Sponsored Links
Hausa NovelsHausa Novels and Love StoriesKyalKyalin Kauna Hausa Novel

KyalKyalin Kauna 35

Sponsored Links

EPISODE 3️⃣5️⃣

Join this group Dan samun KYALKYALIN KAINA

https://chat.whatsapp.com/Izxc95b7WeW9ciRtgIvSXU

Wayanshi dake aljihunshi ne yahau ringing hakan yasa Hamad yaciro wayan yakalla Boss daya gani yasa yagane Hajiya ce, kashe wayan gabaki daya Hamad yayi ya ijiye kan side drawer yatashi yawuce yacire kaya yashiga bayi da freshen up.

Wuraren 2 na dare yake bude idanunshi da kyar dudda alluran bai kamata yasakeshi yanzu ba amman dayake jininshi badai karfi ba tashi yayi, Hamad dake kwance kusada shi yana bacci ya kalla, yadanyi yan seconds yana kallon dakin komi daya faru na dawomai kafin ahankali ya yunkura yatashi zaune daga kwancen dayake yakalli hannunshi dayaga anyi dressing wanda yasan aikin Hamad ne bana kowaba, shiru yayi idanunshi kyam akan fuskan Hamad kafin chan yashiga bin dakin da kallo harya hango wayanshi gefen gado kan side drawer kusada na Hamad, matsowa yayi ahankali yasa hannunshi yadauki wayan kunna wayan yayi daidai wayan Dan na shigowa, daukan wayan yayi yakai kunne batare dayace komi ba, cikin damuwa sosai Dan yace “Sir where are you? Nakasa hakuri saida nabi bayanka I saw ur bike is like you had an accident are you fine”? Dan lumshe idanu yayi yabude jin yanda Dan yadamu amman har akasan ranshi batashi yakeba da dan sauri yace “how is that girl”? Saikuma ahankali yace “I’m okay, how is that girl”? Yasake tambaya akaro nabiyu, anatse Dan yace “she’s fine sir” dan satan kallon Hamad Maheer yayi ganin he’s sound as sleep yasa yace “are you sure? Hajiya bata kara mata wani abu ba I left her door open dana fita” anatse Dan yace “no sir, kana fita I knew something was wrong sainaje dakin naga kofan abude dakaina na kulle na zare key, key yana tareda ni yanzu haka” wani kalan ijiyan zuciya Maheer yasauke kafin ahankali yace “have you given her food bataci komi ba” dasauri Dan yace “yes sir naje nasayo mata abinci na bata” murya chan kasa yace “meka sayo mata”? Dudda mamaki ya kashe Dan dan Oga baitaba paying attention to kowaba ballema yazama interested akan rayuwan wani, ahankali yace “fried rice nasayo mata da chicken da salad a Kilmanjaro” wani irin kalan ijiyan zuciya Maheer yasauke yayi shiru kusan 15min baice komiba bai cire wayan daga kunnenshi ba ya lumshe idanu kawai, chan yace “Dan” dasauri Dan dake kan layin yace “yes sir” sake shiru yayi kaman abinda yakeso yafada yanamai nauyi kafin murya kasa kasa yace “inaso by 5 na asuba ka dauketa drop her outside police headquarter da Babanta ke aiki” dasauri yace “yes sir” ahankali yace “I will send you address na inda nake sai kazo, I want you to cancel schedules dina for this week gabadaya kayi announcing bana kasan nayi tafiya”dasauri Dan yace “yes sir” katse wayan Dan yayi daidai text messages na Hajiya kusan guda 100 na shigowa wayan nashi tsaki yayi ya ijiye wayan batare daya bude ko daya ba yatashi ahankali yawuce bathroom Hamad da tunda yadauki wayanshi yafarka yay kaman yana bacci yabishi da kallo murmushi kawai yayi.

