Sponsored Links
Gidan Aunty Book 1Hausa Novels

Gidan Aunty Book 1 Page 17

Sponsored Links

BOOK 1 📕

Free page 17🦋

Duk binsu da kallo ammi tayi ganin lokaci daya duk sun tsorata,suma duk sai sukai shiru ganin irin kallan da ammi ta bisu dashi, tahee da zoya ma duk tsayawa kallansu sukai, kamar daga sama cikin sauri amrah tace “zani ammi”jinjina mata kai ammi tayi tana sauke ajiyar zuciya, kafun ta karasa kitchen taji saukar muryar sumayya” Ammi nasan kayan sunyi yawa bari na temaka mata”ta karasa tare da dallawa amrah harara batare da ta bari ammi ta ganiba, ita tahee dariya suka bata ma, ko za a yankata aibazata je inda za a ballataba,jinjina mata kai ammi tayi tare da karasa shigewa cikin kitchen din, cikin sauri amrah ta jiyo tana kallanta,”mtswww na tsani shishshigi Wallahi “, kallan rainin wayo sumayya ta bita dashi, “zaki hanani taka ko ina na gidan mune”, dogon tsakin da firdausi taja ne ya katsesu “malamai kunbi kun ishemu inda gaske sansa kuke kuje kuce a aura muku shi mana kinbi kun cika mana kunne” tana gama fadar hakan ta mayar da headphone din kunnenta, ba Wanda ya kara cewa komai sai kallan banzan da suke bin junansu dashi , ihsan kam sharesu tayi tacigaba da game din da zoya ta sa musu , zuwa zaune kusan yan mintuna su asabe suka fito da kayan da za akai masa, har yan rigen rigen tashi ake tsakanin amrah da sumayya,amrah ce ta fara karasa tare da amsa kayan hannun asabe tana yatsina fuska,itama sumayya ragowar kayan ta dauka tana hararar amrah, Tashi tahee tayi da niyar komawa daki ammi ta tsayar da ita, “Kema daughter jirani na aikeki part din dada da na ummey”tana gama fadar hakan ta shige wani daki, mintuna kadan tafito dauke da wasu designers bag guda biyu, lokacin har su amrah sun bar part din, purple din ta nuna mata na dada ,red din kuma na ummey, mikewa zoya tayi “ammi zan bita”murmushi ammi ta sakar mata “toh daughter “kama hannun tahee zoya tayi, kowa na mamakin ganin lokaci daya ta sake da tahee, Kai tsaye part din dada suka fara zuwa Tun a hanya zoya Kezuba mata surutu falon yayi saura daga ihsan sai firdausi dake jin waka.

