Sponsored Links
Amatulmaleek Hausa NovelHausa Novels

Amatulmaleek 17

Sponsored Links

Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

17
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs๐Ÿ’ฏ๐Ÿ”ฅ๐Ÿ‘
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku๐Ÿ’ฏ๐Ÿ‘*

MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI’IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER

08142800199
07068558096

**********
Fara karatun AmatulMaleek ya Sakata qara gogewa a cikin wayewa duk daman Bata cikin duhun Kai a wanke take Dan duk wahalar dasuke a cikin gidan to basa cikin wahalar rayuwar tinda me kyau suke ci Kuma su sha me kyau hakama su kwanta me kyau su Saka me kyau Dan itama kusan komai sabo take sakawa yanzu da Haydar ya Saka Dad dinsu yayi noticing dinta a suna Banda kamanni Dan haka kamar yanda a Baya ake siyawa Abdul duk abinda aka siyawa Haydar to kusan itama hakanne yanzu komai nata ya sauya tana samun komai yanda ya kamata.

Naufal kuwa tini yafara aiki a matsayin director na kamfanin kasuwancin ASH empire Dan haka rayuwa taqara yi masa yanda yakeso duk ba wannan matsayin sukaso ba daga shi har mum Aisha Amma Kuma Basu cire tsammanin kaiwa inda sukesoba dan haka mum Aisha ta dage sosai tana sake cusa Naufal a gun ASH.

Gaba dayansu yaran gidan baa barinsu Jan mota da kansu bisa ga umarnin ASH Dan haka dukkaninsu drivers ne suke kaisu makaranta tareda security Daya hakama duk Wanda ya gama cikinsu driver yake kira yazo ya daukesa har Amatu
Haydar da Abdul kuwa dayake dama yanzu ne suke Shirin rubutawa exam din gama secondary school tare ake kaisu a daukosu tare.

Barnar Naufal tayi yawan da tini mutane suka fara sanin halayyar tasa Dan haka sai Hakan nason taba mutuncin Ash ga wainda suka fara sani batareda shi yasaniba.

Tafiye tafiye sosai Naufal keyi sosai Dan yafi sakewa idan ya bar garin yaje can yayo sharholiyarsa y dawo.

Ana Hakan matan da suka zubar da cikinsa a jikinsu yafi nawa Dan haka sai zancen yafara bayyana ga mum Aisha wadda ta kamasa dumu dumu sakamakon cikin wata yarinyarsa da aka zubar ta rasa ranta sanadin Hakan Dan haka tini zancen ya fita aka fara sharia saiga zance a duniya yafara yawo ‘yan jarida Dake Jira tini aka yada labarin.

Tashin hankalin da baa Saka masa rana ba mum Aisha tashiga gashi Shima Ash Talba din dole sai ya fito yayi magana akan zancen da Yan jarida tinda a kotu ake.

Su Husnah kuwa mamaki sosai suka shiga Amatu Kuma Daman Bata shiga abinda Bai dametaba sosai kawai dai damuwarsu shigowar bacin sunan Ash da ake Neman yi Dan haka suka Dan shiga damuwa Maamah kuw sosai tashiga damuwa Dan Naufal din mutuminta ne Yana yinta ba laifi.

Cikin baqin cikin data samu kanta mata adadi mum Aisha ta samu case din ya mutu Wanda aka tabbatarda ba Naufal ne yake muamala da yarinyar ba Maza da yawa ne Kuma daga karshe ma dai ba wannan ne cikin farko data zubarba Kuma Babu Wanda ya tilastata zubarwa itace tayi Kuma Hakan yaxo da matsala har yayi ajalinta.

Mutuwar case din ya Saka familyn gidan samun nutsuwa da hamdala Amma ASH TALBA ya dakatar dashi daga fita aiki gaba Daya sbd hukuntasa.

Wannan hukuncin baiwa mum Aisha da dadi ba Dan haka ta daga hankalinta sosai,zagi da fada Babu ranar da Bata wuni sai a kwana Bata yiwa Naufal daga qarshe ma tayi rantsuwar bazai qara fita mansion din ba.

