Sponsored Links
Hausa NovelsHausa Novels and Love StoriesZafin Kai Hausa Novel

Zafin Kai 87

Sponsored Links

*_Arewabooks@Mamuhgee_*
87
Kansa kasa yarda yayi da Abinda yaji Dan haka ko ganin gabansa bayayi ya juyo yabar dakin ya fito jiri na juya Kansa sosai ya sauko qasa kaman Wanda yake cikin maye haka ya Isa motarsa ya shiga ya zauna zufa na feso masa Tako ina yanajinsa a wata duniyar ta daban,

Kansa ba zafi yakeyi ba wuta yakeci sosai da sosai,
Bena dinsa ce ake fadan ta taso a wannan rayuwar dayakejinta kaman duniyar wasu dabbobin ce ake fada?

Bena dince ta taso tana wankin wasu qattin Maza?
Bena dinsa ce ake maganar da yanzu tana hannun yan drugs?
Bena dinsa ce ake maganar ta taso cikin yunwa da wahala irin wannan da ko karensa bazai iya bari ya Rabi irin wannan wahalar ba bare ace Macen datayi nasarar da Saar shiga inda babu wata mace a duniya data shigar masa wannan gurbin,
Bena dinsa ce ake fadan ba ita bace asalin macen da ‘dan uwansa ya so ba,ya muaamalantu da ita suka samu ciki ya haifi Amnah ba….

Bilal da sumayyah ana nufin tare suka  Kone a motan Bilal?
Idan haka ne meyasa gawa Daya aka Gani?
Hakan na nufin dayansu na Raye?
Waye cikinsu a Raye?

Innalillahi wainna ilaihi rajiun”

Wannan mutumin daya haifi su Bena mutum ne kuwa kokuwa wani dabban ne Allah yayi da suffan mutane?

Antaba Kaisa Asibiti antabbatar da lafiyansa kuwa?sbd wasu mutanen ana zaune dasu ne kawai batareda ansan mahaukata bane masu asalin Abinda ake kira hauka.

Wata rawa jikinsa keyi sosai zufansa na qaruwa sbd Wani mummunan zazzabin tashin hankalin Abinda Bai taba ji ba ko tsammata a rayuwar ba Daya rufar masa a take.

Hannuwansa na rawa ta tayarda motar Yaja Yana fitowa daga parking lot din gurin Yana daukan iPad din Naseer dake hannunsa ya nema Naseer din Kai tsaye ya sanar dashi ya Siya masa ticket din komawa Nigeria yau din Nan komai tsakan dare.

Naseer na samun sakon ya miqe daga kwancen Dayake cikin mamaki da tsoro da fargaban ko DD din yaji maganar Bena ne.

Fitowa yayi yaje har bedroom dinsa ya dubo yaga baya gidan ya fita yaje ya duba motarsa ma Bata gidan take yasan yasan komai na maganar rashin sanin inda Bena din take Dan haka baida zabi bayan cika umarnin DD din.

Take yayi contacting Wanda zai Siya musu ticket da komai take sukai sa’a akawai jirgin dazai tashi zuwa Nigeria cikin Daren Dan haka dole ya hau hada musu kayansu ba tareda ko Zeenah ta saniba sbd tayi bacci na gajiya da rashin nutsuwar zuciya dasuke ciki musamman ita da kullum Kuka takeyi sbd shakuwa da kaunar dake tsakaninta da Bena ga tsananin tausayinta da kaunarta data qaru a ransu me tsananin gaske bayan da dd babba ya fada musu komai gameda raywarsu Bena din wadda hatta Umme data ji sai data kwana tana Kuka itada Zeenah,dad kaante kuwa Jin yakeyi da shine yasan da Hakan tini da bazai iya bin komai a hankali dinba kama Ababan zaayi a batar dashi gabaki Daya Annen Kuka ai insha Allah aikin zai karye ko baya Nan.

Koda DD ya iso gidan Yana shigowa bedroom dinsa kawai ya nufa ya a sauya kayansa daga na bacci Daya fita dasu baa cikin nutsuwa ba zuwa Riga da wando marasa tsayi ya saka facemask da Fcap ya fito Kai tsaye ya fito
tini Naseer ya saka kayansu a mota Dazata kaisu airport suka wuce.

Har lokacin cikin Wani irin mummunan hali yake sbd zazzabin dabai taba shiga bane a jikinsa hakama zuciyarsa Wani irin wuta take ci dashi tana qarawa jikinsa zafi da zufa.