Zaune dada take kasan lallausan carfet din falon ta, kamshin farfesun kayan cikin da akai mata sai faman tashin kamshi yake, cikin sallah tahee ta shigo falon tare da zoya,amsa sallamar dada tayi tana sakar masu murmushi” sai yanxu kika tuna dani tahura, ai nayi fushi “,sun kuyar da Kai tahee tayi cikin jin kunya” kiyi hakuri dada ba haka bane”, dan ta bile baki dada tayi “ gaskiya kam ki gyara, ko d’an hirar nan ki dunga zuwa kina tayani tunda su wadancan bankadaddun ba zuwa suke ba, sarakine kawai shima kullum cikin fada muke”, kallan ta zoya tayi”dada nifa , kinsan dai ina zuwa ko”,sakin baki dada tayi tana kallanta” kiji tsoran Allah, ni nayi mamakin ganin ki ma yau, ba dai kyau karya kinsani”, dariya zoya tayi tana rufe dan karamin bakinta, sakon da Ammi tabayar abata tahee ta mika mata “Allah sarki,kilishi ba dai mutunci ba ,duk gidan nan ita da hajiya suhaima ne masu kaunata sai sadauki”ta karasa zan Canta tana Shan farfesun ta, kallan tahee dake wasa da hannunta tayi”kinga zamu bata sai wani jin kunyata kike kamar wacce akace miki na zama sirikarki”, sosai dada da zoya suke janta hira tun bata sake ba har ta sake da su, sun dad’e suna hira kafin tahee tace zata kaiwa ummey sakonta,’kin barin ta dada tayi har saida taci farfesun da ta zuba musu zoya sai faman dariya take musu, da zata tafi ma sai da tayi wa dada alkawarin dawowa anjima sannan ta barta,tsakanin part din dada dana ummey ba nisa shiyasa basu dade ba suka karaso, sai bin ko ina tahee take da kallo ganin irin kyan da wajan yake dashi, zoya na gaba tahee na bayanta har suka shiga hadaddan kayataccen falon, sosai falon yake da girma da tsaruwa,ta ko ina kamshi ne ke tashi da sanyin Ac, ganin babu kowa a falon yasa tahee zama kan lallausan carfet din falon me shegen laushi da daukan ido, a guje zoya tashiga wata kofa kusan minti 5 sai gasu sunfi to ita da ummey dake sanye da black abaya sosai kyawun ta na larabawa ya bude shekarunta, wacce ta ganine yasata dan sakin murmushi, tare da zama kan daya daga cikin lallausan kujerun falon, gaishe da ita tahee tayi , yayinda ummey ta amsa mata cikin kulawa, haka kawai taji yarinyar ta kwanta mata arai sabida nutsuwarta, sakon ammi tahee na mika mata, wani murmushin ummey ta saki,”kice mata nagode sosai kuwa, bata gajiya “yadda ummey ta yabi ammin sai kaunar auntyn tata yakara shigarta sosai take santa,mikewa tayi daniyar tafiya ummey ta zaunar da ita “ ina kuma zaki, yanxu zamuyi lunch “ komawa tahee tayi ta zauna bazata iya yi Mata musuba sabida kunyarta da takeji, kallan ummey zoya tayi” ummey kingama a part din dada guduwa tasoyi “,girgiza mata kai ummey tayi cikin yaren larabci “bana hanaki surutu ba”, sun kuyar da Kai tayi”ana asf”ummey bata kulataba sai kallan tahee datayi “daughter taso muje muci abinci”ba yadda tahee ta iya dole ta mike ,tare suka nufa hadadden dining din dake falon,sosai wajan dinning ya hadu kasancewar wajanshi daban a cikin falon bayan antaka 3stairs, dakanta ummey tayi serving Dinsu , sosai kamshi girkin ya cika ko ina , nut spicy herb rice da Greek chicken kebab ummey ta zuba mata ,sai wani yan bowl masu shegen kyau da ta zuba mata salad da sauran dishes din, cikin glass cup kuwa strawberry milkshake ne aciki me shegen sanyi, sosai abincin ya birge tahee amma ta kasa moshi ,sai godiyar da tayi wa ummey kawai, itama ummey serving din su tayi ita da zoya, har sun fara cin abinci ganin sai wasa tahee take da spoon din hannunta ummey ta kalleta” daughter ya naga ba kyaci, ko abincin be miki bane”saurin girgiza mata kai tahee tayi “a’ah ummey yanxu zan faraci” ta fada tare da soma cin abincin a hankali , ummey batace komai dan Sarai ta gane kunyarta tahee takeji,suna cikin cin abincin kuwa daddad’an kamshin turaren da basuyi tsammani bane ya cika dodan hancinsu,da ma duk wani kamshi dake tashi a falon,kasa cigaba da cin abincin tahee tayi zuciyar ta sai faman bugu yake, naman da yake bakinta ma ta kasa taunawa sai faman tsotsanshin take, a hankali cikin daddadar muryashi yayi sallama , amsawa sukai baki daya banda tahee da ta kasa mosi, zoya sai kallansa take tanaso taje wajan sa amma ya Hana ta intanacin abinci,kan daya daga cikin kujerun falon ya zauna tare da crossing legs dinsa , binsa da Kallo ummey tayi , tayi kewarsa sosai da sosai amma a zahiri sai dauka hankalinta be kansa, cikin kasa kasa da murya zoya ta kalli ummey” ummey please ki cewa akhii yazo muci abinci , this once only please “kallan ta ummey tayi tare da dauke kanta,ganin hakan yasa zoya kara marairaicewa “please ummey”, girgiza Kai kawai ummey tayi har lokacin kuma tahee ta kasa ko kwakkwaran motsine, duk maganganin zoya yanajinta Sarai amma a zahiri sai ka dauka bayacikin falon,cikin larabci yaji saukar muryarta” taso muci abinci”,kamar bazai motsaba sai kuma ya tashi a hankali tare da nufar dining din ba tare da yace komai ba, Daidai inda yake shigowa tahee tana facing din sa, sarkewar da idanuwansu yayi te yasata shakewa da abincin da ke bakinta, sosai take tari dan ba hakaramun Shakewa tayi ba…

