Sponsored Links
Dabi'ar Zuciya Hausa NovelHausa Novels

Dabi’ar Zuciya 65

Sponsored Links

65

Cike gidan yake da mutane,wasu suna shiga wasu suna fita,idan ka kalla zakayi tsammanin biki akeyi,eh….kusan bikinne saidai bashi bane,su momma ne suka yiwa garin tsinke,ita da hajiya qarama,da jawahir da biba,suka kuma kawo kayan lefen kaltum akwati dai dai har guda goma sha takwas,set shida shida different colors masu azabar kyau da tsada.

Sunzo da duk wani kayan aure na al’ada da akasan ana neman auren diya mace dashi,nema kuma irin na masu wadata da rufin asiri.

Saukar girma ummanmu tayi musu,don dama tasan da batun zuwan nasu,girki sosai akayi na alfarma,bayan lemuka da samir yasa aka kawo ruwa da sauran duka kayan buqata.

Wannan kaya da aka kawo ya hautsina qauyen dinya cikin mintuna kadan,labari ya bazu ko.ina,sai ga jama’a anata tururuwar zuwa gani,sai ka rantse da Allah wani sha’anin biki akeyi.

Kaltum kamar bata sansu ba tayi gidan habiba dauke da sultan dinta,ba kowa a gidan,don babar yusufa ma tana gidansu,da ita aka karba kayan,habiban ma tana can,sai sallamar jawahir taji.

Cikin farinciki suka rungume junansu,kamar wadanda suka dade basuga juna ba,ta bawa jawahir ruwa tayi alwala sannan tayi sallah,sai kaltum din ta zuba musu abinci cikin wanda ummanmu ta aiko musu dashi.

“Da alama bakinki fa akwai magana”

“Akwai matar the giant saraki” jawahir ta amshe ba tantama ko kwana kwana

“Bayan tafiyarki abubuwa da yawa sun faru,ciki kuwa harda yankewa najwa hukuncin daurin rai da rai da kotu tayi” tayi maganar idanunta na tara qwalla,jikin kaltum yayi sanyi itama,ta fara lallashin jawahir tare da bata baki,har ta samu tadan nutsu sannan ta dora

“Lefen aurena yana gida irin naki kuma kamar naki,Amiru ya karbi soyayyata,ya kuma nemi yardata kan zai aureni….bisa goyon bayan hajiya qarama da momma harma da daddy,bayan sun lalubi dangin mahaifina…..da farko sun doje,amma da suka bincike sosai,sai suka samu dama akwai abinda ke damunsa kafin ya rasu,cikin rubuce rubucen wasiyyar da ya bari suka samu nice,sun karbe ni sun kuma mutuntani,musamman mahaifiyar abbana,qannensa dukka maza ne,don haka babu wani cece kuce me yawa suka girmamani ba wulaqanci,saidai ya samir ya roqesu kan su boye al’amarin,saboda sunaso duniya taci gaba da kallona a matsayin diyar professor rashid azare kamar yadda take kallo na a baya……saidai nidin kunyar kallonsu nakeyi….saboda hanyar da mummy tabi ta samar dani…..abun yana min ciwo kulsum,naga matuqar qoqarin ya amiru daya bugu qirji zai aureni…..” Ta qarasa maganar qwalla na sauko mata.

Cikin sigar lallashi da kwantar da hankali kulsum ke mata magana

“Duk abinda ya faru ya riga ya wuce jawahir,kada jiyanki tasa ki rushe gobenki,yanzu babu abinda yafi kamata dake illa ki fuskanci gobenki,sannan shi a aure…..nagartar mace na iya shafe duk wani aibu dake tattare dashi…kedin nagartacciya ce jawahir,kina da dukkan DABI’A ta qwarai,baki bari ƊABI’AR ZUCIYA na son rai da son kanta ya rinjayeki ya gurbata miki halayya da ƊABI’A ba,kina da matuqar kirki da tausayi,na tabbatar wannan yaa amiru ya kalla,Allah kadai yasan manufarsa na fiddoki a haka da yayi,wala’alla ke wannan ce taki jarrabawar nan gidan duniya,kuma nayi imanin idan kika cinyeta….zata iya zame miki silar shigarki aljanna” kalamai masu taushi tayi amfani dasu wajen kwantarwa da jawahir hankali,ta kuma samu nasarar hakan,don ta sake sosai,suka dinga hira,jawahir na bata labarin abubuwan da suke faruwa da bata nan,gidan yayi dadi sosai,ya koma kamar da,yadda momma ke bata kulawa har yafi yanda mummy ke batan,saboda lokacin mummy tana fuskantar tsangwama saboda ra’ayinsu baizo daya da mummy da jawahir ba,amma a yanzu duka babu wannan.

