Sponsored Links
Hausa NovelsHausa Novels and Love StoriesKyalKyalin Kauna Hausa Novel

KyalKyalin Kauna 30

Sponsored Links

EPISODE 3️⃣0️⃣

For your original Egypt Abayas,home decor, Gold (new and used), shoes that are qualitative and unique at affordable price , siyen daya ko sari (wholesale and retail) contact +201123302418

Instagram @Shopper_topia
WhatsApp group *Maryam’s Egypt abaya *

‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/GoRzZ7ZgslV2alO5hYGAnj

Fita yayi waje da sauri Dan dake falo yabishi abaya, batare daya juyoba yace “I wanna be alone Dan” yawuce yazaga baya zuwa garden nasu wani hadadden garden ya zauna kan wani swinging chair dakeda foam mai laushi sosai kaman gado yatura hannunshi cikin aljihu yazaro taba ya kunna da sauri yakai bakinshi tareda lumshe idanu yana sauke ijiyan zuciya, he just wanna clear his head, baitaba jin abu ya tsayamai arai kaman this girl ba, he’s just thinking about her, yau yay canceling all his schedules sabida ita, what is wrong with him why is he feeling the girl a lot azuciyanshi fuzar da hayakin taban yayi yay shiruuu ya lumshe idanu kawai kaman mai bacci.

