Sponsored Links
Hausa NovelsJarababben Namiji Hausa Novel

Jarababben Namiji 89-90

Sponsored Links

89 – 90*

Amma tantarwai ko ina yike kamar rana,ga yara ‘yan k’anana dake ta wasanninsu a k’ofar gidajensu …kasa daurewa maryam tayi saida ta 6ara tayi magana “baby kajibi yara k’arfe nawa na dare suna wasa a waje basu tsoran a sace masu yara,kaf cikan sufa ba mai shekaru bakwai .
Ga gari ko ina duwarwatsu ni tsoroma zanji in na d’aga kaina kalli wainnan bak’ak’en duwarwatsun.”😄

“Hhh babe akwai tsokana to aibaki saniba da darana mukazo mutum 1 bazaki ganiva sai masu hidimar gidaje saboda garin akwai bala’in zafi ,bama iya fitowa,anjuyane yanzu shine lokacin mu,tamkar rana muke kallon sa,kuma sa’udiyya ba kamar sauran k’asashe bane akwai tsaro sosai”

Jinjina kai kurum tayi”lallai duniya juyi juyi,haka kowa da kiwon da ya kar6esa.”

Sun samu karramawa ta musamman ilahirin mutanen gidan suna falo zaman jiransu,suna sallama kuwa,d’uuuu sukayo kansa suka rungume kotakan ta basu biba…sai Abby ne ya kamota

“Kun kamo wannan garjejen kun rungume, Kun bar bakuwa sagale da hannu.”
Gabadaya yaranne suka yo kanta ,banda uwar gayyan
“Ayyah anty we are sorry. ..yayan ne mun dad’e bamu gansa ba”

Murmushi tayi tana satan kallan ummy raudha “ayyah bakomai”
Jan hannunta sukayi bayan an gaggaisa suka kaita d’akinsu

“Anty ki zauna anan tare damu ko?”
“Uhm ”
Zaro ido sukayi “uhm what? Me uhm yike nufi? Baki yarda ba ” “no i agreed” tsalle sukayi suka rungumeta

“Shikenan munajin dad’inmu…anty kiyi wanka and freshing up,kizo muci abinci mu fita yawo”
“To sarakan yawo ba inda zataje baku ganin ta gajine…yanzufa mukazo k’asar,ai kwa bari sai gobe ….”
Duddurke k’afa suka shiga yi “Yaya mune mayawatan?”
“Yes a ba mata na waje ta kintsa”
Fita sukayi suna tsallen murna kamar k’ananun yara. . ada suna jin haushin ta amma yanzu kallon farko sukaji sonta a cikin ransu

D’aga ido sama tayi tanayuwa Allah godiya
“Nasamu kar6uwa a wajen ‘yan gidan duka ,saura uwar gidan”

Matsowa kusa da ita yayi ya rungumota…”baby ya kika ga family na?” “Hmm sun burgeni ina sonsu”
“Kowa yaganmu sai ya so mu , haka kuma kema kike”
“Aah ni awa? Ga larabawa me za ayi dani bak’ar fata”
“Come on, karki wulakanta mun ke” sassauta murya yayi “baby inaso zan ci?”
“Hmmm zakaci me?”
Kashe mata ido d’aya tayi kafin ya shafo mararta “nan nike nufi”
Zubut ta mik’e “wa? Kai baka gajiya? A gidan mutanen? To bazan iya ba”

Dariya ya saki zai magana aka turo kofan ,dan sunkuyar da kai yayi yina sosa k’eya .

Dallara masa harara tayi
“Sai ka barta tazo d’akina mu gaisa a tsanake kawani zo ka kanainayeta”
“Mom kin daina sona ashe?”
“Eh d’in tafi bani waje,kinga d’iyata zo muje”
A sullu6e ta taso ta biyota.

Rungumo kafad’arta tayi suka wuce can part dinta

K’ulhuwallahu ta tofe ta dashi k’afa uku
Da li’ilafiy

Tambayoyi kam tasha shi Kala da kala ,wani tasan amsa wani tayi murmushi ta duk’ar da kai,saita harbitsa mata ingausan larabci da turanci .

Tayi observing d’inta tas tayi, akwai lack of knowledge a tare da ita saidai tanada kunya da kawaici ,sosai tayiwa julayb sha’awarta…abunda ya Kamata shine a bata training
Don haka dole ta zauna tare da ita kamar yanda bazata bar yaronta ya kuma tafiya ya barta ba

Topah ya kenan,mairo tazo sa’udiyya ba hanyar komowa …….

 

 

 

 

 

Oum Aphnan
[3/14, 07:14] Bamalli✌️: *JARABABBEN NAMIJI*

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button