Sponsored Links
Hausa Novels

Cinikin Rai Book 2

Sponsored Links

[9/10, 9:1
7 PM] Yan Mata: Contract Marriage volume 1

For You Queen Bee🌹
“Relax!” Ya furta a hankali, har lokacin hankalinshi baki daya yana kan laptop. Yana aiki, kamar bai san yadda ta girgiza ba. “Ka ce me?” Ta tambaye shi, in sound tone. “How you endure like this ko? Lalacewar bata kai ki auri tsoho ba ko? To gaya min taya zaki biya ni kudina? Ko so kike mu ajiye zancen aure mu shimfida al’amarin ta wancan side ɗin.” Ya mata wani irin shegen kallon da sai cikinta ya bada wani irin sound na “kulu-kulu!” Ya wani d’age mata gira.
“Wallahi ba zan auri tsoho ba, ina laifin ka ɗauke ni aikin ciyar da kartin mazan da suke kewaye da kai. Tir ni ba yar iska ba ce da zan bada kaina wa tsoho irinka.” Tayi maganar in childish. Kallon yadda take mishi wani irin kallo tare da rufe kirjinta da hannu bibbiyu.
Dariya ne ya subuce mishi, madadin yayi dariyar sai ya tsinci kanshi da wani shegen smirks. “Ok ke yanzu ba auren ne matsalar ba ko? Tsoho me furfura irina ne baki so?”
“Haba Uncle Malik, ko Uncle Elbashir ka gayawa ba zai baka sufot ba, balle wani can a waje, kasan me za a kira ka?”
Zuba mata idanu yayi, tare da yin kwal-kwal da shi, kamar yaro karami.
“Arrrrrrsh ka daina irin wannan kalar tausayin kyau yake maka, ni kuma haushi kake ba ni.”
“Ok me kike so nayi?” Ya tambaye ta domin ya fahimce ta, so take ta shashsntar da zancen auren ne. “Kaga mu bar maganar nan, a fara biyan mutane kudin su!”
” Ba zai yiwu ba!” Ya faɗa kai tsaye, yana me tsura mata idanu. Wani murgud’a baki tayi tana faɗin. “Yo ko namar jikina aka yankan dai zata haura miliyan dari huɗu. ”
“Wayo zaki min?”
“Aahaaaaa!” Ta saka hannu a bakinta, tana faɗin. “Na shiga uku, an fasa aurena wani munafinki ne ya gaya maka zan maka wayo, Ni me biyayya ce idan kaso ma kayi yadda kaso da ni, amma maganar aure gaskiya ban shirya auren tsoho irinka ba!”
“Zainab!” For the first time da aka kira sunanta cikakken, tura baki tayi tana faɗin. “Ni bana son Zainab Zeenobia zaka ce.”
“Tabbas sunanki Zainab, kuma da shi zan kira ki, so ki biya ni kudina da na mutane baki daya, ko kuma na saka a yi ta farautar ki babu dare babu rana!”
“Barazana kake min?”
Ta tambaye shi a nutse, bayan ta mike daga inda take. Ta koma bayan kujeran, ta dan sunkuyar da kanta. “Ba dai barazana kake min ba, idan shi ne ma ka daina tunanin haka, domin ban san tsoro ko barazana ba, yana da kyau ka bi wata kofar ban da wannan!”
“Da zaki daina min magana, ta haka da kin taimakawa abubuwa dayawa!” Ya fada muryanshi tana cracking. Sam bata fahimci maganarshi ba, amma kuma bata fasa abinda take ba, domin wani irin kusanci ne da ya haifar mishi da wasu abubuwan da ya kasa jurewa. Hankad’ata yayi ya fadi can da baya, wanda sanadin faduwar, ya ja mata buga kanta da table din dinner.
Dafe kanta tayi tana kallonshi, ta kai minti goma a zaune, juyawa yayi ya ga yadda ta rike kanta jini na zuba a hancinta.
“Ya ilahi!” Wayar shi ya lalluba sai, kiran Elbashir yayi. “Ka shigo!” Ba iya shi ba hatta Shatima sai da ya shigo, kasa boye halin da ya shiga ne yasa shi nufarta. “Innalillahi, Baby!” D’ago kai tayi, ta kalle shi kafin ta fashe da kukan makirci. “Boy ika cewa ba da gayya na amshi kudin ba?” Gyada mata kai yayi sam ya manta a gaban Malik yake, don haka ta kuma cewa. “Kaga yadda ya min, kashe ni yake son za i yi akan kuɗinsa.” Juyawa yayi ya kalli Malik cikin fushi. “Yanzu kai Malik ko kunya baka ji ba, yar wannan yarinyar zaka nime kashewa akan kuɗinka? Me Baby ta maka?”
“Kudina zaku bani, kai Elbashir ka sakata gaba ka kaita asibiti! Kai kuma kazo nan ina son magana da kai!”
Yadda yayi maganar a nutse zai tabbatar maka, Malik Menk Jordan shi ne a gabansu. “Ok sir!” Suka ce mishi”Ke muje!” Inji Elbashir, “Boy kace ba ni zuwa!” Ta fada tana kwakulo hawayen wanda sam ba dabi’arta ba ne. Shi kuwa da tausayi ya kama shi, sai yake hango rashin Malik. “Ki bishi za a kaiki asibiti ne!” “Ni bani zuwa domin yace sai ya saka a min alluran mutuwa!”
“Ke wacce irin sakarya ne?” Elbashir ya daka mata tsawa, juyawa tayi a fusace ta rike necktie dinshi, kafin ya yi wani tunani ta buga shi da kasa, cire hular kanta tayi, ta gyara zaman daurin gashin kanta. “Ke!” Malik ya daka mata tsawa. Hasken da ya wuce ta idanunta babu shiri yasata nufar Malik da wani kofin Mug.
“A’a! Ke dakata.” Kafin su rufe baki, ta nufi Malik zata rosa mishi mug din nan. Wani irin dukar cinyarta yayi da bayan hannun shi. Ta koma ta zauna dabas a kasa. Kujeranshi shi ta guragu ta dauka, zata maka mishi, Shatima ya rikota. “A’a” hankade Shatima tai, ta nufi Malik. Wanda ta gama karantarta, kafin ta kai Mishi duka da karfe, ya kai kauce, ya kuma fisgota, ya dauke kunnenta da wani irin mari da yasa ta suma lokaci guda. “Bashir! Ka wuce da ita, Menk Jordan World cares.” “Ok Malik” “duk abin da ake ciki ka tabbatar ka sanar min!” “Tow Malik!” Sabata yayi s kafad’arshi, suka fita ko inda Shatima yake bai kalla ba ya ce mishi. “Mene ne alaƙarku?” “Ina son aurenta ne!” Ya gaya mishi gaskiya domin Malik ya kyaleta.

“Hmm! Kasan dai ta shiga takun saka da ni?” “Malik yarinya ce!” Shatima ya fada a hankali. “Ba yarinya ba ce, tasan me take yi, idan kuma yarinya ce zaka biya ni kudina ne?” “Amma Malik ba wani abu bane a cikin dukiyarka, idan ka yafe mata.”.”ban san wannan zancen ba, domin ta sayar da ranta. Ciniki muka yi na bata kudina. Ita da kanta da duk wani abun da ta mallaka yana hannuna ne, na ja maka layi akanta, kada na kuma ganinka da ita.”

“Malik” juyawa yayi ya kalli Shatima, “Shi kenan Malik an gama!” Yaji haushin Malik sosai, kai taya ma ba zai ji haushinsa ba, domin ya girma da jin haushinsa har yau gani yake nasarar da Malik ya samu shi ya cancanci haka, hassada da kyashin Malik yake ji, wanda idan ya boye sai yaji kamar zai mutu.
—–
Sun hadu da Malik, akan kudiri daya tun a gidan Yari suka haɗu. A lokacin da suka hadu bai tab’a zatan Malik zai zama wani abu ba, domin lokacin shi yake tsayawa Malik idan aka nime cutar da shi. Bai mantawa akwai wani mutum da ake kiran shi. Shaidan bai damu mutuncin ko kaɗan ga hada husuma sakawa yake ayi ta dokuwa a gidan Yarin, kuma Jami’an ganduroba basu isa yin kome ba.

Akwai wani abu daya da yake faruwa a cikin gidan, shi ne na yawaitar yan homo. Yan luwaɗi sun yi yawa a cikin gidan, wanda yasa ko yaya kake sai ka samu lover, wannan abin ya d’aga hankalin Malik,. Domin yasan dai wannan dabi’ar tana cikin manyan kaba’irai. Shi yasa yake cin duka a hannun wadanda da suka fi karfinshi idan sun nime shi da Lalata yaƙi.
Haka ma Shatima, mutane dayawa sun nime shi yaki, sai tafiyar su tazo daya, anan ne suka fahimci ai duk mutum daya yayi silar fadawarsu matsala guda, sannan kowa ya san cewa duk wanda ya zauna a gidan yarin, tow ba mutumin kirki ba ne. Haka yasa baki daya ake kallon duk wanda ya fito gidan yarin yana zaga bayan gida.

Wata rana ana ruwan sama, Shaidan ya turo a dauki Malik domin yafi son Malik. Ya ce duhun fatarshi yana daukar hankalinshi.. sai aka yi rashin dace, aka ɗauki Shatima. Malik yana dawowa aka gaya mishi an zo daukar shi amma sun dauki Shatima. Yasan kuma wanda aka kaiwa Shatima ba zai bar shi ba, cikin fushi da fusatar da yake tare da ita, kawai ya dauki wani katako me kusa, ya nufi can dakin shaidan, ya damu ya kwabe Shatima yana kokarin saka mishi abin, bai san lokacin da ya make kanshi da wannan katoko me kusar ba, sai ganin jini aka yi yana sartuwa a dakin, ya kuma cigaba da dukarshi dai da ya daina motsi, karshe jami’an tsaro suka dauke shi. Aka ji aka rufe shi. Koda aka kai Shaidan asibiti kwanan shi goma ya ce ga garin ku.
Wannan abun ya d’aga hankalin kowa, domin koda aka bude Malik, take ya zama sabon shugaban gidan Yarin. Sannan ya kafa doka babu gay a cikin gidan..
Wannan abin ya dame su sosai, har aka fitar da shi, matsala daya ya fuskanta, ba kome ba ne, Malik yana da tsananin bukata, matukar zai ga mace ta mishi magana, ko yaya ne tow yanzu zai bawa mace dama, babu ruwanshi.

