Sponsored Links
Hausa NovelsKurkukun Kaddara Hausa Novel

Kurkukun Kaddara 34-35

Sponsored Links

*💋KURKUKUN ƘADDARA💋*

*Daga alƙalamin Boss Bature✍️*

*Dedicated to Aunty kubra❤*

*Gargarɗi!!!*

_Ban amince wani ko wata ya yi amfani da wani sashe na book din nan ba ta kowace siga, ko a karanta mini shi a Youtube, ba tare da an nemi izni a wurina ba. Ko a haɗa mini document, idan kunne ya ji jiki ya tsira, ko da Allah na bar mutun zai bi mini haƙƙina!_

E34-35

💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫🔥💫

*_ALBISHINKU MATAN AFRICA DA KEWAYE, SHAHARARRA KUMA K’ASAITACIYAR MAI SAIDA KAYAN MATAN NAN WATO DR MAMAN YUSUF LIKITAR MATA SOKOTO TANA FARINCIKIN SANAR DAKU CEWA ZAKU IYA SAMUN KAYANTA ADUK INDA KUKE A FADIN NIGERIA DA NIGER HARMA DA WASU K’ASASHEN BAKI DAYA, KU SANI A DADE ANAYI SAI GASKIYA KUMA MACE MAI GYARA KANTA BATA BORANCI , INA MARABA DA MASU SIYAN DAYA KO SARI_* .http://wa.me/+2347069711327

*_munada zafafan kaya kamar haka ,_*👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻

*Hadin amarya budurwa ko zawara*

*Hadin uwar gida Mai taken (Maida tsohuwa yarinya)*

*Maijego package (virgin gain)* 📦

*Hadin sabon budurci ga yarinyar data rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar da namiji*

*Sahihin maganin sanyi na Maza Dana Mata Wanda yake fatattakar sanyi cikin Dan lokaci*

*Maganin gyaran nono Wanda zai gyara maki nononki cikin Dan lokaci komai lalacewarsa*

*Maganin hips Wanda zaisa shape dinki ya fita kiyi kyau kema ki shiga jerin Mata masu aji*

*Maganin kiba Wanda zaisa ki ciko kiyi kiba yar dai dai misali kema adinga binki da kallo Idan kin juya Sam rama batayi ba yar uwa*

*Hadin mallaka ba boka ba malam , akwai taimakon da muke bayarwa ga Mai butsarin namiji Wanda cikin ruwan sanyi Zaki dinga juya abunki , haka akwai Hadi na musamman Wanda komai rowar namiji sai kin samu alkhairin a wajanshi,*

*Muna da kalolin gumbuna masu Saka ni’ima sha’awa da dandano*
*Kalolin garrika mash gyara gaban mace da jimawa ajiki*
*Kalolin Zuma masu saukar da ni’ima Nan take da gamsar da maigida*
*Kalolin tsumi Wanda cikin sauki zasu Baki ni’ima da dandano irin wadda akeso*
*Kalolin matsi Wanda suke ciko da gaban mace matse gaban mace da bata Wani irin dadi da dadano*
*Akwai set kala kala Wanda yawansh ya wuce na zayyanasu anan ga Mai bukatar kayana zata iya mun magana Kai tsaye ta hanyar danna wannan blue rubutun* 👉🏻 http://wa.me/+2347069711327

*Muna dahuwar zabo ,dahuwar kaza ,dahuwar kifi ,dahuwar zuciya ,dahuwar Yan shila ,dahuwar tsoka Tara ,dahuwar Kwan mallaka, dambun nama ko na kaza Wanda yake saukar da ni’ima da jimawa sosai ajikin mace*

*Idan nace zan rubuta komai da komai to wannan page din ba zai isheni ba ,Amma ga masu sha’awar siyan kayana Zaku iya mun magana Kai tsaye ta wannan number, haka masu sha’awa su dinga ganin kalolin kayana a status sumin magana ta wannan number sai nayi seving numbers dinki ta hakan ne Zaku dinga ganin kalolin kayana idan na daura*
http://wa.me/+2347069711327

*Ina maraba da Mai siyan Daya ko sari Dr maman Yusuf likitar mata sokoto*

*❤❤❤PRISONERS❤❤❤*

 

Saboda tsabar buguwar da su ka yi, ga6o6in jikinsu sun jigata sosai, Angel tana yashe saman last step na benan, Azeeza da batool sun yi gefen dama atare aka wurgar dasu kamar kayan wanki, Deeja da Parveen da rubina suna ata 6angaren hagu, kowa Ya tarwatse, Sun yi kuka har sun gaji ga takaicin ƴan uwansu da aka tafi dasu ta ƙarfi da yaji, ga kuma takaicin wurgin da akayi dasu kamar wasu dabbobi marasa Ƴanci, ita angel ma hancinta har ya fara bleeding sakamakon bugun ƙasan da yayi, hakan ba ƙaramin tayar masu danish da hankali Ya yi ba, haris Yana zuƙunne gabansu azeeza dake a kwance ƙasa sunata kuka Yana lallashin su, Mubeen da naufal suna a 6angaren da aka wurgar dasu deeja, suna ta aikin lallashi,

Danish ke a zuƙunne Inda angel take kwance ƙasa, ya rasa ya zaiyi da ita saboda sautin kukanta dake neman hargitsa mishi lissafi, yana so ya lallashe Amma ya kasa, Yanke shawarar ɗaukarta yayi zuwa toilet don ya samu ya wanke mata fuskarta ko jinin ya daina zuba, Hannayenshi Ya sanya duka biyun Ya ruƙo waist ɗinta Ya ɗago da ita zuwa saman kafaɗarshi, Ya yunƙura ya miƙe ɗauke da ita Ya nufi sashen toilet ɗinsu,