Wanka yayi yafito daure da towel da karami a hannunshi yawuce gaban wardrobe din Hamad yabude wasu lafiyayyun pajamas milk yaciro masu bala’in taushi ya shirya cikinsu ya feffesa turare sannan yazo dadduma yadauka ya shimfida danyin sallolin da baiyiba.
******

Tun bayan tayi amai yabarta abayi ta wanke fuskanta da gaban riganta tafito tazo tazauna ganin babu kowa adakin, so kawai take taganshi duk idan taji tafiya haka zataita kallon kofa amman taga bashi bane har Dan yakawo mata abinci bata ganshi ba kaman ta tambayi Dan amman tai shiru, har bacci yay awon gaba da ita bata ganshi ba.
5 daidai na asuba akai knocking kofanta dasauri ta tashi dan dama bacci rabi da rabi take gabanta na faduwa kawai bude kofan taji an shigayi ta tsare kofan da kallo jikinta na gayamata ba Maheer bane danda taji kamshin turarenshi wani bangare na jikinta na gayamata shine maybe dare ne saisa baya kamshi daidainan aka bude kofan Dan ne karasowa wajen yayi cikeda girmamawa yace “Oga yace amaidaki gida” da sauri ta kalli Dan saikuma ta kalli kofan harda dan daga wuya kozata ganshi awajen, hakanan jitayi wani iri dudda tanason taje gida but taso shine zai bata news din. “Put this on” Dan yabata wani bakin yadi, kallonshi tayi ahankali tasa hannu ta karba tasa akanta bakin hannun riganta Dan yarike yace “come with me” binshi tashigayi batasan mene ke damunta ba abu taji kawai ya tsayamata awuya saiga wasu hawaye masu shegen dumi sunbi kuncinta zurrrrrrr sun sauko, she wanted to see him ko sau dayane bama tasan meke damunta ba, tanaji haka tashiga mota taji an rufe kofa an fara tafiya, sun dade suna tafiya kusan morethan one hour drive sannan taji anyi parking.

Saukowa Dan yayi daga gaban motan yazo baya yabude tareda sa hannu ya zare mata bakin Yadin daga kai gari har yawaye saidai safiya ne sosai, juyawa yayi yamata pointing headquarter na police da kusan building uku ke tsakanin su sannan yajuyo yakalleta yace “ga office din Babanki chance source namu sunce yana nan he has been sleeping there for quite some time yanzu akwai sakon da Oga yabani nabaki” Dan yay maganan yana kallon fuskan Yasmeen datai wani fayau, anatse Dan yace “Oga yace kada kiyi kuskuren fadin any information about us, gidan mu ko inda kika zauna, ko kiyi mistake din kwatancen fuskan Oga ko nawa ko nawani, idan har kika bada any information duk inda kike saiya daukoki aduniya and that time har abada bazai badake ba kin shiga cikin asset nashi kin fahimta”? Gyadamai kai Yasmeen tayi ahankali, Dan yace “sauko” saukowa tayi ahankali Dan ya maida bayan motan yarufe yakoma gaba yaja motan yawuce abinshi hakanan sai alokacin Yasmeen taji wani mugun kuka yazo mata ita bama tasan meke damunta ba but she’s so sad sooo sad mara misultuwa sabida yanda bata ganshi ba and she don’t know why, ita kadai tsaye abakin titi babu kowa babu ma motoci tadaura hannunta akan fuskanta tana kuka sosai, she just wants to cry and cry and cry kotaji saukin abinda takeji. “Baiwar Allah lafiya” taji muryan wani kaman akanta dasauri tasauke hannunta daga kan fuskanta takai bayan hannunta ta share fuskanta zata juyo inda taji ance baiwar Allah taji ance “Yasmeen!” Dawani kalan sauri tadago kanta, Aliyu ne yana sanye da kayan yan sanda yana fitowa daga mota dudda sau biyu ta taba ganin Aliyu lokacin Baba ya aikoshi gida karban sako but sarai taganeshi, kawai jitayi tasake fashewa da kuka dasauri ya tsaya agabanta yama rasa mema zaiyi yace “daga ina kike waya kawoki nan”?

✨KK✨

 

✍🏻M SHAKUR

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button