Ya samir kuwa tace yafara zama mara kunya ta fadi tana dariya,wallahi baya iya boye soyayyar da yake miki,kinsa momma ce taja masa kunne kan ahir dinsa yazo ya dameki?,ai inajin da ko kwana hudu vakiyi cikin qauyen nan,gaban kowa kuwa banda momma da daddy amsa waya yakeyi,shi da ya amiru kuwa yanzu baram baram jawahir ta fada tana tilliqa dariya

“Me yasa?”kulsum ta tambayeta itama tana tata dariyar tare da jin wata kewa ta mijin nata na kwarara sassan jikinta

“Yace wallahi ya samir din ya fara zaucewa,baya barinsu suyi barci,bashi da aiki sai waya” sai suka sanya dariya gaba daya.

To sai yamma lis su momma suka tashi tafiya,ciki har da ‘yan uwanta daga sudan mutum biyu,sai wasu daga azare ‘yan uwan daddy mutum uku suma,saidai kulsum ta kasa zuwa bare ta hada idanu dasu, momma ta dinga mita

“Shikenan samir ya shiga tsakaninmu kenan yayi mana farraqu?,to ban yarda ba,da sake” da kanta tayi tattaki har gidan habi ta ganta sannan sukayi sallama,saidai jawahir ta roqi momma ta barta,sa dawo tare da kulsum din.

Hakan kuwa akayi,a nan qauyen suka barta,tare da ita suka dinga zagaya dangi,har gidan inna,wadda ta fashe da kuka sanda taga uban kabakin da su momma suka ajjiye mata a matsayinta na kakar kulsum,saboda momman tace duk wani daya danganci kulsum sai yaci arziqinta ya kuma ya qara,kulsum mutum ce,kulsum nagartacciyar mace ce mai kyakkyawar zuciya,wadda kudi ko dukiya ko wani qyale qyale na rayuwa bai dameta ba,sanda zata tafi saiga innar ta zube tana roqarta gafara

“Basai kin nema gafarata ba inna,badai abun duniya kikeso ba,kuma gashi an baki,zaki iya ci gaba da tsinema muda ummanmu” sarai innar ra gane magana ta gaya mata a fakaice,to amma tasan yaran sunyi haquri,sun kuma yi kawaici,kome zata fada kuwa,ita a yanzu nadamarta hade da kunya take,ashe wanda ka raina watarana shine zaiji qanka ya rufa maka asiri?,ashe RABON BAWA DA ARZIQI MUTUWA ce?.

“Allah ya yafemu gaba daya” itace kalmar qarshe da kulsum tayi mata suka baro gidan.

“To haka kawu ado yakumbo indo da umma suwaiba,kaf dangi ‘yan uwa abokan arxiqi babu wanda baice HAIHUWA TAYI RANA ba akan su kulsum din,abun sai son barka da godiya ga Allah S W T wanda yake azurta bawa a sanda yaso.

Yakumbo indo ita ta dauke kulsum da jawahir ta ajjiye gidanta ta fara tsumasu,gyara na gaske take musu musamman kulsum da take ganin ‘yar hannu ce,batasan komai bai gudana ba,har sai wani dare an hadu ana hira,kwanaki bakwai da suka rage su koma gida ayi walimar da za’a raka amare gidajensu,da ita da fatsima da karima wadda a yanzu itama ta sauko take kuma jin kunyar abinda suka yiwa kulsum din a baya,ashe arziqinta yaci uban nasu,gefe ga jawahir da habi dake baiwa danga nono,karime ke tsokanarta kada fa ta koma asake sabon gashi yawa sabuwar amaryar da aka kawo yau yau.

Yatsina fuska tayi tana dubanta
“To da mecece?,kar nake a leda,babu wani abu daya gudana” dariya suka sanya gaba daya,habi ta kama baki ta kasa magana,jawahir tace

“Allah ya samir ya gama hure miki kunne,ya koya miki rashin kunya”

“To meye laifinsa?,yama yi qoqari ai” shewar suka sake saki

“Zaki bayani da babban baqi wallahi,don indai wannan mijin naki ne a yadda dai na ganshi ko…..hmmmm” dukkansu suka sake saka dariya,sai kuma tsoro ya dan tsarga mata,ta basar da zancan aka shiga wata hirar.