A bakin fanfo Ya sauketa, Ta zuƙunna saman ƙafafuwanta, idanuwanta sunyi jawur launinsu Ya ciza sun koma kamar na zombie, hawaye duk sun wanke fuskarta sharkaf, Jikinta har kerma Yake yi, Giants bala’e ne, duk yadda suka ta6a mutun sai yaji jiki,

“Am sorry angel” ya furta hakan Yayin da idanuwanshi ke akan fuskarta, a raunace ta ɗago tana kallon shi without saying anything, ita kaɗai tasan Azabar da take ji ajikinta, Zuciyarta ta hasala, har wani tafarfasa take yi,

Janye idanuwanshi yayi daga kan fuskarta, Yakai hannu saman tap ɗin ya kunna shi, Ruwa ya soma kwararowa, Da tafin hannayenshi Ya dinga tarbo ruwan yana wanke mata fuskarta, Ba ƙaramin sanyi taji ba lokacin daya watsa mata ruwan a fuskarta, har saida ta lumshe idanuwanta, Bayan ya kammala Ya kashe tap ɗin, Ya ɗan juyo yana kallonta,

Cikin sanyin murya yace”zaki sha ruwa? Girgiza mashi kai tayi dakyar ta iya buɗe baki tace”bana jin ƙishi, wanka nake so In yi, U can wait for me out side,” amsa mata Yae da okey, kafin ya miƙe Ya fito daga Cikin toilet ɗin Ya tsaya Abakin ƙopar Yana jira ta kammala, lalla6awa tayi ta miƙe taje bakin ƙopar toilet ɗin ta datse ƙopar ta koma ciki, tsawon mintuna bata fara wankan ba, takaicin duniya ya isheta, tarasa ina zata tsoma ranta taji daɗi, yanzu shikenan an ɗauke su hanna? Suma za’aje a cutar da rayuwarsu kamar yarda aka cutar da su parveen, Ya salam, fashewa tayi da wani sabon kukan mai cin rai, Tana jiyo cool voice ɗin danish daga bakin door ɗin yana yi mata magana,

“Angel stop crying, its hurting me, idan ba haka zan shigo daga ciki,” tana Jin yace haka da sauri ta taja baki tayi shiru don tasa halin shi, Yanzu ya faɗo mata Cikin toilet, Miƙewa Tayi jiki duk ba ƙwari ta zame kayan jikinta ta ɗaura su saman igiya, Ta cika ruwa abokiti Ta soma Yin wankan,

Yana a tsaye Bakin door ɗin ya jingina bayanshi, fararen idanuwanshi na fuskantar ceilling, Yayin da zuciyar shi ta yi nisan kiwo Cikin tunanin Abunda Ya faru ɗazu Zuwansu Giants, tambayoyi ya shiga jefa ma kan shi wata irin lalura ce ke damunsu Hannah? Jinin menene Yake fita ajikinsu? And why tsohuwa bata nuna damuwa a kansu ba? Bakomai yafi ɗaure mashi kai ba, face yarda giants suka nuna rashin tausayi wurin yin wurgi dasu azeeza, don kawai suna ƙoƙarin hana atafi da ƴan uwansu,

Yayi zurfi acikin tunaninshi, kunnuwanshi suka soma Jiyo mashi muryar haris a kausashe yana magana daga Can Cikin ɗakinsu, Da sauri Ya bar ƙopar toilet ɗin Ya shigo ɗakin nasu, kaitsaye Eyes ɗinshi suka sauka akan tsohuwa dake A tsakiyar ɗakinsu Hannunta ruƙe da sanda haris ne agabanta Ya ruƙe qugu, Yana mata maganaTamkar zai rufe ta bugu,

“Saboda me zasu yi wurgi da su? Saboda rashin tausayi da mugunta suka jefar dasu, kamar wasu barguna, gasu nan kina gani da idanuwanki ko tashi sun gaza yi saboda raɗaɗin da jikinsu yake Yi musu, wai mu me aka maida mu ne eye? nifa nafara kokwanto akan kowa ma dake atare damu, ” Yana magana yana watsa hannayenshi kamar zai buge tsohuwa dama fa shi haris akwai zuciya, Idan ya fusata Ya isa masifa,

Tun da haris Ya soma magana, Tsohuwa ta zazzaro kwarkwararrun idanuwanta waje, Kwayar idon kamar zasu rubzo ƙasa saboda tsabar zaro su da ta yi, Bakomai bane yasa tayin hakan face Mamaki da al’ajabin daya kamata, karo nafarko kenan da aka fara samun wani acikin su Ya ɗaga mata murya, haƙika tayi matuƙar girgixa, sai da yakai karshen maganarshi Ya juya mata ƙeya yana ƙunƙuni,

Ruƙe ha6arta tayi idonta akan keyarshi, Muryarta Na rawa tace”HARISU!! yau ni kake gaya ma magana babu tausasa harshe? A ina ka samu wannan ƙwarin gwiwar? Kamanta matsayina ne awurinku? Wato ina can ina tufka ana nan anayi mini warwara,” a wani sukwane Haris Ya juyo Yabi ta da wani irin kallo Yace”Indai akan ƴan uwana ne fiye da haka ma zan Iya fada maki, Wannan matsayin da kike dashi awurin mu kina dab da rasa shi, Saboda Na fara zargin ba ƙaunar mu kike Yi ba,” kasa karasa maganar haris yayi idanuwanshi cike tab da kwalla, tsohuwa sai faman gyaɗa kai take Yi kamar wata ƙadangaruwa,

