙame shi tana cigaba da yin kuka, lallashinta ya shiga yi, yana ɗan bubbuga bayanta da hannun shi,

Zuciyoyinsu duk sun karaya, Fuskar Rubina ɗauke da matsananciyar damuwa tace”Wai shin Jinin wanene acikin su? Ta ya zamu iya ganewa? ɗagowa azeeza ta yi daga jikin javed tana faɗin”I just know it’s not my blood, wlh ba jini na ba ne, sai da na faɗa ma batool cewa banawa bane, Saboda ni ko da na shiga toilet ɗin ban kai ga cire wandona ba, na yi tozali da shi”

cikin shessheƙar kuka batool tace”Nima banawa bane, ba daga jikina yake ba, har na shiga na fito daga Cikin toilet ɗin ban ganshi ba” koda batool tae maganar bata raba jikinta daga na angel ba, ta ƙanƙameta, ji take kamar in ta raba jikinta daga nata za’a zo arabasu ne,

Hawaye ne masu ɗumi suka wanke fuskar angel. Har cikin zuciyarta tana jin wani irin mummunan faɗuwar gaba, muryar na ɗan rawa ta ambaci sunayensu Batool azeeza, “duk suka natsu, suna jiran jin me zata ce musu,

“Since we were all confused, we couldn’t figure out whose blood was in the toilet, abunda yakamata muyi zamu shiga toilet ɗin mu duba jinin da kyau, idan muka tabbatar jini ne, Azeeza da batool kowannan ku zai shiga cikin toilet ya bincika jikin shi, ta hakanne kaɗai zamu Iya gane daga jikin wa jinin ya ɗigo” gaba ɗaya kowa yayi amanna da maganar angel, koda suka shiga toilet ɗin suka duba dakyau, jini suka gani har ya ɗan bushe a ƙasa, Hankalinsu ya ƙara tashi, angel tace abunda ya rage yanzu, su shiga su duba jikinsu, Batare da 6ata lokaci ba, azeeza da batool suka shiga cikin toilet, kusan atare suka fito daga Ciki, Har suna haɗa baki wurin faɗi “Ba daga jiki na yake ba” Lamarin yae matuƙar ɗaure musu kai, To wai jinin wanene toh? dole dai acikinsu ne wani ya zubar dashi, kuma azeeza ta tabbatar musu da cewa sabon Jini ne, domin kuwa lokacin da ta shiga cikin toilet ɗin, da ruwa ruwa jikinshi, kafin yakai ga bushewa,

Kowannan su ya shiga ruɗani, in a low voice danish yace”ku daina wahalar da kanku, Idan ma dagaske jinin ne, Giants ne zasu banbance wanene acikin su,” harara angel ta watsa mashi tare da cewa”danish har fata kake yi azo a ɗauke su”? duƙar da kanshi ƙasa yai batare daya bata amsa ba, haris yace”yanzu duk ba wannan ba, ku zo mu koma ɗaki mu jira mu gani me zai biyo baya” muryar azeeza a rauna ce take fadin”Ni wlh bazan fita daga nan ba, ku rufa mana asiri mu yi zaman mu acikin toilet mu datse ƙopar, ta yadda ba zasu Iya shigo wa su ɗauke mu ba” la66anta har shaking suke yi saboda tsabar firgici.

Tsananin tausayin su ne ya kama ƴan uwansu, haris yace”Azeeza ta kawo shawara mai kyau, mu rufe su kawai acikin toilet, kun ga shikenan munyi maganin Giants ba zasu Iya shiga su ɗauke su ba” Jinjina kai angel ta ɗanyi alamar gamsuwa da bayanin Haris, ta ƙara da cewa”Ni zan zauna a atare dasu cikin toilet ɗin”

Girgiza kai danish yayi yana binsu da wani irin kallo mai wuyar fassaruwa yace”that cannot be possible, if you say you will stop the giant from taking her you’ll bite off more than u can chew………” daƙyar ya ƙarasa maganar ganin irin kallon da suke watsa mashi asaman fuskarshi, Tsabar takaici ya hana Haris furta komai, Sai angel ce tai ƙoƙarin cewa”Kome zamu yi be shafe ka ba danish, u should stay away from us, tun da ba ka supporting ɗin mu that’s mean baka da amfani awurin mu, ka koma saman gado ka kwanta zai fi maka kwanciyar hankali. If not wlh zan yi maka abunda baka tsammani,” angel na rufe baki deeja tace”Danish baya atare damu, na fara zargin cewa Yana atare dasu, shiyasa ko jiya da aka dawo dani duk irin baƙar wahala dana sha, Kowa Yana yi mini sannu duk da bata maganin ciwo amma ina ji daɗi, atlease ƴan uwana sun nuna sun damu dani sun yi kewata, amma danish ko kusa dani baizo ba, sai kace wata maƙiyiyar shi.

hawaye na bin fuskar deeja takarasa maganar, Ran haris ya 6aci sosai, a fusace ya kai hannun shi ya damƙi damtsen hannun danish ya fusgo shi ya ja shi da ƙarfi ya fitar dashi daga cikin sashen toilet din. har cikin ɗakin su bakin gadon shi ya kawo shi, anan ya dakata Ya ɗago suna kallon juna ido cikin ido shi da danish,

“Ba ka da amfani a wurin mu, duk da haka bawai ina gudun ka bane, ko Ina fushi dakai a’a ko ɗaya, har yanzu kana nan a yadda kake cikin zuciyata, sai dai bama buƙatar ka a halin da muke ciki yanzu, Gado shi ne ya dace dakai ka hau ka kwanta” ya ƙarasa maganar tare da jan dogon tsoki, kafin Ya juya ya nufi sashen toilet ɗin. Jikin danish ya yi sanyi, slowly ya ɗan juya baya yana kallon haris dake ta sauri har sai da ya shiga ƙopar tukunna danish ya ɗauke idonshi daga kallon bayan nashi da yake yi,