Shi yasa a lokacin daukar fansa shi, yayi ta gudun mata, amma karshe samun laluran kafarshi tow mace ce, wanda ya haifar mishi da mutuwar kafaffunshi da duk wani masarautarshi. Haka yasa shi boye kanshi, don ko ture Zeeno da yayi, abin da ya faru da shi shekarun baya ya dawo mishi kanshi, mace tayi sanadiyar da ya tasa kafaffunshi, sannan itama don hauka a hatsarin ta mutu, Yarinyar da yaso kuma ta ci amanar yardan da tayi mishi, inda ta dauki Nuratu kanwarshi tow kuwa da bata fara aikata mummunar hukunci kanta ba, Bayan ya rabu da ita ya gane shi din sai a hankali ba zai iya zama babu mace ba, sai dai bayan hatsarin shi an sha kawo mishi yan mata karshe su suke fita duniya suna gayawa abokan harkallan shi nakasashe ne, shi yasa ya hakura da mata, ya kuma hana mata shiga hurimin shi, sai Lalla Salmah, itama bai fi su hadu a shekara sau biyar ba. Duk lokacin da suka hadu da ita sai ta kai mishi farmaki, duk da Nuratu ba ciki daya suka fito ba, itama ƙaddara ta haɗa su, har yake jin ya samu kanwa wacce zai yi kome akanta, ita ta fara ce mishi abin da yake aikatawa kuskure. Ya daina ya hakura daukar fansa yana iya zama alakakai, ba iya kai yake kyalewa ba, yana iya binka har karshen rayuwarka.
Shi yasa bayan rasuwarta yasa Sayyadah Qudussiyah ta kwashe yaran suka tafi can Demark. Ba zai iya kallon yaran ba, ya rasa kome amma baya Fatah ya kuma saka wani na kusa da shi a matsala.
★★★
Menk Jordan World Cares.
(MJWC)
Tunda aka kawota, suka shiga bibiyar ‘lamarin jinin da yake fita ta hancinta, abun da suka fara, shine aka mata scanner da X-ray, kamar Dr Wardah Nyako ta sani, ya kalli sauran likitocin ƙwaƙwalwa ta ce mishi.
“Akwai matsala a cikin kanta, kuyi zooming ɗinshi muga.” Haka aka yi zooming sai dai sun sha mamaki. “Bullet!!” Baki daya suka tsaya a kanta.
“”Miracle ” Dr Wardah Nyako ta furta tana kallon Zeeno. “Ku kira Sir Elbashir!”
Fita suka yi, can sai gasu tare da Nurse.
“Sir kasan yarinyar nan akwai bullet a brain dinta?” Ware idanu yayi yana faɗin. “How can be? Mutum ya rayu da harsashi a ƙwaƙwalwar shi?” “Wannan shi ne ake kiran shi, baiwa da al’ajabi.” Shiru yayi yana kallon Zeeno, wacce irin ƙaddara ce hada ta da Malik.
“Yanzu ya za ayi da ita, domin dai tsautsayi yasa ta fadi , Yallabai ya ce a kawota.” “Zamu jira mu ga tashinta sai mu ji yadda jinyar yake a jikinta.” “Zan fara sanarwa Malik abinda ya ce xan gaya muku.”
Gyada kai tayi tana kara mai da hankali akan Zeeno, fita Elbashir yayi ya shiga Mota. Kiran Malik yayi ya gaya mishi halin da ake ciki, “ku kyaleta a bata abun da ya dace, ku uzurawa rayuwarta, har sai ta kawo kanta. Ba zan lamunci renin hankali ba.!”
book 2 zai zo muku Whatsp da Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/10, 9:17 PM] Yan Mata: War volume 2
“Koda wasa kada ku d’aga mata kafa, sai ta yi danasanin zuwa amsar kudina, idan ta samu lafiya ku farauci rayuwarta kamar ba zata kai ba, ku sakata a Ukubar da zata zo inda nake!”
“An gama Malik!” Ya fada, yana kashe wayar. Biyayyar da take tsakanin Malik da Elbashir biyayya ce me matukar tasiri da sadaukarwa. Har yau babu wanda yasan me ne a tsakaninsu sai Allah, amma dayawan mutane suna kiranshi da bindin Malik ko karen Malik, ko dan koran Malik. Duk abin da ka kira shi yana amsawa, gwargwadon yadda ka ɗauke shi.

Asibitin ya koma, ya tsaya har kusan awa uku kafin ta farfaɗo. Yana zaune. Kujeran da yake facing ɗinta. “Yaushe zamu samu kudin mu?”
Dafe kanta tayi, tana kallon shi kafin ta ce mishi. “Me ya faru n kare a nan?” Watsa mata kallon banza yayi sannan ya ce mata. “Kudinmu muke bukata! Ko kuma mu fara farautar rayuwarki ba dare ba rana, baki da ikon motsi ko kyakyawar numfashi. Daga wannan lokacin ki fara niman mafaka.” Yana kai aya, ya saka kai ya fita, dafe kanta tayi. Tana kara jin wani irin zafi, tabbas tayi kuskuren amsar kudin mutane da shi kanshi, Malik domin tasan ba zasu tab’a kyaleta ba.

Don haka ta sauka a gadon, duba wani drower tayi a dakin ta ga kayanta, ban daki ta shiga ta saka, ta ajiye musu kayansu a wurin, tana fitowa ya bude window ɗinkin, ta bar dakin. Abin mamaki babu wanda hankalinshi ya kai kanta, sai da ta tsare daga cikin dakin, suka zo bata magani me suna gane bata dakin. Ko kafin a cafkota yarinyar nan, ta ware abinta.

A lokacin da security din da suke kula da kofar dakinta,suka kira Elbashir suka gaya mishi, yana gaban Malik. Zufa ne uay karyo mishi ya d’ago kai zai gayawa Malik ya ce mishi. “Ta gudu ba?” Ya kura mishi idanu, gyada kai yayi yana me tsananin kunya da zafin rai. “Hmmm ai zata gudu!”
Shi dai kanshi yana kasa, ya gaza d’ago kan balle har ya iya kallon Malik. “Ba ka nasan me yasa na biye ta ba ne?”
Sake sunkuyar da kai yayi yana me kame hannunshi. “Kayi hakuri Malik!” Girgiza kai yayi yana faɗin. “Kasan waye ni?” Ya kara maganar a sanyayye. Jikin Elbashir ya kuma sanyi, yana me gyada kai. “Na sha gaya maka ita bakuwarmu ce, kasan me yasa.”
Gyada kai yayi yana jin ɓacin rai, matukar yayi idanu biyu da Zeenobia sai ya kusan kashe. Rabon Malik ya mishi irin wannan maganar tun shekaru goma sha uku, da wani abin da ya faru wanda yasan sakacin shi ne. “Kayi hakuri Malik!” Girgiza kai Malik yayi yana faɗin..
” Ba anan matsalar take ba, budewar da bakinta zai yi shi nake tunanin, don haka ba zan gaya maka yadda zaka yi, amma wajibi ne a farauce ta har sai ta gaji ta zo da ƙafarta.”
“An gama!”
“Zan tafi Demark.” “Allah ya dawo da kai lafiya!” “Amin Ya Allah!” Ya tura kekenshi zuwa dakinshi, domin yayi alola domin lokacin sallah isha ya karato.

Bayan fitar Elbashir ya tara security guard na gidan bakiɗaya, ajiye musu hoton Zeenobia. “Yallabai baya bukatar kwarzane a jikinta, duk abin da zata yi kada ku mata kome kawai ku sakata a gaba da farautar rayuwarta har sai ta zo nan da kafarta.” “Yes sir!”
★★★
Tunda ta bar asibitin, bata tsaya ko ina ba, sai Al’umma Charity House, zubewa tayi a gaban jama’n gidan ta ce musu.
“Ba zaka tab’a sanin muhimmancin rayuwa ba, sai igiyar ƙaddara tayi ninkaya da kai a kogin kaddarorri. Na fada wata masifar da mutukar ba Allah ba, babu me fidda ni.”. Ta fada tana me niman wuri ta zauna.

“Wai me ya faru?” Kurawa Innah Idanunta tayi, kafin ta kwace duk abin da ya faru ta gaya musu, sannan ta kara da cewa. “Ban san yadda zan yi ba!” Rasa me mara me mata magana aka yi, suka zuba mata ido. Can Ammyn Abbas ta ce mata.
“Kinyi kuskure!” “Ai nima abin da nake nufi kenan Ammyna, rashin binciken me yasa Amjad ya nime ni. Me yasa bai fuskanci Malik ba?” Kare mata kallo tayi, kafin ta ce mata. “Saboda akwai wani boyayyen al’amari da yake makale da ke, wanda bamu san shi ba, amma kuma Allah ya fimu sanin dai-dai!”
Juya kanta tayi cikin jin haushi ta ce. “Dake Malik tsohon banza ne, wai shi yake kokarin amfani da tab’a mishi kudi da nayi akan lallai sai na amshi tayin auren shi.”
“Allah ya miki tsari. Dan luwadin!” Kamar wacce aka gaya mata mutuwa bata san lokacin da ta ware idanun tayi cikin firgici.”Inna mugun abun yayi yawa, kuma abin haushi tsoho ne fa!”
“Ke tafi can, da ma tsohon Arziki ne, zan tsaya ayi kome,ai rufin asirinmu ne, amma tsohon banza tsohon najadu, ai bai dace da rayuwarki ba. Ki koma sama ki zauna zamu ce bakya nan, ina dalili ayi mutum da budurwan zuciya wato ya boye ta’asar da yake yasa zai auri yarinya danya jagab. ”
“Fisabilillai Innah taya ma za a kalle ni yar madara da ni, ace wai na auri wancan second hand din? Dube ni fa? Yo Allah na tuba dan shekarun talatin ma ai ya min tsofa, saidai ruwa daidai gari.” Ta fada tana tura minchi lips dinta. “Inna ki bar biyewa Zeenobia kuna rage mishi zunubi, amma maganar kudin mutane da Malik zamu tsaya a kai.”
“Kayya Uwarmijina, duka-duka nawa Abulle take? Ina laifin ya saka a hukuntatta a hukumance, sai ya ce zai aureta.”
“Inna cewa yayi na aure shi,zai biya bashin mutane, ni kuma ba zan iya auren tsoho irinshi ba gaskiya ko da kuwa bashin zai biya.”
. Rike kunnenta Ammy tayi tana faɗin, “Zainabia nasan halinki, kin nuna mishi halinki ne?” Gyada kai tayi tana faɗin. “Ammy sakarya sakatarenshi ya ce min fa, Ni kuwa na ja necktie ɗinsa na wani buga shi da kasa.”. “Kash!” Ammy ta fada tana dafe kanta tayi tana faɗin. “Kin ga irinta, ke da zaki bi kome a hankali!”. “Ammyna ni kaina, ban san lokacin da nake fusata ba.” Ta fada a hankali, *Harsashin kanta, ko ya ya nutsa to zata iya rasa hankalinta da tunaninta, Hajiya ku godewa Allah tana numfashi, amma da abin ya kassara lafiyarta babu yadda aka iya haka zaa kyaketa.*
“Zainabia! Fada da fusata ba naki bane, yana da kyau ki fahimci haka. Babu yakin da aka tab’a cin nasarar shi ba tare an zubda jini ba. Yana da kyau ki koyi hakuri rigima da Malik ba abin wasa ba ne. Maza da yawa sun mutu, wasu sun nakasa, akan dukiyar shi ran dan adam ba a bakin kome yake ba, shi abu daya ya sani dukiyarshi. Sannan kuma ganin kamar idan wani abu ya same ki ba zamu yi kuka ba ne? Ni ce a sawun farko da zan yi kuka. Don Allah ki tuna da dan uwanki Abbas idan wani abu ya faru, kece a gefenshi idan babu ke fa? Shi ya dace na barwa amanarki amma ke nake barwa Amanar shi.”