Ganin tana ƙoƙarin juyawa ta koma Cikin dakinta Ne yasa Danish Yin saurin dakatar da ita, ta hanyar yi mata magana” meyasa a koda yaushe muka sanar dake agame da rashin lafiyar ɗaya daga Cikin mu baki nuna damuwarki? jin muryar danish Yasa tayi saurin Juyowa tare da kallonshi, A tsanake Yake tafiya yana tunkarar inda take atsaye, Duk wannan abun dake faru Su azeeza sun natsu suna sauraronsu, a lokacin sun dakata da yin kukan sai dai har yanzu basu iya miƙewa daga kwacen da suke a kasa ba,

A gefen haris Danish Ya tsaya tare da ɗaura hannunshi na hagu saman kafadar haris, still idanuwanshi akan tsohuwa Yana jiran Jin amsar da zata basu, Sai faman zare ƙwalaƙwalan idanuwanta take yi, Da alama zuciyarta ta shiga ruɗani,

Bata gama kiɗima ba, zazzaƙar muryar angel ta ratsa kunnuwanta da cewa”Ki basu amsar tambayarsu mana? Daga anyi magana kaɗan sai ki dogara sanda Ki koma ɗaki, saboda rashin gaskiya, Meyasa kike 6oye mana gaskiya ne? Tun rana ta farko dana tsinci kaina acikin kurkukun nan raina ya bani cewa ba abun arziƙi ake aikatawa acikin shi ba, saboda bai kwanta mini araina ba, Kina yawan yi mana ƙarya, wanda bani kaɗai ba hatta su kansu yanzu sun fara kokwanto akanki, kince mana ana kaisu treatment room domin duba lafiyarsu, to meyasa ake dawo mana dasu a haukace? Maimakon Muga sauƙi ajikinsu saima dai muka ga tashin hankalin akan fuskokinsu, Da jikinsu, mutumin dake yin jinin al’ada meya haɗa shi da ƙaiƙayin gaba? Da kuma gwamewar ƙafafuwa? Uwa uba da fashewar le6e, ga rama, Wannan wani irin treatment ne tsohuwa”! Tayi tambayar tana kallonta, Tsohuwa dai tarasa bakin magana, sai faman gyaɗa kanta take yi,
Angel taci gaba da cewa”Allah dai ba Azzalumin bawansa bane, idan ma cutar mu ku keyi, To ku sani Allah Yana kallonku, Kuma akwai ranar hisabi, ranar da duk wani abu da kuke taƙama dashi aduniyar nan bazai ta6a taimakonku ba…….” Angel bata kai ƙarshen maganarta ba, Tsohuwa ta buga sandar hannunta, Cikin nuna 6acin ranta, Da sauri danish ya dafe kanshi da hanneyenshi,

Ranta amatuƙar 6ace tace”Kin manta abunda na faɗa maki? Nifa bakowa bace agidan kurkukun ƙaddarar nan? Don me zaki titsaye ni kina gaya mini magana yadda kika dama? Meyasa bazaki tuhumi Iyayenku da suka sadaukar daku ba sai ni? Da bani da wata alaƙa ta jini da ku? Ga dukkan alamu baki Ji gargaɗin da nayi maki ba, Ina matuƙar Tausayawa rayuwarku! Domin kuwa duk ranar da kika kuskura Kika bari Ƴan uwanki prisoners suka gasgata maganarki akan tawa, to daga wannan ranar ba zaku ƙara Yin tozali da ni ba, Zan barki dasu ne, Kiga idan zaki iya taimakon rayuwarsu,” Tsohuwa Nakai karshen maganarta, Ta Juya fuu kamar zata tashi sama Ta nufi dakinta, Ta shige taja kopa ta rufe,

Sai lokacin danish Ya zame hannayenshi daga saman kanshi, Wato a lokacin da tsohuwa ta buga sandar hannunta, basu ƙara fahimtar me take cewa ba, tamkar ta wanke masu tunaninsu na tuhumar da su ke yi mata, ita kanta angel ta lura da hakan, Sai dai ko kaɗan hankalinta bai tashi ba, Domin kuwa tasan dole su cigaba da tuhumarta, da zarar an dawo musu da ƴan uwansu da aka ɗauka,

Kallon juna su kayi ita da danish, Kafin ta ɗauke idonta daga kanshi ta mayar dasu kansu Batool, tafiya tayi zuwa inda take a kwance, Ta zuƙunna tare da kai hannayenta saman kafaɗun batool ta ɗago da ita tare da kwantar da kanta saman kafaɗunta,

“Sister, yanzu Haka zamu zuba ido muna ji muna gani, Ana raba mu da ƴan uwanmu”? Cikin shessheƙar kuka batool ta yi maganar, kafin angel ta bata amsar tambayarta, Naufal ya rigata cewa”Haƙuri zamuyi, Giants sunfi ƙarfin mu, Ni dai na roƙe ku nan gaba kada ku ƙara gigin shiga huruminsu, Ina gargaɗinku, Idan ku ka yi haƙuri za’a dawo mana da su ne, kamar yarda aka dawo mana dasu Parveena,

Mubeen yace”Nima abunda nake so naja musu kunne akai kenan, Mutanan nan ƙarfi ne da su, They are extremely dangerous! Da ace tun farko baku Yi yunƙurin tunkararsu ba da duk hakan bata faru ba, kun riga da kunsan halinsu, Basa ji basa gani, duk wani koke koken da za ku yi musu abanza, ba saurarar ku zasu Yi ba”

Danish yace”pls let it be past, tunda sun riga sun tafi dasu, Koke koken Ya tsaya iya haka, ”