Kamar yadda suka ce ya hau saman gado, aikuwa gadon ya haye ya kwantar da kanshi saman pillow, shi kaɗai yasan irin raɗaɗin da yake ji acikin zuciyarshi, ganin yadda ƴan uwanshi suke nuna rashin amfanin shi acikin su, abun yana mishi ciwo acikin zuciyarshi. Daurewa kawai yake yi dan ba yadda zaiyi,

Bayan haris Ya koma cikin toilet ɗin, atare da angel suka tsara yadda zasu shirya ma Giants don su hana atafi da ƴan uwansu, Bayin Allah sun damu da ƴan uwansu sosai, babu mai tunanin abinci acikinsu ba don basu jin yunwa ba, sai dan damuwar da suka shiga, na fargabar kada azo a ɗaukar musu ƴan uwansu,

Haris ne yace da angel ta shiga Cikin toilet ita da batool su datse ƙopar ta yadda giant ba zasu Iya shiga Ciki ba. ita kuma azeeza a ƙarƙashin gado zasu 6oye ta, hanna tace ae zasu Iya gano azeeza tunda suna kallon komai suke Yi, amma ita a ganinta, abar azeeza ta shiga cikin toilet ɗin tare dasu angel, Haris yace su yi hakan kawai, toilet ɗin ƙarshe suka buɗe angel da su azeeza suka shiga Ciki, kafin su rufe ƙofa haris yace”su kwantar da hankalin su, idan an kawo abinci zasu kawo musu nasu su ci,” suka amsa mashi da toh, daga bisani angel ta datse ƙopar da Jam lock,

Kallon juna suka shiga yi atsakaninta dasu azeeza dake a tsaitsaye, fuskokinsu sharkaf da hawaye, sam babu kwanciyar hankali atare dasu,

Tsananin tausayinsu ne ya kamata, gaba ɗaya ta sanya hannayenta biyu ta rungumesu ajikinta, Cikin sigar lallashi take Yi musu magana,
“In sha Allah giants bazasu raba mu da ku ba, bazan bari a cutar mini da ku ba, ina ji ina gani, wlh sai inda ƙarfi na ya ƙare, koda kuwa zan rasa raina ne, amma wannan karan ashirye nake dana fuskanci kowani irin tashin hankali ne” with Confidence angel tayi maganar, babu wasa akan fuskarta.

Hankalin su batool ya ɗan kwanta, saboda jin abunda tace, ɗagowa batool tayi daga jikin angel, idanuwanta sun ɗan kumbura saboda kukan da tasha, cikin sanyin murya tace”Angel, bana so wani ya cutu acikin ku ta dalilin mu, idan har giants sun zo zasu tafi damu, kada kuce zaku shiga huruminsu, ” girgiza kai angel ta ɗanyi tare da cewa”ki daina faɗin hakan, batool da ace kinsan me suke Yi maku idan suka ɗauke ku, da baki ce haka ba, ke kanki bazaki so atafi dake ba, mutanan nan basu da imani basu da tausayi, kashe mana rayuwa suke son yi ta yadda ba zamu ta6a amfanuwa ba, burinsu shine su ƙarar damu,” tamkar zata fashe da kuka ta kai ƙarshen maganar, azeeza dake kwance jikin angel, taƙi ɗagowa baiwar Allah, Jikinta sai kerma yake yi, ta ƙanƙameta tamkar zata koma cikin cikinta, wani irin faɗuwar gaba take ji, ita kanta angel tana iya jiyo sautin bugun zuciyar azeeza, fargabatar kada tsoro yasa zuciyar azeeza ta buga harta mace kafin ma su ƙaraso,

“Mu samu wuri mu zauna, nasan kun gaji da tsayuwa” daga jikin bango suka zauna, still azeeza bata saki jikin angel ba, hannu bibbiyu ta ƙanƙameta koda suka zauna, itama batool ta ɗan kwantar da kanta saman kafaɗar angel, toilet ɗin yai tsit ba ka jin hayaniyar komai, tsawon lokaci kafin angel ta fara faɗa musu addu’o’in da zasu karanta na neman tsari, saboda tsaro,

Lokacin da angel ta datse ƙopar toilet ɗin, Ajiyar zuciya kowannan su Ya sauke, Haris yace dasu su koma ɗaki su zauna su jira su ga waye zaizo ɗaukarsu azeeza, Hada ja musu kunne akan karsu kuskura su bari tsoro yasa su faɗa ma giants inda suka 6oye su azeeza, duk runtsi duk wuya suja bakinsu su yi shiru, Suga iya gudun ruwansu, suka amsa mashi da toh,

atare suka nufi cikin ɗakin, Idanuwansu akan danish dake kwance saman gadonshi, haushin shi duk ya kama su, wani sullu6iyo dashi,

Suna yunƙurin haurawa su zauna saman gadajenshi, kwatsam suka soma Jin motsin buɗe kofa tacen saman bene, wa’Iya zubillahi zoka ga tsantsar tashin hankali akan fuskokinsu, A matuƙar ruɗe suke kallon matattalar benan ,

Takun tafiyar giants suka soma Jiyo wa acikin kunnuwansu, kafin su bayyana su uku masu kawo musu abinci hannayen su ruƙe da farantai, wata irin nauyayyiyar ajiyar zuciya suka sauke ganin basu zo da shirin tafiya da wani ba, Bayin Allah hada murmushin su, saboda sun sa ma ransu cewa baza a ɗaukar musu ƴan uwansu ba,

Da ido suka bi giants da kallo har suka sauke musu farantan abincin, da sauri suka nufi saman dining carpet ɗin suka zazzauna, babu wanda yae tunanin yayi ma danish magana akan yazo yaci abinci, sai ma ta ƴan uwansu suke yi dake acikin toilet, ƙasa ƙasa da murya suke yin magana don kada giants su ji su,

