Sponsored Links
Arubuce Ta Ke Hausa NovelHausa Novels

Arubuce Ta Ke 66

Sponsored Links

Page 66

 

Sun dauki mintuna a haka sannan ta daga kanta suka hada idanu,shima ita yake kallo,haka kawai taji wata kunya ta kamata,saboda kallon da yake matan ya mata nauyi sosai a gangar jikinta da zuciya,hakanan bata saba ganin kalar kallon ba a tattare dashi,saita cusa kanta a qirjinsa tana shaqar wani bala’e’en qamshi da fatarsa ke fiddawa

“Eheenn…..baby na ta fara sanin kunya ne?” Tambayar data sakata ji kamar zata nutse,sai kuma ta janye jikinta da sauri tana fadi cikin fidda idanu waje

“Hajiya!” Dukkansu bin falon sukayi da kallo,ba hajiya babu burbushinta,sai suka kalli juna a tare,kafin yayi komai ta rigashi miqewa tana narke ido

“Hajiya fa uncle” amsar da shima bai santa ba,yasan dai yana gaba tana biye dashi,komawa tayi ko ciki ta shige.

Tare sukayi hanyar dakinta,suna zuwa widad din ta lafe daga bakin qofa,shi ya tura ya leqa,saiya samu hajiyan zaune cikin dakin daga qasan carfet ta miqe qafafunta

“Oh,hajiya kina ciki kenan” ya fada cikin jin kunya da nauyi yana shafa kansa,mazewa tayi kamar ba abinda ya faru

“Wallahi,kasan ko yaya tafiya take ba’a rasa jiki da gajiya,kaima ya kamata ka shiga ciki ka huta hakanan,sai Allah ya kaimu anjima”

“To hajiya a huta lafiya” ya fadi cikin jin nauyi,sai data murmusa sannan ta amsa mishi,ya maida qofar ya rufe sannan ya juyo suka hada ido da widad din.

Qwalla ce ta cika mata idon tana dubansa a shagwabe

“Ban mata sannu da zuwa ba”

“Tace ta yafe,naje na huta,anjima saina rakoki ko?” Kafada ta maqale alamun bata yarda ba,sai ya qara taku ya matsa ya buda qofar kadan

“Shiga to ku gaisa” nan ma ta sake maqale wuya,sakin qofar yayi ya koma da baya ya rungume hannayensa yana kallonta

“To ya kikeso ayi?” Hawayen dake maqale ne ya sauko mata

“Ba kaine ba……kaine ka jawomin Allah” dariya ta taso masa,ya murmusa yana kallonta

“Ni me nayi tsakani fa da Allah” kuka ta sake masa,da sauri ya kalli qofar dakin sannan ya dawo da dubanshi kanta,ya tako da hanzari ya iso gabanta

“Sorry….. sorry,kiyi shuru mana please,kafa hajiya taji,nayi alqawari zan rakoki,zan kuma gayawa hajiyan laifin nawa ne shikenan?” Kai ta gyada masa,sai ya saka hannu a aljihunsa ya fidda handkerchief ya soma dauke mata hawayen,idanunsa na manne da manyan fararen idanun nan nata dake yawan daukar hankalinsa,ya jima baiga abu mai daukan hankali kamarsu ba,daga bisani ya sauke dubansa kan mitsitsin labbanta jajaye da taketa motsasu kamar zatace wani abu,tsigar jikinsa ta zuba,ya dauke idonsa daga nan yana cije labbansa,ya gama yaja baya jikinsa na wani irin mutuwa,ko a ina ta samu irin wannan fitinannen turaren?.

Kasa jurewa tayi ta jashi zuwa dining tana buda masa abubuwan data dafa,a mamakance yake kallonta,baiyi shakka ba saidai mamaki,yasan halinta a dan zamansu bata qarya,at last ya rasa me zaice mata

“Bari na huta,ki zaba duk abinda kikeso idan na bude jakata a matsayin gift na wannan abincin” murmushi tayi

“Ni hajiya nayiwa fa”

“Ya salam” ya fada a qasan ransa yana lumshe idanu, yarinyar ta gama dashi,yasan ta fada ne har ranta da kuma quruciya,batasan hajiyarsa itace weak point dinsa ba

“Yes…..i know, that’s why nace ki zaba duk abinda kk so,hajiyata duniya ta ce,itace komai nawa” kai ta gyada masa tana murmushi

Wanka kawai ya sakeyi,ya shirya cikin toilet don kada ma tace zata masa bore,lallabawa yakeyi,yana da buqatar ta a kusa dashi sosai,ko bata kawar masa da qishirwarsa ba dumin jikinta zai masa amfani ko yaya.

