Sponsored Links
Gidan Aunty Book 1Hausa Novels

Gidan Aunty Book 1 Page 15

Sponsored Links

Free page 15 🦋

Karfe 8:30 na dare, amrah ce sanye da d’an karamin towel da ko gwiwa bai karasa mata ba,sai uban gashin attachment din dake yawo a bayanta ,waka ta saka tana tikar rawarfa sai da ta gaji dan kanta sannan ta kashe tana sauke ajiyar zuciya. Toilet ta nufa da nufin watsa ruwa ko d’an kwali babu akanta, ta karasa kenan zata kunna fanfo, abinda ta ganine ya firgita ta tare da sakin gigitacciyar kara, a guje ta juya da niyar komawa , amma kafin ta karasa wajan komar wata irin mage ce ta fito ta wajan fara tass da ita, wata karan amrah ta saki, tuni ta fita a hayyacin ta sai faman ihun neman agaji take, dan karamun towel dinta ma tuni ya fadi a jikinta, saukar bulalar dataji a fatar jikintane yasata sakin razanannan kuka, sosai bulalar ta shigewa, bata gama shafa wajan ba ta karajin saukar wata bulalar, kuka kawai ta fashe da shi, ba tsaya ba aka dunga zulamata wannan bulalar, gadan gadan farar Magen nan tayo kanta, ganin haka yasa amrah sakin wani gigitaccen kara tana zube a kasa sumammiya.

*******
Tana shiga daki ta fada kan gadanta sai faman murmushi take saki ita kadai, sosai take sakin murmushi idan ta tuno fuskarsa da irin yadda yake hade fuska, take fargaba da tsoransa ya kara shiga jikinta, musamman da taji ammi na kiransa da son.Lumshe idanuwanta tayi amma still shitake gani ,duk da tsananin tsoransa da ya dirar ma , amma sosai ya burgeta a iya ganin da tayi masa. Wanka ta tashi tayi kafun ta kwanta tana adduar bacci, mintuna kadan bacci ya dauketa.

Sosai wasu irin halitta ke binta, yayinda tarike hannun wani da ba’a iya ganin fuskarsa, amma sai faman kareshi take daga cutar dashi dasuke kokarin yi, tun tu’ben da tayi ne yasa ta faduwa, shima Wanda tarikewa hannun ya tsaya har yanxu ba’a iya ganin fuskarsa, kafun suyi wani kwakkwaran motsi , wadannan halittun sun zagayesu sai tsalle suke saki , daya daga cikin sune yayi kanta yana zaro harshe , daidai yana kokarin cabkota wani irin girgiza ya karade ko ina, take a wajan wata katuwar farar macijiya ta bayyana a wajan, daga gefenta kuma wata farar kuliyace me shegen haske , sosai ta fito da farar farcinan, yayinda bakinta yake abune sai faman “meow meow “take cewa. Zabura wadannan halittun sukai kafun su fara Kai musu sara da faratansu, sosai macijin nan da Farar kuliya sukai musu jina jina lokaci daya suka bace batt ba aganinsu. A firgice tahee ta farka da ga mummunan mafarkin data fara duk jikinta yayi gumi sai faman zufa take hadawa, adduar neman tsari ta fara karantawa har taji nutsuwarta ta Daidai ta kafun ta mike tashiga bandaki, mintuna kadan tafito dauke da alwala, nafila tayi tare da adduoin da oumma ta koyasu hartaji ta kara samun nutsuwa kafun ta mike ta koma bacci.

