Sponsored Links
Arubuce Ta Ke Hausa NovelHausa Novels

Arubuce Ta Ke 55

Sponsored Links

Page 55

Da numfashinsa da idanunsa ya dauke lokaci guda sanda taja zanin nata sosai qasan marar tata,har jan pant dinta yana bayyana

“Ya Allah” ya furta yana sake rintse idanunsa,har suka gama bai bude ba sai da yaji nurse din na magana

“Zaki iya tashi?” Ta tambayeta,ya bude idanunsa a hankali ya maida kanta,sai ya taka a hankali zuwa gabanta,ya miqa mata hannunsa,idanunta a qas, karon farko da kunya tayi mata mugun kamu fiye da ko yaushe ta miqa masa hannun nata,ya dagota a tausashe.

Sosai ta zauna saman gadon tana gyara daurin dankwalinta, likitan ya shigo yana qarasawa gaban computer scanning din yana duba scan din data bari a jiki

“Ba wata matsala,zan rubuta mata magunguna,zata samu relief in sha Allah”.

Koda suka fito dinma tana riqe a hannunsa,gaba daya ta narke masa,tana ta sharar qwalla,ummu take tunawa da yadda take kula da ita idan bata da lafiya,dan riqetan da yayi sai takejin kamar tana tare da ummun ne,don haka ta narke masa sosai kamar yadda takewa ummu.

Tun a pharmacy din cikin asibitin ya siya magungunan,fruit kawai ya tsaya ya siya a hanya suka wuce gida.

Dakinsa kai tsaye ya wuce da ita,ya shiga kitchen da kansa ya dauko gorar ruwa da cup,ya zuba abinci a plate ya zauna da kansa a gabanta yana dubanta

“Kici abinci,magani zaki sha” kai ta girgiza,fuska yadan hade kadan,ya zama serious,ya debi abincin da kansa yakai bakin bakinta

“Oya….karbi” haka ta dinga bude bakinta yana saka mata abincin,har yanzu hawayenta yaqi tsayawa,duk ta narke,kamar yadda takewa ummu,bai saba daukan shagwaba irin wanna ba,sai ya rasa ta inda zai bi da ita,a haka ya samu tadanci,ya balla mata magungunan ya bata tasha,sannan ya miqe yana kallonta

“Ki huta kadan,sai na rakaki ki kwanta” ya fada muryarsa can qasa,saita gyada kai tana rintse ido,kawai yadda zata tafi dakin ta kwanta ita kadai take hasasowa.

Toilet ya shiga,ya sauya kayansa zuwa jallabiyya mai sulbi saqar qasar india,ya daura alwala,ya dawo cikin dakin ya shimfida abun sallah yana dan duban sashenta,ta sanya pillow daga bayanta,idanunta na a lumshe,amma da alama idanunta biyu,sai ya juya ya kabbara sallarsa.

Tun tana satar kallonsa da kadan da kadan har bacci ya soma rinjayar idanunta,tayita dagewa batason hawa gadon sosai,yana fusgarta tana qwacewa,har yaci qarfinta,ta kwanta riris saman gadon,bacci mai dadi yayi gaba da ita saboda sassaucin ciwon data samu.

Da murmushi akan fuskarsa yake dubanta sanda ya idar da sallar yaga tayi bacci,ya qarasa addu’o’in sa ya sauya kayan baccin sannan ya matso dab da ita,ta ranqwafa saman kanta yana kallon fuskarta sosai da sukayi gab da juna,siraran tausasan labbanta masu kama da an shafa musu ban lebe suka dauki hankalinsa,ya miqa hannu a hankali ya dora saman lips din nata yasa yatsunsa ya shafasu kadan,saita motsa,ta turo baki gaba cikin shagwaba

“Ummu na…..ummu don Allah fa ni….” Ta fadi tana yin juyi,abinda ya sake kawo kusancin dake tsakaninsu sosai har suka fara musayar numfashi,ta haye kusan rabin cinyarsa,ya kalleta yadda tayi relaxing a jikinsa,jikinsa ya bashi idan yace ma zai tasheta ne wata really rigimar ce,don haka kawai sai ya zame ya kwanta,hakan kuwa sai ya zamar mata kamar wata hanya data samu ta shige jikinsa sosai,harda curewa waje daya kamar kwanciyar yaro a cikin mahaifiyarsa,taja hannunsa kuma ta riqe gam tana cewa