Tunda yafita take kallon kofan gabanta na faduwa sosai kafin kaman wacce ta tuna wani abu bargon jikinta ta yaye sannan gently tasauka dagakan gadon tamike tsaye kaman ba itane mara lafiya ba, kanulan dake hannunta ta kalla, cije lips nata tayi kafin tazare alluran daga jijiyanta haba saiga jini yarda igiyan ruwan tayi ruwan na diddiga a akasa takai yatsanta ta danne inda jinin ke bulbulowa tadauki dan kwalinta ta warware da kyau ta lullube jikinta dashi tadaure awuyanta tafara tafiya ahankali zuwa wajen kofa ta taba kofan amman akulle hakan yasa tadawo tana kalle kallen dakin saikuma da sauri tai wajen babban window dakin, ahankali tasa hannu ta yaye labulen takalli wajen window babu kowa awajen kaman ma bangaren daban ne dan ba asalin tsakar gida ne wajen ba dan bataga gate ko mutane ba, karafunan window ta kalla dasuke atsaye batada wani kiba zata iya wucewa idan ta rike numfashinta besides she’s a bit flexible, dage net din window sama tayi tareda bude glass na window ahankali batare data bari yayi karaba tajuyo takalli kofan gabanta na bala’in faduwa tana addu’a Allah yasa kada yazo dakin, ahankali tasa hannunta jikin window takai waje zuwa shoulder nata, wani kalan twisting kanta tayi kanta ya fita da kyar zuwa wuya, kirjinta tai kokarin ficewa ta kasa dan tanada boob cikakku yan manya bawai duma duma din nan ba, yanda take kokarin fito da boobs din bakaramin zafi yamata ba, dagewa tayi ta fito da kirjin nata tashiga sauka tana jawo kafafunta kafin finally takarashe fita, wani kalan dadi dataji mantawa tayi ma da yanda duka jikinta ke ciwo da kafanta da karfen window ya kurje, bata damu da babu slippers a kafanta ba, bamatasan takamaimen inda takeba dan clearly nan ba asalin compound dazaiyi leading to gate bane, but dadin datakeji kaman an mata kyauta dasauri tashiga tafiya ahankali batare datayi making any heavy sound ba kar akamata babu ko guard daya, tadanyi tafiya mai dan nisa kaman daga sama taga wasu manya manyan karnuka guda uku sunsha gabanta sun bude baki sun zazzago harshe dake tsiyaya da yawu suna wani kalan jiniya zasuyi haushi suna kallonta, tunda take aduka rayuwanta bata taba ganin manya manyan karnuka bakake irin wayan nan datake gani gabanta ba, gabaki dayan rayuwanta normal karen layi tasaba gani akwai karnuka a layinsu kuma basa cizo amman wayan nan karnukan bama suyi kama dana Nigeria ba dan bijimayen kare ne, sun zazzago harshe suna kallonta kaman sunga party bones chak ta tsayar da tafiyan datake ganinsu sunsha gabanta tana kallonsu suna mata wani kalan kallo sunzazzago da harshe kaman sunga lafiyayen nama, rawa lips nata yafara tace “A’uzubillahi mina……..” “wooooohhh!” karnukan sukai mata wani mahaukacin ihu tareda yin wani tsalle zasu kamata, gabaki daya mantawa ma tayi da escaping take kokarin yi wani wawan ihuuuuuu tayi. “Wayyoooo Ammmiiiiiii” gabaki dayan karfin gudun da Allah yabata tafara tana wawan ihu karnukan suma sun haukace suna binta su ukun zanga zanga sunga bakon fuska agidansu. “Wayyooooo Allah na!! Kare, kare, helppppppp, zasu cijeni……….” yanda karnukan ke woooh woooh zaka dauka sunga barayi guda dari ne agidan. Chak yabude idanunshi tareda mikewa tsaye da sauri jin muryan Yasmeen dakuma kukan karnikan gidansu ahaukace, dawani kalan sauri gudu gudu yafito daga garden dan yasan tsaf karnukan nan zasu yayyaga naman jikinta inhar itane yakejin muryanta, daidai Yasmeen dake bala’in gudu tana kuka sosai karnukan na binta tayo hanyar garden din, ganin Maheer tsaye gaban garden yazuba hannunwanshi biyu acikin aljihun wandonshi yana kallonta da mamaki dan adaki yasan ya barta batai wata wata ba wani kalan uban tsalle ta daka tahau jikinshi ta mugun manna fuskanta awuyanshi tai wrapping hands nata around back of his head, tai wrapping legs nata a waist nashi ta harde kafafun gam, daidai karnukan suma sunyi tsalle zasu kamata daga jikinshi wani kalan tsawa yadaka musu. “Kikito!” Chak karnukan suka tsaitsaya suna kallonshi, daidai lokacin securities na gidan da Dan duk suka taho wajen da gudun su dan sunji ihun ta da kukan karnuka da hannu yamusu alamu su tafi, chak ya tsaya kaman kankara yakasa cemata tasakeshi yakasa tabata yakasa sauketa, no one has ever cling onto him like this kaman yanda Yasmeen tayi, every single breath nata yana jinshi not just afatan wuyanshi har cikin wuyan nashi down to all his tissues and organs, yanda chest dinta ke manne da nashi ba yanda heart beat nata ke racing kadai