Sponsored Links
Arubuce Ta Ke Hausa NovelHausa Novels

Arubuce Ta Ke 67

Sponsored Links

Page 67

Kusan a manne fuskokinsu yake,yanajin saukar hawayenta,amma kuma bazai iya dakatawa ba,saboda wannan ce kadai hanya guda daya zata rage masa zafi,ya gwammace yayi duk wani kalar rarrashi da zaiyi daga baya.

Ya kusa minti goma w offsha biyar a haka sannan jikinsa ya saki gaba daya har ta samu ta qwace kanta tana masa kuka sosai.

Da qyar idanunsa ke buduwa,yana zube a wajen yana kallonta,ta koma gefe ta rakube tana kuka sosai,saboda qirjin nata dake mata zafi,haushinsa sosai ya cikata,taji kaman ta bude ido ya ganta a wani wajen ba a nan ba.

Sai da energy dinsa ya dawo sannan ya tattara qarfin nasa ya miqe a hankali,ta runtse ido sanda yake gyara zaman daurin towel dinsa,ya tako qafafunsa a nutse ya iso gabanta ya tsugunna dab da ita,ta qurewa bango amma baya takeson ta sake ja

“Relax…..am sorry kinji” harara takeson balla masa amma kuma yayi mata kwarjini da yawa, maimakon haka saita maida fuskarta tsakanin qafafunta ta boyeta,tun yana tsugunne sai daya zauna sosai yana lallashi,daqyar ya ciyo kanta,ya hada mata ruwan wankan ta shiga bandaki ta fara yi,data fito sanye da zumbulelen hijabinta tana ta qunci,tace ita ba’a nan zata shirya ba,salin alin ya bude mata qofar dakin ta fice dakinta.

Da baya ya sake komawa ya zauna yana murmushi,wani nishadi ya samu kansa a ciki,ya yamutsa sumarsa sosai kwanyarsa na dawo masa da duk wani wani second daya daya shude sanda take cikin jikinsa

“Oh my goodness” ya furta a hankali,ko a yanzun yana iya jin qamshinta cikin fatarsa,wani irin softness jikinta yake dashi irin wanda bai taba jin kamarsa ba,ya buda dukka tafukan hannayensa yana tuna santsi da laushin gashinta,saiya maidasu ya cure waje daya zuciyarsa tana jin inama zai sake samun wannan chance din.

Kusan awa guda ya bata a zaune a wajen yana karanta tunanin baya,da qyar ya miqe yayi wanka,amma sai ya kasa fita,ya koma falo ya zauna ya tsiri hira da hajiya,hakan kuma ita sai ya takurata,saboda abinda ya faru a tsakaninsu ba mahalukin daya taba mata irinsa,duk giftawarta idanunsa a kanta,daga qarshe ta haqura tayi zamanta a kitchen tana tsara me zata dafa musu yau da abinda zasu tafi dashi hanyar bauchi gobe,bai fita daga gidan ba sai da akayi sallar azahar sannan ya wuce headquarter din tasu.

Daren ranar qiri qiri taqi yarda ta kwana a dakin,hajiya nata mata hannunka mai sanda, har ta fahimci bata gane ba tayi mata quru quru

“Zan tafi hajiya,bari mu gama hada kayan naku” haka ta yita cewa hajiyan,tun tana idanu biyu.har bacci ya dauke hajiya,hakan ya bata damar yin kwanciyar ta hankali kwance saman babban bargon data dauko ta shimfida a qasa,don sun barwa hajiya gadon.

**********K’arfe tara na safe sun kammala shirinsu gaba daya,suja farfajiyar gidan ana shiga da kayansu booth din motar da zasuyi tafiyar,widad da muneera na tsaye daga gefe har aka gama,motar nada wajen zama biyu,sai wajen zaman driver,hajiya ce ta fara shiga seat din da yake da maqotaka dana driver

“Bazan shige ciki ba abbas saboda qafata”

“Ba matsala hajiya yayi hakan” yana shirin yima muneera magana kan ta shiga gefan hajiya sai weedad ta fara takowa,tsaf ya fahimci abinda take shirin yi,jiya kawai dama kawaici yayi mata,a yanzun sai yayi kamar bai ganta ba,sai da tazo daf dashi ya sanya hannunsa ya riqe hannunta da kyau,baiko waiwaya ba bare kayi zaton ya riqeta din,cikin sauri ta daga kai tana kallon fuskarsa,yasha muur da kyau,baiko kallon sashen da take kamar bashi bane ya riqeta.

