Sponsored Links
Arubuce Ta Ke Hausa NovelHausa Novels

Arubuce Ta Ke 96

Sponsored Links

Page 96

Wata wawiyar ajiyar zuciya ta saki tana samun nutsuwar ruhi da gangar jiki sanda taga sun dauki hanyar kaduna,duk da jikinta babu wani qwari sosai saboda zazzabin daya gallabeta,amma at least ta samu wani sassaucin.

Dan waiwayo yayi kadan ya dubeta,sannan ya cire hannunsa guda daya daga kan motar ya kama dogon hancinta yadan ja

“Hankalinki ya kwanta ko?” Saita sakar masa murmushi, murmushin da yayi masifar kewarsa,yaketa kuma struggling na ganin tayi shin amma bai sameshi ba sai yau.

Tun basuyi nisa ba ta soma bacci,wani irin nannauyan bacci da shi kansa abbas din ya dinga kallonta,ko sau daya baiyi.marmarin tashinta ba,baccin ma datayin dadi yayi masa,aqalla yasan zata rama bashin baccin da batyi ba kwana biyu,sai ya kunna radio station yana sauraren labarai,da sauran programs da suka jibanci harkokin tsaro,da ya gaji ya maida karatun qur’ani,wanda ya qarawa baccinta dadi sosai,baccin da bata farka ba sai da suka isa kaduna.

Tun daga wannan ranar bata sake binsa bauchi ba,don ko cewa yayi zasu weekend yanzu zata rage walwala,gaba daya garin ya fita a ranta,shima bai takurawa, don asalinsa ba mutum bane mai takura da tsanani akan abu bane,sai ya barta yaje yayi kwana biyu ya dawo,har kusan watanni uku.

Cikin hakan bikin diyar yaaya bara’atu ya taso,ya gaya mata,duk da bataso amma ta gaza nuna masa,yana da tsananin kirki da karamci,yana mata kyautatawar da duk duniya baya ga ummu bata ganta a wajen kowa ba,wannan ya sanya duk wani abu da tasan bayaso ko zaiji babu dadi take nisantarsa(bawai don tasan muhimmancin hakan ba,kawai saboda yadda kyautatawarsa taje da nauyi a idanunta).

Kaya ta fitar ta bayar akayi mata dinkuna masu kyau, zuciyarta duka babu dadi,cike da tsanar bauchin amma haka ta dinga shirya,duk da tana boyewar amma ya karanci akwai abinda ke faruwa,don kuzarinta ya ragu,a sanyaye take komai.

Ana gobe zasu tafi da daddare,yana zaune kan sofa bed yana shan black tea din data hada masa ita kuma tana rufe wata qaramar jakarta data zuba qananun abubuwan amfaninsa da tasan zai buqata,duk inda ta gifta idanunsa yana biye da ita,baya gajiya da kallonta,barin yau din da tayi kwalliya ciki wani mini skert da wata riga da sukayi matuqar karbarta,zuwa lokacin komai nata ya cika yayi yadda akeso ya zamana a jikin diya mace,ta zama wata ‘yar duma duma da ita,haske da laushin fatarta ya qaru,hakanan tsahon gashinta cikarsa dama baqinta,lips dinta ya qara zama pink sosai haka idanunta sun sake fitowa,ta fannin mu’amalarsu ya sake zama wani mayenta,shi kansa baisan yadda akayi ya sake horancewa ba,baiqi duka dare ya dinga kasancewa da ita ba,baya gajiya da ita,wata baiwa ke gareta ta musamman mai dimauta tunanin mutum,saidai widad din tashi har yanzu raguwa ce,batayi qwarewar da yakeso tayi ba,kullum hakan ta kasance sai yayi zaman lallashi,shagwabarta da sangarta take zube masa,shima sai ya biye mata.

Ajjiye mug din hannunsa yayi yana fakon isowarta,aikuwa tana zuwa giftashi ya sanya hannu ya fincikota jikinsa,yayi mata kyakkyawan masauki saman cinyarsa dake bayyane a waje cike da gargasa,hannuwansa ya saka ya zagaye qugunta dasu ya sake matso da ita sosai,ya saka fuskarsa a tsakiyar dukiyar fulaninta yana shaqar qamshin dake fita a wajen.