Maganar ma rashin ganin Bena ganganci ne ake fada bayan ansan yanda tayi rayuwa hannun mutumin dayake amsa sunan ya haifesu Dan haka shine na farkon zargi ma akan batanta,
Fatansa dai yanzu yafara zuwa ya tsaya gabansa suyi magana ta billions tinda itace yarin dayafi Ganewa akan komai.

Idan kudine matsalansa to zai nuna masa kudinsa ko uwarsa ce calculator saiyayi batan lissafin da zai Basa shikuma Abinda yakeso daga garesa na Ina Bena take.

Hakama zai ninka masa ninkin su ya siyar masa da yancin Annen Bena ko nawa ne ya fada zai Basa daganan zai aikasa inda yakamata ace tini an Dade da aikasa sbd Bai yarda shi din me hankali bane.

Suna Isa airport ko awa Daya Basu rufa ba jirginsu ya daga zuwa Nigeria.

Dagawansu baifi da awa Daya ba Zeenah ta ankara da cewan ita kadaice a gidan take tahau Neman wayar Naseer Bata samu sai ga sakonsa Daya tura mata tin kafin su tashi ya shigo a lokacin na cewan D ya sakasu komawa Nigeria a Daren.

Tana ganin sakon hankalinta yayi mummunan tashi gigice ta kira dad dinsu ta fada masa.

Shima tashi hankalins yayi sbd yasan zafin kan DD bazai bari a tsaya ana komai a nuku nuku a boye ba sbd kada sunan family ya lalace akan Benan Nan ya fahimci yafison kowama ya sani sunan Kaantes ya dade Bai Baci ba.

Da Kansa ya fito dakinsa zuwa dakin dd babba ya sanar dashi halinda ake ciki.

Shiru dd babba yayi Shima baiso Hakan ba dan haka yace suma ba amfanin zamansu a nema musu jirgi gobe su koma.

Dad kaante na ficewa wayarsa ya daga ya kira Abbakar ya sanar dashi a sake budewa Ababa wuta harma dasu Safnah din asake Bude musu wuta ta yanda Wanda yakeda hannu acikin batan Bena zai iya yin Abinda zaa ganesa da wuri kafin DD ya iso zafin abin zai iya baci sosai.

Yana gama waya da Abbakar baccin dake idanuwansa ya kaurace gabaki Daya sbd baisan me Dame DD ya saniba a cikin Daren dazai iya barin qasar a take.

Umme ma hankalinsu tashi yayi data samu labarin abinda yake faruwa na tahowar DD Dan haka ta kasa samun nutsuwa kwata kwata.

************
Ababa a Karo na biyu Abbakar ya sake kawo masa kudi tareda buqatan son gaisawa da Anne wai Bena zatayi magana da ita a waya.

Shiru yayi wannan Karan qin karban kudin yayi ya Dan dake ya koma cikin gida ya jima kadan ya fito ya Kalli Abbakar yace batajin dadi bazata iya fitowa ba ta kira ni zuwa anjima zan hadata da Annen.

Hakan Daya fada ya saka Abbakar cewa shikenan sukai sallama ya miqa masa kudin dayazo dasu baiyi Niya ba Amma sbd kada a Gane komai saiya amsa kudin kawai Yana washe bakin qarfin hali sbd lamarin yafara isarsa.

Abbakar na wucewa yakoma cikin gida Yana hada zufan tashin hankali da tsoro sbd ya tabbatarda akwai abinda yake faruwa,

Wai shi wace qaddarar ce ma ta Kaisa hadewa dasu Safnah?

A baya duk barnarsa dayake abarsa cikin rufin asiri da lumana,
Tafiyar Bena zir na Neman janyo masa masifu kala kala Dan haka wlh bazai yarda su jefasa masifar datafi wadda yake ciki ba ta sanin gaskiyarsa da kaantes sukai akane haihuwar Amnah.

Hande data ga Yana hada zufa ransa bace Yana Neman recorder dinsa da yayiwa mummunan boye wadda duk Abinda su haj Nuratu bulama da Safnah suka tattauna dashi akan abubuwan dasuke buqata.

Hakama abinda Basu saniba a ranar da suka Basa kudin Nan Bai baro gidan ba Saida ya qyalla Ido akan me aikinsu Rabi Daya ga yanda suke maganar komai a gabanta bayan takawo masa kayan Sha
Hakan ya tabbatarda masa da tasan dukkanin sirrinsu.

