Sponsored Links
Bakar Ayah Hausa NovelHausa Novels

Bakar Ayah 18

Sponsored Links

Page 🖤18🖤

 

 

Wulgawar Bombee innayi tagani tana cin abinci, yaukuma ta dawo da wuri.innayin tafaɗa a ranta,kullum sai yamma liƙis take dawowa idan ta tafi makaranta,wani lokacinma sai dare yayi tukunna.Sau uku mlm Ahmadu yana kamata yana dukanta,amma ko kuka batayi,sannan kuma bata faɗi inda take zuwa ba,sannan kuma bata fasa kaiwa daren ba.
“Inna Daneji Addah Bombee tadawo tana ɗakinmu”
“Yauɗin kotaji magana babannku kai,amma a wanne yanayi tashigo”
“Uhm hannun duk jini har ya bata mata uniform ɗin jikinta”
Innayi ta faɗa a hankali,cikin sigar gulma,saboda kar addar tata tajiyo ta,aikuwa Alƙalamin ya ƙarye,dan duk maganar da takeyi a kunnenta sarai.
“Jini kuma wanne iri,yauni kuwa mai zangani a duniyar nan,hadda jini”
“Ahh toh Bombee ai tazama abinda tazama sai du’a’i,ke kuma ban hanaki shiga harkarta ba ne,sai tazo tana dukanki koh”
Inna laari tafaɗa tareda zabgawa innayi harara,yanzu kowa yasan inna laari haushin Bombee takeji,saboda a rana idan ta duka innayi yafi a ƙirga,wani lokacin ma wai dan kawai ta kalleta,a wajen kwanciya kuwa wajibine saita yi mata na bacci. In abun bai zo ba kuwa saitayi sati bata kulata ba.
Hanyar ɗakinnsu Daneji ta nufah tareda tsayawa akan Bombee,wacce take zaune a tsakiyar gadon ta bawa ƙofah baya.
Zaro ido Daneji tayi data kalli yatsun Bombee,dan dama su tazo gani domin da ta tabbatar da zancen innayi,aikuwa hakane farcenta zaƙo zaƙo duk jini a jikimsu tamkar faratun mayu,yaushe ta tara wannan faratun haka babu wanda yasani.
“Bombee menene haka a hannunki kaman jini,na wanene?”
“Jinin bello ne,yatareni zai ɗau fansar abinda nayiwa ƙanwarsa,nikuma na yanka masa fuska da farcena”
“Yanzu dan yazo ɗaukar fansa saiki yanka masa fuska,bazaki kawo ƙara ba gida,kinkuwa san hukuncin hakan”
“Nasani kuma babu abinda ya isa yayi daga shi har iyayensa,idan aka sake nima zan sake,batun nakawo ƙara kuma menene amfaninsa,shin tunda nake an taba ramamin idan wani ya zalunceni,saidai a bani haƙuri zancen ya wuce,dan haka ni gaskiya bazan sake yarda da wanannan tsarin ba,dole na kawo nawa tsarin nima”.
Dan takaici Daneji bata sake cewa komai ba,saima fita da tayi tabar ɗakin,abin yafi ƙarfinta yanzu kam.
Fitowa tayi daga ɗakin tana miƙa tareda yin hamma,ruwa ta ɗiba a bokiti tashiga banɗaki tayi wanka. Lokacin data fito innayi tashiryah cikin kayan islamiyyarsu da jakarta a hannu.
“Ke wato ina jinki kina gulamata ɗazu koh,idan kin dawo daga makarantar ki wankemin kayana,idan basu fitaba kuwa……..hmmmmm bazan ƙarisa ba”