“A ina zamu ɗibar musu abincin mu kai musu”? hibba ce tai maganar, hannah tace”ku daina magana kada Giants su ji mu, abunda za’ae mu ɗauko kwandon batool mu ɗibi abinci, sai mu ajiye, bayan sun tafi sai muje mu kai musu acikin toilet ɗin,” haris yace”kin kawo shawara mai kyau,” batare da 6ata lokaci ba, hanna ta miƙe taje ta ɗauko kwandon daga ƙarƙashin gadon batool ta dawo ta zuƙunna gaban farantan, ta yaye jan ƙyallan da aka rufe faranti na farko dashi, fried fishes ne aka kawo musu, manya manya sun soyu sai maiƙo suke Yi, a ƙalla kowa zai samu ɗaya, Kifin akwai tsoka jikinshi sosai, A hankali take kai hannu tana ɗaukar kifin tana ajiyewa acikin kwandon, ganin ta ɗauki uku, yasa haris yace”Ki ƙara ɗaya kodan saboda danish” duk da fushi da yake yi dashi hakan bai hana shi jin damuwa dashi ba, Hanna tace toh, tasa hannu ta ƙara ɗaukar ɗaya ta ajiye, Ta ɗibar musu fruits tare da robar ruwa guda uku ta ɗauka, miƙewa tayi hannunta ruƙe da kwandon taje bakin gadon batool ta ajiye shi ta dawo ta zauna, a tsanake suke Cin nasu fried fish ɗin, Suna ci suna satar kallon giants dake atsaye sun goya hannayen su saman ƙirjinsu yadda kasan Gumaka, ko gajiya da tsayuwa basa yi,

A 6angaren su angel dake acikin toilet, Tuni bacci yai awon gaba da azeeza da batool, duk suna akwance saman jikinta, itama angel ɗin wani irin bacci take ji ga yunwa dake addabarta, sai faman lumshe idanuwanta take yi,

Daga wajen ƙopar toilet ɗin ta soma Jin ana yi musu knocking ras taji gabanta ya faɗi, hatta su azeeza dake baccin jin bugun ƙopar yasa suka farka a firgice suna faman zazzare idanuwan su,

Muryar hanna suka jiyo tana faɗin”Ni ce angel, ku buɗe mini kopa, breakfast ne na kawo maku” Kusan atare suka sauke ajiyar zuciya, duk sunyi tsammanin ko Giants ɗin ne suka zo tafiya dasu,

“Ku jira na amso mana abincin” tai maganar tare da zame jikinta daga nasu ta miƙe ta nufi ƙopar, ta cire jam lock ɗin, ta janyo ƙopar tare da leƙo da kanta waje,

Hanna ta gani atsaye ita da haris, kwandon Yana a hannun hanna ta ruƙo shi,

“Angel Giants sun zo kuma sun tafi, Ni ina ganin kamar ɗigon jinin nan ba jini bane. Tunda da ace shine, Giants zasu tafi da su azeeza ne, Amma kinga har sun kawo mana abinci sun tafi” shiru angel ta ɗanyi tana nazarin maganar Hanna. Ita gani take kamar jini fa ne, kawai dai bai kai ga zuwa bane gaba daya shiyasa basu zo sun ɗauke su ba

Muryar haris ce ta dawo da ita daga zancen zucin da take yi,

“Nima ina tunanin ba jini bane gaskiya, tun da ga shi har zunzo sun tafi batare da sun buƙaci tafiya dasu ba” abunda za’ae yanzu ku fito mu koma cikin ɗakin ku zauna ku yi breakfast ɗinku” Gyaɗa kai angel tayi badan taso ba tace”Allah yasa abunda muke hasashe ya zama gaskiya, bari nayi musu magana su fito mu koma daki amma kafin nan, zan taimaka musu su wanke fuskokinsu,” haris ya amsa mata da toh .kafin ya kalli hanna yace”Mu jira su acikin ɗaki” juyawa suka yi atare suka koma ɗaki,

Badajimawa ba, Sai ga angel ta fito hannayenta ruƙe da nasu azeeza, Bayin Allah har faɗa wa sun ɗan yi saboda damuwa, Ƴan uwansu ba ƙaramin daɗi suka ji ba, da su kayi tozali dasu,

A saman dining carpet suka zauna su uku, Hanna ta ajiye musu kwandon. Angel da azeeza suka ɗauki fried fish ɗinsu A hankali suke Ci, Sauran ƴan uwansu duk suna a kewaye dasu suna kallonsu, ganin batool ta kasa ci ne yasa haris yi mata magana yace”batool meyasa baki ci? Muryarta na ɗan kerma tace”Hannuna Zafi yake yi mini” sai lokacin suka tuna da cizon da azeeza ta gartsa mata, Zuƙunnawa haris yai agabansu, ya kai hannu cikin kwandon ya gutsiri tsokar kifin ya mika mata abaki, ta ɗan buɗe shi tana Ci, sai ƙara kwantar musu da hankali ƴan uwan nasu suke Yi, bayan sun kammala Ci, suka sha fruit ɗinsu, tare da ruwa,

Angel tace yakamata suje suyi wanka, jikinsu duk zufa, suka amsa mata da toh, har tana cewa idan bazasu iya yin wankan ba zata taimaka musu suyi, batool tace ita zata Iya, azeeza kuma tace tafi son angel tayi mata wankan, hannun su aruke dana juna suka nufi toilet, bayan tafiyarsu, Haris ya ɗauki kwandon yana kallon sauran Fried fish din daya rage na danish tare da Rabin gwanda, Ta6e baki ya ɗanyi kafin ya nufi gadon danish, Ya ajiye mishi kwandon daga gefen shi yace”Idan kaga dama ka ɗauka ka ci, breakfast ɗin ka ne” ko motsi danish bai yi ba, ya runtse idanuwanshi, kuma ga dukkan alamu idonshi biyu ba bacci yake yi ba,

Watsa hannu haris yai alamar bai damu ba, Ya wuce abunshi, bayan wani lokaci, angel tafito daga Cikin toilet tare dasu azeeza, Wani irin sanyi suke Ji, asaman gadajensu suka kwanta, angel ta lullu6esu da bargunansu, Cikin ƙanƙanin lokaci bacci yai awon gaba dasu,

