Sponsored Links
Bakar Ayah Book 2Hausa Novels

Bakar Ayah Book 2 Page 37-38

Sponsored Links

Page 🖤37••38🖤

 

Washagarin ranar Asabar aka É—aura auren Aliyu Abdullahi da kuma Jawaheer Adulmumin & JALEELAH UMAR.
kan sadaki ko waccensu dubu hamsin hamsin.
GabaÉ—aya gidaje biyun babu masakar tsinke na mutane.
Lokacin da iyayen Jaleelah sukaji cewar mata biyu za’a auramasa Lokaci guda Æ™in amincewa sukayi,bayan sun san yanada wasu biyun dama.
Saidai abune da anriga an yi nisa,an ɗaura aure alƙalamin ya bushe,saidai muyi musu fatan zama lafiya kawai.
Duk da cewar Jabeer ya yage kan cewar bazayyi evrnt ba,amma Hajiya zeenah ta haÉ—a masa walima na uwa a harabar gidansu,wanda dukkka matansa zasu halatta idan ankawo su da yamma.

Maleekah ce tashigo sashen Bombee taci kwalliyah,ƙannen ango ba zama,ƙaramin akwatine a hannunta,tundaga bakin falon take zuba sallama,Bombee najinta bata kulataba,sai Hilyaan ce ta amsa mata wacce take zaune a kujera.
“Uwargida sarautar mata,munzo dannar Æ™irji fah,dafatan dai bakya suma ana zuba miki ruwa,kishiyoyi biyu lokaci guda”
“Mai ya kawoki keda kike tsaka da hidima?”
“Uhm kayan dazaki saka a walima na kawo miki,na bawa Lubnah nata ma,amma fah da alama mommah bataso baki kayanba,dan kamar karta bayar tayi,anty maryam wata Æ´ar tsamar kukayi ne”
“Wannan tsakanina ne da ita bai shafeki ba kinji,yanzu dai mayar mata kayanta,dan ba wani biki dazanje”
“Habaaaa anty maryam,ni wlh duk cikinsu ke ma nakeso na gani a wajen,dan allah kizo kowa na tambayan ina matar yah Jabeer ta biyu,kubiyu tunda aka fara biki baku fita daga sashenku ba,kowa na cewa baÆ™in ciki kuke,tunda har anty Lubnah tace zataje dan Allah kema kizo”
“Hmmm to naji uwar surutu naga kina shirin fita ina zuwa,ko matan yayannaki zaki É—akko daga É—aurin aure uhm?”
“Ahh habadai,zamuje É—akko yah Abdulkareem ne a Airport,shi yah Abdulmaleek jiya ya dawo da daddare.
Lahh ashe ma anty maryam baki san Brothers É—ina ba,karki damu ai sun dawo kenan,Abbah ne yace lallai su dawo Æ™asarsu suyi aiki,zan kawo miki su ku gaisa sosai.”
“Bayan surutu wasu zaki gayyato min sashena kuma,to karma ki fara,maza shige kije zanzo taron”
Juyawa tayi wajen Hilyaan wacce takeyin game a waya,Inayah kuwa bacci take akan kujera..
Yau yini suka zo mata dukkansu,innayi tana bacci itada inna Danejo a É—aki.

Haba big bros daga É—aurin aure zai tafiya wajen amarya,ba zaka tsaya Dr.AK (Abdulkareem)ya dawo ku gaisa ba,rabonsa da gida fahi think 7 to 8 month,tun mutuwar sis hafsa koh?”
“Kake zancen rabonsa da gida ya dade,kaima ka dade ai vaka nan,daga Cewa Ka tafi yin wata 3 kaine kusan wata 6,ai abba yayimin daidai daya dawo daku dukka gida,bama ya wancan likitan bansan ya zayyi ba da zaman Æ™asarnan yanzu”
“Hmmm ka barsu kawai Khaleel,duk yanda zasuyi ma zasuyine,daÉ—i sukeji ai su tafi sai sanda sukaga dama su dawo,sun girma har yanzu babu mai zancen aure a cikinsu.
Nikuwa ganinan kawai na buÉ—i ido na ganni da mata huÉ—u,kaman ana zamanin Era”
Dariyah Khaleel yakece da ita shida A.M(Abdulmaleek),wanda hakan yasake ƙular da Jabeer har wuyah.
“Haba big bro ka kamanta ratar dake tsakaninmu dakai da yawane,ga wanda zakayiwa nan abokinka ai,shine babban tujuru,ni barina fita Little sis na jirana zamu É—akko wancan likitan a filin jirgi.
Favorite É—in Mommah kenan,tun É—azu take maganar ya iso kuwa?”
“Tunda kuka shigo duniyar nikam dama na zama bango ai mai daÉ—in jingina”
Jabeer ya faÉ—a yana sake gyara zaman hularsa.
“Kuma fah JJ Gaskiya A.M yafaÉ—a,kai kayi huÉ—u ni banida ko É—aya,watan gaba zan turo ayi maganar mu da Madeenah dai inaga”
“Hmmm zo mu fara bi takan waccar kafin mu shige wajen Jaleelah”