yakeji ba har dumin flat empty stomach nata yakeji, ta rirrikeshi so tight kaman her whole life depends on that kaman zata shige cikin jikinshi ta manne su koma daya, batare dayace tasakeshi ba yajuya yafara tafiya da ita yashiga cikin garden din binsu karnukan sukayi, wucewa yayi wajen kujeran dayake zaune akai ahankali ya duka zai zaunar da ita, dan gyaran murya yayi danji yayi muryanshi yamakale cikin muryan da bata fita sosai yace “let go off me” batare data sakeshi ba tashiga kokarin bude idanunta karaf tai ido hudu da karnukan wani kalan fashewa tayi da kuka tasake chukuikuyeshi sama da nada hawayen datakeyi na sauka akan wuyanshi yana gangarawa cikin riganshi, every drop of warm tears nata kaman yana kara mishi jin wani abune gameda ita aranshi, baisan lokacin da cikin wata sanyin murya kaman ba nashi ba yace “sakeni” makemai kafada tayi still tamaki bude idanun cikin kuka da murya kaman na yarinya tace “nika rikeni” wani kalan zirrrr yaji jikinshi yadauka jin muryanta akan wuyanshi, murya chan kasan makoshi yace “why is that”? Cikin kuka kasa kasa tace “you are my savior!” Amsa maganan kanshi yayi hannunshi sukahau shocking ahankali yamike tsaye chak da ita yakalli karnukan dake kallonsu ahankali yace “are you scared?” Fuskanta har lokacin na makale awuyanshi tace “yes” wani kalan soft cool ijiyan zuciya yasauke shi kanshi he can’t explain what he’s feeling right now, kallon karnukan yayi yace “Kikito, Robit and Lucy go, go, go” yay maganan yana dan shuresu da kafa dasauri suka tafi juyoda kanshi yayi yakalleta yace “can you let me go now sun tafi” awani kalan hankali taciro kanta daga wuyanshi yabita da kallo bin duka wajen tayi da kallo ganin babu karnukan yasa awani kalan hankali tajuyo da kanta takalleshi hada idanu sukayi itada Maheer dake mata wani kallo kaman yaune yafara ganinta aduniya, faduwa gabanta yayi batasan meya faruba but kaman idanunshi sun hana nata motsi samin kanta itama tayi da zubamai idanunta da ruwan hawaye yacikasu sosai eyelash nata sun jike sabida kuka tana kallonshi dasu, tunda tazo gidan nan yaune rana na farko datasan ta kalli fuskan mutumin nan da kyau he is super handsome! Tunda Allah yayota bata taba ganin namiji kyakkyawa irinshi ba. “Pablo!” Kaman daga sama sukaji muryan Hajiya arude Yasmeen tashiga kokarin sauka daga jikinshi tana kallon Hajiya arude gabanta na faduwa, batare daya saketa ba yana kallon fuskanta ko gezau baiyiba yace “ina zaki bakisan akwai ciwo akafanki ba” dawani kalan sauri takalli kafanta sai alokacin taga jinin daya diddiga awajen dan juyowa yayi yakalli Hajiya dake kallonshi idanunta sunyi jazur sannan yaduka yazaunar da ita kan swinging chair din kaman wata yar yarinya yana kallon fuskanta, sauke kanta tayi kasa takasa kallonshi sai yatsunta datake wasa dasu, jaye idanunshi yayi akanta da kyar ya kwalama Dan kira. “Dan” “yes sir” Dan ya amsa da sauri yazo garden din, tsugunnawa Maheer yayi agabanta yakai hannunshi ahankali yakama kafarta dasauri ta kalleshi shima kallonta yayi bai damu da dattin da kafan yayi ba ga duk jini yasauke idanunshi daga kanta yajuyo yakalli Dan yace “get me first aid box I think this stubborn gurl tataka wani abu” dasauri Yasmeen takalleshi jin yakirata stubborn girl shima dagokai yayi ya kalleta, watsamai harara tayi kasa kasa tareda turomai baki, dauke kai yayi daidai Dan yakawo first aid box din, dasauri Hajiya tazo wajen hannunta takai azafaffe zata dauki kafan Yasmeen dake kan cinyanshi tace “kabari I will clean up the wound for her” “don’t you dare touch her!” Maheer yafadi da kakkausan murya, chak Hajiya ta tsaya, hanyar shigowa garden din yanuna mata da idanu strictly yace “ki bar nan” kallonshi Hajiya tayi da mugun mamaki ganin kallon dayake mata yasa tawuce fuuuu tafita, murmushi ciki ciki Dan yayi kawai yawuce yafita shima, hakan yasa yadauki spirit yabude tareda dago kanshi yakalli fuskan Yasmeen din da kanta ke kasa yace “ke bakijin magana ko” dago idanunta tayi ahankali takalleshi, hawaye ne suka cicciko idanunta cikin wani kalan murya tace “mesa bakace natafi gida ba” spirit din yakai yashiga wanke ciwon dawani kalan sauri takai hannunta kan kafadarshi tace “washhhhhhhh” chak ya tsayarda abinda yake yakalleta hakan yasa dasauri tazare hannunta daga shoulder nashi, cikin wata kalan murya yace “this should be the last time zaki kara taba jikina”.

✨KK✨

 

✍🏻M SHAKUR

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button