Sponsored Links
Dabi'ar Zuciya Hausa NovelHausa Novels

Dabi’ar Zuciya 36

Sponsored Links

Hkan ya baiwa najwa damar juyawa zuwa sashen da kaltume ke zaune a rakube,kamar zakace kyat ta zura da mugun gudu

“Mai aiki na qaro muku” ya fada kansa tsaye yana relaxing saman kujerar da yake zaune,yana jin yadda gaba daya ya gaji.

“Me aiki yaya?”jawahir ta fada cikin wani salo me kama da gatsali

“Jawahir……” Momy ta kira sunanta da qarfi
“Na’am” ta amsa tana duban momyn,da idanu ta gaya mata kada ta sake magana,sai taja bakinta ta tsuke,haushi da takaici na cikata,ta taya zai dauko kucakar ya kawo musu gida da sunan mai aiki,gidan ma irin nasu,gidan professor rashid guda,wanda mutane da yawa ke kwadayin yin aiki qarqashinsu,koda an tashi daukar mai aiki momyn nasu saita zaba,ta kuma jarraba mutum ta aminta dashi take dauka,ma’aikatan daba ita ta daukesu ba cikin gidan batajin basu wuce uku ba,shine kawai zai wani kwaso musu kalar qyanqyami,saboda yana taqama da ikon da yake dashi a gidan,qwafa taja can qasan ranta,tana jin sauran qiris ta rushe komai,ta maye gurbinsa,wannan shine babban buri da muradinta,wanda dashi take kwana take kuma tashi.

Da murmushi saman fuskar momyn,tana qoqarin dai daita komai ta dubi samir din

“Banda abinka son….ai kasan tsarin daukan ma’aikata a gidan nan,ko baya ga haka ma professor kasan baya bari a dauki qananun yara kamar haka,banason wannan ya jawo wani sabuwar matsalar tsakaninku fa?”.

Numfashi ya fidda
“Babu komai momy,a bata wajen zama,zanyi magana da dadyn”

“Shikenan…..”ta fada tana mutstsuka hannaye ta,tana jin wani abu nason kutsawa cikin zuciyarta amma tayi gefe dashi,ta dubi jawahir

“Kuje da ita ki bata daki”

“Kaman zuwaira ke kaisu boys quarters din” jawahir ta fada,sai momyn ta tsuke fuska sosai

“Ba cikinsu zata zauna ba,a bata daki nata na daban” idanu jawahir din ta fiddo,kamar zatayi magana sai kuma ta fasa,mamakin abinda momy ke nufi ya kamata,kamar wata ‘yar gida za’a bata daki guda?,miqewa tayi da hanzari ranta a bace ta soma yin gaba

“Tashi ki bita…..meye sunanki ne?” A hankali samir ya bude baki zai amsawa mommyn,sassanyar qaramar muryarsa ta maye gurbin tata
“Kaltume” ta fada da qaramin sauti mara amo.

“Tashi kije ta baki masauki” kamar wadda ciwon paralyze ya kamawa qafafu haka ta dinga ji sanda ta miqe,tsoro baqunta rauni da kuma firgici sukayi mata qawanya gaba daya,tana riqe da qullin kayanta taci gana da bin gurbin da jawahir kebi har suka isa wani kebantaccen corridor me dauke da dakuna manya guda hudu.

Muqullin jiki ta murza ya bude ta soma shiga,tayi tsaye sanda kaltume ke takowa sannu a hankali,kamar wanda ke shiga wuta

“Dalla malama ki shigo,nan ba bukka bace ko rumbu” ta fada cikij tsawa,tsawar data razana kaltume din,saboda haduwa da tayi da tsoro da kuma ganin yanayin dakin da bata taba katarin ganinsa ba,hakan ya sanya qullin hannunta faduwa saman qafafunta,jawahir ta bisu da kalllo kana ta tabe baki

“Ga daki nan,amma ki sani,ba qyaleki za’ayi ba,duk abinda kika barnatar saikin biya,don haka kibi a hankali” ta qarasa maganar tana galla mata harara,sannan ta kewayeta ta fice,ta bita da kallo har zuwa sanda taja mata qofar.