Harabar da aka gyara domin walimar ba ƙaramin ƙawatuwa yayi ba sosai.
Da ko ina haske wajen yake dukkuwa da cewar yamma ce da rana a sama.
Wajen zaman amare da ango kujeru biyar ne,ta ango daban sai biyu a kowanne bangarensa. An ƙwatasu matuƙa,kuɗi kam in yana magana daya koka..
Gaba É—aya wajen shigar kala biyu akayi,maza Blue shaddah,mata kuma yadi ne mai tsadar gaske pink.
Da mutane suka fara taruwa sai combination É—in yadace da decoration na wajen.
Amaryah Jawaheer aka fara Rakowa itada tawagarta ta tsayah a bakin wajen,sannan sai Jaleelah wacce itama ta tsayah a É—aya bnagaren.
Jabeer ne a tsakiyar su a filin.
Shadda ce a jikinsa kaman ta sauran mazan,saidai kunsan Shigar ango dole zata fita daban da saura..
Suma ga amaren haka take,yadine a jikinsu pink iri É—aya,saidai anyi masa ado da blue a jiki. Sai mayafin dayake kansu shima blue mai adon roses pink.
Dukkansu sun haÉ—u babu da yasarwa.
Mc ne yafara magana ganin bayyanar wanda aka kafa taron dominsu.
“To mashaallah amare da ango su bayyana a wannan fili,yanzu zamu buÆ™aci suje ga wajen zama,saidai zamu buÆ™aci ango ya riÆ™e hannun matayennasa yayi musu jagora”
Idonsa yakai kan Jaleelah wacce take kallonsa da cute fuakarta ta cikin mayafinta mai shara shara wacce tasha kwalliyah,murmushi tayi tareda zura hannayenta a cikin nasa,karon farko kenan dayaji tattausan hannunta a cikin nata,nan da nan kuwa yayi ji wata ni’imah tana jiyartar jikinsa.
A É—aya bangarenma wani hannun yaji yaciga cikin hannun nasa,lallausa kuma mai dauke da hutu.
Juyawa yayi bnagaren itama Jawaheer,wacce ta saka nata idanuwan dara dara a cikin nasa.
A lokaci guda ya runtse hannyen dukka,tareda fara tafiyah suna binsa a hankali har sukayi masauƙi a wajen.
Su Hajiya zeenah wanda suka kallon show É—in sai murmushi suke,duk da taciki na ciki,dan iyah Jawaheer suka so gani dashi bada Jaleelah ba.