Gadonsa ya haye yana lumshe idanu,qamshin da bedsheet din ke fitarwa har cikin jininsa,idanun nasa a lumshe yace

“I hope ba muneera kika bari ta shigo dakin uncle ba” kai ta gyada tana murmushi

“Anty widad ce” sosai ta bashi dariya,har sai daya bude idanuwansa a kanta yana kallonta,tana da wani irin salo da yake sauke masa komai na daga gajiya da bacin rai,yayi mamakin yadda ta iya duka wadan nan aikace aikacen,komai na gidan ya zama akan saiti

“Anty?,su anty manya” ya furta cikin salon tsokana idanuwansa suna lumshewa sakamakon dankwalin dake yafe a kanta ya silale ya fadi,sassalkan gashinta da aka masa wani irin nadi jiya a saloon ya bayyana kansa.

Da fuskar shagwaba ta kalleshi,abinda ya qarawa cute baby face dinta kyau matuqa

“Ni din ko?,ni ba anty bace?”

“Wait….kinaso a dinga kiranki anty?” Kai ta gyada

“Good,zan koya miki wani abu,indai kika tsaya kika iya kike yimin,ba anty ba…..har mommy za’a ce miki” ya qarasa fada yana lumshe idanunsa,cikin zumudi take kallonsa

“Yes,na yarda uncle”

“Good…..bari na huta sosai tukunna…. Amma,zo muga wannan gyaran kan naki” ya fada yana yfitota da hannu muryarsa na qara yin laushi,bata kawo komai a ranta ba ta rarrafa zuwa gabansa,ta kuma miqa masa kan tana jin dadin yabawar da yayi

“Anty rose ce ta kaini fa,tacemin ka taba cewa zaka kawo madam ayi mata irinsa dama”

“Yeah” ya fada da qyar kamar mara lafiya,ya tuna lokacin,hafsa yaso kaiwa,tace bata da wannan lokacin, infact ma tace zaman banza ne da bata lokaci,saboda koda anyin zai yamutse shine da zarar sun dawo,ya kuma sakata zuba ruwa akan,shikenan ya tashi a aiki,gwara ya bata kudin taje ayi mata kitso ko wani gyaran mai sauqi.

Ajiyar zuciya ya sauke,ya saka hannayensa gaba daya ya birkitota jikinsa,a dan tsorace tayi yunqurin tashi,muryarsa a kakkarye yace

“Don’t…..do me a favor please,bacci nakeji ki tayani,ko kin fita ma na tabbata ba kowa,just one hour kawai” wani irin abu taji yana mata yawo cikin jikinta a sanda yake maganar wanda ya zare mata duk wata laka ta jikinta,sai kawai ta maida kanta saman dantsensa dake cike da muscles ta kwantar,a hankali ya nutsa yatsun hannunsa cikin sumarta, numfashin ya fusga da kyau kamar zai qwace ya samu ya nemoshi,sai ya cure jikinsa waje guda,yayin da widad din tayi lamo tana jin faduwar gaba da fargaba.

Tafiyar tsutsa yaci gaba da yi mata saman kanta yana yamutsa gashin da kyau,qamshi da santsinsa yana bashi wani salon nishadi,bai farga ba sai ji yayi tana sauke numfashi a hankali,daya duba yaga bacci ne ya dauketa,ya saki murmushi a hankali yana gyara mata kwanciya cikin jikinsa,ya tabbatar itama akwai gajiya a tattare da ita,don iya ayyukan daya gani tayi ba qaramin qoqarin gasken gaske tayi ba,baima taba kawowa kansa zata iya ba,ko makarantar da rose din ke kaita ya barshi ne kawai suna fita saboda rage zaman kadaici bawai don a koyo komai ba,ashe abun ya wuce yadda ya daukeshi.

Basu hadu da hajiyan ba sai washegari,saboda ya riqeta a dakinsa,tunda hajiyan ta shiga dakin itama bata fito ba, muneera ce ta debo musu komai takai daki,shima ya dauki sauran yakai musu dakin,daga qarshe sai daya kira hajiyan a wayarsa,tace ta bari sai goben sannan ta haqura,saidai fa gaba daya jinta take cikin wani sabon yanayi,ko yaya ta motsa idanunsa yana kanta,duk bayan wasu mintuna sai ya jangwalo abinda zai bada connection a tsakaninsu,tanata zamewa amma kamar sake diga danqo take a tsakaninsu,shi kansa baisan me yake faruwa ba.

Tare sukayi breakfast a falon, muneera da widad nata gyaran wajen hajiya ta dubeshi

“To nifa yau sai gida” da mamaki ya kalleta

“Ah…haba hajiya,ki bari ki qara koda kwanaki uku ne mana,sai mu wuce tare ko?” Kai ta girgiza

“A’ah abbas,ai tunda komai ya kammala zaman me kuma za’a yi?,gwara na koma gida na nima nafi hutawa sosai” kafewa tayi tace bauchi zata tafi,da qyar ya sha kanta ta bari sai gobe,idan yaso sai su wuce gaba daya,da wannan maganar da sukayi ya wuce daki yace zaiyi wanka ya fita headquarter ya bada report na dawowarsa,zai kuma sake daukan excuse na three to four days.

