Sponsored Links
Hausa NovelsHausa Novels and Love StoriesZafin Kai Hausa Novel

Zafin Kai 69

Sponsored Links

69
Safnah na fitowa kaantes Kai tsaye gidan ubanta basheer bulama ta nufa tana tuga motanta tana jujiga qafafunta cikin matsuwa data Isa gidan sbd ganin takeyi kaman zata hadu da Bena a hanya,
Tinda taga Bena a vanzu batada nutsuwan ruhi da zuciyarta,
Kowane sekan,minti ko daqiga datakeyi Bena barazanar rayuwarta ce.
Bazata iva daukan okaci a cikin wannan boye boyenba.
Shin Tayaya ma Bena ta hadu da Bilal ne yayi mata ciki tin farko?
Ababa ya mutu ne kokuwa ya haukace ne da
Bena har tayi ciki a gidansa Kuma take yawo a Raye haryanzu Dan kuwa idan Ababansu na
Raye batajin akwai kudi ko mugamin da zai hanasa daukan matakin rashin Imani akan
Kawo cikin shege gidansa.

Tana Isa gidan aka wangale mata qaton gate din ta shige Mai gadi na mata barka da zuwa ko kallansa bataiba ta wuce ciki Rabi na bayanta suka wuce sashen momy batareda ta biya sashen hajiyarsu ba.
Kai tsaye bedroom din momyn ta wuce lokacin tana waya da yayanta dake can asalin garinsu
Niger akan akwai yiyuwar tazo kusa idan abubuwanta suka fara rauni sbd tareda shi suke yawon dajin bin bokaye.
Safnah na Jin wayar da momy keyi ta zauna kan kujerar dakin tareda rafka mugun tagumi tana tafasan zuciya.
Gama wayar momy tayi ta kalleta tace
“Ki Kwantar da hankalinki na fada Miki ko zamu rasa komai muyi yawo tsirara bazamu bari asirinmu ya tonu ba,
Ke kina tinanin daula kawai zamu rasa Amma ba rasa daulan ne yafi firgita ba Abinda zai biyo baya.
Shiru Safnah tayi sbd azabar zafin dake cin zuciyarta ya hanata iya furta komai.
****Bena sukuku ta wuni a ranar sbd Abu biyu
Daya tsaya ranta ya gajule farin cikinta da walwanta.
Na farko zuwan Dr Ashley ya tinatar da ita tareda tabbatar mata ba lallai gaskiyar haihuwar Amnah na cewan itace ta haifetaba ya boyu har abada,
Tayaya kowa zai karbi wannan gaskiyar?,
Tayaya lamarin zai zo mata?
Ita kanta Amnah idan taji ba itace ta haifeta ba wane halin zata shiga,Kuma kaman batai mata adalci ba sbd ko adduarta iyayenta da suka rasu Basa samu duk da kasancewarta yarinya qarama.
Duka jamaar kaantes dasuke so da kaunarta batasan da wane idon zata kallesu ba.
Numfashi ta sauke tareda rufe idanuwanta ta
Bude ahankali tana sauko gadon da rigarta
Daya cire mata kafin ya tafi.
Canja kaya kawai tayi ta lallaba ta fito ta zauna Palo tareda fara Kallo Dan hana kanta tsananta tinanin da batasan amsar duk Abinda take tambayan kanta ba.
Fruits gananu yanka Nafisat ta kawo mata a bowl me kyau da Dan sanyi kadan tafara ci ahankali tana Dan Kallo sama sama batama
Wani Ganewa sbd hankinta cikakke baya kan Kallon.
Tana Palo aka aka dawo da Amnah daga school
Da kanta taje tayi hidimanta yau sbd Jin takeyi tsananin son yarta ya qaru cikin ranta sbd fargaban ranar bayyanar gaskia ga Amnah dinta tasan ba itace ta haifeta ba.
Gabaki Daya Sauran wunin tareda Amnah a jikinta ta garasa shi ita kanta Amnah din saita tace Mata yau mummy kin qara sona ko?.
Murmushi kawai tayi tana sake shafa bayanta tace “Rabin Raina kullum gara sonki nakeyi koyaushe”
Sai dare ta kunna wayarta sbd Tama manta da wayar kashe take Dan haka tana kunnawa kira na shigowa fitowanta wanka kenan daga ita sai qaramin towel din Amnah da Bata rabo da daurawa wasu lokutan.
Batada niyar duba Kiran sai tagama shiryawa taga waye me kira a Time din.
Amnah Dake kan gado ta Kalli wayar taga ba sunan Amma take ta Gane number daddynta ne sbd duka Numbers dinsa ta haddace su a kanta da farin ciki ta dauki wayar Kai tsaye ta daga tana washe baki da farin cikin ganinsa sd Vidcall ne.
“Daddy shine kayi tafiya Ina school ko”
Ajiyan zuciya ya sauke a hankali tareda kallan
Amnah din yanajin nutsuwa nashigarsa sbd ganinta kawai farin ciki da nutsuwa yake sakasa.
Cikin nutsuwa yace
“Angel ta yafewa Daddy next time zai
kiyaye,kina lafiya right?
Murmushi tayi tana cewa “ok na yafe Amma
nxt time bazan yarda ba, lafiya na kalau”
Ajiyan zuciya ya sake a salihance kafin ya
Danyi shiru na sakanni tukuna ya Bude baki
cikin nutsuwa yace
“Mummynki fa?tana lafiya right?I mean taji
sauki ta Dena ciwo da kukan ciwo??”
Amnah dariya tayi tareda juya cameran
zuwa ta baya Dan yaga mummyn tata dake
zaune gaban mirror kan kujera tana shiryawa
cinyoyinta dake bayyane suna daukan Ido ta
gama shafawa tsadaddan body oil da Dan body spray a jikinta.
Zubawa Bena din idanuwansa da sukai laushi
tinda yazo yayi yanajin sauran nutsuwan da
baigama samuba tana qarasa shigarsa kaman
Wanda Akewa caji haka yaji energy dinsa na
dawowa daidai.
Ganin yanda yayi shiru ya zubawa mummy
dinta idanuwa Yana kallanta cikin nutsuwa
batareda yace komaiba.
Kallan mummyn nata itama tayi ta dawo da kallanta kan daddyn tace
“‘Daddy zakayi Kuka ne sbd mummy ba lafiya??
Taji sauki fa,ta warke gashinan tana komai da
kanta lafiya kalau”