Tabbas kamar maganar ya shige ta, domin lokaci guda zaka iya hango rauninta, sannan zaka iya samun rashin kwarin gwiwa a tare da Idanunta, tsayayyun gashin Idanunta, sun yi luff.
“Ammyna, ba zan tsaya Malik yayi yadda yake so da ni ba.”
“Kuma gaskiya ta fada, a duba al’amarin!”
“Inna baby zancen duba lamarin, dukiyar al’umma aka salwantar ta sanadiyarta, idan muka goyi bayanta kamar mun hakka rami mun cillata ciki ne, mu bata kwarin gwiwar fuskarta matsalarta.”
“Kai ina Ammy ba zan auri tsoho irin Malik ba, gara na dauki raina kawai. Dan luwadi fa? Kuma mutumin da zai ajiye ni ne domin dukiyarshi da na tab’a. Sannan idan aurena yayi, zan kasance mara yanci, dan fitar da samari ke da yan matansu ba zan sani ba, yar kyautattan da saurayi yakewa Budurwa ban sani ba, babu romantic kawai rayuwata ce a kuntacce, na fara ban san kaina ba, na kare akan biyan albashn da ban san dalilin fadawa ta ciki ba, Ammyna ki duba al’amarin haka zan bada rayuwata domin farincikin wasu? Zan iya badawa domin naku.”

Kasa magana Ammy tai, domin tasan taurin kan Zeenobia bai zama dole ta fuskanci abin da take nufi ba, amma kuma zata cigaba da mata addu’a, amma kan Zeenobia tana bukatar du’a’i.

★★★
Khuldu Jahid Khan resident.
Babban estate ne, da ya amshi sunan estate domin ana kiran da billionaires Quarts, eh unguwar masu hannu da shuni ne, domin idan bakaci ka batse ba. Baka isa ka sayi gida a estate din ba.

Wuri unguwa ce da take dauke da kazaman yan siyasa, yan rashawa gwamnati, shafaffu da mai, killers da ake basu aikin na musamman, army robes da suke aikata miyagun laifuffuka wanda kowa yasan an saka hotonsu da sunan ana nimansu.

Daga cikin daya daga gidajen, Amjad Fahad Albagwi yake shi da iyalinsa. Kallon Salim yayi ya ce mishi.
“Yanzu kai Salim ba zaka dauki, 25% ba, ko Zeenobia da tayi aikin 1% muka bata domin bata san cewa hakkinta muka biya ta ba.”

Mikewa Salim yayi ya ce mishi.
“Ka haɗa da sauran ka rike, amma ni ba zan amshi 25% ba, wallahi gara na mutu ban ci.” Yana fadar haka, ya saka kai zai fita, da yasan haka zasu Mishi da ba makawa bai bada damar an shigar da Zeenobia ba.
Kuma ya san zasu nime kashe shi,, amma kafin ya mutu zai fara bayyanawa duniya gaskiya, musamman Malik Menk Jordan. Don haka bai bar gidan ba, ko da ya fito wurin motarshi zama yayi ya fara rubutu da yana gama rubutun ya ya saka a leda, ya hàdiye dakyar, kakari, haka ya saka kai ya fita, domin yana jin wani irin yanayi shi yasa yana tuki, ya shiga video recording, yana gamawa ya cire memory ɗin, ya hàdiye. Sannan ya karamin video ya bar shi kan wayar shi, yana faɗin. “Sakona zuwa ga Malik Menk Jordan!” Kyakyafta idanun shi yayi ya sannan ya kashe wayar.

Sai da ya bar unguwar, ya hau babban gadar da zata kai shi, cikin City, kawai wata babbar motar kaya, ta buge motar shi, sai da ya hantsila cikin kogin Keivroto, kuma yasan dama haka zai faru, kafin, koda yake al’amarin ya faru cikin dare ne, don haka babu wanda ya fahimci tashin hankalin, sai washi gari da aka kai labarin kai tsaye izuwa ga office din counciler, domin a kai al’amarin zuwa ga office din Mayor. Wato me gari.

Lokacin da labarin ya isa office din Mayor, hannun Elbashir ya fada, domin ana shirye shiryen barin Malik kasar ne, shiga babban dakin Malik yayi, ya same shi yana gyara link na hannun rigarshi.
“Morning Malik!”
“Hmmm! Anything else?”
“An hatsari aka yi daren jiya, kuma ana son sahalewan ka domin ciro motar da mamacin!”
“Waye shi?” “Salim Ghaddafi!” Murmushi yayi ya ce mishi. “Fansa yazo dauka kenan?”
“A sakon da na samu daga office din counciler, ya tabbatar min da yana tare da Amjad ga bayanin.”
“A ciro shi, a tabbatar da an kammala binciken kafin karfe biyu na sauya min lokacin tashi”
“Okay Malik” ya fada cikin sanyin murya.
Fita yayi daga dakin, shima Malik yana son tambayar shi ɗangane da Zeenobia amma sai ya share yana me mantawa da zancen ma baki daya.

Kamar yadda Malik ya saka aka Ciro motar da gawar aka fara binciken, ana ka gano abu a wurin ledar da memoryn suna hanjinshi, wayar shi an kai bangaren CID, criminal Investigation Department ne, anan aka shiga duba last sent din shi, last call ɗinshi, abubuwa yawa.
Suna gama tattara kome, suka tura office din Malik, Elbashir yana Office din ya karba, sannan ya wuce shi da sauran security guard suka nufi airport da Malik.
Ba karamin al’amari ba ne, rigima amma dake Malik bai yarda ya shirya rogima yanzu ba, kallon su yake ba yasa shi tattara ahirginsu a gefe guda. Mika mishi takardan yayi da kome da kome.

“Yaron ya turo maka sako, zaka gani amma al’amarinsa akwai daure kai. Hmmm a cikinmu akwai me farautar rayuwarka Malik!” Gyada kai yayi yana me gyara zaman agogonshi. “Zan duba! Yarinyar nan ka kama min ita kafin na dawo.”
“”An gama!”
“Ko kuma ka kyaleta. Ka bincika min meye take so, da shi zan kira ta.”
“An gama Malik!”
“Na yarda da kai, ban sani ba ko dan abin da na tara yana gabanka, idan shi ne ka da ka soke ni ta baya, ka soke ni ta gaba shine jarunta!”
Dukawa yayi yana me sunkuyar da kanshi a gaban Malik. “Duk ranar da ka kamani da cin amanarka, don Allah Malik ka kashe ni.” “Bashir shirunka yana bani tsoro.”
“Malik shiruna halittace ba dabi’a ba ce!” Gyada kai yayi, sannan Elbashir ya cigaba da cewa. “Dabi’a ana sauyata, amma halitta Allah ya tsara abinshi. Ban ce ka yarda da ni ba, amma ina son na gaya maka, rayuwata tana tare da naka, faduwarka faduwata, mutuwarka mutuwata. Malik i give you my words!”

……. “Allah ya maka jagora! Amma ya kake ganin shirin *Plan B* yayi?” Gyada kai yayi yana faɗin “Eh Malik amma last statement din ne bai min ba, don Allah kada haka ya shafi fansarka!”
“Wanda ya min daban, ka je zan duba lamarin!”
Fita Elbashir yayi, daga jirgin ya jira tashin private jet ɗin. .Malik yana barin kasar, aka kira Elbashir.
“Ka haɗa hannu da ni, zan biyaka kome kake so, zan baka duk abin da kake so. Zan maka kome idan kace na maka biyayya zan maka, amma so nake ka durkusa da Malik!”

“Kyautattawa Malik wajibi ne, cin amanar Malik halaka ce, ka fara gudu kafin Malik ya zakulo ka, yana sane da duk motsin kowa, duk inda kake tsammanin hatsabibi Malik ya wuce haka, ya dauke jai ne akan Yarinyar da kuka turo, kada ka manta yanzu haka Malik yana jin mu da kai. Kuma a can bangaren sadarwa ana gab da cimmaka domin IP dinka ya bada abin da ake bukata.

Ita kuma Yarinyar babu ruwana Malik zai ji da ita, da kun bar kome ya tafi yadda ake zaune, da na zaku kunce zakin da yake barci ba, ita kanta yarinyar bata san wacece ita ba, balle har ta iya tunkarar Malik hhhhhhh! Ba ku kuka nemo Malik ne ya nimo ku, ba kune kuka shiga tunanin shi ba, shi ya shiga naku ya tsara muku haka yakin da baku shirya ba, ku fara karbar shi ka gayawa shugabanka, maza bisa kanshi.