Hannu ta saka ta riqe kansa,tana jin tsigar jikinta tana tashi saboda yadda labbansa suka sauka a wajen,ta saki dariya tana janye jikinta baya,ya daga idanunsa da suka fara sauya launi yana murmushin shima ya kalleta

“Kamar baki shiryawa zuwa bauchin nan ba” kanta ta langabar gefe,a zahiri batason zuwan,amma bai kyautu ta nuna masa ba,saita girgiza kai

“Aah,kawai kasala nakeji kwana biyun”

“Nayi noticing canji da yawa,kin koyi bacci,sannan ga overdose kyau baby da kike qarawa,overdose dad……” Hade bakinsu tayi waje daya yau da kanta,don batason ya qarasa fadin kalmar,bala’in sakata jin kunya takeyi,hakan da tayin saita tafi dashi wata duniyar ta daban,tasa ya dimauce ya mance dukka maganar da zai fada din,sanda zata qwace kanta kuma yace baisan zance ba,sai da ya cimma gaci sannan ya samu nutsuwa.

Washegari da wuri suka isa,don sha biyun rana ma a can tayi musu,sassanta ta wuce kai tsaye,gidan duk bai mata dadi ba saboda su mimi basa nan,hajiya tasa anzo an daukesu,an musu kitso da qunshi kamar yaran kowa,an kuma dauki kayansu sai bayan biki zasu dawo.

Wannan karon hafsat din bata hana ba,bata ma isa ta hana din ba don tasan abbas din ko zai jure komai banda wannan,kuma kai tsaye shi yayi kiranta yace ta bada yaran,ta hada musu tarkacen kayansu,gasu dai a ido masu kyau da tsada ne,amma dauda da rashin kula duk sunci mutuncinsu.

Tsaye hajiya tayi kawai cikin takaici tana qarewa kayan kallo,banda ma gidan yana samun feshin maganin qwari da kuma gyaran da uban kewa dakin nasu duk sanda ya samu chance….ta tabbatar ba za’a rasa wani qwaron a ciki ba,hajiyan nada masifar tsafta,sai tattara kayan tasa akayi aka bayar,banda ma masu tsada ne da kuma sauran qwarinsu qazanta ce ta cinyesu,a wajen hajiyan bola ce tafi kamata dasu.

Har ta fitar da kudi ta bayar za’a sake musu sabuwar siyayya mimi tace akwai wasu kayansu a wajen anty widad.

Hajiyan da kanta ta kira widad din tace mimi tace suna da kaya a wajenta,ta fiddo musu dasu umar zaizo ya karba,tana shiga sassanta kayan ta fara hadawa,a killace a tsaftace a kuma goge,umar din ya karba ya tafi dasu.

Tunda ta sauka gidan ranta yayita baci,gaba daya kamar an tattaro dukka bacin rai an aza mata,haka ta dinga dannewa,ta hau gyaran sashen nata,sai data tabbatar komai yayi neat din ta sake wanka ta canza kaya,ta dauki wayarta ta kira abbas don tanason zuwa saloon da qunshi,na qafafunta duka sun fita,kuma batason shiga mutane haka,abinka da farar fata, babban adon hannayensa da kyan ganinsu ayi musu qunshi.

Lokacin yana tsaye a qofar toilet yana amsa wayar Jasmin yana jiran hafsat dake ciki ta gama wanke masa zai shiga saboda dan uban qurar daya hada,bata damu ta shiga ta gyara ba,sai ya bawa Jasmin excuse ya katse kiran nata ya daga na widad din.

Cikin shagwabar nan tata dake sake narkar dashi tace

“Uncle”

“Babyn uncle” ya amsa mata tattausan murmushi yana subuce masa,sunan da hafsat taji ya kira saita miqe tsaye dafe da cikinta ta kasa kunne tana sauraren hirar

“Zanje saloon da qunshi,kaina da hannuwana duka ba dadi”

“Ba laifi,amma baby……ina kishi fa gaskiya,ki zaba duk inda kikeso zan sa a kira miki su har gida special services mana” kafada ta noqe,ita zaman gidan ne bataso har ga Allah

“Don Allah uncle,yaushe rabon da nazo bauchi” ta fada da wata irin narkakkiyar shagwaba da har data sakashi lumshe ido ba tare daya shirya ba

“Shikenan,ki shirya zan fita headquarter yanzu,sai mu biya”

“Thank youuuuuuu” ta fada tana dariya

“You are welcome” ya amsa yana sauke wayar sannan ya sake kiran Jasmin yace mata zai shigo nan da minti talatin.