Jinjina kai Angel ta yi tare da binsu Azeeza da kallo tace”Ku daure ku tashi, ku je toilet ku wanke fuskokin ku,” amsa mata Su ka yi da toh, daƙyar suka iya miƙewa tsaye a daddafe suka Nufi toilet,

“Batool kema kije Ki wanke fuskarki, koma Kiyi wanka” amsa mata tayi da toh, Ta ɗago da kanta daga saman kafaɗar angel, Hannunta adafe da sumar kanta, ta miƙe ta wuce cikin toilet,

Ba Iya wanke fuska Su kayi ba, Hada wanka su Kayi, Time da suka fito, mazan gaba ɗaya sun koma saman gadajensu, Angel ma tana zaune daga gefen gadonta, Kowa da abunda yake saƙawa acikin zuciyarshi,

Lokacin da giants suka zo kawo musu abinci, Fushi suka Yi, suka ƙi zuwa su Ci, naufal yace”da rabon muyi ma kanmu asara, domin kuwa su basu san bihim ba, ko ajikinsu, Mu zamu Ji jiki,” wannan maganar da naufal yayi ce tasa parveen ta sauko daga saman gadonta, Ta nufi saman dining carpet ta samu wuri ta zauna, Ɗaya bayan ɗaya suma sauran suka sauko daga saman beds ɗinsu, Suka Nufi Carpet ɗin suka zazzauna,

Lafiyayyan abinci aka kawo musu, ba don suna jin daɗinshi ba suke Cin shi, Kamar waɗanda aka Yi ma dole, In ka cire parveen dake ta zuba loma, dama ita bata wasa da abinci,

Abinci take Ci amma hankalinta na akan giants dake a tsaye sun ƙame, Harara ta dinga jefa musu tamkar ƙwayar idonta zata faɗo kasa, ita kaɗai take haukanta domin kuwa babu tabbacin ko suna kallonta, Bayan sun kammala Cin abincin, Sauran daya rage Batool ta 6oye musu shi acikin kwandonsu, saboda su samu wanda zasu Ci da anjima,

Bayan tafiyar giants, Safa da marwa suka shiga Yi acikin ɗakin duk babu daɗi saboda rashin ƴan uwansu, an rairaye su yanzu sun koma su goma sha ɗaya, Babu mutun Huɗu acikinsu, dole suyi maraicin rashinsu atare dasu, ga zullumin da suke Yi da fargabar ko awani hali suke Ciki?

Idan suka gaji da zagaye ɗakin sai su koma saman gadajensu su zauna, a haka har dare ya rutsa dasu, Ɗakin Ya yi duhu, Rubina ce ta kunna musu fitilun Ɗakinsu Haske Ya gauraye ko’ina, Kowa Ya kishingiɗa saman gadonshi,

Ta yi tsammanin sunyi bacci Jin ɗakin Yayi tsit, Juyawa tayi tare da fuskantar gadon danish, idonshi biyu Ya kwantar da kanshi saman pillow,

“Meya hana ka bacci”? Amsa ya bata da cewa”ke zan tambaya, me kike Yi har yanzu baki runtsa ba”? Ta6e baki ta ɗanyi”Damuwace ta hana ni bacci, ina jin duk babu daɗi zuciyata”

Shiru baice mata komai ba, sai dai kallonta da yake yi, kamar yadda itama take kallonshi, Gani yayi ta miƙe ta sauko daga saman gadonta, a bakin gadonshi ta zuƙunna tare da ɗaura hannayenta saman mattress ɗinshi

Da ɗan mamaki yace”lafiya”? Murmushi ta ɗansaki kafin tace”Bakomai kawai ina so Muyi fira ne,” mayar mata da martanin murmushin yayi, har dimples ɗin shi ya lotsa,

“Ai ni ban Iya fira ba, in fact ko surutu ban iya ba, sai in ta kama dole,” tace” toh ka ƙaddara ta kama dolen ne, tambaya ce nake so In yi maka hope zaka amsa mini” ɗaga mata gira yayi tare da cewa” Am all ears”

Kame kame ta shiga Yi, abun ma sai yaso ya ba shi dariya, hannun shi yakai saman sumar kanta ya ruƙo gashinta tare da cewa”Faɗa mini mana, indai nasan amsa zan baki,” tace”Dama nayi mafarki ne, kana da wuƙa, shin dagaske ne”? Da budar bakinshi sai ce mata yayi”you’re trying to be smart, tell me the truth waya faɗa maki cewa ina da wuƙa? Nasan ba mafarki ki kayi ba,”

Hararar shi Tayi jin ya ganota, taso tayi mishi wayau,

“Na ta6a tambayar batool, cewa Inaso zanyi amfani da wuƙa, shine take faɗa mini cewa Akwai wadda tsohuwa ta baka lokacin da kace mata kana so ka rage yawan sumar kanka,” Wani kallo taga yana binta dashi, Can kuma yace”me zakiyi da ita”? Dariya tayi tare da cewa”bafa kai zan kashe ba, Nasan abunda kake tunani kenan, ni kawai inaso In rage sumar kaina ne, bama ni kadai ba hada batool itama Gashin kanta yayi yawa yana takura mana” tayi maganar tana yamutsa fuska,

Ta6e mata baki yayi”Nima namanta inda na ajiye ta, ko na mayar mata da ita ko ban mayar mata ba, namanta, ”

A ƙagare tace”pls ka daure ka tuna, Zata yi mana amfani,”

“Angel idan Kina son In rage maki gashin kanki ne, Ba buƙatar Yin amfani da knife, i can use my nails to cut it for u” zaro ido ta ɗanyi da mamaki tace”taya zaka Iya amfani da akaifa wurin rage yawan gashin kaina, baka ga yawanshi ba ne”