Ya turo akuya ramin mayunwacin zaki, ya fara takanshi kafin ya iso kanshi, sannan kace mishi ta yadda aka hau ta nan lissafin zai sauka.”

Daga haka ya kashe wayar, ya nufi wurin motarsu, ko gida bai isa ba aka fara haska labarin, matattan man fetur din kungiyar KJK groups ya kama da wuta. Murmusawa Elbashir yayi, domin akan hanyar Shatima ya kira shi a tsorace.
“Bashir wannan wani irin shirme nekuke aikatawa da Malik?”
“Khamis! Ka kira Malik ka tambaye shi me yake shirin aikatawa, kada ka kuma tambayata.” Ya kashe wayar abinshi.

Ko minti biyar ba ayi ba, Lalla Salmah ta kira shi, “Wai me yasa Malik yake haka ne? Me yasa ba zaka bashi shawara na gari ba?”
“Wai tsaya ni da kuka rena ne zaku gaya min maganar da ta muku?.ku kira Malik ku mishi irin wannan tambayar mana, ai wannan renin hankali ne!” Ya kashe wayar nan.
Sake kiran shi tai cikin burga ta ce mishi. “Amma a dokar kasa bai dace, Malik yayi haka ba, yana ina ne ma?” Zuciyar shi daya ya ce mata. “Yana hanyar Demark!”
“What! Yana hanyar kace?”
Tsaki yayi ya ce mata. “kije a miki wankin kunne!”
Daga haka ya katse kiran.
—-
Lalla Salmah
Mikewa tayi tana zaga falonta, sannan ta kira number Maidah tayi tana faɗin. “Malik zai zo kin sani kuwa?”
“Eh Maama, Nadrah da su Wahiba da Wahida suna ta aikin tarbanshi.”
“Kina ina?”
“Ina gidan Mama Jalilah!”
“Tasan Malik zai zo?”
“Eh nice na gaya maka mata!”
“Kai amma ke jakar ina ce? Wannan yakin neman kafa gwamnati ne ina ruwanki da gaya mata? Listn to me carefully, ki bar gidan yanzu, ki rufe maganar nan,like baki sani ba.”
A hankali ta kitsawa yarta kome sannan ra kashe wayar ta tura mata wani number, tana murmushin da ta barwa kanta sanin sanin ma’anar shi.

★★★
Yar kunama.
Cikin gidan Zulfa ta shiga, tare da mata yan sanda. “Ku duba daki-daki ku fito min da barauniyar nan yanzu!” Sanin halin yan sanda ba mutumci ne dasu ba yasa ta, fitowa tare da musu fyeduwa.
“Nace ba, uwar me za a duba dakin matan aure da tsofaffi? Ba dai nice na ci kudin mutane ba? Oya zoki kama ni!”
“Meye yasa kike ji da kanki?”
“A jini na yake, jin kai da tausayi. Shi kuma wnnan sa nake kimata nake karewa;” ta fada tana me saukowa daga sama!”
Har ta iso kasa, kwalar rigarta Zulfa ta kama! Black ya daki motar su. “Kai dan jagaliya! ” Kafin tayi wani magana, Dondurus ya ja rigar daya daga cikin yan sandan sai da ya b’alla botirin. Murmushi Zeeno tayi ta ce mata. “Kwalata ko mutuncin yar uwarki yar sanda!” A hankali ta sake rigar Zeeno, nufar gabanshi tayi ta ce mishi. “Kada ka kuma haka, kuskurerren lamari ne, cin zarafin macen da aiki ya kawo ta, amma kuma ta wani gefen yayi kyau ko babu kome ka nunawa yar sanda yadda ake ladtar da irinta.”
Shiga bayan motar tayi, suka bar gidan baki daya. “Ke baki da dangi ne?”
“Ina ce ku kuna da shi?” “Ke karamar Yar iskar! Me yawo da maza waye bai san karuwancin da kika yi ba?”
Lumshe idanunta Zulfa tayi, tana jin zafin kalaman da kurtun yar sanda take gayawa Zeeno!
“Madam kin zarafi ne, ki kiyayye kalamanki zata iya tuhumar ki da laifin keta alfarmarta.”
“An sorry Ma!”
“Ke kin san su waye suka tsaya min?”
Tana rufe baki, mutanen Malik suka dukar motar yan sandan.
“Officer! Wannan yaki ne da ake yin shi tsakanina da mutanen Malik wacece ke da zaki kama ni, duk kudaden da ake ihu akan shi naci banza………..😂😹
*Yasin ku tashi kaina da Comments ko na tafi sabon hutu*
book 2 zai zo muku Whatsp da Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/10, 9:17 PM] Yan Mata: Volume 3 My Sinner.

Kafin ta rufe baki motar ta shiga tangal-tangal, dira tayi dama basu saka mata handcuff fa, tana sauka kafin mutanen Malik su iso, Black ya iso da mashin ta haye bayanshi. Da masifafen gudu ya bar wurin. Baki dayansu suke baki suka yi, kafin su dismissed suka bi bayansu.

Sai dai kamar dama jiransu suka su bi bayansu, kawai shaidanun Yaran nan, suka shiga bawa yan sanda da mutanen Malik.
Duk da tana bayan mashin din sai da ta ce.
*Kai gayyan awaki, idan kun isa ku kama ni,idan baku iya kama ni ba ku gayawa Malik ya taso da kanshi ya kama ni, don dai naci dubu sai ceto;” ta musu gwalo, suka kara gaba a guje. Ai ya kamata a ce sun tafi amma Zeenobia don masifa sai da ta bubuga bayan Black, suka tsaya kusa da motar Zulfa, ta wani d’aga mata gira.
“Ohohoho, yar sanda ki cire rigarki ki fara sayar da fiyo wata, idan kin isa ki kama ni ”
. Suka manna a guje, tana dariyar shakiyanci da mugunta, domin dai ta gara kansu. Sanan ta wuce abin ta. Koda suka bi bayansu, su b’ace babu al’amarinsu. Abin ya bawa zulfah haushi, daga ita har mutanen Malik, wato duk yadda ka kai da takaici dai an kunsa maka, mutanen Malik ganin laifin Zulfah suka yi yayinda Zulfah take ganin laifin mutanen Malik. Don kafin kace me fada yana shirin shiga tsakaninsu.
★★★
Demark.
*07:49 pm*
Dai dai lokacin da jirgin Malik ya isa garin kenan, dake akwai Yaran Elbashir a garin musamman masu kula da Ayyukan Malik na kasar, sune suka zo tarbanshi.
A hankali aka buge jirgin domin har bakin kofar aka kawo motarshi, daga yadda aka zuba jami’an tsaro zaka fahimci Malik yana da karfin da ba kowa yake da shi ba, sannan akwai kyakyawar alaka a tsakaninshi da mutanen. Ai ko babu kome garin mahaifiyar shi ce, sannan yana da lasisin zama a kasan domin shima haifaffen kasar ne. Sannan kuma an bashi damar shiga kasar duk lokacin da yaso domin dai yana kawowa kasa cigaban da ake bukata.

Kuma halo yana da damar yadda yake so, don haka tun kafin ya isa gidan da yake zama aka fara mishi tarba na musamman. Duk da saukan dare ne, haka suka wuce da shi fadar shugaban kasar, ya fara kai gaisuwa sannan suka gaisa kafin suka tattauna. Da zai bar fadar shugaban kasa ya ce mishi.
“Nasan ka gaji! Akwai masu kula da kai, zasu maka tausa yadda kake su, an tura su gidan ka. Ka ji dadinka!”
“Godiya nake.”
Haka yayi sallama da shugaban kasa, ya nufi wurin motarshi, aka wuce da shi gida. Juyawa Security Adnan yayi ya ce mishi. “Sir ana kiranka a waya?” Ya mika mishi wayar. “Anne! Kiyi hakuri sai na huta, ki cewa su Angels sai zuwa gobe in sha Allah!”
“A’a babu ruwana, gaya musu da bakinka;” ta fada tana miki musu wayar..”babys kuyi hakuri ba iso karfe takwas saura, ko sallah isha ban yi, na gana da shugaban kasa, yanzu a gaji!” Kamar zata yi kuka ta ce mishi. “Ok Dadi!” Daga ta mikawa Wahiba wayar. “Dadi, kasan mun d’aga bikin karin shekarun mu sabo da kai, me yasa kai ba zaka cika mana alkawarin mu ba.”
“Sorry baby, zan zo gobe in sha Allah!”
Kashe wayar yayi, domin Wahiba tafi Wahida rigima, haka ya isa gidanshi da yake wajen birnin.
Koda ya isa ruwan wanka ya damu an tara mishi, sai da ya cire kayanshi ya sa bathtub, ya nufi ban dakin ya samu ruwan yana tururi, an zuba flower din rose. Yana fitar da wani irin kanshi. A hankali ya shiga cikin ruwan,. Bayan ya cire rigar shi.

Nutsewa yayi cikin ruwan, ya ɗan dauke numfashinsa, sai da yayi second talatin, ua fito yana sauke ajiyar zuciya. Shigowar Maidah, ta dauki shower gel, ta shifa mishi. A hankali musamman kafad’arshi zuwa kirjinshi. Bude idanu yayi ya rike hannunta. A hankali ya ce mata. “Jeki ya isa haka”
Sake hannunta yayi ya fumita daga dakin. Kafin ya fito ta shirya mishi abubuwan da yake bukata, sai da ya jima kafin ya fito ko ina take bai kalla ba, bai ma san dalilin da ya sata zaman jiran fitowar shi ba. Fuska ya daure ya ce mata. “You can go;” tashi tayi ta dauki kimono ta saka a gaban shi.
Tana fito yana dauke ajiyar zuciya, duba kayan sanshi yayi ya ciro robar magani. Watsawa yayi a bakinshi ya shiga taune su, yana hàdiyewa, yabi da ruwa yana dauke ajiyar zuciya.

Koda ya gabatar da sallah isha, tea kawai aka kawo mishi da cookie. Yana ci yana duba sakon da yake cin karo da shi martanin da Khuldu Jahid Khan, ya ce zai kai mishi nan da ba da jimawa ba.
A hankali ya shiga shafinshi na tweet ya ce.
*Ina son na tsaftace Keivroto, don haka ina rokon al’umma su tsayar da tunaninsu aikin mu! Bana cikin masu Kasuwancin sayar da al’ummarsu. Kamar yadda Khuldu Jahid Khan da mutanenshi;*
Mayor Malik Menk Jordan.
Lokacin da Malik yayi posting din gidajen jaridu, suna nan dama jiran takunshi suke kuma kai tsaye yake harba sakonshi, kafin wani lokaci an fara screen shot ana turawa gidan jaridu, kada ku manta Malik baya kasar, kiranshi da wasu manyan mutane suke yi, yasa shi bada umarnin a rufe KJK groups tv, da gidan rediyo dinsu.

