Sponsored Links
Gidan Aunty Book 1Hausa Novels

Gidan Aunty Book 1 Page 61

Sponsored Links

BOOK 1
Page 61

Tsayawa yayi a inda yake gabaki d’aya hankalinsa ya gama tashi ganin ta da wuka a hannunta, kalaman dazu take ta kara maimaitawa,gyada mata kai yayi shima “ ok zamu rama muma amma bani wukar nan tukunna”, kin bashi wukar tahee tayi saima fashewa da wani saban kukan tayi, jikinshi har rawa yake dan ya gane ba ita kadai ce ba, tsoransa karsu cutar da ita, sunan dazu da ta kira ne ya fado masa kafun ya kalli yanda take faman hada gumi duk da sanyin Ac dake fitowa, bayanta ya kalla kafun ya furta “NONNA”, da sauri ta juya tana sakin wukar hannunta, yana gani ta juya taku biyu yayi ya damki Dan tsan hannunta, kara ta sakar masa sai faman fusge fusge take ita kadai, wata iriyar gigitacciyar tsawa ya daka mata yana hade fuskarsa kamar bashi ba, “ki nutsu”, ya furta cikin kausashshiyar murya , nutsuwar kuwa tayi tana sun kunyar da kanta, “ ya sunanki “, shiru tayi tana kara sunkuyar dakanta, “karki bari na sake maimaita tawa “, cikin shashsheka ta furta “sunana LOLA”, dan kallanta yayi jin tayi magana da wata iriyar murya”wacece ke , me yasa kika shiga jikin mata ta”, yanxu ma shiru tayi masa, bece komai ba kafun a cikin dan daga murya yayi Bismillah, rawa jikinta ya fara ,” ah ah zanyi magana ka bari dan Allah “ ta fada cikin rikicewa, banza yayi mata kafun ya fara karatun alkuranin, yanxu kam ihu ta sa masa tana rokonsa karya konata, zaunar da ita yayi kan kujera har yanxu hannunsa na rike da nata kafun ya dakko wani bottle water da ke gefensa ya ajje mata a gabanta, da sauri ta saka hannu zata dauka ya matsar da ruwa nesa da ita “ ruwa , ruwa “ ta fara fada , “zakisha”, ya furta , bata jira ba ta amsa masa da Sauri” zan baki ruwa idan kin gama amsamun tanbayoyina, sabanin hakan kuma zan kona kine “, wacece ke, me yasa kika shiga jikin matata”, cikin wata iriyar murya ta fara kuka , “ ba cutar da ita nake ba, te makonta nake, suna san Kasheta ne kamar yanda suka kashe mun ahalina”shiru yayi na yan sakanni kafun cikin kausashshiyar murya ya furta “Menene hadinki da matata, sannan menene alakar ku da matata da zaki shiga jikinta”, ina bata kariyane kamar yanda Nima ta taba temakona a lokacin baya,ni ba muguwa bace, suna harin rayuwar tane”, su wanene” da mugun firgici ta kallesa , zasu kasheta kamar yanda suka kashe shi, bazan iya va”,wani irin rawa jikinta ya fara,”ruwa !!ruwa!!”, ruwan ya dakko kamar yanda ta bukata amma be bata ba,”banasan jin wannan tatsuniyar taki, kar na sake ganin ki a jikin matata, idan va haka ba zan konaki da ayoyin uban giji, ki gaggauta fita daga jikin matata yanxun nan”,kanta ta daga masa tana rike makoqwaranta, ruwan ya mika bata da mugun sauri ta fara sha, saida shanye duka kafin ta fara sakin ajiyar zuciya,”zan fita daga jikinta, Kai ma nagode da yanda kake kular mun da ita,nasan kana kula da ita amma ka nunkashi sabida kokarin kasheta da suke yi, ganin komai nasu ya fara lalacewa,ka kula da ita “, tana gama fadar hakan tahee tayi atshawa me karfin gaske,kafun ta sulale ta fado kan king da yayi saurin tarota, cikin zafin nama ya dauke tare da kaita cikin bedroom, kallan yanda take bacci peacefully yayi, kokarin kawar da tunanin yun kurin kashe masa mata da akace yake, iska ya furzar a hankali kafin ya furta “ it’s a lie”. System dinsa ya dauka bayan ya canza kayan jikin sa, ya jima yana operating a kanta,lokaci zuwa lokaci yana kara dubata duk da yana kusa da ita, kiran sallah la’asar ne ya tayar dashi, kan gadon ya karasa har yanxu bacci take peacefully abinta, goshinta ya danyi pecking kafun ya bar dakin.