Sauri sauri tayi ta gama wankewa ta fice ta bashi waje,ya shiga ya hada ruwan wankansa da kansa,abinda bai sani ba kenan muddin suna tare da widad.

Sassanta ta nufa tana sakin ashar cikin zuciyarta,ita ta dauka ma wannan karon shi kadai yazo,ashe sai data sake biyoshi,akwai sauran rina a kaba kenan?,saita jinjina kai,ta buda wardrobe dinta ta fiddo kayan sawa,sannan ta buda bandakinta ta shiga ta fara kwaskwarima.

Cikin wata doguwar rigar atamfa da tayi mugun budewa daga qasa ta shirya,brown ce mai adon blue black,tayi amfani da blue black hand bag veil da kuma takalmi,kalar ta haska farar fatarta da kyau, daurin da tayi wanda ta kawoshi gaban goshi ta fidda gashinta ta qasan daurin ya qara mata wani irin kwarjini,ko yaya ta motsa jikinta qamshi yake fitarwa.

Saboda saurin da take ta fita a gidan ta rigashi isa parking lot,tayi tsaye jikin motar tana jiran fitowarsa,wayarta sabuwa da ummu ta aiko mata da ita a hannunta suna hira da bilkisa ta watsapp,tana ta kwasan dariya,don bikisa din ba daga baya ba,ko yaushe qoqarinta taga ta dora widad din kan hanya,ta kuma ganar da ita wace hafsat.

Cikin wasu lafiyayyun indian blazers ya shirya blue black din shima,tamkar yasan color din da zata saka kenam,tun daga nesa kwalliyarta ta tsone masa ido,ya zuba mata dukka idanun nasa yana takowa a hankali,ko qifta idanunsa a kanta qyashin yi yakeyi.

Cikin jikinta taji yana wajen,saita daga kanta ta sauke a kansa,kamar shi,itama kwalliyar sa tatafi da ita ainun,yayi wani mugun kyau,ya koma yaro sosai da bai wuce sha tara zuwa ashirin ba,murmushi ya subuce mata,bakinta ya dinga motsawa tana jiran ya qaraso ta tsokaneshi,saidai dab da zai qaraso din hafsat ta bayyana,ta kwaso sauri cikin baqar abaya data saka ta yafa baqin mayafi wanda ya kasa zama a kafadarta saboda sauri dason ta cimmasu kafin sukai ga fita.

Ganinta sukayi kawai tana kiciniyar bude gaban motar tana cewa

“Banajin dadi abban mimi,ka miqa ni asibiti don Allah” tayi maganar tana shigewa gaban motar.

Da kallo dukkansu suka bita,widad ce ta fara dauke kanta kamar bata ga abinda tayi ba,sai ta matsa ta dauke handbag dinta dake saman motar ta juya zuwa cikin gida

“Ina zuwa kuma?” Dan dakatawa tayi da tafiyar

“Na fasa zuwa ne” iska ya furzar

“Aah,kizo Muje na fara sauketa saina qarasa dake” kai ta girgiza

“Um um…..naje ko gobe ko jibi” ta fada tana qoqarin boye damuwa sa fushinta,kawai ba zata iya hada mota da hafsat din ba,kallo daya tayi mata tasan neman rigima ya fiddota,dazun da umar yazo karbar kayansu mimi taji yana wayar jiya yakai hafsat din asibitin awo

“No….,wuce muje” ya fada yana takowa inda take tsaye,yana karbe jakarta daga hannunta

“Uncle…..”

“Wai ba magana ake dake ba!…..yara suyita musu da na gaba dasu,kaga abban mimi just leave her mu tafi kawai” hafsat ta fada cikin tsawa,bayan baqincikin yadda taga yana lallabarta hadi da riqe mata jaka ya saukar mata ya tsaya mata a qirji.

A sukwane widad din ta waiwayo tana jin wutar dai dai take da ita a yau tana tashi cikin kanta,fes ta kalleta ido cikin ido,cikin lallausar muryarta a nutse ta amsata

“Sorry mommy….bafa dake nake ba……da uncle dina……au mijina na,da mijina nake magana”[3/22, 8:25 AM] +234 813 343 4840: *H U G U M A*

*_A RUBUCE TAKE_*
(K’addarata)
*Arewabooks:Huguma*

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button