“Ummu……na….gode” ajiyar zuciya mai nauyi ya sauke,da alama mafarki takeyi,hakanan ya samu kansa da sake kusanto da ita cikin jikinsa suna musayar dumin juna,ya lumshe idanunsa a hankali yana jin wani abu yana bin jinin jikinsa,zuciyarsa ta fara sauya tsarin bugunta,sannu sannu numfashinsa ya fara sauyawa,ya dinga fita a jejjere,mode dinsa ya canza gaba daya,yasan me jikinsa yakeso,amma bayajin wannan buqatar zata samu,ta yaya ma daga samun kusanci da yarinyar zuciyarsa zata bijiro da wannan babbar buqatar?,bashi da sauran zabi illa qoqarin zameta daya fara yi daga jikinsa,saidai ta riqeshi qam,daga bisani ma da yayi nasarar zameta din,juyi daya tak tayi ta dawo jikinsa,idanunta a rufe amma kukan shagwaba take saki,yayi shuru yana sauraren siririyar muryarta dake fidda wani irin kuka a shagwabe,wanda yake qara sanya tsigar jikinsa zubawa,ya sake rufe idanunsa da kyau yana sake qoqarin zameta a karo na barkatai,amma saita riqo hannunsa,ta kuma cusa kanta cikin qirjinsa sosai.

Duk yadda yaso yayi controlling kansa ya kasa,komai na jikinsa ya gama amsawa,qwaqwalwarsa kuma ta dauki chargy fiye da kima,dukka hannuwansa ya sanya ya jawota cikin jikinsa,shi da ita suka sauke ajiyar zuciya a tare,a hankali ya nutsa hannunsa cikin sassalkar sumarta dake fidda qamshin man kitsonta mai hade da sinadarin menthol me sanyi,cikin sanyi taushi da nutsuwa ya fara yamutsa shi yana jin dukkan wata gaba ta jikinsa tana sake amsawa,abinda ya sanya widad sake sakankancewa cikin baccinta,zuciya da ranta suna bata tana tare da ummu.

A nutse hannunsa ya biyo tsahon gashin nata daya sauka har zuwa gadon bayanta,yana kaiwa qarshe hannunsa ya zarce ta cikin rigarta dake da faffadan baya,lallausan tafin hannunsa ya hadu da fatar bayanta mai santsi da dumi,ya zura hannunsa a hankali yana shafota,idanunsa suna sake nauyi da kyau,zuciyarsa na sake dugunzuma da dokantuwa da samun biyan buqatar ransa,bai gushe ba yana ci gaba da murza fatar bayanta,duk inda yayi qasa da hannunsa zip din na bashi hadin kai wajen zugewa,har yakai can qasa,ya dora hannunsa numfashin sa yana sake gudu kamar wanda yayi tsere,wannan ya sake sanyashi matsa qaimi,ya birkitata a hankali ya soma sabule rigar tata,ya sake dora hannayensa saman wuyanta,hancinsa yana kaiwa wajen,sassanyan qamshin daya zamewa jikinta kamar dabi’a ya zuqa,qamshin da zai iya cewa tunda yake bai taba jin irinsa a jikin hafsat ba,sai yaji bashi da muradin daya wuce yayi sharing qamshin nata da tasa gangar jikin,don haka yasa fuskar sa sosai saman fatar wuyanta,ya kuma fara gangarowa ga qirjinta a hankali yana sauke wani irin birkitaccen numfashi.

A hankali ya fara isowa ga tudun saman qirjinta,abinda ya sanya shi da ita sukaji tamkar an sanya musu wani irin electric shock,ya qanqameta da kyau yana sake zuqar qamshin turaren,yayin da ita kuma taji kamar ance mata tashi!!!,cak kwanyarta ta tsaya waje daya tana son rarrrabe abinda yake faruwa,sanyin daya fara ratsa fatar jikinta ta fahinci saura kadan rigarta ta sauka qasan qirjinta,yunqurin riqe masa hannu tayi cikun matuqar tashin hankali amma ta gaza,saboda yadda jikinsu take rawa gaba daya ita dashi

“Don Allah…..don Allah” ta fara fada cikin mugun rawar murya da kuma kuka,cak ya tsaya kamar wanda aka sanyawa sarqa,ya zame hannunsa daga jikinta a hankali ya mirgina gefe yana fadin

“Hasbunallahu wani’imal wakil” can qasan maqoshinsa,yayin ruf da ciki yana cusa kansa cikin katifar tare da qoqarin dawo da nutsuwarsa cikin jikinsa.

Tuni takai bango,ta tattare dukka jikinta guri daya,tana riqe da rigarta a hannu qam qam,hawaye sun yiwa fuskarta ado,kuka take sosai cikin tsoro da kuma tashin hankali.