Basu daÉ—e da zama ba itama Lubnah tashigo filin da nata kayan irinna su Jawaheer,saidai babu mayafin fuskar irinna amaren.
Bayan zaman an shafe kusan minti goma ana jiran zuwan Bombee,mutane har sun fara magana ƙasa ƙasa,don dama kowa labarinta yakeji bai santa ba. Wai amaryar data kawo kanta gidan miji da safe,koya take oho ba wanda yasani.
Takun takalminta suka jiyo ta shigo wajen,daga yanda suka jiyo takalmin mutum zai san kayane a jikinsa haÉ—aÉ—É—e mai É—aukar rai.
Saidai sabanin haka sai ta bawa mutanen wajen mamaki,Hijabi ne a jikinta pink har ƙasa,sai nikaf ɗin data saka blue,hakama mata biyun da suke binta baya,suma iri ɗayane kayannsu da nata,saidai su nasu nikaf ɗin babu ado a jiki irinnata.
Cike da izzah take bada sautin takalmin dake ƙafarta,bayan tasha baƙar safa ta hannu data ƙafa.
Saida suka rakata ta zauna kafin suma suka zauna a wasu kujeru dake wajen zaman sauran mutane.
Tun daga shigowarsu har zuwa zamansu wajen tsitt yayi baka jin bakin kowa,saboda shigar tasu tabawa kowa mamaki sosai.
Banda Jabeer wanda suka haÉ—a ido ta Bombee ya Jijjiga kai yayi dariyah,dan a iyah saninta yayi na zamansa yasan zatayi yafi hakan ma.
Kuma da alama badan jan hankalin mutane tayi ba,saidan batayi niyyar nuna fuskarta bane ga mutane saboda wani dalili nata.
Abdulmaleek ne yakalli Khaleel tareda cewa.
“Wannan wacce ta shigo yanzu da wasu mata da hijabi itace matar big bro ta biyun?”
“Uhm da alama itace,danni ma bansanta ba”
“Baka santa ba kamar yah,kana garin baka santa ba kuma,taya haka zayyi wu?”
“Haba Abdulmaleek tunda yace maka bai santa ba da alama batason nuna fuskarta ga mutanene,tunda shi ya santa ai shikenan”
“Kai habadai Abdulkareem,duk da rashin son jan maganarka wannan abin jane,zan samu little sis muyi maganar,inason nasan wacece”
“Sai kace dole?”
“Eh dolene kuma kabar wannan zancen,kaima dole dakai zamuje ka ganta taganka”
Ganin Abdulmaleek yasamu maganar sai ja yake,yasa Abdulkareem yin shuru,yayinda a bangare É—aya kuma Khaleel yake tayimusu dariyah.
Haka aka gama taron kowa ya watse,bakin mutane É—auke da maganar matar Jabeer da biyu da irin shigar da tayi.

Ba wuce da amaren sashensu ba,wajen Hajiya zeenah aka kaisu,anan zasu zauna kafin gobe su wuce honeymoon.
Itakuwa Bombee da Maleekah suka taho,sai mita take akan meyasa suka saka nikaf.
Kallonta Bombee tayi bayan ta yage nikaf É—in ta jefar,dan dama duk ya isheta abinka da rashin sabo.
“Wai nikam Maleekah yaushe zaki dunga É—ago abinda yake da ma’anane,kina ganin aikinmu zai tafi daidai idan na bayyana fuskata..
Kaff cikin garin abuja nemana ake ruwa a jallo,ga kuma plan É—in danake na ceton wannan companyn naku,sannan kuma kinga Hajiya zeenah ma zataji daÉ—i ganin ban nuna fuskata ba,duk da nasan abube mawuyaci tacigaba dayin moving É—inta akaina yanzu.
Kinga ni bikinku fah bai dameni ba yanzu ma jinake kaman akan Æ™aya nake sabida zafin kayan jikina,bariga na yage su na huta”.
“Um nace ba anty maryam kafin ki shiga É—aki,kinga Æ™annennaki kuwa su ya Abdul?”
“Eh nagansu mana,ina masu kama dake su biyu,mai zanmusu to daga ganinnansu”
“Ahh babu anty maryam,allah ya barmana ke”
Daga haka maleekah ta zauna suka cigaba da surutu dasu Hilyan.

