Sponsored Links
Duk Karfin Izzata Book 1Hausa Novels

Duk karfin Izzata Book 1 Page 25

Sponsored Links

Episode 2️⃣5️⃣*

……..Ɗago ido Khalid yayi yana kallon su Ahmad san nan yafara Magana “yanzu menen mafita, Khalid bai gama rufe baki ba, Ahmad ma yamiƙe yabi bayan su Aiman, dawo da kallan sa kan yusuf dake zaune Khalid yayi san nan yace “Yusuf mene mafita ni fa gaskiya ina son Zahra sosai wlh ina san muyi Aure kuma gaskiya time yayi daya kamata a che munyi auren idan fa muka biyewa su DON baza mu taɓa yin aure ba awan nan rayuwar, dan su babu Aure a tunanin su kwata kwata,
dogon numfashi Yusuf yaja kafin ya fara Magana “yaya Khalid ni kai na ina matikar son my baby wlh, duk da yarin yache sosai amma ina san muyi aure taje ta karisa girma a gidana amma bansa ya abun zai kasan cheba kanafa jin abun da yaya prince ke faɗe, wai har abada shida Aure kuma ni nasan mawuya chin abune a shawo kan sa ya yarda yayi Aure, “dole fa Yusuf musan abunyi Khalid ya faɗa yana kokarin miƙewa “jirani muje mana chewar Yusuf ya karisa maganar tare da miƙewa shiam, suka jera atare suka fice daga palon kowa yayi ɓangaren sa

Abangaren DON kuwa yana fita palon Abba ɓangaren sa yanufa chikin sauri, yana shiga ɗaki ya zauna a bakin katafaren gado sa, ya dafe kai dan ji yake kansa na sara masa,kamar zai faɗi kasa, tunani ya shigayi, ni gaskiya Abba bai min adalchi ba tayaya zai wani haɗani dawani abu wai shi Aure, dole ma nazo nabar kasar nan, tun kafin Abba ya sake kawo wata maganar.

Awan nan yanayi Aryan ya shigo ya same’sa, gefen sa ya zauna saman gadon yasa hannu ya dafa kafaɗarsa cikin cool voice yafara Magana “calm down my blood kafasan idan ka shiga damuwa nima dole nashiga damuwa, kuma ni nasan ba kasan ka ganni chikin damuwa ko, ɗago green eyes nashi yayi yana sauke su kan face ɗin Aryan, har sai da Aryan ya tsorata ganin yadda idon nashi suka sauya sunyi jaaa sosai ga jijiyoyin kan nan nashi duk sun tashi duk da sanyi A.c dake ɗakin hakan bai hana DON zufa ba, chikin wata iriyar voice mai sauti yace “why, why Aryan why Abba zai nemi ya chazamin kai why yake neman kassarani, “calm down my blood ya isa haka kayi shiru pls Aryan ya faɗa tare da dora hannun sa saman ɗan karamin bakin DON ya rufe masa, yana kokarin sake magana Aunty farida tashigo da sallama, zame hannunsa Aryan yayi daga kan dan bakin DON yana kallonta

Karisowa chikin ɗakin tayi ta zauna a bakin gadon ta ɗayan gefen su kasa DON a tsakiya ita da Aryan a nitse tafara magana “nasan abun da Abba ya faɗa bazai muku daɗi ba amma hakan kar ya dame ku kuyi hakuri, ni nasan Abba ba zai so ya ɓata muku rai ba koma me zanyi magana dashi idan ya huche, yanzu dai banaso wani abu ya dame ku dan kunsan idan kuka shiga damuwa dole nima hankali na ya tashi kuma zan shiga damuwa, ɗan dakata wa tayi da magana tana mai da numfashi, buɗe ɗan karamin bakin’sa Aryan yayi zai yi magana kenan sukaji sallamar Abba, da mamaki suke bin kofar ɗakin da kallon,