➰➰➰➰➰➰➰➰➰➰
🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧

BUNKURE

Duk da tsananin yadda bintalo ke ihun ta hakan be sa yaji tausayintaba sai ma kulle mata baki da yayi da kazamin bakinsa me shegen wari, sosai yake zuba muguntarsa akanta, tsabar wahala kusan sumanta uku , azaba na sawa ta farfado, iya rashin imani saida yayi mata yayi mata kaca kaca ko dan yatsanta bata iya motsawa, se hawayen azaba dake digo mata ta ido, azuciya kuwa ta tsinewa Dije yafi a irga duk da kasancewar ta mahaifiyarta. Saida ya gama lalatarsa sannan ya bawa Dije da ke rabe damar Shigowa ya tafi da ita cikin hade rai, duk jikinta yayi sanyi ganin irin aika aikan da yayi wa bintalo, amma ko saudaya batayi nadamar hakan ba tunda burinta zai ciki, cikin razananniyar muryarsa me tsoratarwa ya daka musu tsawa akan su bace da ganinsa, ganin yadda bintalo ta kasa ko motsine yasasa babbaka dariya” ku sawa ranku aikinku kamar ya tabbatune” sai ga wata kwarya nan ta fado kasa da dan karamun ruwa a ciki jaa da shi, ruwan yasa dije ta dauka ta kwarawa bintalo a gabanta, cikin Karkarwa ta dauka tare da kwara mata, wani irin gigitacciyar azabar kara bintalo ta saki da ya firgita Dije , kara babbakewa da dariya yayi tare da hade ransa , kusan mintuna uku bintalo na kukan azabar nan kafun ta sauke nannauyar nunfashi tare da mikewa da kanta, ganin hakan yasa dijen sakin ajiyar zuciya a haka suka ajiyewa boka kudin da suka zo masa dashi tare da fita da baya baya har suka bar wajan, sai lokacin bintalo ke taku da dingishi dukda azabar da take ji ta ragu babu ita,amma gudun kar a asirinsu ya tonu basu koma gida ba sai wajan shadayan dare lokacin babu wuta, sannan babu me gane halin da suke ciki, zuciyar dije sai faman zillo take akai ta aiwatar da kudurinta kan oumma da suka shige mata hanci , ga wani tsanar su da ke kara ruruwa a
Zuciyar ta.

************
Tunda ya tashi yau be fita ko ina ba sai bayan karfe goma na safe bayan motsajikinsa da yayi, Hakanan yau besan jin kowa a kusa dashi ga yunwa yana jin amma ya kasa motsa koda dan yatsar sane, coffee yake San sha dan haka ya mike cikin takun kasaitarsa kamar kullum, a hankali yake taku sanye Yake cikin black trouser da black singlet , sosai kakkarfar surar jikinta ta bayyana , farar fatar jikinsa sai sheki yake dauka, a hankali ya karasa inda coffee maker din yake, cikin yan mintuna ya gama hada coffee dinsa , a nutse ya zauna kan daya daga cikin sofa din wajen , sipping daya yayi wa coffee din tare da ajjesa, wani irin daci yaji coffee din nayi masa kamar zaisa amai, a hankali ya kara lumshe idanuwansa ko me ya tuna oho, sai gashi ya mike tare da nufar wani daki, ko cikakken minti ashirin beyi ba wani daddadan kamshi ya karade ko ina , a hankali kamshi ya kara kusan towa kafun mamallakin kamshin ya bayyana , sosai shigarsa tayi masa kyau , sanye yake cikin black suit sosai bakin suit din cikinsa ya fito da ainahin kalar farar Tatar’s a da sai sheki take , bakin nan kullum sai kara turuwa yake kamar mai shafa abu wajan, har yanxu fuskarsa a hade take amma sosai yayi kyau , ga diamond watche dinsa sai faman kyalli yake, wayace kare a kunnansa sai faman motsa baki yake ko abunda yake cewa ba aji, be tsaya a ko ina ba sai part din amminsa .