Zafafan hawaye suka sauko mata,wannan rayuwar kuma itace yanzu zata fuskanta,su waye wadan nan da zata rayu cikinsu ne?,me zata tarar,shi kansa wanda aka kira da sunan mijinta wayeshi?,bata da tabbas a kansa bata da tartibin wata amsa guda daya gamsashshiya game dashi,ta juya ta kalli gabas da yamma kudu da arewa na dakin,ta yaya ma zata iya rayuwa a wannan wajen me kama da gidan aljanu?,ko ina glass,da wani abu mai santsi da qyalli,shiba daben sumunti ba,hakanan ba ledar tsakar daki ba,saita zame taja da baya a hankali ta zauna a qasan da batasan na meye ba,kuka na balle mata.

A zafafe jawahir ta koma falon,ta tadda saraki ya fice sai mommyn

“Mommy,ta yaya……” Bata kai ga qarasawa ba mommyn ta daga mata hannu

“Babu abinda kika sani ko kima kika iya sai shirme,wadansu lokutan ina raina hankali da wayonki…..” Daga wannan bata sake cewa sa ita komai ba, taci gaba da kankare farcenta data taras tana yi,saita juya ta kwashe wayarta da headphone dinta ta yi dakinta fuuu,mommyn ta bita da kallo,daga bisani ta dauke kanta tana girgiza kai,nan da wasu mintuna tasan zata dawo da kanta,don haka taci gaba da gyaran farcenta.

Sai daya gama sharce kansa sannan ya lalubi undies ya feshesu da turare ya fara sakawa,sai daya gama sawa ya dubi Aamir

“Zamu leqa wajen hajiya qarama,amma sai zuwa anjima,zan leqa company yanzu kafin lokacin tashi yayi,akwai abubuwan da zan dudduba”

“Ba damuwa,inason na leqa mutuniyar” ya fada yana dan kashingida

“Saika nema kuma abokin rakiya,badai muhammad samir ba” ya amsa masa yana qoqarin bude katafaren ma’adanar kayanshi.

Qaramin murmushi kawai Aamir ya saki,yasan halin kayanshi dama,abu daya da bai yarda dashi ba yayi rakiyar zance,yace shiba yaron kowa bane,baiyi,kuma shima ba wanda zai nema yayi masa,kowa ya iya allonsa ya wanke,rakiyar zance ko gulma.

Cikin kayansa ya dudduba,ya fitar da wani lallausan yadi butter color ya sanya,a nan yabar Aamir yayi Ι—ai Ι—ai,shi ala dole ya gaji,ba yadda samir din baiyi ya tashi su fita tare ba yaqiya.

Tun tana kasa kunne ko zataji motsi ko gilmawar wani,harta saddaqar da cewa an kawota qare kukanka,inda babu wanda zata ji,babu kuma wanda zai jita.

Duk sanda agogo ya kada saita daga kai ta kalleshi,duk da cewa batasan qarfe nawa yake bayarwa ba,yanayin shigowar hasken rana dakin kuwa bashi da banbanci daga shigowarta zuwa yanzun da take zaune a jikin bago kamar wata qadangaruwa,ya kamata ace taji yunwa,amma tunanuka dake cunkushe cunkushe cikin kanta ya hanata taji yunwar arziqi,sannu a hankali lokaci ya dunga motsawa zuwa gaba,cikin jikinta ta dinga jin yakamata ace tayi salla,koda lokacinta baiyi ba,bare tana ji a ranta ma lokacin yayi qila ma har ya gota,saidai batasan inane zata nufa don daura alwala ba.

Zagaye ta dinga da idanunta harta hangi qofar toilet,ta miqe zuwa qofar sannu a hankali ba tare da tana da tabbacin wane waje bane nan,sai a sannan tasan lallai tana buqatar abinci,saboda jinta da tayi fayau iska na dibarta,ga sanyin wajen da taketa jin ya mata yawa.

Tsaye tayi a bakin qofar,ta jima tana qiyasta ta yadda zata budeta,kafin daga bisani tayi shahada ta soma gwada budewar na wasu mintuna kafin ta samu nasarar turata ta bude.

Bin bandakin tayi da kallo,wanda yafi mata kama da daki,don kaf karkararsu bata taba ganin mai kya makwanci kwatankwacin nan wajen ba,take ranta ya bata cewa wani dakinne mai zaman kansa,kenan babu wajen zub da ruwa bare ta daura alwala?,idan kuma tace zata fita ina ta nufa?,ba zata iya maida kanta inda ta baro dazu ba bare ta koma wajensu ta tambayesu.