ƙarisowa chikin ɗakin Abba yayi, mikewa sukayi gaba ɗayan su, suna kallon Abba kai tsaye DON ya nufa yaje ya rungume sa, shiru Aryan da Aunty farida sukayi suna bin Abba da DON da kallo, tunani Aunty farida ta shiga yi anya bawani abun Abba ya shirya musu ba, bata gama tunanin nata ba taji Abba yana faɗin “bana son ɓachin ran ku ƴa’ƴana kune farin chiki na, yanzu dai ke farida jeki haɗa masa complex ki kawo mana muna sha muna hira

……ita dai Aunty farida gaskiya bata yar da da neman sulhun da Abba yazo yi ba, dan tafi kowa sanin halinsa yanzu wata kila wani idea ne tazo masa shiyasa zai musu wayo ta haka, jiki ba kwari tana ta tunani har ta fiche daga ɗakin,

Sakin DON Abba yayi ya haye kan katafaren gadon DON ya zauna yana ta murmushi, haye gadon Aryan da DON ma su kayi suka saka Abba a tsakiya, “Abba ya kamata mu koma bakin aikin mufa Aryan ya faɗa yana kallan Abba, murmushi Abba yayi kafin yache “ku rubuta musu later akan za kuyi wani aiki a nan na tsawon wata uku dan gaskiya ina san kasan chewa da ku a’wayan nan watannin,

…..DON yace “Abba a matsayi na BGS (Brigadier General Safras) ba sai na rubuta wani later ba, Aryan da Yusuf kuma dama a’wajena zasu tambayi permission na hutun, tun da kana bukatar mu kasan che da kai na wata uku su rubuto min later zan sa musu hannu, murmushi Abba yayi sosai kafin ya rungumi DON yana faɗin ilove U my Son, “ilove too my love my pleasure my only Boss, farinchiki kamar Aryan ya nitse kasa dan daɗi, ganin yadda Abba da DON suke zuba wa juna kalan kauna, “eyeee lallai Abba wato haka abun yake ko? chewar Aunty farida dake tsaye a bakin kofar shigowa ɗakin tana ta murnushi hannunta ɗauke da babban trey mai ɗauke da cup 4 na complex, sakin Abba DON yayi ya juyo yana faɗin “Aunty babba kin fa iya sa ido, kariso tayi chikin ɗakin ta ajiye trey ɗin saman table ɗin tsakiyar ɗakin ta zauna saman sofa tana murnushi

A tare suka sauko daga gadon suka nufo ta, kowa ya zauna a saman nashi sofan suna fiskantar juna, Aunty farida zata mike ta ɗauko musu complex ɗin Aryan ya rigata yana faɗin “bari na hutar dake Aunty babba, ɗaukan trey ɗin yayi ya fara miƙawa Abba, ya ɗauki cup ɗaya san nan ya miƙawa Aunty farida itama ta ɗauka, ko da yazo mikawa BGS wani harara BGS ya wurga masa kafin yace “au nine karshe ko “hannu ɗaya Aryan yasa yaja dogon hanchin BGS har sai da yace wash mugu kawai, dariya Abba yayi yana faɗin “daman Aryan kai kake jan hanchin BGS koh shiyasa naga hanchin nashi kullun tana ƙara tsawo Sosai, taɓe baki Aunty farida tayi tana kallon Abba, da mamaki wato ma idan ana jan hanchi kara tsawo yake koh? Tab ai da kuwa hakane lilin baba shine mutun na farko da zai fara bawa ummi rahab tana ja masa dan hanchin nasa yayi tsawo

…..Wani naushi BGS ya kai wa Aryan a kumatu sai dai ina kauchewa Aryan yayi yana ɗan murnushi, bai bari hannun BGS ya sauƙa a jikin sa ba, “wai zaka ɗauki complex ɗin nan ne ko kuma na ajiye, ɗaure fuska BGS yayi kafin yace “bazan sha ba, “oh my lovely bro pls ka sha idan baka sha ba nima bazan sha ba kuma wlh inasan sha amma dole zan haku in dai baka sha ba, ɗan sake fuska kaɗan BGS yayi kafin yasa hannu ya ɗauko cup ɗin yana faɗin “zan sha ne kawai saboda kana son sha kuma bani da wani burin daya wuche inga kasamu abun da kake so, matsowa Aryan yayi ya man nawa BGS kiss, a goshi kafin yace “ina kaunar ka kamar raina my blood, “Hmmmm faɗa ɓatawa my bro ai kaunar da nake maka ba zai faɗu ba