“Idan kin bani dama zan Jaraba” girgiza mashi kai tayi”a’a, Ni dai nafi so Inyi amfani da wuƙar, Idan Allah yasa ka tuna inda ka ajiyeta sai ka ɗauko mini” ta faɗi hakanne saboda ba gashin take so ta rage ba, Wuƙar take buƙata saboda tsaro,

“Its Okey, Kije ki kwanta, duk time dana tuna i will let u know” ya karasa maganar tashi tare da jan bargo ya lullu6e jikinshi har zuwa kanshi, Miƙewa Ta yi tare da juya ta koma saman gadonta ta kwanta, A daren ranar saida ta roƙi Allah Akan Yasa itama ta fara Menstruation kodan saboda giants su ɗauketa sukaita ɗakin nan taga uban me suke aikatawa, Idan Allah yasa Hankalinta bai gushe ba kenan,

Wasa wasa Yau har tsawon One week kenan ba’a dawo dasu Hannah ba, Tun suna sanya damuwa aransu har suka haƙura suna zaman jiran tammani, Tun daga ranar da aka ɗaukesu Kullum sai ta roƙi Allah tsakar dare Akan Ya karesu aduk inda suke, Bayan haka kuma Tana yawan yin addu’ar akan Allah yasa ta fara jinin itama, duk don saboda da taga me ake yi musu,

Yanzu ta kaiga ko tsohuwa basu tambaya dangane da ƴan uwansu, saboda sun fahimci cewa ita ɗin bata da banbanci da totan masara awurinsu, bi ma’ana bata da amfani duk wani magiyar da zasu Yi mata bazata iya Sanyawa adawo masu da ƴan uwansu ba, sai da ta gaya musu ƙarairakinta,

Yau tsawon 3 weeks kenan Suna ta baza ido suga an dawo musu Da ƴan uwansu, Sai acikin satin karshe na watan da suka shiga, Aranar da daddare suna zaune saman carpet Suna fira sun kunna fitilun ɗakinsu, Ba zato ba tsammani sai ga giants Huɗu sun shigo cikin ɗakin nasu Kafaɗunsu Ɗauke dasu Hannah, A wani irin zabure suka miƙe suna kallonsu, wuce wa cikin ɗakin giants su ka yi adai dai bakin gadajensu hannah masu ɗauke da numbobinsu suka kwantar da kowannansu, Atare suka juya suka fuce daga cikin ɗakin,

Azeeza sai tsalleta take Yi tana murna an dawo musu da ƴan uwansu, Su batool kuwa Kallon Kallon suka shiga Yi atsakaninsu, sun rasa gane farin Ciki zasu Yi ko baƙin Ciki? Ga shi dai an dawo musu da ƴan uwansu da suka daɗe suna jimamin rashinsu, Sai dai ga dukkan alamu Basu acikin hayyacinshi, Har ƙwarama lokacin da aka dawo dasu parveen sunyi magana, Amma waɗannan bayin Allahn, Idanuwansu ne kaɗai suke motsi, Numfashin su da hucin zafi yake fita, ƙafafuwansu duk sun tale, Wani abun tashin hankalin ma, Hada Yakushin akaifa asaman wuyansu, fatar wurin tayi jawur, jini ya kwanta, La66ansu sun faffashe, Hankalinsu danish ba ƙaramin tashi yayi ba, Matan kuwa Sun sha kuka kamar ransu zai fita, Angel tace Yanzu babu buƙatar saita yi musu bayani game da cewar cutar dasu ake yi yau dai gashi nan zahiri idanuwansu sun gane masu, Sahun yakushin akaifar dake asaman wuyansu, Haƙiƙa sun yi matuƙar girgiza, hatta mazan saida suka zubar musu da hawaye saboda tsabar tausayinsu daya kama su, daren ranar basu Iya runtsawa ba, A gefen gadajensu Hanna suka zaune suna Jimami, har garin Allah Ya waye, Koda suka je bakin ƙopar ɗakin tsohuwa suka kwankwasa mata, Munafukar bata fito ba, Hakan ya ƙara tabbatar musu da cewa Bata da gaskiya,

Haƙiƙa sunsha wahala wurin Yin jinyarsu Hannah, kamar bazasu Rayu ba, jikinsu yayi tsauri sosai, babu sauƙi saima abunda ya qara gaba, sai da takai ga Komai daga kwance suke yin shi, fitsari kashi, duka dai, a ƙalla sun ɗauki tsawon one month suna yin jinyarsu kafin Allah yasa suka samu sauƙi Jikinsu ya warware, Suka koma kamar yarda suke da, Sai dai babu wani walwala atattare dasu, Suna yawan firgita, Ko kiran sunansu Kayi sai kaga sun ɗan zabura, Idan suna bacci kuma Sun dinga sambatu suna koke koke, Ahaka ahaka dai da taimakon Allah angel Tana yi musu addu’a duk rana ta Allah, Sai gashi sun wartsake, Sun dawo normal, Bayan sunji sauƙi, Sai ga tsohuwa ta shigo ɗakinsu, Wani irin mugun kallo da suka dinga jefa mata, ba arziƙi taja sandarta ta koma Cikin ɗakinta, Angel taso ace su hanna sun Iya tuna abunda ya faru dasu amma sun kasa, kwata kwata basu Iya tuna komai, Da ace sun tuna koda kaɗan ne to kuwa tabbas sauran ƴan uwan nasu zasu Ƙara gasgata maganarta, duk da ayanzun ma ta fara cin nasara saboda kokwanton su Ya ninku akan gidan kurkukun, Sun sha jinin jikinsu, Sun fara tsorata da lamarin, Haris har alƙawari ya ɗauka akan bazai ƙara bari giants su ta6a wani acikin su ba, Sai dai in bayan babu ranshi, danish dai bamu san matsayarshi ba, Shi dai baice komai ba, Iya nuna 6acin ranshi akan fuskarshi ne, Amma su naufal mubeen da javed duk sun ɗauki wannan alƙawarin na hana atafi da ƴan uwansu idan basu da lafiya! Kallonsu kawai angel take Yi domin kuwa tasan babu abunda zasu Iya yi, ba wani ƙarfi gare su ba, balle suce zasu Iya ja da giants, Mutanan da take tunanin Ba cikakkun mutane bane, Ƙarfinsu bana jinsin bil’adama bane,