Sake qudundunewa tayi a yadda take zaunen,sanyin tiles dana ac na ratsata,wanda batasan sanyin meye ba,sai dan banzan takura matan da sukayi,zuwa wani lokaci cikinta ya sake buqatuwa qwarai zuwa ga abinda zai sarrafa ya bawa jikinta kuzari.

Mamaki qwarai ya mamayeta,wadanne irin nau’in mutanene wadan nan?,masu qarancin karamci?,iya rayuwarta da yadda suka ga ummansu nayi akan baqi sam ba haka bane,duk da kasancewarta mai qaramin qarfi,wadda itama idan aka bata da farincikinta zata karba,amma duk sanda baqo ya shigo gidan,nata ko ba nata ba,saita zuba ta miqa mishi,koda bangaren kawu iliya yazo ba nasu ba,ta riga ta saba da ganin hakan,sai gashi yau ta fada hannun wasu mutane,an yasar da ita a wani daki dake mata kama da qiyama.

Qarfe shida da mintina ashirin ta shigo gidan a gajiye daga makaranta,mintuna goma kenan a gaba suka rage a kirayi sallar magariba,duk da cewa kaita ake a daukota amma hakan bai hanata jin gajiya a jikinta ba,tayi mita tayi qorafi kan a bata mota,amma saraki yace ba yanzu ba,yasan yadda jawahir keda tarin qawaye,kasancewarta mai faran faran da son jama’a,ta haqura da tsarin yayan nata,saboda tasan cewa kome ya tsara a gareta baiyi don ya cutar da ita ba,sai don amfanin kanta,bata kuma damu da kalar motar da najwa ke hawa ba,ta tattara ta barwa lokacin da yayan nata ya zaba mata.

A falo ta zube tana ajjiye takardunta,mommy dake shirin shigewa shiyyarta don shiga wakan tarbar mai gidan da bai mata tsufa ta dubeta

“Yanzu nake shirin daga waya na kiraku,yau dadewar tayi yawa”

“Wallahi momy,yunwa da gajiya,bamu zaci muma zamu kai hakan ba”

“To barkanku tunda kun dawo,saiki shiga ki saka a kawo miki abinci”

“Sai nayi sallah momy,saura ‘yan mintuna a tayar,idan naci yanzu kasa tashi zanyi nayi sallar akan lokaci” ta amsa mata tana qoqarin miqewa saman doguwar kujera abinta.

Ganin falon babu kowa saita dauka remote tana canza channel din dake aiki saman screen din tvn dake falon,tare da maida hankalinta ga channel din data sauya.

Sosai program din da take kallo ya dauki hankalinta,har aka tayar da sallar aka idar bata sani ba,motsin shigowar samir da fitowar mommy cikin shigar alfarma ya sanyata miqewa ta zauna,kamar ko yaushe fuskarta qunshe da murmushi takewa samir din murnar dawowa

“Yaya,bari naje nayi salla na dawo naji nasarar da aka samu wannan karon,bamuyi waya sosai ba tunda ka tafi”

“Au,dama bakiyi sallar ba tun daxun?” Tana zura takalminta cikin sauri tace

“Wallahi momy bansan an idar bama” ta hada da mayafinta tana yin bangaren dakunansu da hanzari.

Kayanta duka ta aje sama madubi ta nufi bandaki,saidai ta taras da heater din bandakin nata babu ruwan zafi

“Ya salam” ta fada tana fitowa daga bandakin,ta nufi daya daga cikin dakunan da tasan ko yaushe a gyare su,ba zata rasa ruwan zafi a cikin toilets dinsu ba.

Kanta tsaye ta tura qofar dakin data lura shi daya ne a bude ba tare da wani zato ku tunanin ganin kowa ba,kacibus tayi da kaltum dake kwance a qasa a cure waje guda,tana fidda sautin kuka ta cikin hijabinta.

A matuqar tsorace taja da baya tana shirin bada iska,amma sai tayi ta maza,ta tsaya tana kallon kaltumen gami da karantarta,saida zuciyarta tadan samu nutsuwa sannan ta soma takowa zuwa ciki,ta tsugunna a gabanta a hankali ta dan tabata.

A firgice ta miqe,da alama itama a tsorace take,saita tsaya suna yiwa junansu kallon kallon,tsahon wasu sakanni kafin kaltume ta gyara zamanta ta lumshe idanunta hawayen da suka cika mata idanu suka sake gangarowa

“Me kike a nan?,daga ina kike?” Jawahir ta tambayeta tana ci gaba da dubanta cike da mamaki,kasa bata amsa tayi,saboda mugun qullewa da cikinta yayi

“Keda wa kuka zo?” Ta kuma tambayarta

“Nida wanine,daga qauyenmu” maganar ta daurewa jawahir kai,amma sai tayi gajeran tunani daya sanyata miqewa ta koma zuwa falo.