“Bazata wanke ba idan ke kika haifamin ita,ko wankin kayanta banfara bata,amma ke kin fara bata naki dan mugunta”
“To karta wanke,wannan bai dameni ba,tunda na riga na faɗa mata shikenan”
Da sauri innayi tayi magana cikin muryar kuka kafim inna laari tasake cewa wani abun.
“Ahah inna zan wanke mata kayan idan nadawo daga islamiyya,na iya wanki fah”
Cikin takaici babu yadda zatayi ta jijjiga kai.
Riga da wando tasaka irinna pakistan,wanda mlm Ahmadu yasiyo musu a taraba dayaje kasuwanci,hula da saka kanta kawai,babu hijabi tayi hanyar waje.
“Ke ina zakije haka babu hijabi,dama ba islamiyyah zakije ba naga kinyi wanka”
Daneji ta faɗa,tun dazu sai yanzu tayi magana,dan tasan idan tayi ma aikin banza tayi,an doki kashi.
“Wancan Alwasun yace karna ƙarayin kusada makarantarsa satin daya wuce,nice dama nacigaba da zuwa,saboda akwai abinda nakesom ƙarisawa,yamzu kuwa na gama.
Yawo zanje kawai cikin jeji idan wani abune a aika innayi takirani,tasan inda nake.
A bakin ƙofar gidan sukaci laro da gaji,aikuwa caraf tariƙe kunnen Bombee suka shigo gidan tare.
“Dan bantan ubanki mai kikayi wa bello a fuska,dan tsabar abinnaki yawuce gona da iyaka shine kika yimasa yanka da wuƙa a fuska ko,da nayi haƙuri,amma yanzu kam bazaja sabu ba,kotu zan yi kararku a zo a daureki,abun ai yayi yawa shege da hauka,gabaɗaya a kwanaki kaɗan kin dasawa ƴaƴan anguwa tsagwaron tsoronki?”
Tunkuɗa Bombee tayi a ƙasa a gaban Daneji,har sannan bata bar masifa ba ita ƙarfinta.
Zagi takeyi da uwa ta uba,inda tashiga batanan take fitaba,bakinta har kumfah yakeyi dan masifah.
“Wallahi bazan yarda ba,ku jirayi sammaci a gobe,ƙara zan kai gobe,bama a cikin garinnan ba can Sardauna zan kaiku ƙara kuma da kuɗin tara mai yawa.
Har ina da wannan abun,yaro yana can fuska tayi sumtum idon wajen ko gani bayayi tashi,jiki ya dau zafin zazzabin wahala kamar motace ta bugeshi.
Kuma a goben saita fadawa Alƙali mai tayi masa,daga nafara maganar ɗaukar mataki jikinsa zai fara rawa,yarinya ƙarama tasakashi a cikin asirinta,dolen uwarki ma idan kikaji wahala zaki kunceshi da kanki”
A haka tagama faɗan ta son ranta tafita ta bar Daneji ta sharar ƙwallar baƙinciki,hararar Bombee tayi wacce zaune a ƙasa idonta a soye kaman faɗan ba’a kanta akayi shiba.
Ɗakinta tashige tafara ribzar kuka kozata samu ta huce da suyar da zuciyarta take mata.
“Mtswww ji yanda ta batamin kaya kuma tasaka innata kuka,aradu zanyi maganinki ne,bar ganin ki tuleliya bai dameni ba”
A hankali tayi maganar tana tura baki,kafin tajuyah tabar gidan,ta nufi inda tayi niyyar zuwa tun farkon barinta gidan.