Ranar Daya tabbatarda Basa gida saidaya koma ya samu ganin Rabin Kallo Daya yayi mata maganin Dayake mata dashi ya kamata take ya bayyanar mata da buqatansa ta zai raba duk Abinda ya samu da ita Amma ta sanar dashi duka motsinsu sbd ya tabbatarda zasu iya munafurtansa.

Rabi data San halinsu ciki da waje Kuma taga yanda suke tsoran shedancin Ababa dayafi nasu take ta amince da buqatansa sbd ganin Suma sun yarfada da nasa balain yafi nasu Dan haka Rabi tasan sai tafi zama safe idan tana tareda Ababa Dan haka cikin qanqanin lokaci yagama sanin sirrinsu a gurin Rabi hatta video din yanda suka kashe hajiyar Alh basheer bulama tana dashi duka suna hannunsa.

Bayan ya samu video dinne ma yayi baqin cikin shiga lamarinsu sbd yasan zasu iya Shafa masa kashin kaji Dan haka kafin ta lalace masa tasu zai lalata ya samu Daman silalewa kafin adawo Kansa.

Kayan Daya dauka dauka ya fitane yasaka hande binsa tana Kiran sunansa Amma Sam Bai tsayaba ya fice hande ta tsaya kallan iKon Allah tana tsinewa Anne da zuriarta sbd sun zautar masa da ‘da,
Sauran duk sun tafi ynzu wannan data dawo zata haukatar mata dashi.

Bayan fitarsa wayarsa ya fidda tareda Kiran Rabi yace ta shirya ta gudu ta koma gidan kaantes sbd Tona asirin su Safnah zaiyi porthacort zashi da sassafiyar washe gari daga can bazai dawoba.

Tana Jin Hakan tace maganar kudin dasukai zasu raba Kuma fa?

Cikin masifa da takaici yace ” au baki gode na barki ba zan zareki acikin su shine kike maganar kudi bayan kinsan kema ba fita zakiyiba idan zancen ya fita,
Abinda yasa na barki ki koma Kaantes ki nuna barazanar kasheki sukeyi kika gudo sbd so neke Suma ki ringa sanar Dani halinda ake ciki har na samu na gudu tukuna,idan ha haka ha ai kema inada shedan dake suke kulla komai har kisan dake Akai tinda kingani kikai shiru harda video kinada Amma kikai shiru.”

Motsin da Rabi taji a bayanta ya sakata juyowa da sauri tana sakin wayarta ganin Safnah bayanta tsaye.

Wani irin zufane ya karyowa Rabin tayi saurin matsawa baya zatai magana Safnah ta sakar mata murmushi hankila kwance tana cewa

“Ruwan tea zakiso ki dafamun fita zanyi Yi sauri.”

Kallanta Rabi tayi gabanta na tsananta faduwa Amma ganin yanayinta ya sakata Jin sanyin Safnah din bataji komai a wayar datakeyi ba.

Ajiyan zuciya ta sake a boye tareda cewa to.

Wucewa yayi a sanyaye ta nufi kitchen ita Kuma Safnah bayanta tabi da Kallo tana Jin zuciyarta na Neman kamawa da wutan tashin hankali da baqin ciki Amma bayyanarda fushin ba amfani a yanzu dasuke gab da haukacewa a cikin masifar dake faruwa.

Ko ruwan Bata Dora ba Safnah tace ta barshi.

Daki ta koma ta sanarwa momy komai babu jimawa momy ta fito ta bawa Rabi kudi tace taje ta siyo mata katin dubu biyu a layin bayansu.

Karba Rabi tayi jikinta na rawa sbd hanyar tserewa gidan take nema komai Bata dauka ba ta fito da niyar idan taje Siyan katin bazata dawoba guduwa zatayi.

Tana fitowa tayi bayan layin nasu da babu mutane sai titi tafara sauri tana waiwaye taga babu kowa tafara gudu gudu sauri sauri.

Tana wannan gudun da sauri Bata Ankara ba mota tazo a mugun guje tayi sama da ita ta watsar kan titin a kakkarye ba Rai jikinta jini na fitowa ta koina.

Motar Bata tsayaba saima gudu data qara suka hau titi daidai da kyau suka nufi gidan Ababa kai tsaye babu Wanda zuciyarsa Bata rawa sbd idan Ababa ya Isa porthacort komai ya qare gwara Shima yau ayita ta qare momy a shirye take data kashesa ayau Shima batada baqin ciki da asara.