Ajiyar zuciya kowannan su ya sauke, yanzu sun ƙara tabbatar da cewa ba jinin gaske bane suka gani acikin toilet tunda har marece ya doso amma ba’a zo an ɗauki wani daga Cikin su ba,

Ita dai angel ta kasa samun natsuwa acikin zuciyarta, abu biyu ne ya dameta, na farko Jinin batool da danish yasha da niyar ya taimaka mata wurin dakatar da bleeding ɗin da yake yi, amma wani abun mamaki bai zubda jinin ba sai ya shanye shi, hankalinta bai kwanta da hakan ba, abu na biyu daya tsaya mata arai shi ne wannan ɗigon jinin dake acikin toilet na wanene? Dole akwai wanda ya zubar dashi,

Zuciyarta cike fal da tunani ta ɗan kishingiɗa saman gadonta, da niyar ta samu ta runtsa, juyawa ta ɗanyi tana satar kallon danish dake kwance saman gadonshi, yatsun hannunshi dana ƙafarshi sai kerma suke Yi, hakan ya tabbatar mata da cewa idonshi biyu, ta6a baki ta ɗanyi aranta tace”Haka zaka ƙare, mutun sam baya gajiya da hawan gado, mai matacciyar zuciya kawai” takarasa xancen zucin tana mai jan tsoki, ta ɗauke idanuwanta daga kan jikin shi, ta mayar dasu kan kwandon da haris ya ajiye mashi daga gefen gadonshi, yau kuma kowa zai lallashe shi yaci abincin shi? murmushin takaici ta dan saki, wani lokacin in yana abu kamar ƙaramin yaro, har mamaki yake Ba ta

*after some hours💔*

Kafin marece ya yi sai da kowan nan su ya yi wanka, Suka koma saman gadajensu suka kwanta, har lokacin danish bai motsa ba, Yana ayadda yake lafe saman gado,

Angel tana ƙoƙarin nutsawa cikin baccinta, ta soma jin motsin mutun a jikinta, aɗan firgice ta ware manyan idanuwanta akan fuskar wanda ke zaune saman gadonta, Tayi mamakin ganin batool, fuskarta duk a yamutse. Idanuwanta sun ƙanƙance, tunkafin ma batool tayi mata magana taji wani irin faɗuwar gaba,

Muryarta na ɗan rawa tace”Lafiya? Batool meke damunki”? Cikin sanyin murya ta soma magana”Bana jin ɗaɗin jikina angel, gaba na sai faɗuwa yake yi, na gaza jurewa, shiyasa nazo wurinki, don kiyi mini addu’a, ko na samu naji sanyi araina” ajiyar zuciya angel ta sauke a yayin da take yunƙurin mikewa xaune tace”Wlh har gabana ya faɗi dana ganki nayi tunanin ko jinin ne kika gani yazo miki ashe bashi bane” jinjina kai batool ta ɗanyi alamar eh, tace”Bashi bane, bana jin daɗi ne kawai”

“Tun da nake dake batool ban ta6a ganin ki cikin damuwa ba, irin na yau, kin canza sosai, duk sai naji ba daɗi jikina,” daƙyar batool ta ɗan ƙaƙalo murmushin dole akan fuskarta tace”kada ki damu sister, zan dawo dai dai ne, just fargabar abunda ya faru ɗazu ce tasa duk na canza, Amma yanzu da ɗan sauki”

Ido cikin ido suke kallon juna. angel ta ruƙo hannayenta acikin nata tare da cewa

“Zanyi maki addu’a, amma nafi so naji ki ajiki na, don naji daɗin kwantar miki da hankali kamar yadda kika saba yi mini” murmushi suka sakar ma juna atare,

A saman chest din angel batool ta kwantar da kanta, tare da sanya hannayenta, ta zagayo dasu ta bayanta, sosai tayi tighting ɗinta, wani irin tsananin ƙaunarta take ji, suna matuƙar son junansu fiye da tunanin mai tunani, addu’o’i angel ta soma karantowa tana tottofa mata asaman kanta, har cikin zuciyarta take jin wani irin daɗi yana ratsata, har tana fadin”sister kada ki daina yi mini addu’ar nan, ki cigaba, ina jin wani irin sanyi acikin raina,” murmushi angel tasaki, tare da ɗaura hannayenta saman sumar kan batool dake a dumbuje babu gyara, ta shiga shafata tana faɗin”indai akanki ne, zan iya kwana batare dana runtsa ba, wurin yi miki addu’a, ina matuƙar ƙaunarki my batool, ” muryarta asanyaye ta karasa maganar,

“Mu kwanta mu yi bacci, mu ma, ” acewar batool, a manne da juna suka kwanta saman mattress ɗin, angel taci gaba da yi mata addu’a har sai da bacci ya ɗauke su gaba ɗayansu,”

To jama’a, ɗaki fa ya yi shiru baka jin hayaniyar komai, hankalinsu kwance sai sharar baccinsu suke yi, kamar waɗanda aka yanka mutuwa agabansu,

Lokacin da marece Ya nutsa, deeja tafarka daga bacci ta miƙe ta zauna saman gadonta, hannunta rungume da pillow, ɗaya bayan ɗaya take bin gadajensu da kallo, kafin ta tsayar da idonta akan shimfidar haris, ta jima tana kallon shi, kafin ta ɗauke idanuwanta, hakanan taji tana ra’ayin tabi kowani gado ta kalli fuskokin ƴan uwanta,

Don haka ta sauko daga saman gadonta, Still jikinta ba ƙwari sosai, kamar ɗiyar roba hake take yin tafiya, tun daga kan gadon su hanna taso ma bi tana kallonsu har zuwa gadon azeeza, Ta ɗan dakata da tafiya tana kallonta, wani abu daya ɗaure mata kai bacci take yi amma sai firgita take Yi, numfashinta kuma a hargitse take fitarshi, matsawa ta ɗanyi tare da samun wuri gefen gadon azeeza ta zauna, hannunta ta ɗan ɗaura bayanta ta ɗan bubbugata, aikuwa a firgice azeeza ta farka tana faman zazzare idanuwanta, lokaci ɗaya kuma ta dafe kanta da hannu ɗaya tana faman sauke ajiyar zuciya ganin deeja ce,

