Sponsored Links
Amatulmaleek Hausa NovelHausa Novels

Amatulmaleek 16

Sponsored Links

Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

 

16
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs๐Ÿ’ฏ๐Ÿ”ฅ๐Ÿ‘
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku๐Ÿ’ฏ๐Ÿ‘*

MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI’IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER

08142800199
07068558096

 

***************
Ash dinne yafara gamawa ya dauki tissue ya goge bakinsa tareda miqewa yabar dining din kafin Haydar da Shima ba Wani yunwa yakeji ba tinda yaci a gurin Amah dinsa.

Bayan Dad dinsa yabi Wanda yaji Haydar din biye dashi har zuwa palonsa ya zauna ahankali akan 2 seater ta Turkish luxury sofas Dake palon sun gama daukan sanyin ac da qamshinsa da kusan komai na palon ya dauka.
Wayarsa Dake gefensa ajiye ya Kai dogon hannunsa fari tas ya dauka Yana cireta daga flight mode ya mayar ya ajiye tareda dagowa ya Kalli Haydar din Daya zauna kusa dashi Yana cewa

“Dad maganar AmatulMaleek din maamah Da karatunta Dana fada maka ne,
Ta gama school din tin kusan last year Amma haryanxu Bata qara gaba ba.”

Numfashi Dad din ya sauke tareda dauke kallansa kan Haydar daya marairaice sbd yasan Babu abinda suke tambaya gurin Dad dinsu Bai musu ba sbd sune kadai hasken idanuwansa a yanzu.

Idan Bada Haydar din ya tinatar dashi ba Sam mantawa yakeyi bayan Abdul da kusan koyaushe suke tareda Haydar cewan Asmau nada wata ‘yar sbd baitaba ganinta ba tin tana jaririya Daya taba ganinta haryanxu baitaba ganinta ba shiyasa ya manta da Yaya biyu ne da Asmau,
Amma a yanzu tinda Haydar ya tinatar dashi zaai mata komai na karatu a inda Husnah take inshallah.

Kallan Haydar daya gama Saka sakewa da jiran abinda Dad din nasa zai fada yake,burinsa da tsananin fatan buqatansa ta kasance yayi Yana tabbatarda mahimmancin maganar karatun yarinyar a gun Haydar din sbd Babu abinda ya taba buqatama da har sai yazo ya tambayesa sai ayanzu Dan haka ya sake kallansa cikeda kulawa da kauna me qarfin gaske yace

“Kaje Jameel zai mata komai inshallah zata ci gaba tareda Husnah”

Wani irin murmushin farin ciki da sanyin dayake zuciyarsa be ya bayyana kan fuskarsa ya qaraso ya rungume Dad din ahankali Yana cewa

“Thank you Dad”

Da mamakinsa ya Sakar masa tsadadden murmushinsa Yana dafa bayansa tareda nanata masa yafada mata tayi karatu sbd karatu ake makarantar sosai.

Gyada Kai Haydar yayi cikin farin cikin Yana cewa

“Dad zatayi,zatayi karatu sosai,kaima zakayi alfahari da karatunta inshallah”

Gyada kawai dad din yayi Yana duba wayarsa data kawo haske alaman shigowan kira.

Ficewa Haydar yayi cikeda farin ciki,
Surprising din Amah yakeso yayi Dan haka bazai fada mata yanzu ba.

Bayan ficewar Haydar daga palon wayarsa ya dauka ahankali cikin nutsuwa yakai kunnensa tareda amsa sallamar Wanda yayi Kiran Yana bin bayan Haydar da kallo harya fice.

Mum Aisha ma duk sunbar dining din kowa ya nufi bedroom dinsa Naufal kuwa Yana komawa fita yaso yi Amma rashin layin dazaiyi waya ya Sakasa fasawa dole ya shige da wuri.

Washe gari da safe kusan kowa fita yakeyi masu zuwa school da masu zuwa aiki Dan haka daga Amatu sai mamah da masu aikine a gidan yawanci da safe sai yanzu tinda mum Aisha sun dawo.

Amatu ce ta shiryawa mum Aisha da Naufal breakfast ta Jere musu a palon mum Aisha din sbd abincin dare ne kawai kusan Yan gidan sukeci gaba Daya atare sbd ASH da dare kawai yake zaunawa acikinsu cin abinci sai breakfast Wanda shikuma daga shi sai iya yayansa yake yinsa wannan shine qaidarsa sbd Yana son time dinsa na safe da yayansa kawai.