Sai alokacin Bena ta juyo ahankali ta kalli
Amnah din sbd batasan camera din baya na
Aiki akanta bane
Hannunta Daya ta dada ta Dora kan baki tayi mata alaman tayi shiru.
Shi kuwa Hakan datai ya sakasa sakin murmushin da baiyi Niya ba na maganar
Amnah da ita kanta Abinda tayi din.
Amnah ma dariya tayi zatayi magana
‘Daddynta yayi mata alaman shima tayi shirun karta fadawa Mummy din Yana camera na kanta.
Gyada Kai Amnah tayi tana dariya tareda gyadawa daddynta Kai.
Ya jima a Hakan Yana kallanta sbd iya kallan ma a yanzu dayake nesa ya ishesa.

Bena datake Jin kaman idanuwansa na kanta sbd aduk lokacinda yake kallanta tana Jin kallansa kanta,
Da zata saka kaya hakanan taji Bata sakeba sai kawai ta koma closet na kayansu ta shiryo a can ya fito sanye da Riga da wandon bacci guntaye iri Daya Dana Amnah ta garaso gadon lokacin Amnah tafara gyangyadi Kuma har lokacin Kiran Bai Yanke ba.
Cire wayar tayi daga hannun Amnah ta gyara mata kwanciya kafin ta hau gadon ta rufe
Rabin jikinta ta dauki wayar ahankali zata duba
Abu sai ganinsa tayi zaune sanyeda gananun kayansa dayafi sakawa Yana Shan Abu a cup ahankali da alama ko coffee ko wani abin me zafi sbd Dan tiririn Dayake Yi.
Hankalinsa baya kan wayar Shima Saida ya Dan juyo sai yaganta zaune itama tana kallansa ta Dan dauke Kai ahankali sbd batai niyar barin yaganta tana kallansa ba jikinta duk na mutuwa.