Safnah kuwa itadai babban burinta a tsayar dashi daga zuwa gurin dad bulama kada duniyarsu ta tsaya suyi mummunan karshe.

Suna Isa gidan hankali tashe suka fada gidan Kai tsaye dakinsa suka nufa babu wata wata suka hau dubasa bayanan Safnah tace

“Momy wlh shikenan ya tafi zai Tona mana asiri,
Yasan mune Muna kashe hajiyarsu Dad,
Yasan mune muka sakawa D wannan qwayoyin,
Yasan komai akanmu fa munshiga uku mun lalace,me zamuyi yansu mu datakar dashi…

Cikin tashin hankali momy tace “wlh bazamu bari ya isaba hanya Zamubi yanda muka taka Rabi da mota yanzu haka zamu take kansa da mota Shima mu aikasa inda ya kamata…..

Daga bayansu hande cikin daga murya da tashin hankali da mamaki tace

“Me nakeji?
Ababan ne zaa take kansa da mota??
Ke Safnah uban naki kuke maganar a taka Kansa da mota?
Me kika zama?
Kisa kukeyi yanzu,wace hajiyar Kuka kashe??

Momy dake cike da zallan baqin ciki da tashin hankali na masifa a zafafe ta harbi handen da qafa Daman takiacin tsohuwar takeyi.

Safnah ma data rasa abinyi jakar dake hannunta ta Bude sauran gari qwayoyin dasuka bawa DD suna Jakarta su ta Ciro ko ruwa Basu sakasu ba ta zazzagewa hande a baki momy ta dauki kofin ruwan dake gurin da sauran ruwan da qadangaru suka gama Sha ta zubawa bakin handen take qwayoyin sukai mata cikin ciki jikinta take ya dauko jijjiga sbd jininta na tsufa baiyi karfin na DD ba Dayake matashi Kuma namiji.

Sakinta sukai yashe a tsakar gidan jikinta na wata irin jijjiga kaman ba mutum ba suka fice.

Suna ficewa Ababa na dawowa gidan yayi mantuwa ya tadda hande tsakar gidan a yashe kaman gawa hancinta da bakinta duk jini.

Rawa jikinsa ya dauka da Wani irin mugun zufan tashin hankali Yana kallanta Yana tsoron tabata hannuwansa su fito jikinta Dan haka ya juya da gudu yaje dakinsa ya dauki passport dinsa Daya manta Wanda yayi kwanaki Dan irin Hakan Yana dauka ya fito daga dakin Yana kallan gawar hande dake yashe Yana Jin radadin da Bai taba jinsa a zuciyarsa ba Kuma yasan aikin waye Dan haka zasusan wa suka taba daga yau wasan kowa yazo karshe.

Ledan robar dasuka yar tsakar gidan ta qwayoyin dasuka durawa Annen ya nufa ya dauka da hannunsa bayan ya sakasa a leda ya daure ya dauki ledan roban ya saka cikin wata babban ledan ya daure Kai tsaye ya ajiye gefen hande ya dauko wuta ya babbakawa gidan sbd kada a tararda gawar hande da wainnan qwayoyin a gidansa su sake sakasa cikin masifar Dayake ciki Dan kuwa hukuncin qwayoyin kawai rayuwarsa bazata dauka ba.

Yana gama babbakawa gidan wuta ya fito da sauri lokacin duhun magrib ya wuce Yana fitowa daidai Naseer na parking mota a kofar gidan.

D ne yafara fitowa Kai tsaye cikin gidan da wutar ke ci sosai da a nufa ya fada sbd dubo Annen Bena Yana shiga yaga hande kwance a yashe da leda gefenta.

Wuyanta ya taba dakyau yaji akwai sauran Rai atareda ita Dan haka Kai tsaye ya sunkuceta sbd tinanin itace Annen Bena ya dauko ledan dake gefenta ya fito da ita da sauri.

Ababa kuwa DD na shigewa gidan Naseer bugu Daya yayiwa wuyansa me kyau na maji qarfin matashi take Ababa idanuwansa suka juye zai zube agurin some Naseer ya cirasa sama ya Bude boot din motarsu ya sakasa ya rufe D na fitowa da hande suka saka bayan mota ya shiga suka bar gurin take zuwa Asibiti.
##MAMUH#

*_Arewabooks@Mamuhgee_*

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button