Sponsored Links
Arubuce Ta Ke Hausa NovelHausa Novels

Arubuce Ta Ke 4

Sponsored Links

*Widad*

Alhaji salim musayyib mai fata shine cikakken sunan,mazaunin maiduguri da wanda aka haifa a can,ya taso ya girma ya kuma yi gwagwarmayar karatunsa dukka acan din,nau’in jinsin nan da mutane ke kira da suna SHUWA_ARAB,saboda asalin iyayensu da kuma kakanninsu dukka ba’a maiduguri aka haifesu ba,ba kuma anan sukayi rayuwarsu ba,rayuwar da sukayi a maidugurin duka duka ‘yar taqaitacciya ce,sanadin kasuwanci,asalin tushensu sun fito ne daga qasar mali zuwa yemen,kuma har yanzu danginsa da tushensa suna can gaba daya ko nace mafi yawa daga cikinsu,iyali ga mahaifinsa musayyib suke ta yado a nan,da kuma nashi ahalin shima daya tara.

Matan aurensa biyu dukka ‘yan asalin qasarsa wadanda suka hada masa tarin zuri’a da kuma yara masu yawa,dansa na farko da matarsa ta fari wadda ta kasance balarabiyar qasar yemen shine mahmud,wanda yake mahaifi ne ga widad data kasance ruwa biyu,balarabiyar mali kuma bafulatanar usul daga katsina ta gefen mahaifiya,wannan shi ya taru ya bata wani irin sassanyan kyau daya banbanta da kyawun dukka cousin dinta da kuma sauran ‘yan uwanta,domin ita daya mahaifiyarta ta haifa ta barta a gidan,sai tarin ‘yan uba da kuma cousins da take dasu.

Yanayi na rayuwa da kuma kasuwanci ya maido alhaji salim qasar kano da zama,ya fara tara iyalinsa shima,bayan ya aurar da mahmud arziqinsa ya qara ninkuwa fiye dana da,wanann ya siya manya manyan filaye ya hadesu waje guda,ya kuma yanki wani sashe na gidan ya fara ginin matsugunnin da zai zauna da matansa da kuma yaransa,bayan ya kammala suna gab da tarewa matarsa ta biyu ta rasu,sai mahaifiyar mahmud ce kawai Allah ya qaddara mata zama a gidan.

Mahmud ne kawai ke rayuwa a wajen gidan,girman gidan ya sanya duk yaronsa daya tashi yin aure,za’a fitar masa da tsarin ginin da zai dace da gidan a gina masa ya tare a ciki,wannan yasa sannu a hankali gidan ya zama babban family house dake dauke da sassa sassa guda biyar,kuma kowanne sashe cike yake da albarkar zuri’a wadata da kuma kwanciyar hankali.

Widad ta kasance ta musamman a wajen ummu,saboda ummun ta bude idanu ta gani a matsayin uwa kuma mahaifiya a wajenta,don itace ta raineta tun tana tsumman goyonta har kawo yanzu da shekarunta suke goma sha daya da watanni a duniya.

Soyayyar da ummun itama kewa widad din ta banbamta data kowa,saboda itama tana jinta da matsayi biyu ne a wajenta,d’iya kuma jika,ta manta da raino sanda ta amshi widad da nufin rainonta,don a sannan ta aurar da autarta ma anty halima tuni,kasancewar su din basa zurfafawa karatun boko,kina gama primary ma kika samu miji to tabbas alhaji salim zai bada aurenki ne, matuqar ya yarda da addinin mutum da kuma mutuncinsa,ruwan miji ya barki kici gaba,ruwansa yace a’ah.

Ko kadan rashin uwa bai wani taba widad ba,saboda ta samu dukka kulawa da ‘ya ke samu ga mahaifiyarta daga wajen ummu.

