Sponsored Links
Hausa NovelsHausa Novels and Love StoriesZafin Kai Hausa Novel

Zafin Kai 56

Sponsored Links

56
Simple chicken macaroni salad ta hada musu da zallan pineapples drink mara sanyi sosai sbd
dukkaninsu babu me son Abu me sanyi sosai.

Jerawa tayi a dining ta iso palon cikin nutsuwa ta sanar masa
Juyowa yayi ya Dan kalleta kafin ya saukar da idanuwansa kan dagayen cinyoyinta da jeans din ya lafe.
Dauke idanuwansa yayi tareda Dan kallan time ya Bude baki a hankali yace
“Bana buqatan abinci irin na jiyan”
Numfashi ta Dan sauke ahankali tareda kauke Kai daga kallansa a natse itama tace “Light Abinda zaka iya ci ne”
Gyada Kai yayi batareda ya juyo ya sake kallanta ba.
Juyawa tayi ta bar gurin zata koma kitchen Zeenah ta fito tareda Janta suka nufi dining din dole
ta zauna
Shima tasowa yayi a hankali ya zauna tareda kallan Bena din da kasalallun idanuwansa
kaman mara gaskia haka Ta taso ta zuba masa ta koma ta zauna itama ta zuba suka fara a natse babu me magana.
Kadan yaci yasha drink din sosai kafin ya dauki tissue ya goge bakinsa ya miqe yabar dining din.
Kai tsaye bedroom dinsa ya nufa
Suma suna gamawa suka tattara gurin suka shige.
Sallar ishai tai kafin tayi brush tai Shirin bacci ta kwanta.
Da daddare ciwon ciki sosai ya hanasa bacci bayan zufa babu Abinda yake hadawa duk da ba kaya jikinsa dogon silk wandon pyjamas dinsa ne kawai jikin nasa.
Sosai yakejin azaban ciwon cikin Dan haka ya qarawa AC din dakin qarfi tareda tashi zaune ya jingina Kansa jikin kan gado Yana rufe idanuwansa da suka sauya sbd ciwo a hankali.
Ruwan sanyi yakejin Yana buqata Dan Sha su shiga cikinsa ko zai rage zafin Dayake ji cikinsa.

Hannu yakai ahankali ya dauko wayarsa dake kashe bedside dinsa tareda kunna wutan gefen gadansa.
Kunna wayan yayi Bai tsaya duba time ba ya saka Kiran Zeenah sbd shi ya Saba komai Yi masa akeyi ruwan ba bayajin zai iya miqewa yaje ya dauko gefen cikinsa ya riqe sosai.
Bena ce tafara Jin ringing wayar cikin bacci Dan haka ta Dan Bude idanuwanta dake cike da bacci tafara lalaban wayar ta dago ta duba sunan waye ke kira sbd ta dauka wayarta ce ma.
D” taga an rubuta Kai tsaye ta Gane waye Dan haka baccin ya Dan saketa ta miqa hannunta Daya tana taba Zeenah din wadda Baa tadata idan tana bacci Sam Bata san Hakan.
Ganin Zeenah din taqi tashi ya saka Wani Kiran na Kuma shigowa ta daga wayar a hankali tareda cewa “hello” cikin muryan bacci.
Bai tsaya Jin Ba Zeenah din bace Kai tsaye da muryarsa Shima da bata fita yace “Ina buqatan cold water yanzu”
Yanada fada ya kashe wayan tareda ajewa Yana rintse Ido zufansa na qaruwa. Bena kuwa Ras ta Bude idanuwanta gabanta na faduwan.
Tashi tayi zaune ahankali tana kallan wayar hannunta kaman Bata Gane Abinda ya fada ba sbd qasa qasan muryansa Amma Kuma bazatai karyaba taji Abinda ya fada din.
Numfashi ta Dan sauke ahankali tareda ajiye wayar ta yaye bargon jikinta ta ziro qafafunta qasa ta Sauko tareda zira slippers dinta na masu laushi gashin dayake jikinsu.
Fitowa tayi ta nufi kitchen ta kunna wuta ta nufi fridge ta Bude tareda dauko ruwan me sanyi sosai guda Daya ta dauko Daya marasa sanyi tareda glass cup ta jerasu a trey ta kashe wuta ta fito.
Bedroom dinsa ta nufa Kai tsaye tareda tsaya bakin kofar tayi knocking ahankali hannuwanta na Dan rawa hakama zuciyanta.