Sallama Daneji tayi a gidan gaji da sassafe washagari,dan dama sunyi magana da mlm Ahmadu da daddare akan zataje sasanto gaji kan abinda yafaru.
Wata ƙatuwar tukunyace akan murhu ann ɗumame yara zasuci su tafi makaranta.
Ga gidannan duk tarkacen kayan wanke wanke.
Faɗa gaji take rabawa tsakanin Zulaiha da yayarta akan kunun wai,fa’izah taɗau Zulaiha bayan itace na ashirin ta siyo bana talatin ba.
Sallama Daneji ta cigaba ta kwararawa amma har yanzu gaji bata jitaba,saida wani yaro yakirata tukunna kafin tajuyo takalli danejin.
Ɗan alamar tsorone akan fuskarta amma tayi saurin kawar dashi tareda ƙaƙalo murmushin dole.
“Ahhh Daneji kece sannu daxuwa,ga kujera zoki zauna a zubo miki ɗumame”
“Ahh nagode ma,an tashi lafiyah ya gidan”
“Gida kalau,lafiya naganki da sassafe haka,hala dai mutane gidan kalau”
Abinne yabawa Daneji mamaki har takasa boye mamakin nata akan fuskarta.
“Uhm gaji nace ba,akan zancen kaiwa kararnan nazo,dan Allah a ƙara haƙuri,a sansanta cikin rufin asiri,kaiwa kotun bashida daɗi.
Mlmn ne ya turoni nasake baku haƙuri,sannan za’a biya kuɗin maganin inyaso”.
“Laah karki damu bakomai fah,faɗan yarane dabaka iyarmusu,babu komai yawuce bazai sake faruwaba,ki faɗawa mlm Ahmadu bakomai ya wuce baza’a sake ba”
Kasa jure tantamarta tayi,hakan yasa ta tambayi gaji mai yafaru.
“Amma gaji dan Allah mai ya faru naga kin sanja daga iya jiya,ina fatan dai hakan bayada nasaba da Bombee koh”
“Uhm Daneji kibar zancennan dai kawai,amma tunda kin matsa saƙo daya nakeso ki kaimata,dan Allah ya kice mata ƴaƴana bazasu sake shiga harkarta ba,itama ta taimaka tafita daga rayuwar mu,kowa hadu da daidan sa a yanzu”
Baki sake cikeda mamaki Daneji ta baro gidan gaji,a hanya babu sakar jakin da batayiba akan shin mai Bombee tayiwa gaji da ƴaƴan ta kuwa,kodai zancen mutane dagaskene kai,kai anya kuwa,in akwai wanda yasanta to bayana ne ai,kuma a sanina da ita bata tsafi bare nace shi tayi musu,to mai yake faruwa?
Tana cikin hakanne ta isa gida,zuwa lokacin rana ta fito yara sunata tafiyah makaranta,suma su Bombee sun shirya zasu tafi makaranta.
Daneji bata ‘baata lokaci ba takama hijabin Bombee tareda janta cikin ɗaki.
“Maza maza ina jinki yimin bayani mai kikayiwa gaji naga ta sanja a dare guda?”
Ɗan murmushin dama nasan haka zata faru tayi,kafin ta jijjiga kai.
“Ni babu abinda nayi musu mai zanyi musu”
“Bombee ki faɗamin gaskiya mai kikayiwa gaji take haka,tabbas akwai wani abu,kuma kece kikayi ba kowa ba”
“Inna baki yarda dani ba ne?”
“A da kenan,amma vanda yanzu dakika sauya daga yanda kike”
“Eh to ba wani abu bane babba,kawai dai na ɗan leƙa gidansu ne da daddare nayi musu gagarɗi”
“Gargadin me,ke ƙarama dake zaki iya bawa wannan ƙatuwar matar gargaɗi,ai koni ban isa yimata kashedi ballantana ke,ki faɗamin mai kikayi musu Bombee,ni yanzu kin fara bani tsoro da halayyarki”

 

…………Daren jiya……….

Karfa labari ya gundureku kunga an tsaya a waje guda ɗaya,komai da sannu ake warwareshi.
Dafatan zakuyimin hakuri dai….😏😊😊😊.

 

 

🖤 Sadi-Sakhna ce🖤
ƴar mutan jama’are

 

____****🖤🖤****_____

🖤 *BAƘAR AYAH* 🖤

🖤 _BOOK1_ 🖤

 

Labari/Rubutawa:SADI-SAKHNA
[ _Ƴar mutan Jama’are_ ]

 

 

*WATTPAD*
Https://www.wattpad.com/user/SAKHNA03

*AREWABOOKS*
https://arewabooks.com/u/sadeesakhna

______________****_______________

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button