Mahfood d’a ne ga baaba maisara,wanda suke ‘ya’yan wa da ‘ya’yan qani da mahaifin widad,tun kafin ta kawo haka yake nuna yana da interest a kanta,amma ko daya widad din taqi sake masa balle ya samu fuskar da ko hira ta zauna tayi dashi,saboda ita din wata irin mutum ce,tana da wahalar sabo,hakanan idan kanason ganin kazar kazar dinta da hirarta to cikin gidansu ne,musamman sassan ummu ko na anty madina,indai akace maka baqon guri ne zaka tsammaci cikakkiyar magana ma bata iya ta ba.

Abu na biyu tana da masifar tsoron maza,saboda kullum hudubar ummu shine,idan ta sake ta yarda ko hannunta namiji ya kama zatayi ciki,idan kuma ta samu ciki mutuwa zatayi,wannan yasa sam sam bata yarda ko inuwa su hada,bama shi ba,dukka samarin gidan da suke a matsayin yayye a wajenta haka dabi’ar ta take.

_wannan kenan_

*Bayan shekara uku*

Tun daga daren juma’ar da ya kama gobe sallah gaba daya yanayin gari ya canza daga yanayin azumi zuwa yanayin daren sallah,ko ta ina al’ummar musulmi sai hada hada ake,tituna zuwa layuka,gidajen kitso qunshi zuwa shagunan masu dinki ko ina cike yake danqam da jama’a kamar rana.

Haka ce ta kasance gidan alhaji salim musayyib,babban gidan dake dauke da family masu yawa,a dabi’ar gidan babu tsawwalawa,koda salla ce kowanne sashe yana yin kalar girkin da mace ko matan sashen suka tsara yi,saboda kowanne part akwai store da kuma kitchen din su tare da me aikinsu,saidai idan an gama ranar sallah dukka suna zubawa abincin mai dan dama su aike sashen surukarsu hajiya ummu,duk da ita dinma ba zama take ba, takanyi abinci har kusan kala biyu,sabida karbar baquncin jikokinta dama surukanta matan ‘ya’yanta maza guda biyar da Allah ya bata,su da ‘ya’yansu da kuma ‘ya’yan wajen diyarta halimatu,hakanan su kansu jikokin dake cikin gidan suma kusan a nan suke zuwa su karba nata,sukance yafi dadi.

Dai dai lokacin da sassan anty madina yake a cike da yara yaran matan gidan,wanda ake ta faman saka musu qunshin salla daga mai qunshin da ummu da kanta ke daukowa ayi musu,sannan kuma ga me kitso itama tanata kitse musu kansu duk da baiwar suma da yalwar gashi da suke dashi tubarkalla,babban falon da anty madinan ta ware musu saboda irin wannan hidimar a kacame yake.

Daga gefe daya widad ce zaune,tsahon shekaru ukun data qara kyawunta ya sake bayyana muraran,hakanan alamun girma sun fara bayyanar mata,duk da cewa har yanzu gabunta sakarci da kuma wautarta tana nan,cikakkiyar GOYON KAKA,Qunshinta yafi na kowa jan lokaci,saboda ummun tace na musamman za’ayi mata kamar yadda aka saba,masu zumbura baki nayi masu qorafi nayi,to amma kusan idan da sabo an riga an saba,haka sukayi suka gama suka kuma haqura.

“Aafiya ciremin lallen nan” widad ta fada tana yamutsa fuska saboda jimawar da tayi a zaune

“ke kam kin huta,sauranki kitso” afiya ta fada tana matsowa hadi da fara sabule ledar da aka rufa hannun,harara widad ta jefa mata

“Tabdijan,wa za’ayi wa kitson?,Allah ya kiyaye” ta fada tana bata fuska,kitso babban abokin gabarta ne,sam bata qaunarsa,tun daga quruciyarta kawo yau tsaf zata iya irga adadin sau nawa aka taba yi mata kitso,mutane kance saboda tana da suma me kyau ne da tsaho,kusan sumarta ta zarta dukka ta yaran gidan,tamkar zabarta akayi,hakan kuma baya rasa nasaba da gado da tayi ta wajen uwa da uba,don idan ta ware sumarta tana iya saukar mata har tsakiyar gadon bayanta.