Ya fidda dukka kayan jikinsa yana daure da towel wayarsa ta dauki ringing,ya dawo da baya yana duba me kiran hannunsa a qugunsa,hafsat ce,yayi mamakin ganin kiran nata,tun randa yayi alqawarin bazai sake kira ba bai kuma din ba,hakanan itama koda wasa bata kirashi ba,komawa yayi ya jingina da mirror din dakin ya daga kiran tare da yin sallama,sannan yayi shuru yana jiran jin dame tazo.

Kamar ba zata tanka ba bayan ta amsa sallamar sai kuma tace

“Au ashe kun dawo”

“Eh” ya amsa mata a taqaice,abin ya sake bata ranta

“Yanzu kayi tafiyar wata guda,ka dawo qasar amma ka kasa gayamin ka dawo abban mimi,adalci kenan hakan?” Maimakon ransa ya baci baisan murmushi ya kubcewa fuskarsa ba,rainin wayonta ya fara yawa,idan tayi wani abun kamar zautacciya

“Ai baki da buqatar jin komai daga gareni,so kinga baki da matsala dani”

“Haka ma zaka ce?,duk abubuwan daka yimin kai baka gani?,kullum nice mai laifi a wajenka,kayi tafiyarka daga wajen wata,ka tashi dawowa ka sake sauka a wajenta ba tare da nasan ma ka dawo ba sannan ace ana kyauta min” saita fashe masa da kuka kawai,shuru yayi yana saurarenta,tasan weak point dinsa ne,amma bazai yarda ta raina masa hankali ba,don haka ya aje wayar saman mudubi kawai ya rabu da ita,duk da yana saurarenta.

Jin tanata faman sharan majina baice mata komai ba ya kuma tunzura mata zuciya,kukanta banza shirunta banza kenan?.

“Laifi nane da nayi kiranka” ta fada tana shirin kashe wayar

“Wait…..am on my way tomorrow” baiji ta amsa ba,tadai yanke kiran,duk da haka ya tura mata gajeran saqo saboda ya fita hakkinta yana sake jaddada mata,ya aje wayar saman mudubin yana fidda iska daga bakinsa,hafsat…..hafsat…..ya yarda jarrabarsa kenan a rayuwa,ya taka zai shige bandakin sai yaji an turo qofar,yadan tsaya daga bayan labule kadan saboda yasan me shigowar,kuma tabbas idan ta ganshi a haka komawa zatayi qila harda gudu ma.

Tana ‘yan waqenta ta shigo,ta cire hular data rufe sumarta,ta zare underwear dinta,ta soma tattare doguwar rigarta zata cire ya motsa,don yasan matuqar ta cire qarshe idan ta ganshi tace shi ya jawo mata kuma ba zata yarda ba.

Da sauri ta saki rigar, saidai saura data rage ta tattare saman qirjinta dake tsaye cas,idanunsa suka sauka a wajen,yaji wani abu ya tsarga masa,tun daga saman kansa har yatsun qafarsa,kamar sunfi yadda ya taba lura da girmansu.

Kallon da yake mata da kuma a yadda ta ganshi ya sakata juyawa zata bar masa dakin,taku uku ya isketa,ya jawota cikin jikinsa yana jin yadda jikin nasa ya fara rawa,duk yadda yaso yayi controlling kansa kada yakai hannunsa saman jikinta a yau ya kasa,karon farko a rayuwarta da hannu ya taba kaiwa saman qirjinta,suman tsaye tayi da farko,don yayi mata mugun ba zata,yayin da shima yayi kusan mutuwar tsayen,saboda saqon da suka bayar zuwa ga kowacce gaba ta jikinsa,sun masa ba zatan shima,ya samesu fiye da yadda idanunsa ke wassafa masa.

Motsa hannayensa daya fara yi ta wajen ya maido mata dukka wani tunaninta,kamar yasan ihu take shirin masa ya birkitota ya hade bakinsu waje guda, hannayensa kuma naci gaba da abinda kwanyarsa ke qawata masa.

Wani irin tashin hankali ta shiga,ya matseta gam,ba damar ihu ko motsin ceton kai,sai kawai hawaye suka balle mata,tun tana sanya ran yanzu zai saketa harta saare, yaci gaba da aike mata saqon daya dinga sanyata jin kamar zata mutu[3/15, 9:35 PM] +234 704 440 6400: *H U G U M A*

*_A RUBUCE TAKE_*
(K’addarata)
*Arewabooks: Huguma*

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button