Kallan da yayi mata ya sakata sauke Kai ahankali kafin ta Dan dago kadan tace
“Barka da Isa Ify”
Bai amsaba Saida ya kurbi Abinda yake hannunsa a natse kafin ya kalleta ya amsa
Yana cewa
“Yaya jikinki?”
Kallan juna ta dago sukai kafin ta amsa tana
Dan narkar da idanuwa sd hakanan taji tana tinawa da yanda ta ringa Jin azabar marar kwana Biyun.
Duk yanda yaso suyi fira ko magana sosai
Basuyi ba sbd baisan me zai ringa cewa ba,shi
Idanuwansa ne maganarsa,zai iya wuni Yana kallanta da idanuwansa masu shegen kashe jiki da gigitata Amma bazai iya jero kalmomiba
Dan baisan mezaita fada dinba.
Da kanta ta fahimci baisan me ake fada ba kokuma baisan me zai fada din ba Dan haka tayi masa goodnight ahankali tareda katse
Kiran ta ajiye wayar tana Dan dafa kirjinta saitin zuciyarta ahankali tanaiin wannan Karan bugawan datakeyi cikin sanyi da nutsuwa da Wani irin so Mai tsananin gaske na nutsuwa.
Zamewa tayi ta kwanta daidai tareda Jan rufarta har zuwa kirjinta tana lumshe idanuwanta da shi kawai suke bugatan Gani zahiran a wuni Daya kawai Jin takeyi kaman yabarsu kenan itada Amnah dinta.
Shi Kansa a can bangaren ajiyan zuciyan ya sauke me Dan sanyi tareda ajiye cup din hannunsa Yana rufe Ido sbd Jin kaman Kansa bazai iya daukan gudanar da har sati biyu a tafiyan ba.

*****Washe gari Bena bayan tafiyan Amnah school itama shiryawa tayi Dan tafiya office sbd zuwa office dinne zai hanata zama cikin tinaninsa da jiya zuwa yau yake Neman sauya mata nutsuwa.
Breakfast sukai dukkaninsu tare a dining tanaji
Umme na tambayar Safnah kwana biyu Bata shigowa ko lafiya Kuma Bata kirata a waya ba.
A bakin Zeenah sukaii wai ta tafi gida sai D ya
dawo.
Da mamaki Umme tace
” To shine bazata kira ni ta fadamun ba?
Ni banma San ta tafi gidan ba Dan ko
Momynta Bata fadamun ba hakama hajiya munyi magana da ita jiya Bata fadan ba,
Ke waye ya fada Miki? Batareda Zeenah ta Dena cin soyayyar doya da egg tareda chicken sauce din gabanta ba tace
“Umme meye na damuwa bafa yarinya bace, Lokacinda tabar kaantes na hadu da motanta nikuma na dawo ta waya take sanarmun gida zata kafin D ya dawo.”
Shiru Umme tayi tana mamakin Safnah din ta yanda koba itace ta haifi Dawood miinta ba ai ita mamanta ne tinda ganwar mahaifinta ce
Amma Bata fada mata ba babu Wanda ya sani ta bar kaantes ta tafiyanta,
Da zaman ne ita Daya bazata iya ba da sai itama ta dawo Nan bangarensu harya dawo tinda akwai isasun bedrooms lafiyayyi anan din.
Bena dai Bata dago ba bare nuna tasan ma me ake magana Akai bare Kuma saka baki sbd har cikin ranta mantawa takeyi was lokutan da yanada wata matar sbd ita tin farko ba guri
Daya suke ba so koya koma gurin matarsa
Bata tinawa.
Breakfast dinta tagara cikin nutsuwa kafin ta miqe tayiwa Umme sai ta dawo
Cikin kulawa itama ummen tayi mata adduan dawowa lafiya.
Tareda Zeenah suka fito ita Saida ta biya gurin dd babba ta share kusan 30 min acan kafin ta fito lokacin Zeenah ta jima da wucewa itama motarta ta nufa ta Bude ta shiga ta fice daga kaantes din.
A office dukkaninsu suka wuni sai yamma suka dawo kowa da gajiyansa Da aikin gabansa Dan haka kusan kowannensu ma a dakinsa yayi dinner Bena ce ma Bata Wani jima tana duba abubuwa ba bacci ya dauketa
Dan haka Koda ya kira Amnah ce ta daga ta nuna masa Bena din datai bacci Sai dayayi mata kallan mintina shida kafin ya kashe wayar Amnah ma lokacin baccinta yayi ya kwanta jikin mummynta tareda shige mata magalqaleta tukuna bacci ya dauketa.
**Safnah da momy gabaki Daya acikin kwana biyun sun haukace Basa cikin nutsuwa da kwancivar hankali sbd ta tabbata bokan momy ya mutu inji ganinta Daya fara zuwa dubo mata bayan sunyi waya sbd baa shiga dajin
Kai tsaye sai andubo Maka sbd hadarinsa.
Tinda labarin nutsuwarsa yazo musu suke
Neman zaucewa sbd duk garyarsu da burinsu akansa yake,
Koda suke maganar kashe Bena kisan da bazaa Gane sune sukai ba zasuyi mata Amma yanzu da alama ‘danyar kisa zasu mata ta jininta a hannuwansu.
##MAMUH#
#DBENA
#HOT
#LOVE

*_Arewabooks@Mamuhgee_*

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button