Mintuna 15 da futarsa ta fara motsa idanuwanta kafun ta budesu gabaki d’aya, mamakine ya kama ganin ta kwance akan gado, wayar da akayi mada da text message ne kawai ya fado kanta, duk yanda zata tuna zuwan ta kan gadon ta kasa, sakkowa tayi daga kan gadon bakinta dauke da addua, agogon dakin ta duba, 4 ta wuce da sauri tashiga toilet kafun ta fito ta kabbara sallah , tana Idarwa azkar dinta tayi kafun ta mike , kara kallan agogo tayi mamakinta har yanxu be dauke ba ganin be dawo gida ba, dan karamun bakinta ta turo waje kafun ta bar dakin, shima falon shiru alamar ba kowa a ciki,3rd floor ta hau nan ma shiru sai ac da kamshin turaran da ke buso dakin,dacin da bakinta ya somane yasata nufar fridge din data gani, tana budewa kuwa idanuwanta ya sauka kan kayayyakin ciye ciye dake shake a ciki, fiye da saurin fridge din, wani abun ma bata taba ganin saba, strawberry ice cream din data ganine yafi daukar hankali, janyoshi tayi tana sakin wani murmushin jin dadi, waje ta samu akan gado tana shan ice cream din, tana sha tana sakin dariya sabida yanda dadin ke ratsa mata kwakwalwa, idanuwanta ne suka sauka kan wata yar karamar roba dake kan bedside dinsa, ajje Ice creams din tayi tana janyo robar “ANTI DEPRESSANT” shine abunda aka rubuta jikin robar, har zata mayar sai kuma ta fara karanta abunda ke jikin robar, da wani irin shock ta mike tsaye, tana karanta abunda ke jikin robar, wasu hawayene suka fara sakko mata kawai ta fada kan gadon ta fashe da kuka , saida tayi me isarta kafun ta mike dauke da robar a hannunta, zata bar dakin kenan shikuma yana shigowa da sallama a bakinsa kasa kasa, cikin zuciyarta ta amsa sallamar tasa fuskarta kwata kwata ba fara’a, kallan yanda fuskarta ta dan tashi yayi kafun cikin sauri yayi yunkurun nufar inda take”what’s wrong with my baby”, hannunta d’aya ta nuna masa alamar ya dakata karo na farko a rayuwarta, da wani irin expression yake kallanta, be gama tunani ba ta dago robar drugs din dake hannunta, “ Menene wannan”, ta fada tana zuba masa idanuwanta da suka kara haske sabida kukan da tayi,wani irin harbawa zuciyarsa yayi” sam ya manta daya sha drugs din ya barshi a fili”, cikin dan daga murya kamar ba ita ba ta furta “ maganin Menene wannan kakesha “, kokarin matsota yake ta kara dakatar dashi” please calm down, am sorry I will explain”, bata san lokacin da ta buga robar a ‘kasaba maganin ciki ya zube” me yasa , me yasa , I thought Dagaske kake da kace kana sona, i though da gaske kake da kace kai dady nane, kana shan wancan pills din dukda kasan illar su, u’re a doctor, I thought ka d’auke ni a matsayin matarka, Aushe nayi kuskure ba haka bane, you’re taking this drugs to…. to…”, ta kasa karasa zancan nata sabida wani saban kukan da yake kokarin zuwan mata tana dannewa, wani irin shock ne ya dake shi, jin kukanta yake kamar ana kara cakarshi da maki a zuciya gabaki d’aya ya rikice , cikin sanyin murya ya furta “ please don’t be angry, I will explain “, manyan eyes dinta ta zuba masa hawaye na sauka akan idon nata” bana bukata” kawai ta furta tare da barin dakin, wani irin jirine yaji yana neman kayan dashi yayi saurin samun waje ya zauna , ga baki daya hannayensa ya tusa cikin gashin kansa yana ya mutsasu “ I’m in a big mess , she’s more angry than ever”, ya rasa Wana irin tunani zaiyi , bayaso koka d’an tayi fushi dashi dan bazan iya daukan fushinta ba, da sauri ya mike ya nufi bayanta, yana shiga ya tarar da bata cikin bedroom dinta, ragowar bedroom din second floor ya duba , shima duk bata ciki, muryar da ya fara ji sama sama a falon kasane yasashi nufar falon kai tsaye, TAHEE ce a falon tare da su sumayya da suka zo falon, wani irin ajiyar zuciya ya sauke yana binta da kallo , adaidai lokacin da ta daga idanuwanta itama, tana ganinshi ta d’auke idanuwanta fuskarta a dan hade kadan ta yanda su Ihsan bazasu gane ba.” Oh my god “ ya furta cikin zuciyarsa har yanxu ya masa dauke idanuwansa akanta, su firdausi na ganinshi suka kara gaishe ganin yanxu yana amsa musu gaisuwarsu bakamar daba, kanshi ya dan daga musu alamar amsawa dan kwata kwata ba shi yake bukata ba,so yake ya rungumeta, ya lallasheta ko zata dena fushi dashi, he want to feel her warm , he can’t take it”, satar kallansa ihsan tayi ganin yanda ya tsaya gabaki d’aya hankalinsa na kan tahee dake dannawa waya,murmushi ta saki kafun ta kalli tahee,” sister yau dai bari na cika miki alkawarin Pam cake din ki”, bata jira amsar tahee ba ta mike ta nufi kitchen, firdausi da sumayya ma duk sun ankara dashi dan haka da sauri suma suka mike “muma bari mu tayaki” dukansu basu jira jin amsar taba sukayi saurin guduwa , bece komai dan Hakan yake bukata, ganin ta tashi zata bi bayansu yayi saurin shan gabanta, hannunsa biyu yayi hade alamun pleading, dauke kanta tayi daga kansa zata wuce yayi saurin riko hannunta, fisge hannun tayi kafin ta furta “ don’t touch me again “, tana gama maganarta tayi upstairs, waje ya samu ya zauna kansa na sara masa, gabaki d’aya launin idanuwansa ya canza Sabida yanda yaji xuciyarsa na masa zafi, ya dau tsawan lokaci zaune a kan kujera kamar ya bita amma yana tsoro karta kara wani fushin, ganin lokacin sallah yayi ne yasashi barin part gabaki d’aya .