… Abba dai ido kawai ya zuba musu a chikin zuchiyar shi yana gode wa Allah da ya haɗa masa kan ƴa’ƴansa suke matukar kaunar ju nan su haka,

“Abba na, gobe idan Allah ya kaimu in mun gama raka Ahmad fada, zan bi jirgin yamma na koma, chewar Aunty farida “Allah ya kaimu bai lovely daughter, shiru su kayi suna shan complex nasu chikin ni shaɗi ,

zubur Aryan ya mike kamar wadda akawa allura yana faɗin “Abba sai da safe da mamaki BGS da Aunty farida ke kallansa, Abba kuwa sai murnushi yake chikin ransa yana faɗin, Allah kasa na chinma abun da nake hari afili kuwa sai yace “to my Son yaka mata daman ka ajiye complex nan haka kaje kasha coffee mai zafi, a’sukwane Aryan ya dawo da kallansa kan Abba yana mamakin ya akayi Abba yasan abun da zaije yayi, kashe masa ido ɗaya Abba yayi yana murmushi yace “to ka tafi mana me kuma ka tsaya kana kallan mu, jiki ba kwari Aryan ya juya ya ajiye cup ɗin complex ɗin dake hannunsa a saman table yanufi hanyar fita, yana jiyo muryan Aunty farida na faɗin “wai meke damun Aryan ne muna zaune muna hira kawai kache sai da safe, bayan ga wayan nan manya manyan idon nan naka ba alamar barchi a chikin su, fichewa yayi da sauri dan karma Aunty farida ta jefo masa wani tambayar,

a hankali BGS ya buɗe ɗan karamin bakin nan nashi ya furta “kila ya gaji da hiran ne, da sauri Abba ya chan za musu topic ɗin hirar dan karsu tsawai’ta magana a kan Aryan, yasan BGS ba karamin kwakwalwa bane da shi yanzun nan zai iya gane komai “My daughter ya kamata kema kije ki kwanta kinga yanxu almost 10, “to my lovely Abba tana faɗin hakan ta mike ta ajiye Cup ɗin hannun ta saman trey, san nan ta ɗauki trey ɗin ta juyo ta ansa cup ɗin hannun BGS dana hannun Abba ta ɗora kan trey ta ɗauka tayi waje,

Dawo da kallansa Abba yayi kan BGS san nan yafara Magana “kasan me nake so da kai my Son “aa Abba “abun dana ke so da kai dan Allah ka dai na korar yarinyar nan idan na ai’kota wajen ka, kuma ka dai na yi mata tsawa kaji my lovely Son ya karisa maganar chikin sigar rarrashi, ɗaure fuska sosai BGS yayi kafin yace “Abba ni pls ka daina aiko min su ɗaki, wlh dan ma a’baya kache kar na kara bugun tane Allah da ɗazun da tashigo sai na ɓallata, ka rinka aiko Fahad ko ka kirani awaya mana Abba haba, ya karisa maganar kamar zai yi kuka, “to shike nan zan daina aiko ta tun da baka son,

… hakan yayi maka? mikewa BGS yayi yaje ya rungumi Abba yana faɗin “shiyasa nake son ka my Abba murmushi Abba yayi yasa hannu yana ɗan bubbuga bayan BGS kamar karamin yaro yana faɗin “nima ai ina matikar kaunar ku sosai duk wani abun da zai saku farinchiki shina ke so, “Abba muma mu ma matikar son farinchikin ka ai yayi maganar yana raba jikin sa dana Abba, miƙewa Abba yayi yana faɗin lokachin barchi yayi good night my lovely son, “good night Abba na BGS ya bashi amsa yana nufar, kaban mirrow, Abba kuma ya fice daga ɗakin yanufi part nashi, jallabiyar jikin sa, BGS ya chire ya nufi toilet dan yin wanka.