Gyaran murya kadan yayi sannan ya kira muneera yace ta shiga gefan hajiya

“Saura ki saki baki kima mutane bacci ki barta da kallon hanya” murmushi ta danyi

“Bazanyi ba uncle in sha Allah” hannu yasa ya rufe murfin motar,ya bude seat din baya sannan ya waiwaya ya kalleta.

Cikin sa’a itama shidin take kalla, idanuwansu suka hadu waje daya,har cikin jininsa sai da yaji wani abu mai kaifi ya saukar masa,ya kuma baza saqonsa zuwa kowanne sashe na jikinsa,ya sake dawo masa da sweet memorie dinsu na shekaran jiya,wannan ya sake sanyawa gaba daya jikinsa ya amsa

“Shiga” ya fada da mugun sanyi,narke fuska tayi sannan ta matsa ta shige yabi bayanta,ya maida murfin ya rufe sannan ya yiwa samuel da suka saba yin tafiyar dashi magana kan ya tashi motar suje.

Gefe daya na motar ta rakube,gaba daya fuskarta a narke take,kamar wadda ke jiran qiris ta sanya masa kuka,yi yayi kaman bai fahimta ba,sunata hirarsu shi da hajiya,har taji shurun widad din yayi yawa

“Widad ko.tayi bacci ne?” Hajiyan ta tambaya ba tare data waiwayosu ba,sai sannan ya juya inda take zaunen,tausayi ta bashi da kuma dariya amma ya danne,suna hada ido sai hawayen da take maqalewa ya sauko,ya miqa hannunsa ya lalubo tafin hannunta,duk da yadda take faman boyonsa ya sanya shi cikin nasa,sannan a hankali ya janyota zuwa kusa dashi ya hade duk wata tazarar dake tsakaninsu sannan ya amsawa hajiyan a ladabce

“Idonta biyu hajiya”

“Au to madalla”.

Tun basuyi nisa da tafiyar ba bacci ya dauke hajiya,muneera ce kawai ta rage wadda taketa game da wayar hajiyan,har a sannan tafin hannunsa yana cikin nata yana yamutsawa,santsi da laushinsa ke haifar masa da wata kasala ta daban,maqoshinsa gaba daya ya bushe,ya kalleta ta gefe

“Bani ruwa” ya fada a taqaice,kamar jira dama takeyi ta zame hannunta daga cikin nasa,saidai kafin ta gama zamewa ya maida hannun cikin nasa,ta juyo suka hada ido ya kada mata kai

“Zan dinga hukuntaki fa” yayi maganar can qasa da wata irin gajiyayyar murya,sai tayi narai narai da ido tana kallonsa,ya girgiza mata kai da sauri

“Kinayimin kuka zan cinye idanun” yadda yayi maganar with seriousness ya sanya mata dan jin tsoro,sai ta kifa kanta saman cinyarsa,abinda ya sanya numfashinsa yin qaura na wucin gadi,ita kuma ta tura kanta da kyau tana son goge hawayen daya fara fita kada ya gani.

Da sauri ya saka hannunsa ya daga fuskartata,idanunsa suna rurrufewa,bugun zuciyarsa na fita da sauri

“Ya isa….banaso…..idan nace ki bari ki dinga cewa to,understand?” Kai ta gyada masa

“Good,bani ruwa” a hankali ta dauko masa ruwan,duk da yadda jikinta ke rawa,shima ya lura da hakan,sai ya sakar mata hannun ya karba ruwan,ya balle gorar ya sanya bakinsa bayan yayi bismillah ya soma sha.

Tas ya shanyeta,ya maida numfashinsa,ya juya kadan suka hada ido,tunda ya fara shan ruwan ta zuba masa ido tana mamakin yadda yakeshan ruwan,kamar wanda ya jima baiga ruwa ba,suna hada idon ta dauke kanta,ya saki murmushi,ya gama karantar komai daga qwayar idonta

“Zo kiji” ya kirata can qasa kamar yadda suke maganar tun daxu, saboda muneera da hajiya da suke cikin motar,bata musa ba ta matso dab dashi,sai yasake hade hannayensu waje daya yana kallonta

“Menene auratayya?” yayi mata tambayar kai tsaye,tambayar da ya jima yanason mata ita,tambayar data sakata rufe idanunta gam lokaci guda,zuwa yanzu koda batasan ainihin me yake nufi ba,daga karance karancen data fara ta fuskanci wani abune mai girma,wani babban alaqa ce babban gini da kuma qatuwar dangantaka tsakanin namiji da mace,zuwa yanxu kuma tambayar ta girmi tunaninta,ta kuma haifar mata da wani jin nauyi da kuma kunya.