Aikuwa hankalin kowa ya tashi, sannan kafin ya kwanta. Ya rubuta.
*Zan maka sassauci! Zan biya ka asarar da kayi, ka mikawa hukuma mai laifin da yake bayanka* daga haka ya kashe wayar baki daya.
Kwanciya yayi uana yana sauke ajiyar zuciya, sai dai me? Baki daya daren barci kaurace mishi yayi yana son lallai yayi barci, amma ya kasa.
Karshe tashi yayi zaune yana kallon yadda kome yake faruwa, jan kekenshi yayi ya hau, sannan.ya nufi ban daki.

Alwala yayo ya zo ya bude jakar shi, ya shimfida abin sallah, ya shiga gabatar da sallah. Haka ya raya daren nan da bautawa Allah. Har kusan karfe uku, sannan ya kwanta. Barci yayi gaba da shi.

***
Washi gari bayan ya idar da sallah asuba, ƙwanciyar shi yayi sai karfe sha daya na safe ya farka, ya nufi ban daki, ya wanka yayi ya fito, yana shigowa dakin ya shiga shiri yana nazarin Elbashir da bai kira shi ba.
Yasan yanzu dare ne a wurinsu, don haka ya kyale shi, ya shirya sosai sannan cikin nutsuwa. Vaseline ya sha domin shine man shafawar shi, yana gamawa ya saka farin rigar material, an yiwa rigar ɗinkin senator suit, fari ne sosai rigar kuma shara-shara sai bala’in tsada.
Don har kana iya hango singlet din cikin rigar, trouser dinshi baki ne. Material din kaftani. Me karfi sosai sai wata hular da ya saka, ya fito wani like Igbo Men.

Takalmin Saint Laurent shoe, shi kanshi kallon kanshi yayi a madubi, a hankali ya shafa kasumbar shi, wadanda rabinsu sunyi fari sosai, murmushi yayi maganar Zeeno ya fado mishi a rai. *Ka daina abu kamar yaro, idan kayi haka kyau kake min, ni kuma haushi kake bani* shafa kanshi shi yayi yana lashe kakkauran lips ɗinshi, man Vaseline ya shafa a bakinshi.

Dauko imperial Majesty, shi ne last abin da ya fesa, har ga Allah ganin Zeenobia yasaka mishi kwadayin aure,. Aure yake bukata musamman idan ya tuna yadda suka yi a rangama da abin da Zeenobia ta mishi. Tsigar jikinshi ya mike har tsakiyar kanshi yake jin wani irin motsi. Bude side bed din yayi ya ciro maganinshi ya shiga hàdiya. Sannan ya nufi wurin water dispenser ya dibi ruwa ya kora. Sannan ya fito daga dakin bayan ya ajiye kofin.

A hankali yake tura kekenshi shi, ya iso falon. “Good morning Sir!”
“Morning Adnan! Ya iyalinka da Mamanka?” “Suna lafiya!” Shiru yayi yana son mishi magana amma kuma yafi son a tambaye shi, kamar ba zai magana ba.. “how about Jalilah!” Da sauri ya ce mishi. “She’s fine and healthy!” Sannan ya sunkuyar da kai. “what she don now? Ko har yanzu tana karuwancin da kawalancin ne?” Girgiza kai yayi yana faɗin. “No sir wancan satin ta sallame kowa.” Cizon lips ɗinshi yayi ya ce.”kai ni estate!” Yanzu idan ya ce ya tuna daga SIN din shi Allah zai yafe mishi kuwa?

Yau da ya sauka a garin nan, bai kyautawa kanshi ba. Domin dai shi ya fara lalata Jalilah. Sannan ya koma gefe bayan abun da ya faru da Nuratu ya zargeta har da kiranta karuwa. Bayan yasan kome shi ne silar tarwarsewar rayuwarta. Taya ma zai iya zama da ita, bayan abin da ya faru har hoton Jalilah aka kawo mishi, da makiyinshi, abun da ya fusata shi kenan ta tafi ko ya kashe ta. Domin ya tsaneta.

“Sir muje ko?” “Yawwa Adnan. Kawunka ya kiraka?” “A’a bai kira ni ba.” “Idan ya kira ka, let me know!” “Ok Sir!” A hankali suka shiga tafuya har wurin motarsu. Tunda ya shiga motar, rayuwarshi ta baya take son dawo mishi, kokari yaƙe ya binne kome ya cigaba da rayuwarshi amma ina, tsoron shi daya ka da Allah ya kama shi da laifin abinda ya aikata. Suna isa estate tun kafin ya isa kofar gidan, ya hango Yaranshi. Wani yalwataccen murmushi ya sake. Kamar nuratu ce a tsaye a wurin.
Tsayarwa da motar tayi, yasa suka fara rige-rigen bude motar. Suna budewa, Adnan yana kawo kekenshi. Ma hankali ya motso tare da hawa kan keken, rungumar shi suka yi. “Oyoyo Dadi!” Rungumar su shima yayi yana faɗin. “Happy to see you my angels”
“Dadi I pass my test!” “Masha Allah!” Kallon Wahiba yayi tare da lumshe mata idanu.. “Me too Daadi!” “Anne Yarana sun girma saura aure fa!” Rufe fuskarsu kayi. Kallon Nadrah Khamis Shatima yayi da ta koma gefe tana kallonsu.

Shima kallonta yayi yana murmushi, , cikin gidan suka nufa tare da cewa. “Daadi, yau muna tare da kai har gobe.” “No da la’asar ina da meeting da shugabannin yan kasuwan kasar nan” “but Dadi mufa.”
“Ka da ku damu, zan d’aga lokacin sai dare shi kenan yayi muku.” “Eyeeeeee Daadi!” Inji Wahiba, dama ita kan Sayyadah Qudussiyah ta fada munafuncinta baya motsawa sai ta ga Ubanta.

“Dadi yau Ni zan maka tuwoo miyar kuuka!” Dariya yayi yana kallonta ya ce . “Ke ce ai tuwoo miyar kuuka! My Angel har yau tsinewa Hausa kika fa!” “Ok Dadi zan saka mishi blessing;” “ke tafi can bagwariya, muje ka ci abinci domin nasan baka karya ba!” Murmusawa yayi ya ce mata. “ai kuwa dai!” Nufar table tayi, Yaranshi suka zagaye shi suna bashi abinci.
Wannan ya mika mishi ta nan, wannan ta nan. Sai da suka ji yace ya koshi suka kyale shi, ya ce musu. “Ku shirya mu shiga gari!”
Haka kuwa aka yi, da gudu suka wuce dakinsu. Tare da bugawa Maidah kofa, bude kofar tayi tana. “Lafiya Wahida?” “Kizo zamu je yawo da Dadi!” “Bari na gani” ta rufe dakin ta kira Uwarta. Ta gaya mata.
“Maza shirya sexy dress!” Ok Maama!” Haka yayi shigar wanda rabin Kirjinta a waje, kusan ita ta cinye musu lokaci, kallon agogo yayi ya ce musu. “Angel pass two zan yi sallah sai na idar zan turo a dauke ku!” Kwalla ne ya cika idanun Wahiba . “Muje Daadi babu wacce ta isa a bata mana lokaci.” Ta fada kamar zata fashe da kuka. Can suka ji karar”kwas-kwas-kwas!” Juyawa suka yi suna kallonta, kafin sake baki ganin yadda suka mai da attention ɗinsu kanta, ta glass din Adnan ya ce mata. “Koma ki saka abaya kamar yan uwanki”

Jikinta ne yayi sanyi, fashewa da dariya Wahiba. Irin dariyar bosawa har da niman wuri ta jingina da piilar gidan. Can kuwa sai gata fuskarta a haɗe, tana wani dauke kai kamar ba ita, sannan suka shiga motar bayan Malik Wahiba da Wahida suna motar Malik.
“Daadi yaushe xaka yi aure? Na gaji da zaman nan kasar!” Inji Wahida. “Na kusa! Amma kuma ba naji Gran Mother tana faɗin cewa akwai maganar ku da Nadrah Shatima ba!” Juyar da kanshi yayi yana faɗin. “Zan yi in sha Allah!”
*A’a Malik! Za a fahimci abin da ya faru, don Allah kada ka min haka ina sonka amma bana son wannan abin don Allah!*
Idanunshi yayi bala’in tara kwalla,
Kasa sakewa yayi baki daya hankalinsa, yana kan Yaranshi yaki sake jiki ya kula su Nadrah. Mika mishi Americano coffee ta yi, d’ago kai yayi ya ce mata. “Thanks Maidah Sheikh!” Murmushi tayi mishi tare da mika mishi cup din, “bana shan sugar.” “I know.” Ta fada a kunyance..
*Ya Allah forgive my Sinner* abin da ya furta kenan a kasar zuciyarshi…..
book 2 zai zo muku Whatsp da Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*

*Update safe zaku na samun 3 readmore in sha Allah, na dare in sha Allah zai na kai 5 readmore bi izinillah👏*

Black Arab🧕🏿
[9/10, 9:17 PM] Yan Mata: Volume 4: Al’umma Charity House.