Bayan tagama shirya musu abincin Naufal ne ya shigo palon lokacin mum Aisha din Bata fitoba,

Sanye yake da designers qananun kaya blue Bai Wani Kalli Amatun ba Dan gargadi da iyakar da mum tai masa da duk wata macen Dake gidan Dan haka Koda ta gaidasa amsawa kawai yayi Yana zaunawa sama sama yayi breakfast din ya fice Yana ce mata idan mum ta fito ta sanar mata ya fita.

Ok” kawai ta furta masa batareda itama ta juyo ta kallesa ba daga gyaran palon datakeyi Hakan ya Sakasa dakatawa ya juyo Yana qure kallansa akanta sbd mamakin basarwanta da rashin basa mahimmanci.

Fararen yatsun hannuwanta masu tsayi da kyau ya zubawa hannu tana rufe zip din throw pillow data Dan Bude ta gyara na kujerun palon.

Gangarawa yayi da idanuwansa kan wuyanta da Shima fatarsa take fara tas kaman ‘yar Hutu,
Akan kirjinta ya dawo da idanuwansa Ya kalla yanajin zuciyarsa na harbawa da qarfi.

Motsin juyowarta ya sakashi Maida idanuwansa kan kyakkyawar fuskarta yana juyawa yabar palon zuciyarsa na shiga wasi wasi.

Batasan duk abinda ya tsaya yayi din ba Dan haka aiknta taci gaba da yi harta gama mum Bata fito ba dan haka ta tattara ta ficewarta.

Naufal driver yasa ya fita dashi a Daya daga cikin manyan motacin gidan Dake haraba,
Kai tsaye layuka ya Siya manya masu numbers me kyau kafin suka wuce Kai tsaye gidan dayake buqatan zuwa na Amininsa zayyan acan driver ya ajesa ya wuce.

Dayake suna tareda da zayyan din acan Spain kawai dai zayyan din ya rigasa dawowa Dan haka Yana shiga suka cafke Babu Bata lokaci yasa zayyan ya samo masa lafiyayyar mace anan gidan ya wuni Yana hutawarsa tareda sauke nauyin dayake Jin tin kwanaki Yana cikinsa Dan tinda mum dinsa ta tafi gidansa ya rage Neman mata sosai sbd fadanta da zamanta a gidansa shiyasama kafin su dawo yafi sati biyu rabonsa da mace Dan haka a tsananin matse yake.

Ba qaramin dadi yaji ba a wuninsa gidan zayyan Dan haka sai dare ya koma gida Kuma Yana komawa shigewa yayi kawai Dan Baya buqatan komai bayan bacci yanzu.

Washe gari Bai fita ba sai Rana ya dauki mota da kansa ya fita Kai tsaye Wani guri suka nufa da zayyan Wanda ya kusan kashesa da dadi sbd mata ne masu aji manyan mata ‘yayan masu kudi wasu Kuma manyan Yara Dan haka kusan budurwa hudu yayi lokaci Daya Kuma a ranar ya same yanda yakeso sosai ya huta qarshe a gidan zayyan suka kwana Wanda Shima ba anan yake zauneba gidan iyayensa yake zama wannan gidan hutawa ne kawai.

Washe gari tareda mum dinsa yayi breakfast batareda tasan baa gida ya kwana ba Dan kuwa sosai ya iya takunsa.

Ahankali ya goge sosai da Yan matan dayayi sabbi harya fara gajiya dasu yafara sauyawa Dan dama Babu Wanda maganar so take acikinsu kawai Jin dadine sai hutawa.

Ta bangare daya Kuma kwata kwata ya Dena kwana gidan Kuma Babu Wanda ya sani bayan securities da Babu abinda zasuce,

Acan Spain idan kanada budurwa baka iya kula wata macen sai ranarda kukai break up Amma anan yanzu mata kusan Shida ne dashi lokaci Daya Kuma Babu wacce Baya biyan buqatansa da ita duk da Basu saniba Amma dai sun San bazai iya zama a guri Daya ba.