Tunda suka dawo daga wajen dinner bayan sunje masallaci suka nufi sashen mahaifiyar tasu,abdulkareem ne ya zauna a one seater,yayinda shikuma Abdulmaleek ke zaune a kujerar da madeena take,danne danne take a waya hankalinta kwance,saidai da alama da saurayinta take,dan yanda take jefa murmushi akan fuskarta jefi jefi.
“Ke wato hira kike da chatting koh,wanene”
“Kai yah abdul,yah khaleel ne fah kawai,shima kuma yana tambaya ta abune”
“Ba waninan naga kina murmushi ai,ku yaran yanzu kun baci da hira”
“Kai A.M,menene bacin aciki,yanzu duk wannan ace bazatayi hira ba,to mai zatayi kenan uhm”
“Eh to naji,ke maganace dama a kan matar big bro,meyasa ta rufe fuskarta ne a wajen taron can,kyaune da ita da bata son a ganta sosai,ko kuma big bro ne yake kiahinta da yawa kai”
“Wlh yah Abdul bansani ba,dam nni ma ganina da ita uku ne inaga,saidai ka tambayi mutuniyarka itace mai yini a sashenta”
“Yess yawwa bari my girl tashigo nasan zanji komai daga wajenta ai,dama ku biyunnan ba’a samun abin arziÆ™i daga wajenku ai”
“Hmm kaika fiye surutu kai……”
Yana cikin magaanr ne Hajiyah Zeenah ta shigo sashennata.
“Ahh ku kuma anan kuke zaune,duk rashin son mutanene ko mai,amma shikuma wannan fah dannsan ba rashin son mutanene ya zaunarshi a falona ba kam”
Taƙarisa magana tana kallon Abdulmaleek ɗauke da murmushi akan fuakarta.
“Hmmm mommah wai nan É—in jira yakeyi fah yaji labarin matar bro da tarufe fuska”
Lokaci É—aya Hajiyah Zeenah ta tamke fuska da taji mai abdulkareem yace.
“Mai zayyi mata idan yaga wacece,nifah banason shiga sharri ba shanu tam.
Kuyi harkar gabanku,karma ku damu da saninta tamm”
Daga jin yanda ta kausasa murya akan ta mutum zai gane basonta take ba,dan gashinan a cikin muryar a fili.
Duk falon shuru sukayi da zancen bombee suka kama wani sabo.
Da daddare misalin ƙarfe tara,bombee na zaune tana shan tea taga ƙiran Jabeer a wayarta.
da kaman bazata É—aga ba saikuma ta É—auka,batayi magana ba dan haka shine yayi daga É—aya bangaren.
“Kisameni a falona akwai abinda zan faÉ—a muku”
Daga haka ya kashe wayar,cigaba da kurbar shayinta tayi a hankali saida ta gama kafin ta miƙe ta shiga ɗaki,nan ma ta daɗe kafin ta fito,wandone 3-quater a jikinta sai t-shirt,dukka kayan baƙaƙe,bata saka ɗan kwali akan ta ba iya ribbon ne kawai,ƙafarta kuma ɗauke da slippers.
Tun lokacin daya ƙira bombee ya ƙira sauran,har suka shirya suka fito ita bata taho,in anjima lubnah da Jawaheer su ja tsaki,itakam Jaleelah dama bata santa ba.
Ƙarar buɗe sashenta sukaji,a tare suka kalli inda zata shigo harda uban gayyar wanda yake zaune a Three seater,lubnah na gefensa sai Jawaheer Jaleelah a ɗaya bangaren,dan sune suka fara shigowa,itama Jawaheer saida tayi nata sarautar kafin tazo.
Tun É—azu take hararar su Jaleelah da suke gefen Jabeer a zaune.
Ƙarar slippers ɗinta ne yacika falon,hannunta a cikin wandon ta.
A gaban Jabeer ta tsayah tareda ware masa hannu.
Shuru yayi yana kallonta dan baisan mai take nufi ba.
“Common beb give me a hug”
Tashi yayi tareda bin umarninta ya rungumeta kaman yanda ta buƙata,bakin sa yakai kusan kunnenta tareda cewa.
“Meyasa bakyayimin abu sai kinga idon wasu uhm”
“Ko bakasone to sakeni”
“Ahah ina zanÆ™i wannan jikin mai cikeda taushi da kuma É—umi,inzan dawwama a haka bazan gaji ba,saidai tsiyar inna fita hankalina babu daman a taimakeni saidai a tafi a barni,a kawomin dalilin dazaisa na haÆ™ura,amma bakomai zai kawo Æ™arshen wannan dalilin”
“Sakeni haka ya isheka”
TafaÉ—a tana zame jikinta daga nasa,komawa yayi ya zauna yana yi mata dariyar gefen baki,yayinda ta bishi da harara abinda ya faÉ—a.
Kallon Jaleelah tayi wacce take gefensa a zaune tace.
“Gimbiya tashi ki koma waccar mai É—aya ki zauna koh?”
“Kallon mai kike cewa tayiwa bombee tareda mai da idonta ga Jabeer domin taji mai zaice”
Shuru yayi yarasa mai zaice,shin Jaleelah dake gefensa zai tasa bombee ta zauna ko kuma bombee zaice takoma kujerar gefe,wanda yasan da tayi hakan ya tabbatar saidai ta bar falon.
“Ohh kallonsa kike saboda kinsan yana sonki bazaice ki tashi ba Æ´an mata?,to barikiji wani abu,idan abu mallakina ne ko kuma matsayina,ko bana sonsa a raina babu wanda ya isa yazo yamin shigar kai tsaye ya mallaka,idan takama komai zan iya miÆ™awa domin mallakarsa,dan haka tashi ki koma inda É—aya amaryar take ki bani wajena tun kafin raina ya baci”
Jabeer ne ya buÉ—i baki tareda cewa.
“Jaleelah tashi ki koma wajen Jawaheer ki zauna kinji,nan ba wajenki bane wajen tane a Æ™a’ida”
“Ni banga abin tashin hankali a wajen zama ba,umarninka shine abin bina,tunda ka buÆ™aci na bata wajen babu matsala”
Cikin sanyin jiki ta tashi a wajen takoma kusada Jawaheer.
Murmushin jin daÉ—in yanda ta karbi maganarsa yayi,dan dama hakan yakeso.
Jawabi ya fara ma su na zaman lafiya,inda ya zartar zai dunga yin kwana É—aya a É—akin kowacce daga ya dawo a tafiyar dazasuyi.
Sannan ya sanar dasu wata É—aya zayyi ya dawo.
Bayan yagama jawabin babu wanda ta yi magana,hakan na nuna sun yarda da hakan kenan.
Daga nan kowa yakama hanyar sashensa sai goben.kowa fuska a murtuƙe,musamman ma lubnah da Jawaheer.
Washagari da safe aka shirya tafiyar su Jaleelah honeymoon tareda Jawaheer Duk da saida akayi dambarwa da Jawaheer akan tafiyarsu da wata matarsa.
Tunda safe ƴan aikinta suka fara ƙoƙarin shiryata,wanda wannan ne kwananta ɗaya a sashennata.
Yasha ado kam na alatun duniya na gani na faÉ—a,duk side din babu sashen dayakai nata kyau saboda bajintar da hajiya rabi ta nuna a barin dukiya a bikin Æ´ar tata.
Ruwan wanka masu aiki suka haÉ—a mata,su uku ne hajiya rabi ta haÉ—ata dasu.
Kafinta fito sun shirya mata breakfast da kuma kayan sakawa,ta haÉ—e rai tashirya ta fito zuwa sashen Hajiyah Zeenah inda zasuyi mata sallama su tafi.
Tashiga falon kenan hajiya Zeenah tafito daga É—akinta,Jaleelah kuma na zaune a kujera tana jiran Hajiya.
Tana fitowa kallo É—aya ta wurgawa Jaleelah daga nan kuma tanufi Jawaheer tana ware mata hannu,rungumeta tayi tamkar ba surukarta ba,
“Yakk Daughter kintashi lfy”
“Yeah kalau natashi,yah Jabeer É—in ya fito kuwa”
“Ahah baizo ba inaga yana sashen sa tukunna”
Madeenah ce tashigo falon ,bata kalli Jawaheer ba wacce suke magana da Hajiyah Zeenah,wajen Jaleelah ta nufa wacce ke zaune tamkar gunki.
“Anty Jaleelah ya kwanan baÆ™unta,ko zakizo muje ciki kai kafin yah Jabeer É—in yazo?”
“Lfy kalau Madeenah,uhm to shikenan babu matsala hakan”
“Ke Madeenah baki ganin Jawaheer ne wacce a yanzu take matsayin matar yayanki,bazaki gaisheta ba”
“Uhm mommah wannan ma ai matar yayannawa ce,inaga ai babu banbanci duk wacce na kulama a ciki É—ayane”
Taƙarisa maganar tana bankawa Jawaheer harara,dan dama basa ga maciji da ita,haka lubnah ma,bombee kuwa basu taba haɗuwa ba face to face,shiyasa ta zabi Jaleelah a matsayin favorite ɗinta,yayinda iyakuma maleekah duk cikin amaren babu wacce tayi mata,tana jin ana zancen tafiyar ma bata fito ba,sai anjima tayi sashen Bombee acan zata yini.