Dariya afiya ta saki tana ci gaba da tsokanarta

“Nikam naga lokacin da zaki daina gudun kitso”

“Babu rana”ta amsa mata tana Allah Allah a gama cire mata ta tsallake ta gudu ma daga falon.

“Tubarkalla ma sha Allah ‘yammatan ummu,lallai dole mu caji ‘yan samari kudi,irin wannan kyau haka?” Anty madina dake shigowa dauke da babban farantin data yanka musu fruit ta fada tana murmushi,cikin yanayi na nuna jin kunya abinda ke nuni da soma girman widad dim ta boye fuskarta tana dariya

“Bafa wasu samari anty Allah”

“Aah fada kike wallahi,kowa fa ya sani” wuf tayi ta tashi saboda yadda sauran ‘yan uwanta ke juyowa suna kallonta,wasunsu suna mata dariya ne da gaske har zuciyarsu,yayin da wasunsu kallon hassada qyashi da baqinciki ne suke.jifanta dashi,abu guda daya da bai taba dadata da qasa ba,itakam indai zata jita wajen ummunta to komai lafiya lau,takan manta da dukka wasu qananun abubuwa dake tasowa ko kuma faruwa cikin gidan.

“Ina zaki sauranki kitso ai” anty madina ta fada,sai ta tsaya tana duban anty madina,fuskarta dauke da zallar quruciya ta narke fuska,abinda ke nuna gab take da fara tara hawaye

“Don Allah anty a barshi,nayi bayan sallah” haba ta kama tana kallonta

“Anya widad?,ke wannan sumar bata damunki ne?” Dariyar yadda anty madinan ta saki baki ya kamata

“Ai shikenan,ki biya ta kitchen,ki cewa yalwa ta baki abincin ki kaiwa ma’aruf” sunan da anty madinan ta ambata sai taji kamar tace mata ba zata aiken ba,amma anty madina tafi gaban haka a wajensu,dukkaninsu suna mata kallon babbar yaya, kasancewar dukka manyan yayyansu mata suna gidajen aurensu,a kaf surukan gidan kuma ita dince mai qananun shekarun da suke iya sakewa suke komai tare da ita,itama kuma ta riqesu tamkar qannen nata.

Ba’a son ranta ba ta biya kitchen din ta dauki abincin,ta fito tana dariyar yadda yalwa keta koda kyan qunshin nata,tsakaninta da dukka ma’aikatan gidan qauna ce da soyayya,koda kuwa ba masu aikin sassan nasu ba,idan ka ture wautarta da quruciya da tabara ta goyon kaka,ita din yarinya ce mai matuqar girmama wanda ya girmeta,zaiyi wuya ka sameta da laifin rashin kunya,kai koda laifi akayi cikin gidan da wahala ka samu sunanta a ciki,idan kaji an ambaci sunanta to wata wautar aka tafka,ko kuma ta taba sakalcin nata data saba,wannan ya sanya ummu bata ragawa duk wanda ya tabata,takan ce

“Nasa halin kayata fes,duk wanda yace tayi wani abu idan ma sharri ne zan gane ato,nasan me zata aikata,hakanan kuma nasan abinda ba zata aikata ba”.

Har ta isa qofar dakunansu taji hayaniyar mutane a dakin nasa,da alama baqi yayi abokansa,tsaki taja,ta koma da baya cikin takun da basu fi goma ba,ta tsaya dab da motarsa.

Sai data qarewa motar kallo sannan ta matsa kusa da boot din motar ta dora masa abincin a nan,ta kama gabanta hankali kwance ta wuce sassan ummu.

Saidai tana sallama a sassan taji nadamar dawowa sassan ta kamata,babu wanda ya gaya mata yazo gidan,da babu abinda zai sanyata dawowa yanzu,sun riga da sun ganta gaba dayansu,harda na’eema diyar anty halimatu da tazo gidan sallah,saboda haka duk wata dama ta komawa ta qwace mata babu ita,sai taci gaba da takawa cikin falon tana tsuke fuska,hadi da sake gayyato bacin rai saman fuskarta,uwa uba dama ga yunwa dake cin hanjinta,taqi abincin wajen anty madina saboda ba cimarta ta dafa ba,tace sai ta dawo wajen ummunta.