Bayan komai Ya lafa tsawon Watanni uku wani iko na Allah, cikin matan ba wanda ya ƙara Yin Menstruation, kamar an ɗauke musu da jinin, Hakan ba ƙaramin daɗi yayi ma angel ba, Yanzu hakalinsu ya ɗan kwanta,

Ganin sun samu natsuwa yasa Ta fara jan hankalinsu zuwa ga addinin musulunci, Idan dare Yayi bata barinsu Yin bacci, Tarihin annabawa take basu tun daga kan tarihin Annabi Muhammad (SAW) Cikin hikma take Basu tarihin, Kuma ga dukkan alamu ba ƙaramin daɗin shi suke Ji ba, domin kuwa idan ta fara basu tarihin, Ko fitsari mutun ke ji sai kaji yace a jira ya dawo sai acigaba, idan kuwa tace ta gaji abari gobe zata ƙarasa musu kamar su yi mata hauka, Taci wahala sosai Wurin janyo hankalinsu duk da bata ci nasara ba saboda duhun jahilcin dake akansu, Suna Yi mata tambayoyin ƙural da suka fi ƙarfinta musamman haris, Da yace idan har akwai Allah wanda ya halicce su to meyasa bai ta6a zuwa ya kawo musu ziyara ba? Ire iren irin waɗannan tambayoyin sune kesa tana karaya wani lokacin, Ita dai tayi iyakar bakin ƙoƙarinta wurin sanar dasu gaskiya, Sauran kuma tabar ma Allah domin kuwa shi kaɗai ne zai basu ikon musulunta idan yaso, mutun huɗu ne acikinsu ta lura da suna matuƙar son Addinin, Batool, Azeeza da Javed, sai kuma parveen, sauran kuwa kokwanto ne Ya hana su yarda da ita saboda wasu tambayoyin su da ta gaza amsa musu, shi danish bama tasan a wata matsaya yake ba, Yana dai son tarihin annabawan da take basu, Sai dai Babu alamar yana da niyar kar6ar addinin nata, mutun huɗun nan da suka nuna suna da interest sune suka fara kar6ar addinin musulunci acikinsu, Ta biya musu kalmar shahada, Kusan Yini guda suka ɗauka tana ta fama dasu akan su maimaita sun kasa furta ta, Sai cikin dare Wani iko na Allah tana sake biya musu sai gashi sun maimaita lafiya lou batare da inda inda ba, Tayi farin Ciki sosai kamar ta zuba ruwa a ƙasa tasha, Duk da farin Cikin nata ragagge ne tun da sauran basu kar6a ba, Tafi damuwa akan danish saboda tana ji aranta idan har ya kar6i addinin zai taimaka ma sauran ƴan uwan nashi saboda suna jin maganarshi sosai, duk da haka bata ƙyale shi ba, ta addabi rayuwarshi ta hana shi sakat, Sai yana tsaka da yin bacci ya dinga jin muryarta acikin kunnanshi tana karanta mashi kalmatusshahada, wato da tsiya sai ya kar6i addinin, babu yarda batayi dashi ba, Amma Yaƙi bata haɗin kai a ƙarshe da ta gaji ta ƙyale shi badan ta haƙura ba, Ta dai bashi lokaci ne ya ɗan sarara, duk da haka bata yi fushi dashi ba, Sai ma ƙara janshi da take yi ajikinta, saboda sanin mahimmanci da yake da shi, dole saida shi wasu abubuwan zasu tafi dai dai, a 6angaren su batool da suka musulunta, tafara ƙoƙarin Koya musu addu’o’i da karatun kur’ani, sai dai wani abu dake ɗaure mata kai, Wahalar da suke sha wurin furtawa, Ita parveen ma hada amai take Yi idan angel ta matsa mata akan ta furta karatun kur’ani, ita kuma azeeza daga anfara sai ta kama bacci, ba ƙaramin takaici angel ke ji ba, daga bisani tayi wani zazzafan nazari, Acikin kwanakin kowani sati akwai wace rana da idan dare yayi tayi musu karatu suke amsawa lafiya lou batare da sun kakare ba, a irin ranar ne ta ta6a yi ma danish karatun kur’ani da daddare lokacin da giants suka dawo dashi kuma dai dai lokacin ne take basu tarihin annabawa batare da ta samu targaɗe ba, Kuma a irin lokacin ne su batool suka furta kalmatusshahada batare da sun yi inda inda ba, duk irin lissafin kwanakin da take yi Tun lokacin da daddynta Ya gudu da ita bata ta6a bari lissafin kwanakin wata sun ku6uce mata ba, Sai dai wannan karan ta kasa gane wace rana ce wannan mai tarin albarka? Meyasa take samun dama A ranar? Bata iya hasashen wace rana bace sai dai tana ganeta ne da alamominta, duk irin ranar ta zagayo bata bari ta tafi abanza, kusan kwana suke Yi da daddare tana Koya musu karatu tare da yi ma sauran ƴan uwan nasu da’awa kota samu suma Su kar6i addinin, Allah mai yarda yaso, Sai gashi ɗaya bayan ɗaya suna zuwa wurinta suna cewa suma zasu musulunta, cikin waɗan da suka kar6i addinin musulunci akwai, batool, azeeza, Hannah, Hibba, deeja, parveen, Eve, yasmin, Angel, Batool, rubina, Cikin maza mutun uku, Javed, Naufal da Mubeen, yanxu mutun biyu ya rage mata acikinsu, Haris da danish, Su kaɗai suka yi mata cikas, Duk da Tayi matuƙar yin farin Ciki, Da Allah ya bata ikon musuluntar dasu Hanna, Ranar da suka kar6i shahadar ko bacci bata yi ba, A tsakiyar gadonta ta zauna tana kukan farin ciki tare da Yi ma Allah godiya, daya bata wannan damar, Nima dai Na matse kwallata kuma na tayasu murna koba komai sun tsira da imanin da su ka yi, Allah zaiji ƙansu,