“Azeeza lafiya kike ta firgita kina bacci? Ko dai baki da lafiya ne”? Tayi mata tambayar cikin nuna damuwarta,

Muryar azeeza adisashe tace”Hankalina ba a kwance yake ba, deeja bana jin daɗi, baccin nan da kika ga ya ɗauke ni har mafarkin Giants sai da nayi” idanuwanta acike tab da kwalla takai ƙarshen maganar,

Janyota deeja tayi zuwa jikinta ta dan rungumeta da hannu ɗaya, tana lallashinta,

“Ki kwantar da hankalin ki My little sis, muna atare dake, babu abunda zai faru daku,”

Azeeza tace ina jin ƙishin ruwa,” da sauri deeja ta raba azeeza daga jikinta, ta sauko daga saman gadon ta nufi gadon batool ta zuƙunna ta tura hannu ƙarƙashi ta ɗauko robar ruwa, Ta miƙe ta koma gadon azeeza, ta zauna tare da cire murfin ta kwafa mata ita abaki, sosai ta shiga shan ruwan,

A wani irin firgice Azeeza Ta jefar da robar ruwan dake ahannun deeja. Ta zabura ta yunƙura ta duro daga saman gadonta ta faɗo ƙasa, Ta shige ƙarƙashin gadonta, Jikinta sai kerma yake yi, Lamarin yae matuƙar ɗagawa deeja hankali, muryarta da alamun ruɗu take kwala ma azeeza kira tana tambayarta lafiya? Meyasa ta jefar da ruwan! Kafin deeja tayi yunƙurin saukowa daga saman gadon azeeza da niyar ta duƙa ƙarƙashin gadon ta janyota, kwatsam ba zato ba tsammani taji motsin buɗe ƙopar ɗakin su hankalinta a matukar tashe ta ɗago tana kallon Benan, Ba ita ba hatta masu bacci sai da suka farka jin sautin buɗe ƙopar, wani gabjejen Giant na ya faɗo Cikin ɗakin, mai faffaɗan ƙirji bayyanar shi tamkar baiyanar mutuwa ne agaresu, Wani abun ɗaure kai ma Giant ɗin daya shigo yasha banban da waɗanda suka saba zuwa kawo musu abinci, domin kuwa shi hada Star ɗaya a jikin baƙar rigar jikinshi daga gefen hannun hagu, sai lokacin deeja ta gane dalilin dayasa azeeza ta gudu ta 6oye ƙarƙashin gado, Wata irin faɗuwa gaba ce tazo ma deeja, lokaci ɗaya ta fasa ƙara mai matuƙar firgitarwa muryarta na rawa take ambaton”Innallahi wa’inna ilaihirraji’un! wayyo Allahna mun shiga uku! Mun bani!’ wannan maganar da deeja tayi ce tasa duk wani mai bacci ya ƙarasa wartsakewa, Hankalin angel da batool yai matuƙar tashi, a matuƙar ruɗe angel ta ruƙo hannun batool suka sauko daga saman gadonta, da gudun gaske taja ta suka faɗa cikin sashen toilet ɗinsu, Suna shiga ɗaya daga cikin makewayin, Angel ta zura jam lock ta datse ƙopar, tana juyowa batool ta faɗa jikinta tana kuka take faɗin”Angel tafiya za’ayi dani, naji ajikina nice aka zo ɗauka, shikenan za’a raba ni da farin Ciki na ina ji ina gani, za’a ɗauke ni a tafi dani inda za’a cutar da rayuwata, Ba lallaima ne a dawo dani Cikin ku ba” Fashewa da kuka angel tayi Cikin shessheƙa tace” wlh bazaiyiyu ba, haƙurina ya ƙare, komai xai faru sai dai ya faru amma wlh bazan bari atafi dake ba, duk runtsi duk wuya ina atare dake, Sai dai su kashe ni” gaba ɗaya sun shiga matsanancin tashin hankali, su biyu acikin toilet sun ƙanƙame juna

A hankali giant ɗin yake saukowa daga saman staircases ɗin, haris yai matuƙar harzuƙa, Su rubina duk sun zazzare idanuwansu, damuwace ƙarara kwance akan fuskokinsu. Wasu har sun fara kuka, tun kafin ma a ɗauki ƴan uwan nasu, Duk wannan budurin da akeyi danish bai motsa ba, haka zalika Azeeza bata fito daga inda ta 6oye ba, domin kuwa tuni ta jima da sumewa,

Yadda kasan zaki Haka giant ɗin nan Ya tunkaro wurin gadajensu, Yana zuwa tsakiyar ɗakin Yaja burki ya tsaya ga dukkan alamu kamar kallonsu yake yi duk da basu Iya gane hakan. Tunda jikinsu gaba ɗaya a lullu6e yake da baƙaƙen kaya, hatta idanuwansu

Ƙasa ƙasa da murya haris yace”ku ƙyale shege kada ku faɗa mishi inda suke muga ya zaiyi, Na rantse yau sai dai ayi duk wacce za’ae amma bazan Bari wannan ƙaton Ya ɗauki ɗaya daga Cikin mu ba”