Yadda ya rutsata da ido haka tabar idanun nata a kulle,wayyo Allah kawai take fada a ranta,itadai wannan iskancin ya fara isarta,inda ya barta kusa da hajiyar da duk haka bata faru ba,sai ya saki murmushi yana sakar mata hannyenta,bai sake cewa komai ba,haka itama,a haka har baccin ya soma fusgarta,sai yayi mata makari da manyan kafadunsa,sanda baccinta ya fara nisa kwance tayi bisa kafadun nasa ba tare data sani ba,wannan ya bashi wani irin yanayi mai dadi sanda suke keta dazuzzuka,yayin da tayi wani bacci mai dadin gaske bisa kafadun nasa.

Cikin ikon Allah suka iso bauchi lafiya,yayi yayi da hajiya ta fara sauka gidansa amma tace sammm a gidanta zata sauka,dole haka ya wuce da ita gida,sanda suka isa gidan akwai mutane,yaranta matan su uku duka suna gidan su da yaransu,sun gyare gidan sunyi duk wani abu na tarbarta,kowa kallon widad yakeyi,cikin watannin ta sake girma da cika,tayi wani fresh,abinka da farra fata idan ya samu hutu,cikin girmamawa ta gaida kowannensu,tunda dui cikinsu babu sa’arta,sun haifeta ma,qaramar cikinsu ce take ganin zasuyi sa’anni da anty deena.

Ina ka saka ina ka aje suka dinga yi da abbas din,shima da yake mai.kirki ne kuma na mutane sai yadan zauna shima a cikinsu kusan awa daya,lokacin har maqota da sauran matan kawunnansa sun fara shigowa yuwa hajiyan barka da zuwa,kusan kowa ya shigo idonsa akan widad

“Amaryar abbas ce?” Haka suke tambaya,kowa da abinda ke cikin ransa,ya kusa shafe awa daya sannan ya miqe da zummar tafiya

“Dauko mayafinki ku wuce widad kinji,sannunki kema da qoqari ansha hidima,Allah yayi albarka ya bada zuri’a ta gari” baki baba usaina ta tabe,matar daya daga cikin kawunnansa,wadda suna da ‘yar alaqa da hafsat din,fuska ta marairaice wa hajiyan,qasa qasa take gaya mata

“Don Allah hajiya a barni a nan na kwana” can qasan ranta tana fargabar yadda yake liqe mata,a yanzun baya jin shakkar tabata,idan mommy hafsat ta gani tace mata meye?,gwara tana nan din,basu hadu ba bare ta gani.

“Yaa abbas,ka barta zuwa anjima din kamar haka takeso tace ko?” Qanwarsa ta fada wadda ke kusa da hajiya,ta kuma ji abinda take fada din

“Idan ka fito saika biyo ku tafi,idan ma baka zo din ba zan sanya a rakota” hajiya ta qara masa bayani.

Idonsa ya maida kan widad din data wani lafe a gefan hajiyan,suka hada ido sai ya dauke kansa,itama janye nata idanun tayi cikin ranta tana jin kamar ta tsira,ya gyada kai

“Shikenan hajiya,a huta lafiya”

“To Allah yayi albarka,a gaida kishiyoyina” a hankali ya juya ya fice daga falon

“Tirqashi” baaba usaina ta fada,yaaya bara’atu ta daga kai ta kalleta

“Baaba usaina lafiya ko?” Baki ta tabe a fakaice,amma a zahiri sai tadan murmusa

“Ina ganin rashin kunya irin ta yaran zamani,kema banda abinki hajiya kibar masa matarsa su wuce mana”

“A’ah gwara ta zauna a gaisa sosai,aita kwan biyu dama bataxo ba” hajiya ta amsa mata cikin bagarar da zancan,don batason dogon zance.

Sai da suka tsaya a hanya ya sake yin siyayya sannan suka wuce gidan,ba wani zumudi ko kadan a tattare dashi,abu daya ke sanyawa yaji dokin zuwa gidan,yaransa da yayi kewarsu.
[3/15, 9:35 PM] +234 704 440 6400: *H U G U M A*

*_A RUBUCE TAKE_*
(K’addarata)
*Arewabooks:Huguma*

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button