A zaune ya sameta cikin shigar manyan mutane da ta saba , sosai tayi kyau cikin shigarta, kujerar da take zaune ya nufa tare da langwabar da Kai kadan, kallansa tayi tare da dauke kanta, bai ce komai ba sai hannunta da ya kamo ya dora a fuskarsa , a fusge ya furta “sorry ammi”, ajiyar zuciya ta sauke daman ba fushin take dashi ba ganin yaki zuwa haryanxu kuma tayi kewarsa ne yasa ta yi masa haka, a hankali ya furta “ina kwana ammi na “, murmushinta da baya boyuwa ta saki “ ka tashi lapiya son” lumshe mata ido yayi kawai batare da yace komai ba , ganin hakan yasan ammi tasan yan miskilancin ne a kusa, kadan suka taba hira yana amsawa kadan kadan,shafa gefan fuskarsa tayi” da alama wannan son din nawa ne ci komai ba” kara lumshe mata ido yayi tare da bude wa alamun amsa . Mikewa tayi “bari na dafa maka abinci ko” riko hannunta yayi tare da kallanta “ coffee” shine kadai abunda yace mata , jinjina masa kai tayi tare da nufar kitchen din, a tsaye ta samu tahee da asabe na aiki a kitchen , sosai tahee take jin dadin hakan sabida tana Kaunar taga ta iya abinci hala hala , ba tare da ta kalla taheen ba ta soma magana, “tahee hadawa son coffee kafun na kammala dafa masa abinci”, suman tsaye tahee tayi , zuciyar ta sai bugawa take gashi bata da dalilin musawa, kamar wacce zata saki kuka haka ta hada coffee din tare da fita falo , ko ina na falon mayataccen kamshin turaran da ke mata dadi ne ya cika wajan, Zuciyarta sai faman zillo take sabida tsoro, a hankali ta karasa inda yake bayan tayi sallama , cikin in ina ta soma magana “ina.. kwana”, kamar wacce tai da gunki ko motsi beba sai ma sarrafa wayarsa da yake cikin nutsuwa , kamar wacce zata saka kuka ta kara cewa “ina.. kwana”, yanxu ma be motsaba balantana tasa ran amsawar, siraran hawayene suka dan zubo mata kadan tare da sun kuyar da kai, kamar daga sama tayi saukar muryarsa “ fine” , wani murmushi ne ya subuce mata, sosai taji dadin amsawar dayayi, a hankali ya sa fararan dogon yatsunsa tare da dauka cup din, a hankali ya fara sipping, zuyawa tahee tayi da niyar komawa tazo daf da kitchen din ta tsinkayi muryarsa “ who permit you to leave”, sun kuyar da kai tayi tare da dawo wa ciki “ bakowa “ ta bashi amsa , tsawan mintuna goma tana a tsayen , kofin hannunsa ya ajje tare da kyara zama, another cup,”Tom “kawai tace masa tare da nufar kitchen din, har lokacin ammi na tsaye tana masa abinci da kanta, kallanta ammi tayi sai yanxu, sauke ajiyar zuciya tayi “wani cup din yace na hada masa”kallanta ammi tayi sai dai bata ce mata komai ba sai jinjina mata kai da tayi, wani cup din ta kara hadawa tare da nufar inda yake har yanxu zuciyarta bata bar bugawa ba, sallama tayi a falan kamar bazai amsa ba , sai ya amsa a hankali, batare da wani dalili ba lokaci daya taji kanta ya sara mata Daidai lokacin da zata mika masa coffee din, a maimakon ya sauka a hannunsa sai ya subuce ya zube a jikin hadaddan suit dinsa …….

         (😳😳Tahee )……

Manage plx ….

Masu comment ina Godiya sosai da sosai

MASU BUKATAR COMPLETE DIN GIDAN AUNTY YAYI MUN MAGANA TA WANNAN NUMBER 07041879581 .

MASU BUKATAR A TALLATA MUSU KASUWANCINSU SU TUNTUBENI TA WANNAN NUMBER 07041879581 AKAN NAIRA 500 KACAL.

💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖

DUK KARFIN IZZATA ( star lady )

GIDAN AUNTY (mss Lee )

JINI DAYA (mrs bbk)

YA FITA ZAKKA( maman sayyid)

BABY (mhiz innocent)

💖💖💖💖💖Mss Lee ✍️.

‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/JyvVuOvzYyF19np8UmFKV4

💖💖GIDAN AUNTY 💖💖
(a heart touching love story)

Story & written
By
Mss Lee 💖

PAID BOOK

LITTAFIN GIDAN AUNTY NA KUDI NE AKAN NAIRA 300KACAL , MAI SAN CIGABA DA KARANTAWA HAR KARSHE ZAI BIYA KUDINSA TA WANNAN ASUSUN :
7041879581 OPAY
AYSHATOU GALADIMA , sai a turo da shaidar biya ta wannan number 07041879581.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button