Da magariba bayan sun bar gidan habi tayo wajen ummanta,sai umman ta kama hannunta zuwa qofar wani daki,ta tura ya bude,cike fal dakin yake da kayan jeren cikin gida da kayan qyale qyale,masu kyau masu tsada kuma na zamani

“Ki duba da kanki kaltum,kar kiji kunya,idan akwai abinda babu kiyi magana za’a siyoshi kafin ku tafi” idanunta cike fal da qwallar qaunar da umman nata ke mata

“Ummanmu….duka wadan nan kayan?” Kai ta gyada mata

“Nakine kaltum,duka abunda na mallaka a duniya naku ne keda habi,saboda bani da kwafinku” rungume umman nata tayi a jikinta sosai,tayi kuka tayi kuka,tayiwa bilalu addu’a,sannan tana tsaye aka dinga fito da kayan tana gani.

Komai yaji yayi daidai,babu wani abu da babu shi koda kuwa ina za’a kaita a aure,sun jima suna hira da ummansu har zuwa sanda babansu ya shigo,bakinsa dauke da sallama,kai bakace shi bane.

Sannu da zuwa tayi masa ta miqe zata shige daka kamar yadda suka saba a baya

“Kulsumu” taji yayi kiranta,saita tsaya cak

“Zo nan” ya kirayeta,ta dawo da baya,tazo gabansa ta tsugunna

“Fushi kike dani har yanzu ko?” Yayi maganar muryarsa na rawa,saiga hawaye na sauka,abinda ya daga hankalin kaltum kenan,ta girgiza kai da hanzari

“A’ah baba”
“Idan ma kinyi ai bakiyi laifi ba,amma ina roqonki don girman Allah ki yafeni,bana buqatar komai daga wajenki banda yafiyar,koda bazan tsira da komai ba a rayuwata ba damuwata bace indai na tsira da yafiyarku”

“Ban riqeka ba baba,kai kayi silar kawoni duniya,na yafe maka,kuma kaima ka yafemin idan na taba bata maka” adaren su ukun suka zauna sukayi hirar da suka kafa tarihi,irin hirar da tun haihuwarta basu taba ba.

Ana ya gobe zasu tafi saiga lantana Allah ya kawota ita da nasuru,da fari kunyar kulsum ta dunga ji tana buya,wai kada taga kamar taci amanarta,saida zasu fita da yammaci xasu karbo wasu kaya wajen yakumbo indo,tayi wa lantana ba zata ta fada gidanta,sun sameta tana ta ware tsarabar doya da manja da dankalin turawa da takanyo,ta saukesu da ruwan da lemon roba cikin mutantawa da kuma jin kunya,xata fice kulsum tayi caraf ta damqota

“Na kamaki,waini lanatana kikejin kunya?,me kika yimin banda alheri?” Kanta ta sadda qasa,saidai yadda kulsum din keta dibanta da tuna mata da rayuwarsu ta baya ya tabbatar mata babu komai a ranta kulsum din,daga qarshe ta shaida mata ita dadi ma taji data auri nasurun,saboda sun dace matuqa,sukayi sallama ta hada mata doya da yawa tace ta kaiwa ummanmu,dama kuma ta saba kai mata duk sanda ta dawo,ba zata samu zuwa walimae tarewar kulsum din ba saboda tayi nauyi,amma ta karbi address dinta,ta tabbatar mata da cewa tana nan zuwa in sha Allah duk sanda suka shiga garin.

Kudin da tazo dasu taga sam babu wata buqata da ummanta ko babanta ke dashi,saita rabasu gida hudu,kaso biyu ta bawa habi wadda keta tunanin irin san’ar daya kamata tayi,ta bata shawarar sarar atamfofi da hijabai,kaso daya ta aikawa da wasila,daya kashin kuma ta aikawa da asiya,duk da tana tunanin ba zata karba ba,saiga asiyan da kanta tazo godiya,inna laure ta rakota,saida suka gama godiyar asiya ta fashe da kuka,suna neman gafarar ta,bata wani tsaya batama kanta lokaci ba tace ta yafe mata,sabida ta riga ta wucen wajen ita.