“Daddy ya saba lokacin shigowarsa yau,ko wani abun ya tsaidashi?” Samir ya tambayi momy.

Fuskarta qunshe da fara’ar nan tako yaushe tace

“Eh….yace min suna da taron jam’iyya,amma tunda na kirashi naji bai daga ba,basu gama bane” agogon hannunsa ya kalla

“Ok”ya fada,yana shirin sauke idonsa daga kan agogon muryar jawahir ta bayyana

“Momy….wace yarinyar ce acan dakin take kuka?,tacemin ita da wani sukazo daga qauyensu,shi ya kawota” maganar taja hankalin samir sosai,shaf ya manta da yarinya kwata kwata,saboda koda ya fita din ma baiyi zaton za dade haka ba

“Kuka kuma?,ko bata qoshi bane?” Tayi tambayar tana kallon samir wanda baisan irin amsar da zai bata ba

“Gaskiya banga ma alamun abinci a wajenta ba kwata kwata,don kamar ma yanayinta yafi kama da name jin yunwa” ta fada tana raba kallonta tsakanin mommy da saraki

“Kada dai ace basu kai mata komai ba…..inasu tambaya…..jeki tattaro minsu” ta soma magana cikin fada kamar zata ari baki cikin matuqar bacin rai,har falon na amsa muryata saboda yadda take fadan cikin nuna fushinta.

“Idan kin shiga ki samo abinci da ruwan Lipton me zafi,ki barsu basai kin kirasu ba” cewar samir bayan ya tsaida jawahir cikin wata iriyar murya me cike da nutsuwa,sannan ya fara takawa a hankali yana dosar dakin da yake tsammanin an ajjiyetan.

A tsorace ta dago sanda taji an kuma bude qofar,suka hada idanu,yabi fuskarta da kallo,wadda ta qara muni saboda yadda idanuwanta suka kumbura da labbanta sakamakon kukan data shaqa,sai yayi sallama,wadda ta sanyata sakin ajiyar zuciya,ta kuma yi qoqarin amsawa,ya tako a hankali yana kallon dakin.

A zahirin gaskiya shi kansa yasan ba lallai ta iya sakewa a dakin ba,saboda bambancin yanayi dana rayuwa dake tsakaninsu

“Kinci abinci?” Abu na farko daya fara tambayarta kenan,qas tayi da kanta bayan ta zare idanuwanta daga cikin nashi,wasu sabbin hawaye suna sauko mata ta girgiza masa kai,sai ya qaraso ciki,ya murza qofar toilet ya budeta yana duban bandakin,yanzu haka fitsari da bayan gida,da duka sauran buqatunta na bayan gida riqesu kenan tayi tsahon wannan lokacin,Saiya saki qofar yana juyowa,dai dai lokacin da jawahir ta dawo dauke da babban plate,wanda aka cika da shinkafa da miya da nama,sai hadin coleslaw daga gefe,hannunta daya ruwan roba ne da lemo.

Zuciyarsa na yabawa sanin ya kamata irin na jawahir yasa ta ajjiye abincin gaban kaltume,sannan ya baiwa kaltume din umarnin ta dauka taci,yace da jawahir data wuce toilet don daura alwala,bakinta cike da tambayoyi da bata furtasu ba,idan ta fito tayi masa kiran baba zuwaira,sunan daya ambata ya sanya kaltum daga kai,tana raba idanu cikin dakin,tamkar zataga tata mahaifiyar dake da wannan suna,saidai wayam,bazaiyiwu ta ganta bama,ta maida qwallar dake shirin xubo mata,taja plate din abincin kamar yadda taji yana umartarta,ta sanya cokali amma saita zubawa abincin idanu wani abu yana tsaye mata a maqoshi.

Ummanta ta tuno,wadda a yanzu haka take can ita daya tana rayuwar kadaici,babu ita babu habi babu bilalu,kome taci yanzu?,ko waye yake tayata hira?,waye yayi mata shara?,wa zai dinga mata wanki?,wazai faranta mata bayan babansu ya bata mata ranta?,qwalla na qoqarin rufe mata idanunta ta soma ture hadin coleslaw din gefe,wanda take kallonsa a baqon abun da yafi mata kama da jagwalgwalon da ba zata iya ci ba,ta soma kai lomar abincin a bakinta a hankali,ba tare da tabi takan ruwan Lipton da aka ajjiye mata a cup ba.