Shiru babu alaman yajita Amma batai saurin sake knocking din ba ta Dan Jira Wani mintin Daya kafin ta sake Dan buga kofan a hankali.
Ahankali ya Bude idanuwansa a Dan galabaice ya Kalli kofan cikin qaramin sautin da baiyi tinanin taji ba yace
“Shigo”
Numfashi taja kirjinta na sake bugawa kafin ta Dora hannunta a handle na kofan ta Bude ahankali tareda turawa Wani sanyi da qamshinsa Dayake kame da dakin suka sauka fuskanta da
hancinta taji kirjinta na tsananta duka
Ta Maida kofan ta rufe ahankali ta juyo babu haske sosai a dakin da yawa Amma tana iya ganin
komai.
Ahankali yakai hannu ya qarawa wutan dakin haske sai alokacin tagansa zaune jingine da gadon
jikinsa ba kaya
Kiris ya rage ta Sako ruwan hannunta Amma ta qanqame trey din tana dago qafafuwanta da qyar
ta nufosa kanta a qasa.
Ahankali ya Bude idanuwansa Shima sai alokacin yaga itace ba Zeenah ba Dan haka ya Maida idanuwansa ya Dan rufe tareda miqa hannu cikin nutsuwa yace ta Basa ruwan.
Ajiye kayan tayi akan Wani luxury table dake tsakiyar makeken dakin tukuna ta dauko robar ruwan me sanyi ta miqa masa.
Yana karba ya Bude ruwan Kai tsaye tareda dorawa bakinsa yafara Sha a hankali.
Juyawa tayi zata fice Bata Isa kofa ba ruwan ya dawo masa ta hanyar Amai me qarfin gaske sbd ruwan sanyin Kansa ba abin shansa bane.
Toilet ya nufa Kai tsaye tanajin Yana zuba aman take ta fahimci baida lafiya Dan haka sai ta kasa ficewa ta juyo ahankali ta Kalli ruwan daya aje din ko rufewa baiyiba ta dawo ahankali ta dauka ta rufe ruwan ta Maida kan trey ta dauke pillow dake jikinsa ya fado qasa gurin saukowansa ta durqusa ta dauka tareda mayarwa kan gadon tana gama sauya masa Wani so� luxury beddings
Yana fitowa daga toilet daure da towel jikinsa na tsiyayan ruwa da gumin Dayake Yi har lokacin

Yana fitowa daga toilet daure da towel jikinsa na tsiyayan ruwa da gumin Dayake Yi har lokacin
na zafin cikinsa.
Kallanta yayi ahankali tareda qarasawa kan gadon ya zauna ahankali batareda ya kalleta ba yace ta dauko Wani ruwan me sanyi.
Kallansa tayi cikin sanyi zatai magana Amma ta kasa ta juya take ta dauko Wani ruwan me sanyi Koda ta dawo ya kwanta jikinsa na fidda Wani tiririn zafi.
Ajiye ruwan tayi tareda kallansa taga idanuwansa rufe Dan haka batada zabin Daya wuce juyawa taje ta tada Zeenah ko zasu kira masa likita ne.
Tana fita dakin dakinsu ta koma tayita kokarin tada Zeenah Amma Zeenah din tace Mata kanta na ciwo Bata buqatan tashi yanzu.
Jin haka sai batama tsaya fada mata DD din ne baida lafiya ba ta juyo ta dawo Palo tana kallan kofar bedroom dinsa batasan mekuma zatai ba.
Samun kanta tayi da zaunawa a palon tareda shiga tinani har bacci ya ringa Dan fizgarta kadan.
Tashi tayi zata koma dakinsu taji Bude kofan bedroom dinsa ahankali ta juyo daidai yanason fitowa ganinta yasakasa komawa Yana cewa ta qaro ruwan sanyi.
Wannan Karan Daya ta qaro ta koma dakin tana shiga ta taddasa kaman yanda ta taddasa farko zaune tsakiyan gadan ya jingina bayansa da kan gadan.
Qarasowa tayi Bata ajiye ruwan ba ahankali ta Bude baki cikin sanyi tace “Shan ruwan sanyin zai kawo wata illar”
Bude idanuwansa dasukai jajir yayi ya kalleta cikin gajeran sauti yace a cikinsa yake buqatan ruwan ta zuba masa ahankali.
Bazata iya zuba masa ruwan Kai tsaye ba dan haka ta fita taje ta dauko sabon Dan qaramin towel me qaranci sosai ta jiqasa da ruwan sanyin sosai ta hadiye Wani numfashi daqyar kirjinta na dokawa ta hau gadon ahankali matsawa inda yake hannuwanta na Dan rawa ta Dora towel din