Muryar Hanna Cikin shessheƙar kuka take take roƙon giant ɗin tana faɗin”Dan Allah kada ku raba mu da ƴan uwanmu, Idan ma ɗaukar ta zama dole to ni ku ɗauke ni ku tafi dani amma na roƙe ka ka ƙyalesu, sun tsorata sosai zasu Iya rasa ransu, ”

hannah na rufe baki, sauran matan suka fashe da kuka suna roƙonshi, bayin Allah hada ƙoƙarin saukowa daga saman gadajensu suna yi mashi magiya akan ya ƙyale musu ƴan uwansu, su sun amince ya ɗauke su amma kada ya ta6a musu Azeeza da batool, tabɗijancan Iska na wahalar da me kayan kara, sufa duk atunaninsu zai ji tausayinsu Ya ƙyalesu, Sai dai abunda basu sani ba, Zuciyar giant tamkar dutse take. basu da tausayi ko misƙala zarratin, babu ɗigon Imani akansu, Su fa kawai Umarni suke bi daga sama, haris da ranshi ke a6ace yace”Ku daina wahalar da kanku, babu alamun zai saurareku, tun da ba tausayi ne dasu ba, Ae mun riga da mun 6oye su, kuma babu wanda zai nuna mishi inda suke idan yaga dama yai ta tsayuwa daga yau har jibi, idan ya gaji ya kama hanya ya koma,” haris fa ya ɗauko ta da zafi,

Tunda suka fara magana, gabjejen giant ɗin nan baiko motsa ba, Kamar yana sauraron me suke tattaunawa,

Da mamaki su ke kallon Giant ɗin, ganin ya ɗaga hannayen shi biyu yai clapping ɗinsu, Cikin rashin fahimtar me yake nufi yasa suka zazzare ido suna kallon Juna,

Danish ne ya fara motsawa daga saman gadonshi, Ya miƙe ya sauko da ƙafafuwanshi ƙasa, ya ɗan ɗago ya kalli giant ɗin dake a tsaye na wani lokaci kafin ya ƙarasa saukowa daga saman gadon, Yaje gaban giant ɗin ya sara mashi, a matuƙar ruɗe suke kallon danish, abun mamaki abun al’ajabi

Daga bisa ni, su ka ga danish ya juya Ya nufi sashen toilet ɗinsu, gaba ɗaya suka bi shi da ido, Batare da wani ya motsa ba, Zuciyoyinsu cike da fargabar me danish zaije yi acikin sashen toilet ɗinsu,

A lokacin batool da angel suna a zuƙunne jikin bangon toilet, sun ƙanƙame juna, Unexpected Angel tajiyo motsin buɗe kopa, tashin hankalin da ba’a sama shi date, Ƙopar dake a rufe kafin su shigo ta ciki ta sanya jamlock ta garkame ta, A matuƙar ruɗe take kallon Jikin ƙopar ganin jam lock ɗin yana motsi da kanshi ya zame kanshi, ƙopar ta buɗe, saboda tsabar tsoron da taji tuni zufa ta wanke fuskarta, batool kuwa tuni jikinta ya ɗauki wani irin zafi na fitar hayyaci,

Duk a tunaninsu giant ne zai shigo wani abun al’ajabi sai ganin danish su ka yi ya faɗo Cikin toilet din, yana ƙarasa shigowa, Ya miƙa ma Batool hannu yace ta taso su tafi, wani irin kallon tashin hankali angel da batool suke binshi dashi, Ganin taƙi miƙa mashi hannunta yasa shi yin saurin damƙo damtsen hannunta ya janyota ta ƙarfi ya fiddo da ita daga Cikin toilet ɗin, da gudu angel tabiyo bayanshi, ta cafko hannun batool tana ƙoƙarin ƙwato ta, amma abun ya faskara domin kuwa ba ruƙon wasa yai mata ba, Adai dai lokacin da danish ya fado Cikin ɗakin, su haris suka ga ya ruƙo batool, zuciyarsu tai matuƙar karaya, lamarin yai matuƙar girgixasu, tsabar ruɗanin da suka shiga yasa suka gaza ta6uka komai,

Kafin su yi wani yunƙuri, Danish Ya ƙarasa gaban Giant ɗin tare da batool Ya damƙa mashi ita, Giant ɗin ya sanya hannu biyu ya ɗauki batool saman kafaɗar shi batare da 6ata lokaci ba. ya juya ya nufi hanyar fita daga ɗakin, Al’ajabi ya hana su motsa, Suna ji suna gani giant ya tafi da batool tana ta kuka tamkar ranta zai fita,

Nan take angel ta yanke jiki ta faɗi ƙasa asume, kamar jira suke Yi giant ɗin Ya fita, Haris yai wani irin kukan kura ya duro daga saman gadonshi, Ya kai ma Danish farmaki, kwalar rigarshi ya damƙa ya jijjiga shi, Hawaye na fita Cikin idanuwanshi yace”Ka kashe mu danish! Ashe dama baka da hankali? Kai wani irin wawan mutun ne sakarai soko maloho, wanda baisan Ciwon kanshi ba, wlh ka karya mini zuciyata ko a mafarki ban ta6a tunanin zaka Iya ruƙo hannun batool ka damƙa ma giant ita, don aje acutar da rayuwarta, ashe na yaudari kaina bansani ba, mugu azzalumi, wawa daƙiƙi….” Kafin haris ya ƙarasa maganar shi, Gaba ɗaya sauran ƴan uwan nasu suka tarar ma danish, bugu ta ko’ina suka shiga kai mashi, Kamar sun samu jaki, Hada matan duka suka nannaɗe hannayen rigunansu suka dunga bugunshi, amma ko gizau baiyi ba. Har saida suka fasa mishi hancin shi da bakin shi jini ya soma zuba, tukunna suka sake shi, anan ƙasa ya kife idanuwanshi sunyi jawur tamkar garwashin wuta, wani irin jiri yake gani, ya rasa meke yi mishi daɗi, ta ko’ina ga6o6in jikinshi raɗaɗi suke yi mishi domin kuwa ba ƙaramin bugu suka yi mashi ba, sun haɗa mishi Jini da majina sun xautar dashi,

Kowa sai faman haki yake yi, Kuma babu wanda yaji tausayin shi, suna a tsaitsaye cirko cirko suna kallonshi, sai faman juyi yake yi, tun da suke dashi basu ta6a jin tsanar danish ba sai yau daya nuna musu true colour dinshi, mugun zargin shi suke yi, tabbas shima yana atare da giant shiyasa yake goya musu bayan duk abunda suke yi. Ɗan jakar uba,