Hannunsa ya saƙala ta bayanta zuwa cikinta,tana tsaye a jikin table na dining tana gogewa.
“Nizan tafi yawon cin amarci ta amarena”
“Na riÆ™eka dama,nace kada katafi?”
Sake kwantar da kansa yasakeyi a gadon bayanta tareda yin magana,wanda hakan yakasata ajiye duster taja gwauron numfashi.
“Mr.groom wannan salon kuma namenene,ko so kake na fola maka na hanaka tafiya,shiyasa kakeyin haka”
“Bahaka bane zanyi missing É—inki ne”
“Hhhhhh missing shin kana tunanin yakamata kayi amfani da wannan kalmar,dan Allah kaje tafiyarka suna jiranka,inna gama aikin gidannan inada abinyi sosai”
“Wai kina nufin bazakiyi kewata ba,bazakiji babu daÉ—i ba idan natafi?”
“Saboda kai iska ce ko ruwa,da babu su babu rayuwa,babu É—aya Æ™anwar biyu,barina je ana Æ™irana a waya,Allah ya bada sa’ar shaÆ™atawa”
Daga haka tacire jikinta daga nasa tayi É—akinta,ta barshi a wajen yana kallon hanyar data bi,haka kawai ya tsinci kansa da jin rashin daÉ—in tafiyar da zayyi ya barta,jiyake inama tace zataje su tafi,yasan hakan bazai taba yiyuwa ba.