Bata jima da fita ba wasila tazo da nata kukan da neman gafara,itama cewa tayi ta yafe matan,saboda ubangiji ya ruga daya hukunta kowa dai dai da laifinsa,to me yayi saura?.

******** Cike da wata irin nutsuwa me ratsa zuciya gangar jiki da ruhi yake rufe kowanne sashe na gidan,har zuwa sanda yakai ga qofar qarshe wadda zata sadashi da ainihin falon gidan,saiya daga kansa a hankali yana kallon sama,wadda ta hada hadari me kyau daya fara feso yayyafi yas yas a jejjere me dan yawa.

“Alhamdulillahil lazi bini’imatihi tatimmus salihat” shine abinda ya furta,bayan samun kansa da yayi tsakiyar falon gidansa da yake mallakinsa,wanda tako ina qamshi yake fitarwa mai taushi da dadi,komai kuma na falon kalar fari ne da light ash.

Tafiya yaci gaba dayi yana sanya hannunsa yana fidda babbar rigar jikinsa ya riqeta a hannunsa,komai na jikinsa farine qal kamar hannu bai taba tabashi ba,tun daga samansa har qasa.

A hankali ya tura qofar dakin da yake da tabbacin a ciki take a zaune,dakine wanda babanta yayi mata komai na ciki,bayan dakin da umman ta ta shirya mata,da kuma wanda shi karan kansa samir din yayi mata,amma sai ta zabi zama ana babanta,saboda tasan cewa da uba ake ado.

Maida qofar yayi ya rufe,fuskarsa na fidda wani yalwataccen murmushi,sallama yayi da tattausan muryarsa data qara laushi,tun daga bakin qofar ya tsugunna ya zare takalminsa,safa kawai ta rage,sannan ya miqe a nutse,idanuwansa a kanta ya soma takawa zuwa inda take zaune,duqunqune cikin fararen tufafin lace mai taushi,da sassalkan mayafi mai ado irin na jikin lace din.

Waiwaya yayi ya hangi wata dunqulalliyar kujera ta cusion,ya sanya hannu ya janyota zuwa gaban gadon inda take zaune,gab da ita,gwiwoyinsu na gogar na juna,hannunsa ya sanya ya lalubo hannayenta ya riqesu ga cikin nasa,sannan ya sake maimaita sallamar da yayi dazun.

Da dasashiyar muryarta mai sanyi ta masa masa,ta sanya hannu a hankali ya zare mayafin data rufe kanta dashi

“Look” ya fada yana ci gaba da tsura mata idanu,wani shegen dinki akayima lace din kamar qasar arna,saidai ya qayatar dashi matuqa,ya kuma ja hankalinsa

“Karki fara karya alqawari tun yanzu….. please ummu kulsum” ta tuna dukkan wani alqawari data dauka masa a shekaran jiya,hanyarsu ta zuwa gidan qunshi,yabi ya dauketa,ya isa da ita wani guest house,sun dade acan yana karanta mata karatun yadda yakeson rayuwarsu ta kasance,da qyar ya maidata gidan qunshin.

Daga kan nata tayi yadda ta buqata suka hada.idanu,babu kwalliyan komai kan fuskarta,sai qamshi na bala’i da jikinta ke fitarwa tako ta ina,saboda amfani da tayi da kayan kamfanin YERWA INCENSE AND MORE.

Dukka hannayensa ya sanya yana goge mata fuskarta
“Ya akayi kikayi kuka da yawa,ko zafi bakiji,babu ac dakin ba fanka” anutse ya tashi ya isa makunnar ac ya kunna kana ya daidaita,ya dauki remote na fanka itama ya saita ta kadan,har zuwa lokacin yayyafin na nan,saima qara qarfi da yayi.

Inda ya tashi ya sake dawowa ya zauna,na wasu sakanni sannan ya bude baki cike da nutsuwa

“ki rage kayan jikinki ki watsa rawa,sai samu sauqin gajiyar jikinki” ya fada yana dubanta,kallonsa tayi sai kuma ya dauke idanunta da sauri

“A’ah….sai zuwa da safe”

“Banason musu” ya fada yana miqewa

“kafin na dawo ki shirya,minti goma kawai” sai ya dauki babbar rigarsa ya soma takawa zai fice daga dakin,ya fuskanci kamar a darare take dashi,shi yasa bai matsa mata ba,ya zabi bata space.

