Sponsored Links
Amatulmaleek Hausa NovelHausa Novels

Amatulmaleek 24

Sponsored Links

YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

 

24
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs๐Ÿ’ฏ๐Ÿ”ฅ๐Ÿ‘
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku๐Ÿ’ฏ๐Ÿ‘*

MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI’IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER

08142800199
07068558096

 

************
Bayan tafiyar maamah daga Husnah har Dad dinta suna shiga damuwa da rashin mafita ta Dan lokaci sbd magana ce a Bude,
Idan har ba Naufal Amatu ta aura ba maamah bazata bisu su koma ba,
Sai Idan Faisal zaa bawa shine zaita Takoma Wanda shikuma bazai iya daurawa Faisal aure da AmatulMaleek ba sbd tasa ‘yar da bazai iya rasawa ba,
Hakama idan maamah Bata komaba still yarsa da gidansa suna cikin hatsari da tsaka me wuya.

Husnah data rarrafo gabansa ya zubawa idanuwansa Yana zurfafa a tinani..

“Dad Dan Allah Kada kabari a daurawa Amatu aure da duka Yan kauyen Nan,
Dad zan shiga Wani hali idan Hakan tafaru,
Dad mum dina idan da zata Tashi ayau itama zatace Karka bari a lalatawa maamah rayuwar Amatu,
Dad kayimun alqawarin komawa da maamah..

Shiru tayi tanason furta abinda yake bakinta na son fadan a daurawa Amatun aure da Haydar sbd a wanna lokacin ita kowama zaa daurawa Amatun a daura Amma Banda Faisal ciki kuwa harda Dad dinma Koda zai aura Amatun yafi mata a maimakon Faisal ya aureta Dan haka ta zabi a daura da Haydar Dan kawai kada a daura da Faisal hakama sbd maamah ta koma dasu Dan haka ta sake rikicewa Dad din tareda shiga mawuyacin halinda ya sake Sakasa halin damuwa akan yanayinta da kalaman maamah harma da duba tashin hankalin da duk aketa yi a wajen har lokacin.

Abdulhameed yasa yaja Husnah yayi cikin gidan da ita aka barsa a gurin shi Daya Yana jiyo yanda su kawu ke rantsuwa kan rantsuwar Babu inda Asmau zataje da AmatulMaleek aure zasu daura mata tayi gidan mijinta ayau din idan yaso Asmaun ta koma rayuwarta ta daula dasuka sabo.

Faisal ma acikin mawuyacin halin rashin sanin mezai faru yake,
Ga Abdulhameed ma nasa hankalin a tashe yake idanuwansa sunyi jajir musamman gano yanda AmatulMaleek idanuwanta sukai jajir batareda hawaye sun gangaro mata ba Amma yasan a zuciyarta tafi kowa shiga mummunan hali akan duka wannan tashin hankalin zaune kawai take Amma hannuwanta rawa sukeyi Dan haka ta rufesu cikin doguwar hijabin jikinta kowane lokaci zuciyarta zata iya bugawa.

Husnah ma gaba Daya a tsinke take cikin tsoro da tashin hankalin hukuncin da Dad dinta zai Yanke,

Maamah ma zaune kawai take Amma hannuwanta Dake hade da juna rawa sukeyi kaman yanda zuciyarta ke rawa,

Tsakanin waje da ciki Abdul yayi zuwa yakai so goma yakasa zama Shima a tsinken yake kaman yanda Suma a wajen duk sai rarraba idanuwa sukeyi Kowa a matse yake suna jiran fitowan ASH da hukuncin Daya Yanke Dan yanzu sun yarda sai abinda yace din zaayi Amma dai Banda aurawa Naufal sbd tini hayaniya tayi tsanani tsakaninsu da iyayen Naufal din dasuka kasa danne irin diban albarka dasu kawu suka ringawa Naufal Daya rugusa rayuwar Amatun.

Faisal ma a tsinken yake yakoma abin tausayi a cikin qanqanin lokaci sbd shi baida Wanda zai tsaya masa,
Su kawu sun tsayawa yayansu,
Iyayen Naufal sun tsaya masa hakama Amatu ga ASH TALBA zai tsaya mata itada mahaifiyarta
Shi kuwa Abdulhameed kawai yake tareda shi sedai Abdulhameed din baida iKon basa auren yayar tasa ko Hana masa.