“May I have the sit?” Ta tambaye shi, murmushi yayi ya ce mata. “why not!” Zama tayi tana kallon yadda yan mata da samari suke yawo cikin shakuwa, tare da Romantic moments.
“Wani mataki kika tsaya na karatu?” “Degree a medical Lab!” “Masha Allah! Zaki cigaba da ne ko zaki yi aure?” A kunyance ta ce. “Duk abin da ya samu zan yi.” “Kina da boyfriend ne?” “Na’am! What? Boyfriend?” Sai kuma tayi kasa da kanta tana girgiza kai. “But why are you dressing like that?” Hadiye yawu tayi. “Ba kin san haramun bane? Dukkan mu da security babu muharraminki a cikin mu, but why you dress like whore? Kada ki kuma domin ko Nadrah bata tab’a irin wannan shigar ba, ina miki magana ne a matsayin abokin Mahaifayarki, not babansu Wahida kada na kuma ganinki da irin wannan shigar, idan kuma don ni ne kada na kuma ganinki a guest house dina, kin ji ko?” Idanunta cike da kwalla da mamaki ta ce mishi. “But ya aka yi ka gane ni ce?”
“DKNY Golden delicious, ni ne mutum na farko da na bata shi, tun bai kai matsayin da yake kai ba, so ina sane da duk motsin mutum musamman idan akwai abin da na sani a tare da shi.” DKNY Golden delicious turare ne me masifar kamshi da dadi, musamman mata sun amfani da shi. Malik yana da dabi’ar kyauta turare. Tashi tayi zata tafi ya ce mata. “Thank you.” Gyada kai tayi ta bar wurin, har kusan magriba suna wurin kafin dare yayi suka bar wurin.

★★★
KJK MANSION…..
Duk wanda yake ilahirin gidan, yaji yadda yake farfasa kayanshi. “Wallahi sai naga bayan Malik!, Sai na kashe Malik ni zai nakasawa arzikina.” Yadda yake masifa kamar zai kashe wani yasa babu wanda ya iya mishi magana. “Kai ya kuka yi da Elbashir?” Cikin tsannanin tsoro ya ce mishi. “Malik he refused!”
“Kace me?” Hadiye yawu yayi ya ce mishi. “Ka haɗa min zama da CM yau.”

“CM yana Demark zasu bude sabon kamfanin sadarwan hadin gwiwa da Malik a can!” “Babban bura uban bala’i har za a ci amanata? Ina yarinyar da ta yaudare shi tana iya?”
“Ya rjgada ya saka a farauci rayuwarta, daga mutanen shi har yan sanda duk wanda ya ganta ya kawo mishi ita a raye!”
“Ni kuma mace duk wanda ya kashe ta, zan bashi miliyan ashirin nasan zai bukaci ganinta a raye, tow a kashe ta.”

“Amma haka ba zai kuma rura wutar.” “Uban uban wutar fitinar! Nace fitinar taci kaniyarta.” Gyada kai yayi, sannan ya binciko hoton Zeenobia, aka turawa mutanen KJK, su fara farautar rayuwar Zeeno.
>
Sai dare likis suka koma gida, “yau ina kuka je?” “Gudun ceton rai!” Gyada kai Ammy tayi, tana faɗin. “Ba damuwa!” Daga haka ta wuce dakin ta rufe, zama tayi tana cire takalminta. Maganar Asp Zulfa yake dawo mata, “bana zo nan don kamaki bane, nazo ne na gaya miki. Rayuwar mutanen da suke kewaye dake suna cikin hatsari, ko yayya kika matsa daga gare su, za a iya farmaki. Ya rage naki ki mika kanki ga hukuma domin ta haka ne masu bibiyar ki zasu hakura babu wanda ya isa farautar rayuwarki tunda kina hannun yan sanda.”

Shiru tayi tana nazarin al’amarin, zuwa yanzu ta fahimci girman Allah da buwayarshi, duk inda zata shiga dole ta shiga ita ɗaya. Kamar tayi ta kuka domin yau da ita daya ce, barin kasar zata yi amma al’ummar da suka yi imani da ita fa? Mutanen da suka yarda da ita fa, ya zata yi da rayukansu? Kawai zata zauna kawai a kasheta.
Tun daga wannan ranar, bata kuma barin gida na. Har ya kasance ana ta zuwa nimanta amma babu labarinta, domin sai da ta share kwanaki goma a cikin gida a dakinta.
Ranar juma’a da da dare, suka fita bakin ruwa shan iska. Ko waye ya gaya musu ta fita, kawai tana zaune taga mutane sun fara fara kewayeta dauke da makamai.

“Kece wannan?” Kallon hotonta tayi . Kallonsu tayi ta ce musu, “Kanwar Babarku ce!” A fusace daya kai.mata duka ta kwauce. “an biya mu, mu kashe ki don haka, ki zabi irin kisar da zamu miki!” Gyara zama tayi tana faɗin. “Ai shi kenan idan kuka kama ni zan tsaya har na gaya muku yadda zaku min na mutu, idan kuma baku da rabo kudin ya tafi a banza.” Aikuwa suka nufeta baki daya, dake tafisu danyen kai, yashi ta watsa musu a fuskarsu, baki daya sannan ta dauki wani katako, ta shiga mukka musu ta ko ina, bata gama lillsasu ba. Mutanen Malik da yan sanda suka nufo wurin.
“Kai waye ya gayyato min waɗannan awakan.” Da gudu ta juya tare da ɗaukar motar mutanen KJK, suka shiga wasan tsare a cikin garin Keivroto city. Wani shu’imin gudu suke ita da su, a tunaninka zaka dauka namiji suke bi, a’a sam mace ce da ta isa mace. Yar gaggara, uwar masara jin magana da taurin kai.

Sai da tayi wata irin gudu, kafin ta isa wani wurin shagali, ta tsayar da motar. Sannan ta kutsa cikin mutane ta saje da su. Tana hango mutanen Malik. A cikin mutane, wani sanda ta samu tana zuwa ta bayanka, zata make ka dashi ta wuce.

Abun sai ya zame mata abin Tsokana da zolaya, duk wanda ya gani sai ta baje shi, kafin wani lokaci ta musu illa. Sannan ta wuce abin ta. A hanyar da zata wuce ta hango Elbashir zaune yana zukar hayakin taba. Kallonshi tayi yana tsaye. “Kin gama gudunki?” Murmushi tayi ta ce “happy to see tail din Malik, idan ka isa wurin shi, kace naci banza!” Ta falla a guje, take da kai mishi wani irin bugu da karfen hannunta. Kaucewa yayi ya bata hanya, ta tsalleke shi tana dariya, “Waw ka gayawa Malik, ya fito farauta na da kanshi. Shine zan yarda ya cika namiji.” Tana fadar haka, ta haura wani katanga ta fara tsalleke gidajen mutane. Cikin fun babu daren da ya kai wannan daren dadi da armashi. Ciro wayar shi yayi ya shiga niman Malik.
“Malik ! Yarinyar nan akwai Evil spirit a tare da ita, wallahi ta bani tsoro” “Elbashir da fatan baka yi fitsari ba?”
“Eh ban yi ba!”
“Me ya faru?”
“Malik KJ ya saka mutanenshi su kashe ta, duk inda take!”
“Tow su kashe ta mana!”
“Malik su kashe ta kuma?”
“Eh su kashe ta!”
“Ok shi kenan Malik!”
★★★
Kwanakin shi goma da zuwa, kuma har ya gama abin da ya kawo shi, yana son isa South Africa duba wani ginin da yake na kasuwancinshi. A hankali ya bi wayar da idanu. Kafin ya shiga duba cantact din mutane, KJK ya gani a sanyayye ya danna kira. Kamar ba za a dauka ba ya dauka.
“Waye ne?”
“Mikawa dan kwaikwayon karen.” Ya fada da kwarin gwiwar shi. “Waye kai?” “Dodonka ne bisa layi, shudin riga, farin dokin tsare, bakin wando kaftani doki me jiki brown. Ƙwayar idanu zaiba, fari kyakyawar matashi dan kimanin shekaru ashirin da bakwai. Bindiga kirar Germany, snippier, wanda karfin gudunta ya zarce dari tara da digo daya. Garin Abhu Dabi, kasar Dubai. Kalma daya tak akan Yarinyar da kuka nakasa mata rayuwa, yau kuke bibiyar rayuwarta, zan tashi Matashin da yake bisa dokin nan!”

“Kai… Kai….. kai…!! Malik ka da ka fara, kai gayawa Antoni su kyale yarinyar nan, Rayuwar Arif yana cikin hatsari maza a dakatar da su!”
“Hmmm! Kada ka damu, wanzamin ya gama maka gyaran fuskar? Ka shafa wuyarka ko ka ce a duba maka zuwa kunnenka. Ina tafiya ne bisa lissafi da hanya ta, ka sake gaba na kuma turo wani wanzami kayi tunanin abin da zai faru haka sauke kan dan banza irinka zan yi. Kuma na gaya maka, idanunka ya fita kan Yarinyar.”

Kashe wayar yayi, ya cigaba da tafiya da kekenshi. A kofar fita ya hango Jalilah ta ci kwalliya cikin Blue berry gown. Kafarta sanye yake da DG shoe, sai yar karamar pose..
Tayi kyau, dauke kai yayi ta nime wuri ta zauna. Wayarshi ce tayi kara ta dauka, “ina jin ka!” “Malik akan yarinyar nan ce, haka za a kyale KJK ya kashe ta.”
“Yaushe ka fara damuwa da rayuwar wasu?”
“Malik yarinyar babu ruwanta!”
“Yaudarata tayi ta ci min kudi, akan me zan kyaleta.”
“”Malik don Allah kayi hakuri, Yarinyar!”
“Elbashir idan kana son yarinyar ka gaya min kawai ayi muku aure ” ya kashe wayar. Ta cigaba da harkan gabanshi kamar babu halittar Mutum a falon. “Malik!” Ko kadan bai ji wani abu ba, sai ma cigaba da abin da yake. “Nazo na gaya maka gaskiya, ba nice na aikata.”
“Dude you keep quiet?” “Amma ya kamata ka saurare ni, nima lokacina yayi wallahi sai na zubda mutuncinka a idanun duniya.”
“Idan kinso ki zubda Kinji, I don care. Sannan da kike cewa zaki zubda shi, hala madara ce da zan ta riketa a kwarya kada ta zube, and ki fita ki bani wuri ”
Takaici yasa ta fita daga cikin dakin tana faɗin. “Sai na lalata maka suna!”
“Ki kara himma har abada zaki kare rayuwarki baki san asalinki ba. Jalilah Bulama Shuwa;”
Cak ta saya tana me juyawa a hankali, kamar wacce ruwa ya cinyeta. “Kasan asalina ne? A ina dangina suke?” Banza yayi mata, shima ya dauke kai kamar bai santa ba, duk magiyar da take mishi Malik mirsisi yayi yaki kulata da ta ishe shi, ya kira Adnan yayi mishi waje da ita.