Haƙiƙa Danish ya yi breaking heart dinsu, hawaye ta ko’ina akan fuskokinsu, Ji suke kamar su tattake shi ya mutu su huta, tun da baida amfani acikinsu, tare da shi ake haɗa baki a cutar da ƴan uwansu,

“Daga rana irin ta yau kada ka ƙara kiran mu da sunan ƴan uwanka, mugu azzalumi” Javed ne yai maganar, deeja tace”dama tun jiya da aka dawo dani, naga sauyi atare dashi, ko sannu baiyi mini ba, ashe hada shi ake haɗa baki a cutar damu,”

Mubeen yace”ae ni banso muka barshi da rai ba, wlh da mun sani mun karkarya ƙasusuwan Jikin shi, ” yana magana yana cije le6e,

“Danish baida tausayi baida imani, yau ya tabbatar mana da hakan, shi ɗin ba jinin mu bane, don haka ya tattara ya san inda dare yai mishi tun kafin muyi silar mutuwarshi,”

Duk wannan suratan da suke Yi, danish yana kwance, numfashinsa na fita sama sama, daga gani yana acikin mawuyacin halin da shi kanshi baisan Ina zai tsoma ranshi ba,

Hancin shi dake bleeding jini duk ya wanke farar fatar fuskarshi, muryarshi adisashe yake faɗin “ku taimaka mun da ruwa in sha” wani irin kallo mai kama da harara suka shiga jefa mishi, haris yace koba ruwa ba? Ka jira ka gani, don ubanka, ” rai a6ace yaje ya ɗauko robar ruwan dake a ƙarƙashin gadon Batool ya dawo ya tsaya agaban danish, Ya buɗe murfin robar ya watsa mashi ruwan duka akan fuskarshi, yana gamawa ya jefar da robar ruwa aƙasa yace”Iya taimakon da zamu Iya yi maka kenan, ni banga ma amfanin kallonka da muke Yi ba, ku wuce muje mu xauna. Mubar shege ya ji ajikin shi”. Yana ji yana gani ƴan uwanshi suka juya mishi baya, Suka nufi gadajensu su ka zazzauna, zuciyoyin su acike da alhinin rashin Batool da suka Yi,

Hanna ce ta lura babu angel acikinsu, babu wanda ya lura da cewar ta sume a bakin ƙopar shiga sashen toilet dinsu.da sauri ta miƙe daga zaunan da take a gefen gadonta, sai da ta fara zuwa karkashin gadon batool ta ɗauko wata robar ruwan, Ta nufi inda angel take kwance ƙasa, Ta buɗe murfin robar ta ɗan ɗebo ruwan a tafin hannunta ta watsa mata saman fuskarta, nan take angel taja dogon numfashi ta fatser dashi, muryar ta cikin shessheƙar kuka take ambaton sunan batool tana faɗin An raba ni da ƴar uwata, innallahi’wa’ inna ilaihirraji’un! Wannan wata irin rayuwace

“Angel ki tashi xaune,” muryar hanna ce ta katse ta, jikinta duk ba daɗi, daƙyar ta samu ta yunƙura ta miƙe xaune tana faman huci sumar kanta duk ta tarwatse har tana kokarin rufe mata idanuwanta, bakowa ta ke kallo ba face danish dake kwance a ƙasa yana juyi, hannayenshi dafe da forehead ɗinshi,

Da buɗar bakinta sai cewa tayi”me danish yake yi araye batare da kun kashe shi ba”? Fuskarta babu wasa tai maganar, haris yace”munso muyi hakan amma sai muka ƙyale shi, bawai don mun haƙura ba ne, Xamu jira ne har time da za’a dawo mana da batool muga awani yanayi take ciki, idan ta tsira shima xai tsira da ranshi, muddin kuwa batool tarasa ranta a silar shi, wlh shima sai yabi bayanta, duk irin ƙaunar da nake yi mishi, xan rufe ido ne da hannu na zan kashe shi. Inya so nima daga bisani in haɗiyi zuciya in mutu”

Zuciyar angel har wani tafarfasa take Yi, sam ba haka taso ba, ta yi niyar tayi mishi bugun mutuwa har saiya haukace, Amma sai ta haƙura ta ƙyale shi ganin irin yadda jini ya wanke fuskarshi, koba komai Ya ɗanɗani irin zafin da suka ji acikin zuciyoyinsu,

“Angel, ki tashi muje saman gado ki kwanta” girgixa kai angel tayi tare da cewa”Kibarni anan kawai, ba inda zanje yau sai naga abunda ya ture ma buzu naɗi,” gyaɗa kai hanna tayi tare da miƙewa ta juya ta koma saman gadonta ta zauna,..

Duk sunyi zugudum cike da zullumin awani hali batool take aciki, a lokacin da ba su yi tsammani ba, suka ga hasken ɗakinsu ya ɗauke, duhu ya mamaye idanuwansu, Da sauri javed Ya miƙe ya lalubo fitilunsu Ya kunna su, ɗakin yayi haske, yau fa ba bacci dare ya koma tamkar da rana, Jimamin rashin ƴar uwarsu suke ta yi, ba wanda ya damu da danish, gaba ɗaya sun manta da azeeza dake a sume Cikin ƙarƙashin gado,

Har dare ya tsala, babu wanda ya runtsa acikinsu, sai daga bisani ne, Haris ya lallashe su, har ya samu suka kwanta, shima ya kwanta zuciyarshi duk ba daɗi, yana matuƙar jin tausayin danish, amma haushin shi ya hana ya taimake shi, bashi kaɗai ba. Hatta sauran ƴan uwan nashi, duk sun damu. Da danish, tsoransu kada ya rasa ranshi,