Idanunsa yana kanta harta fara cin abincin, dai dai lokacin baba zuwaira tayi sallama,fuskarsa ta sake fiye da daxun yana dubanta,tana da wani qima da daraja dukka cikin tarin ma’aikatan gidan,hakanan itama take dubansa da tata fara’ar

“Biba(sunan da suke kiranta dashi can wani lokaci daya shude,har zuwa yanzun kuma shi bai fasa kiranta dashi ba) baquwa ce da Allah,pls ki dan zauna da ita,ki nuna mata bandaki da sauran abubuwa,duk abinda kika ga akwai damuwa ko motsala ki sanarmin kai tsaye,karki damu da momy” kanta ta kada cikin gamsuwa tana bashi tabbacin haka,saiya juya ya kalli kaltume sau daya sanda taketa faman qoqari sarrafa lomar datayi,saboda banbamcin taste da spices da seasonings na girki da bata saba jinsu ba,wanda a yanxun tana jin abincin na mata wani qamshi ne na daban wanda bai mata dadi sam a harshe da zuciya,saiya nufi qofa yana zaro wayarsa,tare da qoqarin kiran ahalan,wanda koda yaushe shike tiri tiri da professor,da shirya masa duk schedule dinsa,ya tabbatar xai samu cikakken kwatancen inda suke a yanzun.

 

37
D/Z

β˜€οΈπŸ”΄β˜€οΈπŸŸ β˜€οΈπŸ”΄β˜€οΈπŸŸ β˜€οΈπŸ”΄β˜€οΈπŸŸ β˜€οΈπŸ”΄β˜€οΈπŸŸ β˜€οΈπŸ”΄β˜€οΈπŸŸ β˜€οΈπŸ”΄β˜€οΈπŸŸ 
*_K’AMSHI,K’AMSHI RAHAMA NE MATAN DA SUKA AMSA SUNANSU MATA SU SUKA SAN MUHIMMANCIN DA K’AMSHI YAKE DASHI MUSAMMAN A WAJAN MAI GIDA ,_*πŸ’ƒπŸ»πŸ’ƒπŸ»
*_Zafafan turarruka masu zazzafan k’amshi hade da wasu irin manyan sirrika na mallaka cikin sauki ba boka ba malam hajiya , Zaki jefe tsuntsu biyu da dutse d’aya , domin zamowa star azuciyar mijinki_*🌟🌟πŸ”₯

*_nasan dai kunada labarin mashahuriyar Mai Saida kayan k’amshin Nan Wanda akafi sani da *HUMKAM GIDAN K’AMSHI* *_a wannan karon ma ta sake kawo maku da sabbin kayanta masu abun al’ajabi Wanda da kud’i k’alilan zaku more zafafan turarruka Kuma ki shiga jerin Mata masu aji_*

 

*IDAN SARI KIKE BUKATA INA BADAWA SANNAN INAGYARAN JIKI CIKI DA WAJE SHIN KINA FAMA DA INFECTION INA HADA MAGANIN SA DA IZININ ALLAH KISHA KI WARKE*
*Kadan daga cikin kayan da muke dasu*πŸ‘‡πŸ»πŸ‘‡πŸ»πŸ‘‡πŸ»πŸ‘‡πŸ»πŸ‘‡πŸ»

*BLACK KAJII*
shin kina bukatar turaren da Zaki turara gidanki ya dauke maki warin sanyi ya kwana biyu Yana k’amshi ,?ki saye black kajiji Zaki Gane banbancinsa da sauran wannan ba k’amshi kawai yake ba idan kina turara. Jiki dashi Yana maki maganin kala kala ciki kuwa har da na sanyi , nemi naki Kar ayi Babu keβ˜€οΈπŸŸ’β˜€οΈπŸŸ πŸŒŸ08132506044 HUMKAMINCENSE

*ANA WA HABIBY* Wannan harkan na oza room ne special turare Dan matan aure kadai yana dauke da abubuwa Wanda bazan fadesu anan ba sannan bashi kadai bane akwai Crazy powder da na ke hadawa dashi zakisha garin sannan kishafa turaren hmm

 

*SUDANESE HUMRA* Turare dake dauke da sirrika Mai DAUKAR hankali kamshin ya banbanta da sauran turare Hajiya babbar sirrine Wannan hadin manyan Mata 08132506044 HUMKAMINCENSE

*GLOWING OIL*
Wannan yasha bam bam da irin Wanda kuka Saba gani ,Yana kashe kuraje Yana cire tabo Yana maganin kezbi da duk wani matsalan fata ,stretch marks duk Yana ciresu ….