Shi ba zai dake ka ko ya zage ka ba, amma zai daki inda sai ka kusan mutuwa kafin ya sarara maka. Washi gari ya wuce South African, inda ya sauka a Cape Town

A Nelson Mandella streets ya sayi filin ana mishi, wani hadadden apartment y hadu iya haduwa, ga injiniyoyin da suke aikin. Kwananshi uku ya tattara ya dawo Keivroto city da safe ya sauka, ranar juma’a. Bayan sallan juma’a ya tura Elbashir da Lauyanshi akan suje su rufe mishi gidan. Ko kuma su sako Zeeno a gaba a duk inda take.
—. Dake kwana biyu daga ita sai yan sanda da mutanen Malik suke wasan tsare-tsarensu. Tana can inda take boyarta Black ya kirata a waya.
“Zeeno an kore mu, hadu nan suna mana watsi da kaya.”
“Shit!” Juya kanta tayi tare da fitowa daga gidan da take zaune, ta nufi office din yan sanda.
“Nazo shigar da kara ne?”
“Karar waye?”
“Malik Menk Jordan!” A yadda tayi maganar da fully confident yasa baki daya yan sanda suka juya suna kallonta. “Me ya miki?”
“Yaje yana koran mutane daga gidansu!” “Ok bari a kira kansilar birni ya haɗa ku da shi.”
Haka aka yi kuwa, can sai ga Elbashir da Lauyan Malik. “ta kawo karar Malik Menk Jordan!” “Gaya musu bayan niman kashe ni da suke son yi bai ishe su ba, sai sun d’aga mu ba bisa ka’ida ba!”
“Shi kenan, mun yarda da laifin mu Asp ko zaa bamu damar mu sassanta kanmu a gida!”. “sassantawa na kalau ban yarda ba a kai mu kotu kawai!”
“Hmm! Zeeno ku tafi ku sassanta!” Bata san dalilin da ya sa ta bi shawarar. Suka fita kai tsaye gidan Malik suka nufa. Yana zaune a hankalinshi yana kan Tv.
“Barka da zuwa yar gudun hijira!”
Zama tayi, ya juya ya kalleta sannan ya tura mata takardan gabanta. “An gama biyan kowa kuɗinshi!” Daukar takardan yayi ya ce mata. “kika ce kinci kudina kin ci banza?” Kallon Elbashir tayi ta zabga mishi harara. ” Ku bani wuri!”

Ya kuma tura mata wasu takardu, “wannan takardun a hannun dan uwanki Abbas ba samu, ya saka gidanshi a kasuwa. Kuma na sayar domin ya fashin rayuwarki!” Mikewa tayi jikinta yana rawa. “Me na maka da zafi!!?”
“Kudina!” Ya gaya mata hankali kwance, “me kake bukata?” “Filin gidan Al’umma Charity House!” “A’a Malik Menk Jordan, ka nime wani abu. Ban da wannan gidan na haɗaka da Allah!”
“A’a ni gidan nake so!” “A’a shi abin da ya rage mishi taya zan barka ka raba shi da ita?” “Kin san wannan wurin itace rauninki, me yasa kika ci amanarmu?”
“Malik ban ci amanarka ba!”
“Idan baki ci ba, dawo min da kudina!”
Dafe kanta tayi, “Malik!” ” Ba zan kuma sauraron abun da zai fito bakinki ba, fita ki bani wuri!”

“Don Allah ka saurare ni!” “Security!” Ya d’aga muryanshi yayi tare da kwalawa jami’an tsaro kira, suka fita da ita a wannan karon bata da ra’ayin amfani da karfi domin fadar kawai ya dubi girman lamarin ya bar musu gidan, haka suka fitar da ita daga Mansion ɗin, ta tsaya tun farkon dare har dare ya raba. Malik yana cikin gidanshi, har Elbashir ya bar gidan tana wurin lauyarshi ya bar gidan tana tsaye bata bar kofar gidan ba.

Security suna zuwa suna gaya mishi, tana tsaye, duba Cctv yayi ya ganta tsaye tana kallon kofar gidan, har ya juya zai tafi yaga wani mota yazo da gudu ya wuce ta gabanta. “kai ku shigo da ita;” ya fada da dan sauri, haka kuwa aka yi. Security suka shigo da ita cikin gidan, a falo suka barta ta cigaba da tsayuwa.

A hankali ya turo kekenshi, yana kallonta. “Dame zaki kare Al’umma Charity House?” “Da kare rayuwata ina me bin umarninka!” “Ok zauna mu sake tattaunawa akan cantract marriage!” Wani irin kallo ta mishi. “Idan baki shirya ba, Jeki amma ki sani gobe zan saka a make min gidan nayi gidan shakatawa!” Zama tayi da kyau, tana hadiye yawu ta ce mishi.
“Ina jinka!”
“Ina jikimar?” Shiru tayi yau bata da bakin magana duk abin da Malik yayi daya ne.
“Ok gashi nan ki duba abin da bai miki ba, dai a gyara a saka sabon tsari!”
Ɗaukar takardan tayi tana karantawa.
*{One Year Cantract Marriage}*
Malik Menk Jordan and Zainab Nasr Hadejia.
1-Babu jagaliyanci.
2-Babu taurin kai
3-Dole ayi min biyayya
4-Kwana daki ɗaya
D’ago kai tayi ta kalle shi, kafin ta ce mishi.
“Na yarda da sharuddan amma ban yarda da kwana daki daya ba! Sannan auren wata shida zamu yi”
“Cigaba da dubawa dai! Kafin kiyo korafin ki!”
5-Dole ki tayani Mijinki kula da abin da yake nashi!
“Kace kawai baiwa ka dauko saboda miliyan dari huɗu zaka mai dani baiwa!”
“Cigaba dai!”
7- Dole ki kilace kanki as matar aure.
“Ba saba yawo babu me daure ni a gida! Wallahi kuwa” ta fada tana bata rai.
“Cigaba da dai”
8- Dole ki sauya shigar da kike.
9- A auren shekara guda, zaki haifa min Yaro ko Yarinya.
Jikinta daukar wani azazzben rawa ya ɗauka, ta ce mishi. “Na rantse da Allah ba zan tab’a hada jiki da kai ba, dube ka tsoho da kai, duk ka tsufa da gashi buya-buya.!”
Murmushi yai ya ce mata, “duba last number!”
10- Idan baki yarda ba, na baki nan da awa ashirin da hudu ki dawo min da kudina har da wanda na bawa mutane sai kin biya ni.
D’ago kai tayi jikinta ya jike jagwab da zufa. Muryanta yana rawa ta ce mishi.
“Kana da imani kuwa?”
“Ki ajiye a ranki ba ni da shi!”

“Yanzu wannan dokokin duk zan bi?”
“Idan basu miki ba, sai a sauya na me da daukar zafi!”
“Zan bi dokokin amma ban da kwana daki daya, babu batun haihuwa, sannan zan tafi duk inda nake so, sannan batun saka kaya na yarda amma kilacewa ne ba zai samu ba. Sannan a auren mu babu body cantact, babu!”
“Na ji amma ki kawo sharudan ki, sai na ga wanene zan iya bi.”
“Bani da sharuddan da zan gindaya maka, amma kiji a ranka budurwa kama ta ta kare a auren tsoho, ban san dan abubuwa da ake yi a soyayyan ba, sannan ka auna kanka mana, sannan ace kawai don nayi laifi sai a hukunta ni da aurenka, ka duba wace ce ni? Ni ma ina son soyayya kamar kowa, ina son kulawa kamar kowa, duk yadda kaso kayi da ni, ai ni ce na kawo kaina.” Tana gama fadar haka ta mike zata fita.
“”Koda auren Cantract ne xan yi treath dinki,kamar masoya i give you my words. Ki saka idanu ki gani, zan kuma baki damar kiyi rayuwarki yadda kike so.”
“Kana son amfani da ni ne, domin biyar bukatarka, idan ka gama ka wullar dani.”

“Kawai ka tsaya ne akan auren yarjejeniyar amma da a tawa ra’ayin ne ba zan amince da wannan auren ba, domin baya cikin sharuddan Muslunci.”
“Eh amfani da ke zan yi kina da ta cewa ne?”
“Bani da shi, kuma bana fatar nayi amma ka sani Allah zai saka min ne lokacin da baka da tsime baka da dabara, idan kaso ka cinye ni, daya ne!”
Murmushi yayi yace mata. “Ai bana cinye mutane, sannan bana hadama abin da n sani nake yi! Idan kin ga ba zaki iya ba, ki tafi babu dole amma ko yanzu haka na saka bolldoza a kofar gidan al’umma charity House, kin san aikin buldoza ai ” ya fada yana wani murmushin mugunta. Zaro wayarta tayi tana kiran Black. “Ya ake ciki?”
“Zeeno ga shi an kawo kayan aiki za su rushe Al’umma Charity House!”
“Ok Ina zuwa!” Kashe wayar tayi tana faɗin. “Ka kashe ni ga ni a gabanka me ya rage?”
“Bana kashe mutane,abin da na sani ina cinye duk wanda ya tab’a min kudina!”
“Ka zama mashani ka kashe ni ka huta….
book 2 zai zo muku Whatsp da Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/10, 9:17 PM] Yan Mata: Volume:5 Mrs Mayor
Cikin dattako da nunawa bai wani damu da abin take ganin ya mata ya ce mata, “Kin ga taimakon juna zamu yi, idan ba don ina da hakuri da mutunci ba, waye zai dauki abin da kika mishi? Har gida kika biyo ni ki tsaya ki sauraren ni kika k’i ya kike so na Miki? Sannnan kudin da na biya bai ci a ce an tausaya min ba, kawai sai ki shiga gaya min magana son ranki?”

Idanunta cike da kwalla ta ce mishi..”ban gane kana da hakuri da mutunci ba? Ni kaga bani da su ne?” Kallonta yayi sama da kasa ya ce mata.
“Kin ga auren nan, taimakon juna zamu yi. Sannan idan kin ga ba zaki iya ba. Tow biya ni kudina!” Kura mishi idanu tayi, wato kalmar nan ne kwalelen kare da hantar kura. Duk yadda taso ya kawo wata mafitar sai zuba mishi idanu tayi ta ce mishi.
“Malik! Babu wata mafita ne sai aurenka?”
“Mafita yana hannunki, idan kina sha’awar rayuwar iyalan nan suyi shi kan titi ba damuwa lokacin damina muke shirin fuskanta.” Ya fadi haka yana me juya kekenshi zai bar falon. “Na amince! Na Amince amma bisa nawa sharadin.”
Juya kekenshi yayi yana fuskartatta.
“Idan na aure ka, babu wani abin da zai shiga tsakanin mu!” D’aga kafad’arshi yayi alamar duk ɗaya. “Babu kai babu al’umma charity House. Sannan batun zan haifa maka yara babu shi, domin idan na samu mijin da ya bai kai ka ba, zan aure shi kuma dole ka sake ni!”