Yana fita ta sauke ajiyar zuciya,ta ware mayafin kanta hade da dankwalin tana qarewa dakin kallo,sannan daga bisani ta miqe a hankali,ta tabbatar yaja mata qofar sannan ta nufi bandaki.

Ruwa me zafi sosai ta hada tayi wanka,taji dadin jikinta kuwa sosai,harma taga baiken kanta da ada taqi yarda tayi wankan,ta fito a gurguje ta shirya cikin wata tattausar doguwar rigar barci ta dora madaidaicin hijabi saman kanta ta zauna gefe daya,tana sake qarewa dakin nata kallo.

Da sanyin nan nasa dai yayi sallama yana turo qofar dakin,ta amsa mata itama a tausashe,tana satar kallon fuskarsa,qamshinsa ya baibaye dakin gaba daya,wani kyau taga ya qara mata,fuskarsa ta sake fresh,kamar wanda aka bawa kyautar wata.

Babbar dardumar da ya shigo da ita ya shimfida,bayan ya ajjiye plates da cups daya shigo dasu,sannan yayi mata izinin ta taso,a nutse ta tashi,ta tsaya daga bayansa hannun damarsa,kamar yadda qa’idar sallar jam’in mace daya da namiji guda daya take.

Matsakaitan raka’o’i guda biyu sukayi,suka sallame,bai juyo ba yana fuskantar alqibla ya fada jero addu’o’i,addu’o’i masu dauke da fa’idoji da kuma tarin ma’anoni masu yawa,ta lumshe idanu tasirin addu’ar na ratsata,ma’anoninta na mata amsa kuwwa cikin kanta,har zuwa sanda ya kammala,ya shafa,ya waiwayo yana dubanta.

Idanunta ta sake rufewa zuciyarta na bugawa sanda ya dora hannunsa akanta,gaban goshinta,ya karanta addu’ar data dace kowanne ango yayi sanda aka kawo masa amaryarsa,ko kuma mutumin da ya siya sabon abun hawa.

Da kansa ya miqe ya dauko ledar da ya shigo da ita,ya bude komai ya kuma zuba sannan ya kauda ledojin ya sanya farantin a tsakaninsu,idanunsa cikin nata yana son lalubo qwayar idanunta da suka cika taf da tsoro,tsoron dakan sanyashi yin murmushi,baisan su waye suka gaya mata labari me yawa haka kan daren farko ba data tsorace masa sosai,cikin hikima ya dinga hilatarta,har ta dan sake,ta sha sassanyar fresh mik din daya cika mata cup da ita,saidai daga ita din bata iya sake cin komai ba.

Ya rigata tashi,ya barta tana ta laqai laqai dinta,saiya koma gefan gadon ya zauna yana duba wayarsa,duk da cewa fiye da rabin hankalinsa yana kanta,har zuwa sanda ta gama tana kammale wajen,shima sai yayi amfani da wannan damar ya gama shirya duk wani plan dinsa,bayan yayi rub da ciki kan gado yana hangenta daga kwancen.

“Ummukulsum” yadda ya kira sunan nata da wani shaqaqqen sauti,sai da da haifar mata da faduwar gaba da wata irin kasala,Bai jirayi amsarta ba yace

“Kizo ki kwanta,ruwa na sake qarfi,sanyi kuma garin yake dada yi” itakam har ga Allah a tsorace take,sai ta fara takawa a hankali xuwa bakin gadon,kamar kazar da qwai ya fashewa a ciki……saidai kafin ta qarasa wata walqiya ta haske sararin subhana,ta kuma ratso har dakin nasu ta window din da daddadar iska ke ratsowa,wadda tafi ta fanka da ac dadin shaqa da lafiya a jiki,ta runtse ido cike da tsoro,kafin kuma tayi tunanin meye abunyi na gaba,an kwararo tsawa,wadda ta korata da gudu,sai gata tsamo tsamo saman gadon,ruqunqume da saraki.

Murmushi ya saki mai cike da jin dadi
“Alhamdulillah” ya furta qasan ransa yana yiwa Allah godiya da ya kawo masa ita cikin sauqi,sai ya laluba makashi switch na fitilun dakin ya kashesu gaba daya,ya maida gurbinsu da wasu kalolin fitilu masu bada dim light,kalolin da suka maida dakin a idanu wata kala me kyau da qayatarwa.