Kasancewar private jet ne yasa kawai tafiya ce babu wani tsaiko a ciki.
Dubai suka nufah,inada Jaleelah ta zaba,taganan zasu nufi singapore inda itakuma Jawaheer takeso.
Jaleelah ce ta kalli Jawaheer a cikin jirgin tareda yimata magana,ganin Jabeer ya shiga banÉ—aki.
“Uhm nikuwa kaman kece Cat lady bah?”
Zaro ido Jawaheer tayi tareda ƙwaruwa a abinda ta zuqa,waiwayawa tayi ganin babu kowa ya kusa kafin tace.
“How on earth kika sani?”
“Lahh ba wani abin damuwa bane,naga baki daÉ—e da buÉ—e acct É—in bama”
“Shine nace taya kika san nice cat lady a ciki,bayan bamu taba haÉ—uwa dake ba bare muyi wannan maganar,saidai idan kema…….”
“Ehh haka ne nima,Kinsanni a wajen saboda baki san nice bane,zan faÉ—amiki user É—ina saboda wani dalili.
Nice black slender a wajen,hannunta ta buÉ—e ta nunawa Jawaheer wani tatoo a hannunta na hagun.
Zaro idon da Jawaheer tayi a yanzu har yafi na É—azu ma.
“Kina nufin kice dama kece wannan babbar…….”
Bata gama maganar ba Jabeer yadawo,dan haka suka sanja topic ta hanyar magana akan wani abun taban.

 

_*SADI-SAKHNA CEH*_

____****🖤🖤****_____

🖤 *BAƘAR AYAH* 🖤

🖤 _BOOK 2_ 🖤

 

Labari/Rubutawa:SADI-SAKHNA
[ _Ƴar mutan Jama’are_ ]

 

Anshiga Sashen na KuÉ—i,in kasan baka biya ba karka karantamin littafi,Ka É—au hakkina bisa kanka tamm!!!

Makarantan Arewabook ku danna zai kaiku cikin littafin

https://arewabooks.com/book?id=62d939a19904b02ce6fa2b31

Masu karatu ta whatsapp kuwa,zaku biyah Naira 300 kacal ne.

3131951977
Auwal Sadiya
First bank
Shaida tanan
09035784150

Masu saka katin wayah zaku turo katin 300 na MTN tanan layin..
09035784150
No VTU

Mutanen niger kuma zaku biyah kuÉ—inku tanan
300f
+227 97 21 16 15
Shaida tanan
09035784150

______________****_______________

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button