*MOWAR MACE*
turaren mowar mace turare ne da larabawa suke amfani dashi Wanda da yawa mutanenmu Basu San da wannan iccen ba Mai dauke da magani k’amshi da sauran abubuwan masu matukar amfani ga fata ba
Shi wannan iccen yanasa hasken fata yanasa fata tayi laushi da santsi sannan d’an alk’awari ne matuk’ar kina amfani dashi zai tsirga maki cikin fata ta yadda ko Bakiyi amfani dashi ba zakiji k’amshin shi na fita ta cikin fatar ki ,ke amfanin iccen mowar mace yanada yawa jaraba ko don gyaran fatarki , πŸ’ƒπŸ»πŸ’ƒπŸ»πŸ’ƒπŸ»πŸ’ƒπŸ»πŸ’ƒπŸ»

Muna gyaran jiki na amarya da uwargida zakizo har gida ayi maki gyaran jiki irin na Mata masu aji zakiyi kyau kiyi fresh ga kamshin da zai Kama jikinkiπŸ’ƒπŸ»πŸ’ƒπŸ»πŸ’ƒπŸ»

Munada πŸ‘‡πŸ»πŸ‘‡πŸ»πŸ‘‡πŸ»πŸ‘‡πŸ»
*JAS OUD* (hatsabibin turare kenan )

*AL’AJAB* ( Mai abun mamaki kenan )AL’AJAB Turaren tsuguno mai abubuwan Al’ajabi Yana maganin sanyi (infection) Yana matse HQ (Tightening)sosai 08132506044 yasa HQ dumi yasa jikinki da hq kamshi lokacin da kike AMFANI dashi idan Yana shiga gabanki zakiji wani Dadi na ratsaki Yana k’ara Dadi da Yana ciko gaba ya rikita ogaπŸ™ˆ

*FIRST LADY* na Mata masu aji turaren Kaya Dana daki
HAWII
KAJIJI
HALUT
πŸ‘ΈπŸ» *_PRINCESS_*
_Sabon turare Dana hada na shafawa ajiki da gashi *PRINCESS* Yana da Dadi cool kamshi gare shi babu hayaniya na fad’a muku sabbin turaruka na Nan tafe princess na daya daga ciki kisayi *PRINCESS* kiji sabon Hadi me sanyin kamshi babu kosarwa da ace zan iya zabi tabbas zan zabi princess a matsayin turaren gashina zan dauki princess ya zama shi zan farawa shafawa jikina idan zan kwanta zan dauki *PRINCESS* sbd yara na Dan kamshi bamai hayaniya bane musamman zan rika yi musu amfani dashi *PRINCESS* salon na daban kamshin daban dadin na daban *PRINCESS* Zabin ku ne Zabin Humkam shine farin cikin ku Masoya *PRINCESS* gidan kowa_

Duk wad’an Nan turarruka ne hatsabibai masu rikita mazaje masu wani irin k’amshi Mai shiga zuciyar masoya πŸ’ƒπŸ»πŸ’ƒπŸ»πŸ’ƒπŸ»

*SHU’UMAR HUMRA*
ke daga jin sunan kinsan ta dabance mashahuriyar humra ce ta tayi shuhura wajan birkita tunanin Yan maza , humra ce da indai namiji yajita a jikinki to komai muskilancinshi sai ya susuce maki tana tado da sha’awa shauk’i sirrin mallaka, cikin kankanin lokaci ki rikita maigidanki da daddadan k’amshin ki😍😍😍πŸ₯°

 

*HUMKAM GIDAN K’AMSHI INA NAN ZAUNE A KANO GA MASU BUK’ATAR ZAFAFAN KAYANA INA AIKAWA KOWANE GARI DAKE NIGERIA HAR MA DA K’ASASHEN K’ETARE*

*Zaku iya tuntubata kai tsaye ta wannan number wayar*

08132506044

*KO KU DUBANI A SHAFINA NA INSTAGRAM*
_humkam_turare wuta_

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button