kan fatar cikinsa da babu kaya jikinsa ruwan sanyin ya sauka cikinsa tareda gangarawa jikinsa ahankali ya bude idanuwansa take numfashinsa na Neman daukewa.
Saukan mayun idanuwansa akanta yasa Bena hannunta ya tsananta rawar data saka tafin hannunta sauka kan qasan cikinsa ta shafi cibiyansa a take dukkaninsu suka Kalli juna.
Saurin janye hannunta tayi tana goga masa sanyin a Dan rude shikuma ahankali relief ya fara saukan masa sbd zafi ne sosai cikinsa keyi Amma sanyin ya taimaka masa.
Saida ta sake saka wasu ruwan sanyin jikin towel din ta sake rage masa zafin cikin tsawon lokaci kafin ya samu dawowa hayyacinsa ahankali ya dago ya kalleta itama Jin idansa akanta ya sakata dagowa idanuwansu suka shiga na juna a hankali tayi saurin janye nata har lokacin tana Jin nasa akanta.
Rudewa tafara Yi da Jin idanuwansa akanta ba tsammani tsaban rudewa ta sake Sakin towel din tattausan tafin hannunta ya sauka kan fatarsa wannan Karan riqe hannunta yayi da hannunsa tareda dagowa Yana sake kallanta tsikan jikinsa gabaki Daya suna miqewa.
Hannunta Daya riqe yasata rasa balance nata a zaune sbd a hannun ne qarfinta na zaman yake Dan haka ba tsammani ta fada jikinsa ahankali kirjinta da nasa suna mannuwa da juna wannan Karan rintse idanuwansa yayi ahankali sanyin AC da rigar baccinta ta kama Yana sauka kan fatar jikinsa Yana sake sanyaya masa jikin Dan haka batai tsammani ba taji hannuwansa ya zagayota kirjinta na qarasa mannewa da nasa ita kanta Saida ta rintse idanuwan.
Babu komai akanta Dan haka qamshin Olay dake cikin gashinta yafara shiga hancinsa tareda asalin nata qamshin Daya sani suka ringa shiga hancinsa Kai tsaye suna Neman dawo da zazzabinsa Daya sauka.
Ahankali ta daga hannuwanta ta sauke kan bayansa zata janye jikinta Amma ta kasa Hakan sbd mutuwar da jikinsu yayi su dukan.
Shiru sukai kowannensu idanuwansa a rufe numfashinsu ne Kawai ke sauka jikin junansu,nasa yana sauka cikin wuyanta ahankali da nutsuwa ita Kuma nata na sauka kan kirjinsa da babu kaya tana tayar da tsigan jikinsa da duk saukan dumin numfashin nata.

Shi bacci yafara daukewa ahakan cikin sanyi da gabalaitan da yayi daga jiya zuwa yau din,
Ita kuma sai daga baya nata baccin ya dauketa tana jira ya saketa ta tafi sai kasalanta ta saka baccin dake idonta tun farko dawowa ya dauketa.
Da Asuba Zeenah na tashi sallah taga babu Bena,
Fitowa Palo tayi nanma Bata ganta ba Takoma daki ta duba wayarta taga wayarta ajiye.
Toilet ta shiga nanma bata Nan Dan haka tayo alwala ta fito Bata tada sallah ba Saida ta sake fitowa ta nufi dakin yayan nata zata sanar dashi Bena fa bata gidan tana Kaiwa kofar bedroom din ta dakata sbd tinanin ko Bena din tana ciki,to Amma Tayaya?yaushe?
Danne zuciyarta tayi ta Hana kanta bugawa Takoma daki ta tayarda sallah tayi tagama har lokacin tana cikin yar shakku da fargaban inda Bena din zata tafi cikin dare tinda tare sukai bacci Tama rigata yin bacci Kuma ita Tama kasa Tina Bena din ta tayar da ita da daddare.
Har kusan 7 na safe babu Bena ba labarinta Dan haka 7 din na wucewa ta tashi ta fito tareda musu ordern breakfast daga Wani one of the best restaurants dake Lagos.
Bena kuwa cikin kasala ta motsa ahankali tareda Bude idanuwanta dake da sauran bacci har lokacin ta samu idonta cikin nasa yana Mata Wani irin Kallon data kusan somewa sbd tsayawar bugun zuciyanta.
Tashi tayi da Dan sauri daga jikinsa Datake kwance kaman baby.
Shikuwa har lokacin kallanta yakeyi da idanuwansa dasuka koma yanda suke suke gigitata
mutane da kwarjininsa kyansu tareda haskensu. #MAMUH#
#DBENA
#KAANTES
Next Chapter

Leave a comment
Comments
Post
No Comments posted yet
Contact Us
Arewa Books Publishers WhatsApp: 09031774742
Email: info@gmail.com
Navigation
Home About
Legal
Privacy Policy Terms of Service
Social
Facebook Instagram

FAQ’s Blog
Copyright ©️2023, ArewaBooks | ALL RIGHTS RESERVED

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button