Su Auwalu da uzaifa kusan su hudu kowannensu yaje yayo wanka ya shiryo cikin shaddodinsu na Roba sun hallaro sbd jiran Wanda Rabon tsaleliyar mace zai fado kansa yau ba sai gobe ba su ragargaji amarci.

Lokaci me tsayi ASH TALBA Bai fitoba Saida su kawu suka ringa zuwa dubawa Amma Babu me iya magana sbd Babu abinda yake da sauke a tareda shi,
Qarshe ma securities dinsa ne suka zagaye kofar gidan dole kowa ya zauna ya nutsu Jiransa su kawu ma ganin sukeyi tinda yazo gwara a daura yananan tinda tamkar Uba yake ga ‘yayan Asmau.

Samarin hudu harda Faisal Babu Wanda kudinsa na sadaki basa jikinsa hakama cikin iyayen Naufal Uncle dinsa Daya yanke a ransa idan fitinar bata samu mafita ba zai biya sadakin Amatun ya aureta kawai Dan kuwa yasan duk macen da Naufal zai kutsa yaso yiwa fyade ta cika mace hakama duba da Barr Faisal Daya mace akanta duk kyau da kudinsa da gatansa to tabbasa takai,
Hakama ya Kalli Abdulhameed da kyau dayake uwa daya Uba Daya da ita dole acikin kyanta ita datake mace Abdul Bai kamota ba.

Kiran sallan Azahar na karfe biyu akai sai alokacin ASH yafito kowannensu idanuwansa akansa kaman zasu fado qasa suna jiran abinda zai fada.

Cikin nutsuwa da kamewansa Kai tsaye ya sanar dasu suyi sallah tukuna.

Ba musu kowa ya nufi Neman butar alwala sbd Allah yagani kowa dai a matse yake da ayi me yiyuwa a gama.

Shi kawu abinda zaayi a gama yakeso ASH din idan zai tafi ya basa abinda zai basa,
Suma sauran kowa da abinda ya matsu yakai garesa a lamarin.

A cikin gida ma kusan kowa jiran yanda zata kasance akeyi,
Iyayensu uzaifa murna sukeyi yayinda matansu Auwalu suke cikin baqin ciki da takaici tareda adduar Allah yasa a aurawa Wanda zai kwashi Amatun su koma inda ma suka fito Dan su zamanta a kauyenma barazana ce garesu fa mazansu da Allah ya jarabta da Sonta Dan kyanta da rayuwarta ta daban.

Daga mota Babban security dinsa ya kawo masa babbar roban bottle water sbd Jameel Baya Nan da shine me kulawa da komai na ASH din.

Karban ruwan yayi yai alwala securities dinsa duk suna zagaye da gurin wasu a bayansa harya gama.

Wata sabuwar tabarmar aka dauka aka Kai masallacin kauyen da Babu shimfidar kirki a cikinsa aka shimfida ta aciki
Daddaiku mutanen Dake masallacin sunata kallan ASH TALBA Wanda yake Dan bawa wasu daga cikinsu hannu suka gaisa,
Liman da me gari tini suka baro inda suke sukazo suna Dan ranqwafawa gurin gaishesa cikeda girmamawa ya miqa musu hannuwansa da kaman saika wanke hannu da sabulu zaka taba sbd tsaftarsa da hasken fatarsa me kyau.

Sallah aka tayar wadda kusan kowa yau adduarsa ta musamman ce ga Allah Dan kowa da abinda yakeso ga ASH TALBA da duk gurin acike yake da kwarjinsa da qamshinsa da Babu Inda Bai cike ba acikin masallacin kowa sai Bude hanci yakeyi Yana Jan qamshin.

Koda aka gama sallar Babu Wanda ya tashi Dan Babu me niyar fita sai sai sungama kallan ASH TALBA
Su kuwa ahalin Sanda Fulde babu me niyar fita yabarwa Wani ya samu damar cusa kansa a gun ASH din Dan abasa auren Dan haka kowa ya kasa ya tsare.

Kawu bello da kawu ashiru Dake gefen Daman ASH ya juyo ahankali ya kalla cikin nutsuwa da kamewansa data gama cika musu idanuwa ya Bude Baki da kalamansa masu nutsuwa da girma yace

“Auren AmatulMaleek zaa daura yanzu kamar yanda kukai rantsuwar daurawa ayau amatsayinku na iyayenta idan Kun Bada dama da duk Wanda na zaba….