Idan akace Naufal Neman mata yake kaman an ragewa lamarinsa girma ne Dan kuwa tamkar bunsuru haka yake da mata,
Sam baitaba gajiya da Neman mata ba,Baya iya kwana Bada mace ba,Baya iya wuni Bai Hadu da mace ba Sam Kwata kwata dai bazai iya rayuwa batareda yana samun mace ba.
Dawowansa Nigeria Babu abinda ta qara masa sai lalacewa da tabarbarewa sbd a yanzu Kam matan ma wasu sune suke nemansa sbd kwadayi da son abin duniya tinda kallan babban ‘dan the grt ASH TALBA ake masa Wanda a yanxu yake matsayin Dan takarar governor na jaharsu duk da ASH din Sam Baya shaawan siyasan shiyasa ma yaqi komawa state din yayi zamansa Abuja Dan Baya buqata manya ne suke son tsayar dashi.

Duk Nisa da lamarin Naufal yayi mum Aisha Bata ganeba sosai Dan haka taci gaba da cusashi agurin ASH musamman yanzu da lamura suka dauki zafi a harkar siyasar sosai gidansu ya koma Saida aka qara masa securities da jamian tsaro sbd komai yanata sake tabbata.

Suna sosai Naufal Talba yayi sbd rayuwar Dayake zubawa da Yan mata yayan manya da yanda yake sakewa Yan mata kudi kaman baisan zafinsu ba.
Abokansa biyu ne zayyan Mande da Fahad Sadam Kuma Suma dukansu yayan manyan ne da bayan su kashe kudi basusan wahalarsu ba sai mata da su kadai abinda suke buqata.

AmatulMaleek kuwa lokacinda labarin cigaba da karatunta ya sameta tayi farin ciki me tsananin gaske tareda Jin girman kaunar haydar a ranta ta Qaru Husnah ma ta tayata murna Dan haka suka maamah da kanta ta tafi da Amatu gurin ASH suyi masa godiya.

Da daddare bayan sun gama dinner kowa ya watse Haydar ne yaje ya sanar da Dad din Maamah na son ganinsa,
Baya yiwa maamah shamaki da kansa kamar yanda ko mum Aisha datake jininsa idan zata gansa saita kirasa a waya Amma maamah koyaushe tace tanason ganinsa Yana Bata wannan damar sbd matsayinta daban daban yake a gurinsa sbd yayansa da matarsa dayasan son datakewa Asmau hakama yayansa a yanzu basuda Wanda suke so a duniyarsu kamarta idan ya cire kansa.

Haydar dinne a gaba sai maamah sai Kuma AmatulMaleek din datake bayanta suka shigo a natse tareda sallama qamshinsa Daya shiga hancinsu tareda sanyi ya sakasu sake shiga nutsuwansu Dan kuwa akwai Wanda qamshinsa kawai zakaji kasan ya cancanci respect,to kamshin ASH TALBA kusan Hakan ne kanajinsa zakasan ba qaramin mutum zaka ganiba.

Idanuwansa masu haske akansu suka shigo batareda ya lura da AmatulMaleek Dake bayan Maamah ba Saida Haydar ya ambaci sunanta tukuna Dad din ya lura da akwai mutum bayan Asmau.

Kujera ya nunawa Maamah din yace ta zauna ta zauna sbd akwai sakewa ba laifi tsakaninta dashi, AmatulMaleek kuwa aqasa ta zauna gefen Maamah din tareda Dan dagowa cikin nutsuwa ta gaidashi muryarta a natse ba rawan jiki ko sanyin murya kawai dai asalin nutsuwanta.

Kallo daya yayi mata ya fahimci itace AmatulMaleek ‘din Asmau ya amsa da kulawa tareda mayar da hankalinsa kan maamah suna sake gaisawa tayi masa godiya sosai Akan karatun Amatu itama Amatun cikin nutsuwa ta miqa tata godiyar.

Tinda suka shigo Amatu Bata iya dagowa ta Kalli fuskarsa ba sbd Wani irin kwarjini da haiba ne yake cika duk inda ASH TALBA yake musamman ita da Bata Saba ganinsa a zahiri ba sedai a waya ko hoto uwa Uba yanzu da ake kirarinsa da sunan governor guda.

Haydar kuwa tinda suka shigo shidai nasa idanuwan akan Amatu suke har suka gama suka fice Ya bisu Yana tsokanarta akan zai fadawa Dad din ita zai aura idan ya tashi aure.

Harararsa Tayi tana murmushi Dan batasan ma me zata ce masa ba Dan takaici.
##MAMUH#

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at๐Ÿ‘‡
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button