****Abu Daya da mum Aisha Bata sani ba shine hanasa fita shine ya bullo sabuwar matsalar cikin Mansion din,
Bai Dena fitaba sbd Yana ficewa yaje yayi abinda zaiyi ya dawo batareda ansan ya fita din ba Dan haka Neman matan nasa ya rage tinda Baya samun isashen time sosai a waje,

Ta bangare daya rashin samun yanda yakeso a aynzu yasa idanuwansa suka dawo Kan ‘yan matan gidan masu aiki yafara farautarsu Daya Baya Daya yana lalabewa duk da qyamarsu yakeyi Amma dai tinda Yana samun yanda yakeso sai yana manejinsu hakanan.

A qanqanin lokaci kusan Yan matan biyu masu aiki ya Maidasu kaman matansa Babu ranar da baya kusantarsu idan yayi yau da wannan gobe da dayar zeyi.

*****AmatulMaleek datafi duk matan dasuke gidan kyau Tim daga masu gidan har masu aiki itace maqale a zuciyarsa da idanuwansa,
Kyakkyawa ce hakama Mai aji da kamewa ce Sam saikayi sati nawa a cikin gidan batareda ka Sakata a idanuwanka ba Dan Babu abinda yake fiddota sai ayyukan da baa rasaba tinda karatu yanzu Baya barinta ma ayyuka tini maamah ta dauke mata iyakacinta karatu da hutawa sai ranakun datake gida take Saka hannu a wasu ayyukan gidan.

Ta bangare daya siyasan ASH TALBA ya dauko zafi gadan gadan sbd lokacin zabe Daya gabato sai gidan yakoma tsaronsa yanata qara ninkuwa Dan Babu abinda Ash ya hada da tsaro tareda kariyar familynsa.

Husnah Bata Nan tana porthcrt gurin Hutu tareda Haydar gun dangin mum dinsu wadda daga can kafin su dawo zasuje dubota.

Abdulhameed ma wannan Karan ya sake zuwa kauye Shima ya dubo dangin nasu mahaifin a karo na uku Dan haka daga AmatulMaleek sai maamah sai su mum Aisha.

Kwadayinsa Naufal ya fara bayyanarwa akan Amatu Dan haka maamah tafara shiga fargaba da shakku Amma dai Bata nuna komaiba ganin itama Amatun tafara shiga taka tsantsan dashi.

Mum dinsa ganin wadda yafara kaiwa hari baqin cikinta ya tsananta ta kallesa a lokacinda suke zaune palonta tace

“Wane irin Dabba kakeson zama ne Naufal akan mata?
Wace masifa da balai ne wannan ni Aishatu take bibiyata,
Nayi Dana sanin dawowarka ma Dana sani nabarka acan qasar Kayita abinda kaga dama idan yaso ranarda ASH yasan abinda kakeyi Saiya dakatar da duka kudinsa da aka Sakar Maka kana wannan ta’addancin alokacinne zaka gane me nake nufi daka nutsu mu samu gurin zama da gurbi a wannan dukiyar……

Magana ya Bude Baki zeyi ta katsesa cikin baqin ciki da takaici tana cewa

“Ka fitarda macen aure kawai kayi aure tinda bazaka iya kame kanka ba kayo mummunan gado harka zarta,
To wlh Bazan iyaba,idan ka lalatamun komai to tabbas saikaga yanda baka so Dan wlh Nima dubu Daya bazaka sake samu ta hanyataba tinda zuciyarka ta Dade da mutuwa a gurin mata.”

“AmatulMaleek kuwa da wuri da gaggawa kayi saurin dauke idanuwanka akanta Dan duk kaje ka lalata musu ita to ko ni wlh Kila qarshen zamana a karkashin ASH yazo bare Kai Dan akan Asmau zai iya aikamu inda mukaqi jinin zuwa wato inda muka fito Dan haka Maza Maza ka cire kwadayinka akanta tinda ka riga ka gama lalata Yan aikin gidan Nan tas,
Kai ko qyama bakaji ne?
Bazaka iya hakuri ba bayan kwana bibbiyu kaje ka samu na wajen ba ka biyasu ka sauke buqatarka Amma ace Yan aiki ma nema kake,mtswwee.