Abangaren Aryan kuwa yana fitowa daga part na BGS kai tsaye, part nashi ya nufa da sauri yana shiga betroom ɗin diyana na fitowa ta kawo masa coffee ta ajiye zata fita, karo sukayi kanta ya bugi faffaɗar kirjinsa ta fame chiwon nata wani ihu azaba ta saki tayi baya zata faɗi, da sauri ya rikota, nan take jini ya fara zuba daga goshin nata, rungumeta yayi sosai ajikin sa da kyar ya iya furta “sorry kiyi shiru, “yaya Aryan zafi ya kemin sosai “na sani nasan zai miki zafi amma ki daure ki daina kuka kinji muje na duba miki, ya karisa maganar tare da raba jikin su, ya kama hannun ta suka koma chikin ɗakin saman sofa ya zaunar da ita, ya zauna gefen ta ya zuba mata ash eyes nashi yana kallan yadda hawaye wani ke bin wani a kunchinta calmly ya fara magana “ba na che ki dai na kukan nan ba, turo ɗan karamin bakin nan nata tayi “to zafifa yake min, hannu yasa yana goge mata hawayen yana faɗin “to ki daure kinji bana son kukan naki ne ko kaɗan yana damun na idan ki nayi, ba kiga yadda ki kayi tsara kwalliyar ki ba ko so kike ya ɓachi “a’a bana son ya ɓachi “to kiyi shiru kinji, gyaɗa masa kai kawai tayi, shi kuma ya mike ya ɗauko A box,ya dawo kusa da ita ya zauna

A hankali ya fara gyara mata chiwon nata, sai was Allah na take faɗi shi kuma yana che mata sorry, har ya kammala san nan ya miƙe ya mayar da Box ɗin ya koma gefen katafaren gadon sa ya zauna,

…ɗaure fuska yayi sosai yana kallonta “ke wai bana che kada ki sake kwalliya da daddare ba, baki da lfy ma amma sai kin zana waɗan nan abubuwa a ɗan karamin face nakin nan ko? turo ɗan karamin bakin nan nata tayi kamar biro kafin tace “kayi hakuri bazan sake ba “kullun haka ki ke chewa ba zaki sake ba amma sake… Bai karisa maganar ba ash eyes nashi ya sauƙa a kan kayan jikinta,

wasu shaggun riga da wando ne, Black jeans ne ya matseta sossi santala santalan chin yoyin nan nata kamar zasu fasa wando, sai yar figaggiyar T-shirt pink colour itama ta matseta kana ganin shap na breast nata sosai daman gasu nan masha Allah tula tula dasu, ga kanta ba ɗan kwali ta saki wan nan bakin lallausan gashin nan nata har baya,sai shekin gashin ke yi, ta zubo wani ɗan kaɗan ɗin gashi ta gaban goshin ta, tayi make up nata iya make up,ga wani shegun high heel pink da ta sa a kafar ta, mamaki ne ma yaka mashi wai wa ya koyawa yarinyar nan duk irin waɗan nan abubuwa, nan take yaji ransa ya bachi sosai chikin tsawa yace “ke kina da hankali kuwa haka daman ki ka fito,kika keto gaba ɗaya part part na gidan nan har ki ka zo nan ko? chikin tsoro ta ɗago dan jin yadda yayi maganar, ba karamin raza tayi ba data kalli yadda fiskarsa ta sauya lokachi guda, asukwane ta miƙe zata gudu,