*********Tun lokacin da suka baro part din ammi suke wa juna kallan kaskanci, daman ba shiri suke da junansu ba musamman da ya kasance suna san mutum d’aya , har suka karasa part dinsa ba Wanda yace wa kowa kala,duk da fargabar dake tattare dasu haka ko waccen su ta shiga falon dan bakantawa yar uwarta, bakowa a falon kasa ganin hakan yasa amrah nufar center kujerun tare da ajiye tray din hannunta, itama summy cikin gadara tanufi inda amrah ta ajje nata inama ta dora natan, ganin hakan yasa amrah saukar da na sumayya, itama sumayya sai abun ya bata haushi ta dan kwalar da na amrah, cikin kankanin lokacin suka fara ture turen abinci,a lokaci daya suka sa hannu tare da ture abinci junansu, take a wajan komai ya fadi kasa ya fashe Daidai lokacin da king ya fito daga wata kofa,bin ku waccen su yayi da rinannun idanuwansa , a part dinsa zasuyi masa wannan iskancin,kwata kwata basu ankara da shi a falon ba, amrah da tafi tsiwa ta tunkari sumayya , lokaci d’aya suka fara danbe da junansu, bece musu komai ba sai koma daki dayayi , cikin kankanin lokaci yafito hannunsa goye a bayansa sosai ransa ya baci, basu ankara ba sai saukar belt da sukaji, cikin bacin rai yake jibgarsu,”how dare you”, sosai suka firgita, sai faman hakuri suke bashi, sai da yasan sun daku sannan ya kyalesu, cikin nutsuwarsa ya zauna kan kujerar dake zaman mutum daya tare da crossing legs dinsa, ko wannansu zubewa yayi a kasa tare da yin kneeling, kowannansu na nadamar zuwa part din, kara had’e ransa yayi tare da kallan tulum abincin da suka bata,”it them all”, daga nan be kara cewa komai ba, sosai sumayya taji wani kukan na zuwan mata dan bata dade da cin abinci ba, amrah ma sai faman zare ido take hawaye na zubomata, belt din dake gefe ya dauka cikin sauri ko wannansu ya karasa inda suka zubar da amincin har da Wanda suka tattake, suna kuka suna tusa abiinci da suka zubar, ko wannansu ba yunwa sukejiba,sai tura tula abincin suke abaki,da Dinsu daya ko zuwa ne ya zube mutum zea iya tsugunnawa yasha sabida tsabtar wajan, saida suka cinye abincin tass ko wannansu na nishi sannan yasu suka gyara ko ina nafalon,yana zaune kan kujera saida ya tabbatar sun wahala sannan ya tashi ba tare da yace musu komai ba ya bar part din tare da nufar part din ummey.
🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧
🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧
BUNKURE
Tun lokacin da suka dawo cikin dare Dije ke safa da marwa, sai tunanin yadda zata zuba wa su oumma magani abakin kofa take,ga bintalo dake kwance sai nishi take gabanta sai zafi yake mata,ta dade tsaye tana zagaye dakin kafun ta saki wani murmushin mugunta, samun waje tayi itama ta zauna ganin yadda bintalo ke ta faman nishi, ita kanta tasan da ita boka ya kusanta sai taji azaba balantana bintalo , amma duk da hakan bataji tayi danasanin yin hakan ba tunda Burinsu na daf da cika inyaso sai su koma wajan bokan ya basu abinda bintalo zayi anfani dashi takoma budurwarta..