Bakin kawu bello na rawa yayi saurin cewa

“Tabbas mun amince mun bawa duk Wanda kazaba aurenta a daura a yanzu.

Kawu ashiru ma Dayake Jin qamshin kudi aduk lokacinda ASH ya motsa shi kudi kawai yake hangowa da Jin qamshi yace

“Tabbas mun amince har Naufal dinma idan kace shi kakeso mun basa Allah ya Bada zaman lfy da hakuri,zasu daidaita ne daga baya idan sungama rigingimunsu.”

Su Auwalu kowa kasa kunne yayi zuciyoyinsu na tsalle,
Faisal kuwa rawa hannuwansa keyi zuciyarsa na bugawa hakama iyayen Naufal.

Boyayyan numfashi me dumi ya sauke batareda yace komaiba ya Ciro wayarsa yayi rubuto ya ajiye.

Minti Daya Bata gama cikewaba saiga AK babban security dinsa Ya shigo da sauri ya wuto har inda ASH din yake ya ajiye masa daurin kudin dasuka Saka kowa hadiye yawu a gurin suna kallan kudin.

Auwalu take yaji shi in kudin zaa bawa Wanda zai hakura to ya hakura ya janye yabarwa ‘yan wahala.

Sadi ma Jin yayi yafison kudin akan Amatun,
Uzaifa ne yafara wasi wasin daurin kudin ko Amatu.

Kallansu ASH yayi Dayan bayan da idanuwansa masu kyau da tsari Yana karantar kowannensu da a Fili son kudin ya take Wani maganar auren Amatun batareda sun fada ba.

Wani numfashin ya sake saukewa me zafi a boye tareda rintse idanuwansa a karo na farko dataji krjinsa yayi nauyi da abinda yake Shirin faruwa dashi din ayau Wanda baitaba tinani ko kawo Hakan akansa ba Amma baida zabi ko mafita bayan wannan din sbd kashe matsaloli da fitintinu harna da bawa maamah Mafi girman adalci da halaccin data buqata na tsawon shekarun datai tana kulawa da iyalinsa da Gidansa bisa Amanar da Babu Wanda zai iya masa Hakan.

Kudin ya Kai hannunsa Akai ya dauka ya miqawa kawu bello cikin nutsuwa da Hana kowa fahimtar abinda yake ransa ya Bude Baki Kai tsaye yace

“Ga sadakin AmatulMaleek dinnan a daura mata aure a yanzu”

Hannu biyu kawu yasaka ya karba hannuwan na rawa sosai harsai da kawu ashiru ya Saka hannu ya kama masa sbd kada kudin su zube qasa yanda hannuwansa ke rawa.

Tsit masallacin ya dauka aka rasa Wanda zai motsa bare magana
Su kawu kuwa Babu abinda suka tsaya jiki na rawa suka kalli su me gari da liman suna cewa

Bismillah ranka ya Dade megari da liman ayi haramar daura auren,batareda sun tambaya waye mijin ba.

Sauran jamaar masallacin tini suka fita suka farfadowa mutane aure zaa daura ba Bata lokaci jamaa suka ringa dirarowa masallacin take ya cika anata rarraba idon daurin auren wasu Kuwa ASH TALBA kawai suka ringa zuwa Gani Wanda duk Taron Jamaar gurin har lokacin tirarensa ya doke duka qarfin warin zafin dayake tashi duk da securities sunso Hana kowa shiga masallacin Amma ASH ya Bada damar duk Wanda yazo abarsa ya shiga.

Sbd son zuciya Dana Rai take aka fara kokarin daura auren da Basu San waye mijin ba Saida akazo ambatar sunan mijin Kawu bello ya Fadi sunan da ya Saka duka masallacin daukan shiru tareda shiga mamaki da firgici lokaci daya.

Shi kansa madaurin auren rudewa yaso yi dole aka nutsu aka daura auren da sai bayan da aka daura me sanarwa cikin babban sauti da farin ciki ya sanar da “AN DAURA AUREN MAI GIRMA ASHRAF MUH’D TALBA da ABEEDA AMATULMALEEK SANDA FULDE AKAN SADAKI NAIRA DUBU DARI BIYAR”
##MAMUH#
for more pages join vip or follow me at mamuhgee arewabooks

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at๐Ÿ‘‡
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button