*_RIGIJI GABJI!_*πŸ”₯πŸ”₯

*_WANI KAYA SAI AMALE_*πŸ”₯πŸ”₯πŸ”₯

*FITATTUN ZAFAFAN DA BABU NA BIYUNSU*πŸ”₯πŸ”₯

*JERIN GWANON LITATTAFAI ABOKAN TAFIYAR JUNA MASU MABANBANTAN LABARAI DA FASAHA*

*_’YAN BIYAR DIN NAN NE FA_*

*_SARAKAN LABARUN_*

*NISHADI*
*CAKWAKIYA*
*GWAGWARMAYA*
*BARKWANCI*
*TSANTSAR DARASIN RAYUWA*

*TARE DA*

*ZAZZAFAN SALO NA SOYAYYA MAI RIKITA TUNANI DA TSUNDUMA MAI KARATU CIKIN TAFKIN SHAUQI*

*SUN SAKE SHIRYAWA TSAF,DAUKE DA WANI TARAGO MAI CIKE DA LABARAI MASU ZAZZAFAN ZAFI!!!*

*KIN SHIRYA MADAM?*

*MAZA ANTAYA NAKI KUDADEN KIBI SAHUN AYARIN MATA MASU AJI TA HANYAR BIYAN KUDIN NAKI KARATUN WADAN NAN LITTAFAI KAMAR HAKA*

*DAUD’AR GORA* Billynabdul

*KI KULANI* Missxoxo

*IDON NERA* Mamuhghee

*RUMBUN K’AYA* hafsat rano

*A RUBUCE TAKE* Huguma

*ZAKI IYA BIYA KAI TSAYE TA WANNAN ACCOUNT DIN*

0022419171
Maryam
Access bank

Saiki tura shaidar biyanki ta wannan number

09033181070

*MASU TURA KATIN MTN KO VTU KUMA ZASU TURA WA WANNAN NUMBER TARE DA SHAIDAR BIYANSU*

09166221261

*Yan nijer πŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺkuma zasu tuntubi wannan number*

+227 90 16 59 91

*Muna godiya da ci gaba da zabin zafafa biyar a koda yaushe*πŸ™πŸΎπŸ™πŸΎ*H U G U M A*
*_A RUBUCE TAKE_*
(K’addarata)

Page 05

*MAAB LUXURY HOME*

*_idan kaji gangami akwai labari_*
*_SABUWAR DUNIYA CE_*
*ALFAHARIN UWAR GIDA*
*FARINCIKIN AMARYA*
*MAIDA TSOHON GIDA SABO*
*DUNIYAR QYALE QYALE*
*KAYA NA ALFAHARI DA TAQAMA*

*_Ba iya kyawun idanu suka tsaya ba,harma da ingancinsu da kuma qwarkonsu,ka dade kana mora kana kece tsara a tsakanin tsararraku da sauran mutane_*

*nasan zaku tambaya ina ne nan?*

*MAAB LUXURY HOME*

😊 *Kai daga jin sunan ma babu tambaya*

*_duniyar qawata muku gidajenku ku ganku kamar a wata nahiya ko wata duniyar_*

*Suna kawo kayan kitchen rankatakaf manya da qananu*

*Kayan gado dana parlor*

*Kai…suna kawo kowanne nau’in kayan ado na cikin gida*

*Karkiyi qasa a gwiwa kuma kada kiyi sake ma dafe,maza garzaya ki nemesu a*

_adress dinsu dake No 22 Ahmadu bello way,kano state_

*Ko kuma kuyi order din kayanku kuna daga gida ta shafinsu na instagram*

@maabluxuryhome

*Facebook*
@maabluxuryhome

*Ko ku nemesu ta lambar wayarsu kamar haka*
08034631010

*Kyau inganci da rahusa shine takenmu*😊😊🀝🀝🀝🀝
____________________________

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button