Zafi zuciyarta keyi kaman zata fashe Dan tana cikin baqin cikin wannan muguwar kaddarar ta hada jini da hamis Da Danta ya dauko halinsa.

Fadanta da zafinta koyaushe Sosa ran Naufal sukeyi Shima sbd idan ta fada kalamanta Sam Babu alkhairi a cikinsu koyaushe Dan haka Bai iya cewa komaiba Shima ya miqe yabar palon Dan kuwa ayanzu yake Jin AmatulMaleek din a ransa ko aurenta ze iya yi Dan biyan buqatansa idanma har be samu yanda yakeso ba kenan
Idan Kuma mum din ta matsa akan maganar auren Amatun zai aura kawai kowana ya huta.

AmatulMaleek data gaji da kadaici sai kawai ta fara fita wasu lokutan zuwa guraren Shan iska musamman tinda Hutu sukeyi gashi ba kowa.

Ana cikin Hakan Barr Faisal turaki ya ganta a cikin gidan zuciyarsa ta kamu da kaunarta alokaci Daya duk da ya jima sosai da familyn TALBAs din Amma Bai taba ganinta sbd shine lawyer din Madame Abeeda Kuma shine babban ‘dan Wani yayanta Dake porthcrt da maman babansa da maman Abeeda uwa daya Uba Daya suke Dan haka dadynsa yayan madame Abeeda ne,

A UK sukai zama taredasu Abeeda har suka rigasa dawowa Nigeria Amma Shima ya jima da dawowa kawai dai Baya zuwa Nan dinne sbd madame Abeedan Bata Nan hakama da Husnah kawai yake communicating Shima sbd Husnah dinne tafi nemansa koda yaushe har shaquwansu yayi qarfi sosai da sosai,

A bangaren Husnah Faisal turaki ba iya Dan uwanta take kallansa ba,
So ne take masa me tsananin gasken da kusan ko familyn mum Abeedan sun sani,so ne me tsananin gaske gaba Daya ma she’s obsessed,
Bata iya boye sonsa duk da tsakaninsa da ita baitaba fada mata so hakama yasan yanda take tsananin sonsa sedai bayajin zai iya takura kansa ya aureta batareda yana sontaba,Hakan zai cutatar da ita yakuma cutatar dashi Amma Sam ta kasa gane Hakan shikuwa a matsayinsa na dan Boko sosai da sanin YANCI ya gama ratsashi bayajin zai iya auren damuwa da takura tareda cutatar da juna Dan kuwa Yanda yake Sonta na tsakani da Allah har zuciyarsa ta Yan uwanta bayason ya aureta su lalata rayuwarsu gaba Daya ya zabi tsayawa kan raayinsa duk maganar da iyayensu da Yan uwansa keyi ya tsaya akan Hakan.

Ayau Kuma Daya zo duk da Husnah batanan yazo ne sbd aiki Daya dawo dashi Abuja da zama Dan haka yashigo su gaisa dasu mum Aisha harma da Naufal dayake mutuminsa.

Sosai yayi mamakin ganin AmatulMaleek wadda yake Jin sunan a bakin Husnah tin shekaru…

AmatulMaleek dinne tayi serving nasa duk Wani abin motsa Baki tareda gaidasa cikin nutsuwa ta juya ta fice daga babban palon gidan Takoma daki Dan dama fita zatayi zata wankin Kai.

Mum Aisha da lokaci Daya taso fahimtar Barr Faisal akan kallan Dayabi AmatulMaleek dashi take taji Babu ma abinda zata so a yanzu Daya wuce barr din ya aure AmatulMaleek din tabar gidan kafin Naufal ya janyo musu abinda zai riguzasu akan kwadayinsa da Amatun Dan tasan tinda ya qwallafa Rai akanta sai Allah idan zai hadiye wannan tsinannen kwanadayin nasa Dan haka zama ta gyara tafara yin bayanin waye AmatulMaleek din a gidan tareda yabon halayenta.
#MAMUH#

 

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at๐Ÿ‘‡
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button