A wani dare Ne, dukkansu Sun kwanta bacci, Angel tana a kudundune cikin bargonta, kwatsam ta soma Jin shessheƙar kukan mutun acikin kunnuwanta, tun bata ɗauki abun serious ba har sautin kukan ya fara disturbing ɗinta, Sai kuma ta dinga jin hannun mutun asaman jikinta kamar ana bubbuga ƙafarta ƙasa ƙasa ta jiyo miryar mutun yana yi mata magana, A hanzarce ta yaye bargon jikinta ta ɗago da idanuwanta masu ɗauke da bacci biji biji take Iya ganin fuskarta, tana a zuƙunne gaban gadonta, fuskarta sharkaf da hawaye,

Mutsustsuke idanuwanta ta yi da yatsun hannunta don ta samu damar ganin kowacece, koda tayi arba da deeja sai taji gabanta ya faɗi rass! Tun kafin ma takai ga faɗa mata abunda ya kawo ta,

“Angel Jinin nan ne ya dawo mini, Na shiga toilet in yi fitsari shine naganshi, hankalina Ya tashi sosai bansan Ya zanyi ba,” fuskarta a yamutse tayi maganar, dafe kai angel tayi tare da ambaton”INALALLAHI WA’INNA ILAIHIRRAJI’UN! wannan wata irin masifa ce, mun shiga uku! Ni nayi tunanin Kun daina gaba ɗaya, ashe da sauranshi,” idanuwanta cike tab da kwalla tayi maganar,

Ruƙo hannunta deeja tayi acikin nata”Dan Allah angel, Ki san yadda za’ae ki hana atafi dani, wlh gani nake kamar idan aka ɗauke ni wannan karan baza’a dawo dani ba,” tana kuka ta yi maganar, Hankalin angel ya tashi matuƙa, Saukowa Tayi daga saman gadon ta nufi gadon Danish, Hannu takai ta ruƙo bargon daya lullu6a dashi ta yaye shi, Bubbuga ƙafadarshi tayi tare da ambaton sunashi”Danishi!danish!” daƙyar ta samu ya farka, Yana faman yamutsa fuska Yace”menene”?

“Pls ka tashi deeja bata da lafiya, Menstruation ne Yazo mata” ware idanuwanshi ya yi jin abunda tace, Saboda ya gane me take nufi, tun da tayi musu bayanin komai dangane da jinin,

“Dan Allah Danish kada ku bari Giants su ɗauke ta, mu taimaka mata,” yunƙurawa yayi tare miƙewa ya zauna saman mattress ya jingina bayanshi jikin bango, batare daya ce komai ba, idanuwanshi na akan deeja dake a zauƙunne sai kuka take Yi,

Ganin baida niyar tanka mata yasa ta wuce gadon haris, ta tada shi, daya farka ta sanar dashi abunda ke faru wa, Jikinshi har 6ari yake Yi, duk yabi ya ruɗe ya sauko daga saman gadonshi, Yana tambayarta Ina deejan take, Tun kafin ma ta bashi amsa sai ga deeja ta nufo su, Tana karasawa gabanshi ta fashe da kuka, Ruƙo hannunta yayi acikin nashi Ya janyota jikinshi Yana lallashin ta yana faɗin”ta kwantar da hankalinta, Ba wanda ya isa ya tafi da ita sai dai ahaɗa dashi atafi amma bazai ta6a bari giants su ɗauke ta ba, muddin Yana numfashi” Angel taji daɗin kalaman da haris yayi duk da tasan zaiyi wuya ya iya hana su tafiya da ita, Ga wanda taso Ya harzuƙa can saman gado Amma Yaƙi cewa komai, Haushin shi duk ya cikata, ta tsani halayyarshi ta lalaci da rashin son ta6uka komai,

“Haris Bari in tada su Naufal, In yaso sai mu haɗu mu duka mu hana su tafi da ita” Yace mata”toh” ɗaya bayan ɗaya tabi kowannan su saman gadanshi ta tada shi, duk wanda ya farka, Yaji abunda ke faruwa sai gaka ya zare ido saboda fargaba da tashin hankali, A tsakiyar ɗakin suka hallara su goma sha huɗu, sun sanya deeja a tsakankanin su suna jiran giants su ƙaraso, da alama yau sun shirya yin faɗa da Giants,

Motsin buɗe ƙopar ɗakin tsohuwa suka Jiyo, Da sauri suka kai idanuwansu kanta, a lokacin ta ƙarasa fitowa daga Cikin ɗakin Hannunta ruƙe da sanda, fuskarta a yamutse babu annuri babu walwala, Ɗagowa tayi tare da kallonsu