Ganin sunyi tsit Yasa ta fara tunanin ko sunyi bacci ne, duk da tasan zaiyi wuya yau su iya runtsawa, sai dai su yi likimo, amma wannan duk bai dame ta ba, Don yau taci alwashin saita dura tagar nan kodan taje ta taimaki rayuwar ƴar uwarta, kamar yadda tayi alƙawari, bazata bari a lalata mata rayuwar ƴar uwarta ba, yunƙurawa tayi tare da miƙewa, taje saman table ɗinsu ta ɗauko fitila, Ta juya ta nufi cikin toilet ta buɗe ta shiga ciki, wannan karan ko jam lock bata sanya ba, a buɗe tabar ƙofar, domin kuwa jininta akan akaifa yake, Komai zai faru sai dai ya faru ko a mutu ko arayu,, tsakanin ita da danish, yau saita dura tagar nan, Ita kaɗai tasan irin ƙuncin da take ji acikin zuciyarta, bayan ta ajiye fitilar a ƙasa, da ƙarfi ta janyo bokitin ƙarfen ta jingina shi jikin bangon tagar, tana ƙoƙarin hawa taji motsin mutun ya shigo Cikin toilet ɗin, a waske ta juyo baya don taga wanene, Bata yi mamaki ganin shi ba, ai yanzu ta daina ganin shi a matsayin mutun, ita da taga zahiran ɗazu da jam lock ya cire kanshi,

A tsaye yake jikin shi duk ba ƙwari, wani abu daya ɗan ɗaure mata kai, Jini daya 6ata fuskarshi yanzu babu shi, aranta tace”nasan bai wuci shi ne ya lashe shi ba, tun da ɗazu ma naga yasha na batool, Maye kawai, ”

Yadda suke fuskantar juna, kamar abokan gaba ne suka haɗu a filin daga, banbancin kawai babu makami ahannun su,

Cikin muryar fushi tace”kada ka kuskura ka matso ku sa dani, because I can harm you, I hate you Danish, I don’t wanna see you, you are a bad person without faith and compassion,”

Muryarshi tamkar zai fashe da kuka yace”You should understand me, I am innocent, I am doing what is right……..” wata irin tsawa ta daka mashi yayin da take nuna shi da index finger ɗinta tace”ban damu da duk wani abu da zaka ce ba, wawa daƙiƙi, wlh rantsuwar ɗan musulmi, idan har ka kuskura kace zaka hana In dura tagar nan sai na yi maka mummunar illar da zata sa ka gaza takawa da ƙafafuwanka,”

A matuƙar ruɗe danish yake kallonta, baisan ya zai yi ya fahimtar da ita ba,

Ganin yana yunƙurin taka ƙafarshi xai tunkarota yasa ta takai hannu ta fusgi bokitin data ajiye ta ɗaga shi sama tana faɗin”Idan ka kuskura ka ƙara taku ɗaya, I will drop this bucket on your head idiot,” a wani irin raunace yake binta da kallo, duk da irin gargaɗin da take yi mishi hakan baisa ya dakata da yin tafiyar ba, yana tunkararta, ganin dai dagaske so yake ya hanata, aikuwa da sauri ta ajiye bokitin ta haye tare dakai hannu ta ɗaɗɗago da glass ɗin, Ta dure shi ƙasa, Tana yunƙurin hawa bisa tagar, Taji ya damƙi ƙafafuwanta daƙarfi, a ƙoƙarin ya janyota ta faɗo Cikin rashin sa’a ya zame wandon Jikinta gaba ɗaya ya sabule ƴan fararen cinyoyinta santala santala suka bayyana a suffarsu, saboda tsabar jaraba ko waiwayon wandonta bata yi ba, A haka ta dire tagar ta faɗa ta baya………………”

Ta tafi tabar danish a tsaye hannun shi ruƙe da wandonta, don ma Allah yasa rigar uniform ɗinsu tana da ɗan tsayi ta rufe ass ɗinta duka,

(Akwai gwarama ranar monday🤣).

*(Duk irin ƙoƙarin da nake yi wurin Yin typing da daɗi da ba daɗi, da alama wasu basu gani, duka 2 groups da nake sanya Takun farko ya zarce 2k members amma har yanzu paid group ko 200 bai kai ba, wai haka yanzu ina dab da kammala takun farko, bansan me kuke jira ba, koda yake akwai waɗanda dama jira suke agama su koma suna karantawa ta bayan fage 🤔,ƴan amana dai sunata biya su da suke so su karanta halal ɗinsu, ko ince su da sukasan Ciwon marubuta, waɗanda su ka yi payment sai sunyi hakuri dan idan nagama free pages zan ɗauki hutu na ɗan wani lokaci before in dasa, amma ba jimawa zanyi ba, fatan za’ayi mini afwa)*

*Ga masu son cigaba da Karanta Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne kacal, Labarin yanzu nake Cikin rubuta shi babu Complete sai dai ka biya asanyaka agroup inda zaka dinga samun update akai akai, Inka biya za’ayi adding naka a paid group kuma za’a sanyaka a comment section, Sa’annan Ba’a share Ko yin forwarding duk wanda yayi gigin fitar da littafin, akwai ta inda zamu ga sunan shi da alamar yayi forwarding to zamu cire shi a group ne👌 Kuma yaja ma kanshi zamu ɗauki mataki👌*

*Littafin Kurkukun ƙaddara 3 part ne, Yanzu muna gab da ending na Takun farko free kenan, Sai kuma Takun tsakiya wanda ya kasance na kuɗi ne, da takun karshe duk akan 500 zaku karanta shi*

*Ga wanda ya shirya Yin payment, ga details nan, Idan ka tura kuɗin zaka bamu shaida, Bamu kar6ar kati, Ta bank ake turawa ko ta pos, In yaso saika ɗauko hoton reciept ka tura mana*

*3196407426*
Bature Hafsat Muhammad
First bank

*Zaka tura da shaidar Biyanka ta wannan Numbers ɗin (0816985 6268) ko kuma ta (08103884440)*

*Kada Ku bari A baku labari💃 Salon na daban ne🤩*

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button