A hankali ya daidata kwanciyarsa,ya kuma sanyata da kyau cikin jikinsa,yana sauraren yadda zuciyarta ke bugawa,da gasken gaske take tsoron walqiya da tsawa har haka,sai yaci gaba da riqonta cikin jikinsa,yana shafa gashin kanta da ya bayyana,bayan dankwalibta yayi nasa wajen tuntuni.

Sai data fara dawowa dai dai sannan ta tuna wautar data tafka,saita motsa tana yunqurin zame jikinta daga nasa,sake sakata yayi tsakanin qirjinsa,ya cusa kansa ta cikin wuyanta ya lalubu kunnenta ya rada mata

“Amma dai ya kamata a bani tukucin aikin da nayi ko?” Bai jirayi amsarta ba ya fara aiwatar da abinda yake ganin shi kadai ne a yanzu abinda ya rage masa ya qarasa maidata tashi halak malak,tun yanayi a sannu har dukka jikinsa ya amsa,ya koma aike mata da saqonni masu zafi cikin kuma zafi.

Cikin sakanni kadan jikinsa ko ina ya dauki rawa,sai kace wanda aka tsoma cikin ruwan qanqara,sai da ya tabbatar ya dorata a hanya itama sannan ya fara yunqurin zarcewa,ta sake masa kuka dai dai sanda ruwan saman ya kece da qarfin gaske.

“No….no…..no ummukulsum, you promised me……ba zaki hana ni ba…… please ummu” kasa qarasawa yayi saboda yadda bakinsa ke rawa sosai,ya miqe ya zauna ya sake janta jikinsa.

Da kalaman bakinsa ya sake aiki ta bashi dukkan yardarta,cikin tausayi da tausasawa diya mace,bisa bigire na girmamawa da sanin darajar halittar ya tafi da ita,wanda kusan a jininsa yake,girmama dan adam,musamma diya mace.

Saidai duk yadda ya tafi da itan bisa lalama…..hakan bai hanasu dukkaninsu ji a jikinsu ba,kasancewarsu farin shiga,da basusan komai ba.

Koda suka isar da sallar asuba kasa daga idanunta tayi ta kalleshi,kanta a qasa,shi kuma yaqi matsawa ya bata waje taji da abunda ke damunta,ya tsareta da idanun nan nasa da suka qara daraja da kima daren jiya zuwa yau.

Ganin da gaske ba zata kalleshi ba sai ya qaraso ya kama hannayenta

“Am sorry matata…..nasan na miki rauni da yawa…..amma bani da wani option daya ragemin,ina fatan zaki yafemin…..kuma wannan zai zama kamar harsashi ne da muka kafa ta gina ingantacciya kuma sabuwar rayuwa cikin duniyar soyayya” wata irin qauna da tausayi mai girma suka kamata,shi da abunsa?,shi da halalinsa amma yake bata haquri,lallai shi din lu’ulu’u ne,tsintarsa saimai dimbin sa’a

“Kayi dukka yadda kaga dama dani,ba sai da amincewata ko yardata ba,ni halalinka ce ta har abada” kamar xai tsaga qirjinsa ya sanyata haka ya dinga ji,bai samu sasaucin azalzalarsa da zuciyarsa keyi ba,sai daya rungumeta tsam na tsahon wasu mintuna sannan yace

“Ina da tabbacin kinji yadda zuciyata ke bugawa,kuma duka saboda ke ne…..don Allah….kimin alqawarin zaki rayu dani,komai wuya komai dadi,ba zaki taba barina ba,komai girman laifin da nayi miki,ki hukuntani yadda kikeso,amma bazan iya jurar rabuwa a tsakaninmu ba” ya fada yana sake matseta cikin jikinsa