Babu wanda yayi yunƙurin yi mata magana, Sun ɗaure fuskokinsu, Saboda mugun haushinta da suke Ji,

Azeeza ce tace”ni dai bari in je in roƙeta kada ta bari atafi da deejan mu” har ta ɗaga ƙafa zata je wurin ta, Haris Ya damƙi hannunta tare da cewa”Ashe baki da hankali? Idan kinje kin roƙe ta me zata Iyayi mana? In banda ƙarya”? Wannan maganar ta haris tayi matuƙar girgiza tsohuwa,

Angel tace”Allah ya kamata ki roƙa ba ita ba, saboda shi kaɗai ne zai Iya taimakon mu amma waccan matar, Ba abunda zata yi mana,” takai karshen maganar idonta akan tsohuwa,

Jinjina kai tsohuwa ta yi jin abunda haris yace, daga bisani ta Dogara sandarta zuwa inda suke atsaye taci burki ta tsaya, ɗaya bayan ɗaya ta shiga binsu da wani irin kallo, sun rasa gane kallon menene take Yi musu, Juyawa tayi tare da kallon danish dake zaune saman gadonshi, Dama shi kaɗaine baiyi yunƙurin miƙewa ba, da alama baya goyon bayan abunda suke shirin aikatawa,

“Saboda shi yafi ku wayau da hankali shiyasa bai biye maku ba,” tsohuwa ce tayi maganar a lokacin da ta janye idanuwanta daga kan danish ta mayar dasu kan angel, Ido cikin ido suke kallon juna,

Murmushin takaici ne ya bayyana akan fuskar tsohuwa,

“Koda gigin wasa kada ku kuskura kuce zaku Hana giants tafiya da deeja!! ina gargaɗinku idan har kuna son zaman lafiya to ku daina yunƙurin shiga huruminsu…..” Haris ne ya dakatar da ita ta hanyar daka mata tsawa yace”Wai ina ruwanki da rayuwarmu ne? Bakin nuna baki damu da mu ba? To ki fita sabgarmu mana? Idan ke bazaki Iya hana su tafi da ita ba, to mu ki barmu muyi da kanmu” rai a6ace yai maganar,

Muryar danish ce ta ratsa kunnuwansu, a yayin da yake saukowa daga saman gadonshi yace”Haris ka sassauta kalamanka, Abunda tsohuwa ta faɗi gaskiya ne, Baza ku Iya ja da giants ba, Kuna Yunƙurin jefa rayuwarku cikin hatsari ne, Na rasa ya zanyi in fahimtar daku,” wani irin mugun kallo haris ya jefa mashi,

“Danish kana goyan bayanta ne? Bayan duk irin ƙarairakin da take yi mana, da kuma Nuna rashin damuwarta akanmu , Sannan da ita fa ake haɗa baki ana cutar da rayuwar ƴan uwanmu amma duk ahaka kake binta”? Zuciyarshi a hasale yayi maganar, sam baiyi tsammanin danish zai mara mata baya ba,

“Haris u ave to understand me, Bazamu iya yin komai ba, saboda mu ba komai bane, Ni bana so na rasa wani acikin ku…….” Kasa karasa maganar yayi ganin irin kallon hararar da angel ke jefa mashi, shiru yayi tare da duƙar da kanshi ƙasa,

Tsohuwa ta dasa da cewa”Bawai bana son taimakon ku bane, kawai ba yadda zanyi ne, Ni kaina giants sunfi ƙarfi na, matsayinsu da nawa ba ɗaya bane, sunfi ni ƙarfin iko, Idan nace zan hanasu tafiya da wani daga Cikin ku zan rasa raina ne……” Angel tace”Oh ashe ta ranki kike Yi? Su baki damu da rayuwarsu ba, Ae ni nayi tsammanin har rayuwarki zaki iya sadaukarwa akansu ashe ba haka bane, ƙaunar da kike yi musu ta bogi ce, Ni na tabbata da ace ƴa’ƴan da kika zuƙunna kika haifa ne da baki faɗa musu wannan maganar ba”

Girgiza kai tsohuwa tayi wannan karan idanuwanta hada farin ruwa kwance acikinsu tace”Bazaki ta6a fahimtata ba, Koda ace na sadaukar da rayuwata akansu nayi abanza, saboda yin hakan bazai canza komai ba, Ae ƙwarama Ni dana 6ata tsawon shekaru ina rainansu, Iyayensu fa da suka sadaukar dasu? Suna can suna sharholiyarsu sun ma manta da suna da wasu ƴa’ƴa da suka sadaukar, Nifa kaɗaice na damu daku, Ni da ban haɗa alaƙar komai daku ba, ae na cancanci a jinjina mini”

Maganar tsohuwa ta yi matuƙar girgizasu, Kallon kallo suka shiga yi atsakaninsu, batare da wani ya kuma Yin magana ba,

“zan Koma ɗakina, Amma kafin nan zan ƙara ja maku kunne, Kada Ku kuskura ku shiga hurumin giants, Idan Kunne Yaji Jiki ya tsira” tsohuwa na kammala maganarta, Ta juya tana dogara sanda ta shige Cikin ɗakinta, Idanuwansu akan abayanta har saida ta 6ace ma ganinsu….

*Domin neman ƙarin bayani 08103884440 ko 08169856268 Text on whatsapp only banda phone calls, Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, Ga wanda ya shirya yin payment, zai iya yi mini magana, Cikin next month Takun farko zai ƙare in sha Allah, zamu nutsa Cikin labari*

share fisabilillah❤👌

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button