Yau tunda sassafe Dije ta tashi ko alwala batayi ba bare tayi tunanin yin sallah , maganin da boka ya bata take faman jujjuyawa, kafin cikin sanda tafito daga cikin dakin su ta nufi nasu oumma , bakowa kuwa a wajan kasancewar Gari be dade da wayewa ba , kofar dakin su tahee tashiga bubbugawa sai da taji motsin an nufo kofar tayi saurin zuba maganin tare da komawa baya taheer ne ya bude kofar da niyar fitowa,jiyai an hankadashi ya koma baya ,ga wata yar iska da ta kara de wajan, ganin yana kokarin komawa Dije ta daka masa tsawa “ina kuke muna fukan Allah kufito”, ganin tana kokarin tara musu mutane ne yasasu fitowa taheer agaba oumma na biyedashi, ganin sun tsallaka garin maganin yasa dijen kyalkyalewa da dariya , binta sukai da kallo ganin irin dariyar da take kafun kuma ta yatsina fuska “inna tace ubanme kuke bakufito kunyi aikin da kuka saba ba, ga ruwa can babu kuje kudebo danshine aikinku”, tana gama maganar ta tabar Wajan sai faman sakin dariya take, duk binta da kallo sukai ganin irin dariyar da take kamar zautacciya, basu koma dakin ba suka fara ayyukansu cikin kankanin lokaci suka gama ,taheer ya tafi wajan garba mefaci da yake koyan gyara awajan sa , dakin yayi saura sai oumma ita kadai.

🦋🦋🦋🦋……

Ruwa oummey ta mika mata, ita da zoya sai faman sannu suke mata, amaimakon tarin ya lafa sai ya kara taso mata, tashi tayi cikin fitar hankali Sabida yadda ma’kogwaranta ya rike mata, a guje tayi hanyar barin wajan, kokarin dakatar da ita ummey tayi amma kwata kwata tafita hanyacinta, dausasan hannayensa yasa tare da janyota, kokarin fuskewa take haryanxu tarin yaki lafa mata , ganin hakan yasa oummey nufar daki da niyar dakko first aid box, hannu daya kawai yasa yana taffing din bayanta, yayinda yake hura mata iska a saman fuskarta, ya dau dogon lokaci yana hakan kafun ta fara sauke a jiyar zuciya nunfashin ta nadawo Daidai, ruwan da oummey tazuba mata ya nuna mata batare da ya kara kallan inda take ba, ruwan ta dauka tare da shanyewa tass tana sauke ajiyar zuciya Daidai lokacin da oummey ke dawowa wajan ganin tarin nata ya lafane yasata sauke ajiyar zuciya….,,

Comment and share ✍️

LITTAFINA PAID BOOK NE AKAN 300 kacal , amma daga yau Tuesday zuwa ranar asabar duk Wanda zai biya 200 zai biya amaimakon 300 .

Za’a biya kudin ta wannan asusun 7041879581 Opay, Ayshatou galadima sai a tura shaidar biya ta wannan number 07041879581.

💖💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖💖

_🦋Duk karfin izzata
_🦋Gidan Aunty
_🦋Sarki sameer
_🦋Ya fita zakka
_🦋Jini d’aya
_🦋Baby

MSS LEE💖💖✍️✍️
‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/JyvVuOvzYyF19np8UmFKV4

💖💖GIDAN AUNTY💖💖
(a heart touching love story)

Story &written
By
Mss Lee 💖

PAID BOOK

PLX WAYANDA ZASU BIYA KUDINSU DAN ALLAH KUYI HAKURI  ANSAMU KUSKURE BA OPAY BANE PALMPAY NE YANZU ZAN KARA RUBUTA MUKU DETAILS DIN

7041879581 Ayshatou galadima , palmpay .

GIDAN AUNTY NA KUDINE AKAN 300KACAL ,ME BUKATAR SAMUN CIGABA HAR KARSHE ZAI BIYA KUDINSA TA WANNAN ASUSUN 7041879581 PalmPay
Ayshatou galadima sai a turo da shaidar biya ta wannan number 07041879581.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button