Aban garan su ihsan kuwa suna shiga cikin kitchen din suka kulle kofar, kwai kwayar yanda suka ga king na kallan tahee suka fara, “wayaga Romeo and juliet “ cewar ihsan , dariya suka saki gabaki d’ayansu, kan kujerun dake kitchen suka zauna suna dasa saban hira , daman space suka basu kar king ya koresu, sun dade suna hira abunsu kafun su fito falo, ganin babu kowa ne yasasu sakin ajiyar zuciya , da Sauri ihsan tayi hanyar kofa ,kallanta sumayya tayi alamun karin bayani” kun manta pan cake mukace zamuyi mata, tana fitowa kara zaunar da mu zatayi , ni kuma ban shirya shan masga ba Wajan yaya”,ga baki daya basu yi wannan tunanin ba, gudun karta fito tazo ta samesu sukayi saurin barin part din.

Tahee kuwa tana shiga daki wani saban kukan tayi kafun ta shiga ban daki, Wanka tayi ganin ana kiran sallah tayi alwalarta, ta kabbara sallah bata bar daddumar ta ba sai da akayi isha’i, wasu English wears ta saka masu daukar hankali blue colour , cikakken gashin kanta ya sakko har bayanta duk da hular da ta saka, wani irin masifaffen kyau tayi na musamman amma fuskarta har yanxu a cin kushe take, Fararan hannunta da yan yatsunta sun fito fes da masu musamman da kunshin hannunta ya kara fito da farinsu,Daddadan kamshin turaran princess ne ke tashi a cikin dakin ta ko ina, message din data gani akan wayarta ne ya sata sakin baki “ sorry sis karkizo kiga bamanan ummey ce ta kiramu”, ba kowa bane ya tura mata text din face ihsan, hararar wayar tayi kamar suna gabanta,kafin ta fito daga dakinta, karo suka ci da king da gaba daya yanayinsa ya canza, kallo daya tayi masa kafun ta d’auke kanta “ sannu da zuwa “ ta furta zata bar wajan, ya rungumota ta baya yana sakin ajiyar zuciya, cikin disashewar murya kamar mara lapiya ya furta “ I can’t take it any more , please am so sorry, bayanda Kike tunani bane,” raba jikinta tayi da nashi kafun ta furta “ your dinner is ready”, am not hungry, ya furta yana binta da kallo, bata kuma ce masa komai ba tayi wucewarta kan dining, apple ta dauka guda daya ita ma, ta wuce dakinta, zuciyar ta na raya mata ta kallesa amma ta danne, tana barin Wajan ya dafe kansa dake sara masa, tayi masa kyau sosai yau , and he don’t like her frowning face, cikin sanyin jiki ya nufa dakin shima , yana kallan yanda take shan apple dinta cikin kwanciyar hankali, bece mata komai ba yace toilet,ya dade a ciki bayan ruwan sanyin da ya sakar wa kansa, ganin zazzabin nasa na kara yawa ne yasashi kashe ruwan, shima wasu kayan bacci ya dauka white colour masu kauri sabida yanda yake jin sanyi, turare kawai ya fesa ya fito, yana fitowa yatarar da fitula aka she sai lamp din da aka dan kunna, sai tun zuciyarsa ya rike yana cije lips ,sallar da ya saba yake so yayi amma ya kasa sabida ynda yake jin jikinsa, a tunaninsa tayi bacci ne shiyasa ya na hawa bed din ya janyota jikinsa yana sakin ajiyar zuciya,kara rungumeta yayi kamar wacce za a kwace masa ita, tun lokacin da ya rungumeta ta bude idanuwanta ga zafin jikinsa dake ratsa nata jikin,tausayi ya bata kamar tayi magana sai kuma tayi shiru har bacci ya dauketa, “ am so very sorry “ yake fada a cikin zuciyar sa….

Mss Lee 💖

GIDAN AUNTY
07041879581

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button