Dakin ya dauki shuru na wasu sakanni,har yanzu kansa na cikin katifar,yana sauraren kukan da take rerawa,wanda ya dinga jinsa har tsakiyar kansa,wani tunani yazo mata,ta soma maida rigarta da sauri sauri,saidai ta gaza zuge zip din,sai kawai ta sauke qafafunta qasan gadon ta miqe ta nufi qofa.

Cikin jikinsa yaji alamun takunta,ya daga rinannun idanunsa da har yanzu basu gama komawa dai dai ba yabita da kallo,duk da dakin ba wadatar haske amma kuma yana iya ganin bayanta daya bayyana sosai saboda rashin zuge zip din,wani irin baya dake dauke da wani shape mai jan hankali daya taimaka wajen fidda shape na mazaunanta da qugunta.

Bayajin koda yayi magana zata fita daga maqoshinsa,don haka ya miqe kawai cikin wata iriyar kasala da mutuwar jiki,kamar wanda yasha abun maye,taku uku ya cimmata,ya isa jikin qofar,ya murza key sannan ya waiwayo ya zube mata idanuwansa gaba daya yana kallonta

“Koma ki kwanta” ya fada da dakusashiyar muryarsa,saita janye gefe tana maqale kafada,bai sake mata magana ta biyu ba,illa hannuwansa daya sanya ya dauketa cak,bai direta ko ina ba sai saman gadon,ya kwantar da ita saman pillow,yaja mata duvet sannan ya sunkuya yana kallon qwayar idanunta sosai

“Sleep……banason na sake jin kukanki,idan kuma kika sake tashi….tom” ya fada yana gyada kansa,alamun akwai abinda zai biyo baya,sai ya matsa yaja da baya,sannan ya juya ya shige bandaki.

Runtse idanunta kawai tayi tana qoqarin danne kukan nata,wani haushinsa da tsanarsa takeji,ashe dan iska ne sosai haka?,tunda take ba wansa ya taba yi mata abinda yayi matan sai shi,boye kanta ta sakeyi sosai cikin duvet din tana share hawayen daketa bulbulowa daga idanunta.

Ya jima cikin toilet din sannan ya kunna ruwan zafi dana sanyi ya daidaita temperature dinsu,ya sakarwa kansa shower,bai taba zaton yarinyar zata kunnashi haka ba,akwai wani irin magnet tattare da ita dake saurin jan zuciya da kuma gangar jiki,yayi shuru ruwan yana gangara a sassan jikinsa,yana tuna qamshi da dumin fatarta,da wani laushi kamar fatar jariri,irin yanayin da yakeso tattare da matarsa,irin yanayin daya jima yana fasaltawa,hannu yasa saman kansa ya sharce sauran ruwan da bai gama diga ba sannan ya fita daga qasan shower din ya samu babbabn towel ya daura ya fito daga bandakin.

Koda ya fito turare kawai ya samu ya shafe jikinsa dashi ya sauya wata rigar,ya koma can daya side na gadon ya zauna yana kallonta yadda take nade waje daya,batayi motsi ba ko kadan,saidai duk da haka ya karanci bacci ya fara daukarta,saidai baccin baiyi nauyi ba,ya sauke ajiyar zuciya ya jingina bayansa da fuskar gadon yana sauke idanunsa kan agogon dake saman bedside yana duba time da date,yana buqatar zuwa bauchi lallai,saidai yau din Monday,zai iya jira har sai ran Friday kuwa?, tambayar da ta masa nauyi,kwanakin kuma yaji sunyi masa nisa da yawa,sai kawai ya jawo wayarsa,ya yanke bari ya kira hafsat din,at least ko hira da zata sake bashi nutsuwa ya samu daga gareta.

KI KULANI miss xoxo

DAUDAR GORA Billynabdul

RUMBUN K’AYA hafsat rano

IDON NERA Mamuhghee

A RUBUCE TAKE huguma

_sinkin labaran dake dauke da dukkan wasu nau’ikan salo da kuke so_

_masoya ku biya kudinku ta wannan hanyoyin_

0022419171
Maryam sani
Access bank

Saiku tura shaidar biya ga
+234 903 318 1070

*Masu katin waya ko VTU zaku tura ta nan*
09166221261

*Al’ummar nijerπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺ zaku tuntubi wannan number*
+227 96 09 67 63

*Thanks for choosing us*πŸ”₯πŸ”₯πŸ”₯πŸ”₯πŸ”₯πŸ”₯*H U G U M A*

*_A RUBUCE TAKE_*
(K’addarata)

*Arewabooks:Huguma*

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button