Taku ɗaya yayi ya tamki kugunta ta baya, tsabar raza da tayine bata san, lokachin da ta fasa ihu ba, asukwane yasa hannu ya toshe mata baki, chikin tsawa ya furta “kimin shiru,shiru tayi jikinta har bari yake . zame hannunsa yayi daga bakinta ya juyo da ita suna fuskantar juna, nan take kuma sai yaji ɓachin ran nasa duk ya kau sosai yake kallon face, nata a ranshe yana faɗin “yarinya sai kyau kamar ita tayi kanta komai tayi kyau yake mata,

Ganin yayi shirune yasa diyana ɗago blue eyes nata karaf suka sauƙa chikin nashi, murya na rawa lips nata sai kerma suke saboda tsoro kamar mai jin sanyi tafara magana “yaya Aryan kayi hakuri wlh ba laifi na bane Aunty farida da che tache… Bata karisa maganar ba sakama kon fisgota da yayi ta faɗa faffaɗar kirjin sa, dan ba zai iya jure kallan yadda lips nata ke motsawa ba,mutuwar tsaye diyana tayi dan gaba ɗaya ji tayi kamar baa duniya take ba, ran kwafar da kansa yayi sai tin kunnen’ta chikin wata iriyar kasalalliyar murya ya fara magana kasa kasa “karki sake saka irin waɗan nan kayan kinji ko? idan ma kina so sakawa kisa a iya ɗaki kawai idan zaki fita waje kisa hijabi kinji ban son na kara ganin ki haka.

….da kyar ta iya ɗago kanta daga kirjin nashi dan ta samu iskan da zata yi numfashi kasan chewar ya matseta sosai,bata iya wani numfashi da kyau, a hankali ta buɗe ɗan ƙaramin bakin ta muryar har rawa yake tafara magana “to yaya Aryan ai Aunty farida che tache na rinka sawa idan zan… Bai bari ta karisa ba ta ɗora ya tsan sa a saman lallausan lips nata yana girgiza kai kafin yace “a’a koda Aunty farida ta sake chewa ki saka kiche mata na hana ki kinji? kuma ai ita Aunty farida gobe ma zata koma ni dai kar na sake ganin ki da irin wan nan kayan bana so, to kawai tace masa tana numfashi da kyar saboda matse ta da yayi,

Shiru sukayi dukkan su shi yana kallanta ita kuma tana kallon kirjinsa, Almost 5mnt a haka, san nan diyana ta ɗago blue eyes nata slowly ta sauke su kan face nashi, karaf suka sauka chikin ash eyes nashi, dan kuwa ita yake kallo, da sauri tayi kasa da kanta dan bazata iya kallan chikin idon sa ba, “yaya Aryan na gaji da tsayuwa wlh jinake kamar zan faɗi “to ni kuma ban gajiba, da sauri ta ɗago blue eyes nata tana kallonsa ganin yadda ta ɗago ne yasa yashiga tunanin me ya faɗa ne, dan shi kwata kwata bai ma san me ya faɗa ba, sauko da ash eyes nashi yayi kan ɗan karamin bakin ta, yana kallan lallausan lips nata, da sauri ya sake ta yana furta a’uzubillahi minasshe ɗanin rajim, a chikin zuchiyar sa “ke wuche ki tafi ɗaki dare yayi kuma karki sake fitowa da irin kayan nan, yana kai karshen maganar ya juya yanufi toilet da sauri wai danma kar ya sake kallonta,

Kwas kwas kwas diyana ta juya jiki ba kwari ta nufi waje,

Aryan kuwa wanka yayi ya fito a gurguje ya shirya cikin kayan barchi riga da dogon wando masu kyau da tsada farare tas masu laushi, ganin dare yayi sosai yasa shi hayewa katafaren gadon sa batare da yashi coffee ɗin ba ja blanket yayi zuwa chikin sa ya sage gudun A.c ya lumshe ido ba jimawa barchi yayi awon gaba dashi

 

 

*💫STAR LADY💫*

💖The Talent Troupe Writer’s 💖

 

*DUK ƘARFIN IZZATA*

💖Story And Written💖
⬇️
*Star Lady*

 

Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai

 

*

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button