“Nayi maka” ta fada da zazzaqar muryarsa dake sake tsumoshi,sai da yayi yaqi da zuciyarsa sannan ya kaita nesa,ta hanyar daga mata qafa da yi mata alfarma ta koma bacci abinta,amma gashi,sai baccin ya gagareshi,don haka ya dauko qaramin qur’ani ya dawo gaban gadon daga qasa ya zauna,kamar me gadinta,yana karantawa qasa qasa,yadda sautin bazai damu kowa ba,duk bayan wasu ayoyi idan ya karanta sai ya daga kai ya kalleta,ta saman fuskarta zaka iya ganin yadda idanunta suka tasa,wanda hakan ke alamta maka taci kuka,ya saki murmushin gefan baki yana tuna daren jiyan,wani irin dare da bai taba zaton akwai irinsa ba akafatanin rayuwar dan adam,ya kasa jurewa,sai daya dan miqe kadan yayi kissing soft lips dinta zuwa goshinta sannan ya dawo ya zauna,ba ita kadai yake ganin kima ba,har umma da tayi qoqarin tsare mutuncin diyoyinta har sai da suka kaishi inda ya kamata ya kuma cancanta(qalubale gareku yammata,gurbin ido ba ido bane),talauci tsangwama da babu basu sanya umman tayi watsi da tarbiyyarsu ba,ta yarda su rasa komai amma banda mutunci(qalubale gareku iyaye mata).

Lokacin data farka taji dadin jikinta sosai,ta taras da abinci yana jiranta,saqon gaisuwa daga momma,da kuma saqon bankwana daga ‘yan qauyen dinya cewa sun wuce gida.

Tun jiya suke gaya mata ba zasu dawo ba,ta dauka cewa fadi kawai suke,ashe da gaske suke,saita narke zata masa kuka,ya zauna dirshan ya lallashi abarsa,don shikam hakan yayi masa,ko banza zasu sake,zata kuma huta itama ta warke babu sa’idon kowa.

Cikin kwanakin amarci ake bugawa iya amarci,amarcin da har takai tsakanin amiru da samir ko a waya,duk da cewa layi daya suke,amma akwai gidaje kusan shida a tsakaninsu,abinda tsahon rayuwarsu bai taba faruwa ba,matuqar suna gari daya.

A kwana na bakwai ne ma amirun ya nemi samir,sun dan jima saman waya suna hira,sannan ya hada jawahir da kaltum.

Hirar tasu kusan ta sabuwar rayuwar da suka tsinci kansu ne,saidai alhamdulillahi,kowacce al’amura na tafiyar mata dai dai.

Batasan cewa samir ya biyota dakin ba,kunya ta sanyata take zata gudu,yayi caraf ya kamota yana cewa

“Tunda kika iya hira haka rai rai yau kam akwai daukan magana,ki shirya” saiya fadar mata da gaba,ta marairaice masa,shima sai ya narke mata,hakanan ta bada kai bori ya hau,saidai salon qauna da tarairayar data gamu da ita ya shafe sauranb tsoron dake ranta.

Wasa wasa daga samir har amiru sai aka daina ganinsu,qarshe dai daddy ne ya cire kunya ya wankesu fes,yace daga ranar litinin me zuwa yana neman kowa,saboda gyara da zasu fara yiwa company,da kuma bude sabon reshe wanda yafi wannnan girman,zai dauki ma’aikata kusan dubu da wani abu,don tuni daddy ya shaidawa duniya ya ajjiye siyasa,ya kama kasuwancinsa kadai ya isheshi,siyasa qaddararsa ce dama,kuma yana fatan ya cinye jarrabawarsa.

Dole ran Monday din babu kunya suka shirya suka fitan,kowa na kewar matarsa,suka tadda daddy suna wani sussunkui da kai suka gaidashi,ya share kamar bai gane me sukewa ba,suka shiga maganar data tarasun,ganin haka suma sai suka sake,suka kuma shiga tsara abinda zai fishshesu.

🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥

*_DA ZAFINSU_*

*_A TSARE SUKE_*

*_SUN TANADESU_*

*_CIKIN SALO NA HIKIMA DA BAN SHA’AWA_*

*_ƘAWATATTU kuma ZAFAFAN DOCUMENTS HAR GUDA 25 na ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR da aka tanadar muku dasu_*

*_tun daga batch 01 har batch 05,duka bisa farashin rangwame_*

*_MAZA TUNTUBESU TA WADANNAN LAMBOBIN WAYAR KAMAR HAKA_*

_WADANDA SUKESON TURAWA TA ACCOUNT SU YIWA WANNAN NUMBER WAYAR MAGANA_

08184017082

_MASU TURA KATIN WAYA KO VTU KUMA_
09134848107

*_TARON GAMAYYAR ZAFAFAN MARUBUTA…..MASU ZAFAFAN ALQALUMMA_*

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button