…. “Taya zan sake ki bayan aurenmu baki daya na shekara ɗaya ce!” Ya fada yana kallon fuskarta. “Ba zan iya auren shekara guda ne, kin ga daga wannan lokacin zaki iya auren kowa ma kai ko jinjirin da aka haifa yau zaki iya aura. Maganar gaskiya babu saki sai lokacin ya cika.”
“Malik kayi min alkawarin ko bayan mun rabu ba zaka tab’a al’umma charity House ba?”
“Wannan alƙawari nayi miki, ba al’umma charity House ba, rayuwar duk wanda yake cikin gidan abin karewata ne, domin na auri Yarsu.”
Takawa tayi tare da sunkuyawa ta ce mishi.
“Daga ranar da ka gaza kare rayuwarsu, da tawa rayuwar zan barka kuma zan farmake ka da yaki har sai na kai ka kasa. Malik ina jin wani abu a raina wanda ban san meye shi ba, sai dai daga ranar da na samu kaci amanata. Wuka zan dauka sai na huta nan” ta tab’a daidai bugun zuciyar shi.”

Lumshe idanun yayi ya zuba mata, sannan ya ce mata. “Ni bana cin amana, shekaru goma sha uku baya ma,na kare rayuwar mutanen da suka yarda da ni, na dauki amanar da aka bar min kuma ina fatar na cika shi. Gaya min bayan wannan me kike so!”
“Bayan shi kada ka sake kace zaka fara soyayya da ni, domin ba iyawa zan yi ba.” Murmushi yayi ya ce mata. “Xnoo yar kunama, me zai saka na fara soyayya da ke? Ai soyayya ta yara ce, masu jini a jika ni kuma ɗan gurgu ina zan kai soyayyar zukekiyar budurwa irinki!”
Hararanshi tayi tana faɗin. “Budurwan zuciya irin taka ya saka maka sha’awar auren yarinya karama”
“Ai gani nayi yarunyar kwaila ce, babu kome a kirjinta sai kirgan dangi!” Da sauri ta kare kirjinta. “Allah ya kiyaye, ni ba yar iska ba ce” “tow Allah ya baki hakuri!”
Kiran sallah farko yasa shi, kallon agogon da yake daure a hannunshi, ya ce mata.
“Mrs Mayor, zan shiga sallah zaki fara duty dinki ne ko sai an kawo min ke?”

Kamar ta rufe shi da duka, gashi ita ba gwanar kuka ba. “Wallahi ka fita idanuna ko na zage ka;” “tow Allah ya baki hakuri, ga daki nan ki shiga ki jira kafin gari ya waye, hakkina ne bawa rayuwarki kariya daga yanzu har ranar da zamu rabu!”

“Salon na shiga a yanke min kaina!” Murmusawa yayi ya ce mata. “har da bakinki zan saka a cire min!” Ya wuce ya barta nan, sai lokacin ta fara jin barci, ta nufi dakin, bude kofar tayi ta tura kanta da sallama, Idanunta ya dauka akan wani dream furniture’s na kasar South Korea, me masifar kyau. Royal blue me ratsi gold and gray. Hatta carpet din tsakar dakin gray and gold ne, juya kanta tayi tana kallon wardrobe din dakin wanda yake manne da bango, duk da na gadon ne yana hade da madubi, a hankali ta taka wurin dress mirror, da aka jera kome kamar da macen da take rayuwa a wurin. A hankali ta taka har gaban Mirror, tana d’aga kayan kan mirror din tana duba expensive costume’s, duba expire date dinsu tayi taga akwai lokaci sosai, wani kwalbar turare ne ya burgeta ta dauka, tare da duba sunanshi.
“Shumukh!” Ta furta a hankali, budewa tayi ta fesa a bayan hannunta, kamshin ya mata dad’i. Bata san lokacin da ta fara fesawa ba tana dariya. Jin shigar sallah asuba yasa ta ajiyewa ta nufi ban dakin, hadiye yawu tai tana kallon ban dakin da kaɗan dakin ya fishi girma. Har inda zaka yi alwala akwai, wurin ta nufa ta zauna tai shiru.
Mikewa tayi ta bude wasu drower din banɗakin ta dauko rigar wanka, sakawa kofar key tai, sannan ta gabatar da wanka sosai, tana me amfani da lady Gaga shower gel. Tana gama wankar ta fito ta gabatar da alwala sannan ta fito daure da rigar. Kayan jikinta kuma, ta jefa shi a Wash Machine. Ta nufi drower din, doguwar rigar abaya ta samu, sannan ta saka hankali kwance. Sai wani hijab da tasaka da shi tayi sallah, tana idarwa ta zauna sai tayi azkar har gari ya waye.
Sannan ta je ta cire kayanta ta busar da shi, a lokacin barci ne a Idanunta sosai, shanyawa tayi a banɗakin, ta fito a daddafe ta fada gado, rub da ciki.
Tund barci yayi gaba da ita, shima Malik barci ne yayi gaban dashi, bayan dawo masallacin gidanshi.

*09:30*
Ya farka yayi wanka, sannan ya shirya cikin jallabiya. Sannan ya fito a hankali yana kallon falon wayarta ya hango inda ta zauna jiya.
Dauka yayi ya shiga kallon wayar infiinix ce da taci ubanta, murmushi yayi ya zaro wayarshi da take charge a falon ya kira Elbashir.
“Lafiya lau, idan zaka zo ka biya ta Menk Jordan system world ka tawo min da Sumsung babbarsu baki ɗaya ina jiranka.”
Bude da sakon yayi, wato saboda bata dauki duniya da zafi ba, wayarta babu ko yar security code.
*Zeenobia kina ina ne?*
*Don Allah kiyi magana, mutanen sun tafi*
*Zeeno ba zan iya barci ba ne*
“*Allah ya tsare ki a duk inda kike*
*Daughter ina kike? Muna cikin tashin hankalin rashin dawowarki.*
Murmusawa yayi yana shafa kanshi, wato su din sune duniyarta, ita kuma rayuwarsu.
10:16am
Elbashir ya shigo gidan, kallon shi yayi yana faɗin. “Malik me zaka yi da waya?”
“Zan bawa Mrs Mayor ce!” Gyara zama yayi ya ce mishi. “Good morning Malik!”
“Morning Elbashir!”
“Wace ce ka samu haka?”
“Zaka ka dai jira zuwa an jima!” Suna zaune har sha daya, kunna tv Elbashir yayi. Malik ya ce mishi. “Dan rage sautin tv nan, zai tashe ta!”
“Malik wace ce haka ka samu?” Domin shi ya manta batun Zeenobia.
“Ai jiya mun daidaita kanmu, aure zamu yi.”
“Auren lafiya? Kodai asiri ta maka!”
“Ban sani ba” ya fada yana kallon labaran, har Elbashir ya tashi ya nufi inda aka shirya mishi abin karyawa ya ce. “Me za a zubo maka!”
“. “Bar shi sai ta tashi!” Zama yayi ya fara cin abincin, domin ba zai iya da sabon halin Malik ba. Ko Zeenobia yake tsammanin, bai san lokacin da abincin ya haura mishi kai ba, ya juya yana kallon Malik, shima shi yake kallo. “Sannu kaci a hankali.”
“Malik yarinyar nan ce zaka aura?”
Dauke kai yayi yana kallon tv, ana nuna matattan man fetur Khuldu Jahid Khan, “da fatan gwamnati ta kwace wannan wurin.”
“Ai babban abin shi ne tuhumar shi da ake yi, kuma ya tabbatar da nashi ne. Gaskiya Malik ka iya dukan mutum ba fada ba zagi”

Wayar Zeenobia yayi haske, kurawa number idanu yayi. “Kenan Shatima bai rabu da ita ba?”
“Kamar Ya?”
“Na mishi iyaka da ita!”
“Kasan dai ya riga ka fara sonta, kuma akan me zaka shiga tsakaninsu gaskiya Malik akwai sonkai a lamarinka!”
“Me nayi na son kai?”
“Ka rabu da yarinyar ka bar shi da ita.”
“Kasan yar Nasr Hadejia ce, sannan ba zan barta hannun mutumin da bai da aiki sai mugunta da zalinci, kada ka manta Rahilah sakamakon zalincin shi ta rasu ta bar Nadrah, ka zata naki auren Nadrah ne domin kai na? Na ki aurenta ne domin amfani da ubanta zai yi da ita, ina tare da. Shi ne a matsayin wanda ya kula da ni lokacin muna gidan yari. Bayan nan hatta numfashina idan da xai san yadda zai datse min ita tow ba makawa Shatima zai yi don haka ka kula. Lalla Salmah itama nata haukar bai bata lissafi daidai ba.”
Shiru yayi ya cigaba kallon kofar da wutsiyar ido, har wurin karfe daya daura sannan ta bude kofar, fuskarta ya kumbura sakamakon barcin da ta sha ba na wasa ba.
“Shi ne ba a tashe ni ba?” Ta fada tana duba wayarta. “Me kike nima?” “Wayata mana, zan kira gida!” Mika mata yayi, ta fara Duba sakonnin mutane.
Kiran Hafsy tayi ta ce mata.
“Baby gani nan, ki cewa Ammy gani a hankali!”
Kashe kiran tayi ya kira Number Shatima.
“Boy ba ga kiranka?!”
“Jiya ina kika shiga hankalin kowa a tashe?”
Kallon fuskar Malik tayi, ba yabo ba fallasa ta ce mishi. “Ina Menk Jordan Mansion ne!”
“Innalillahi! Meye yayi Miki? Dan Luwadi ne fa, dudduniya tasan baya niman mata sai maza, ina bai miki kome ba?”
“Hmm-Hmmm!” Ta fada a sanyayye.
*Baby gani nan zuwa!”
Katse wayar tayi ta cewa Malik.
“Zan tafi”
“Wuce ki karya!” Yadda yayi maganar yasa ta wuce, domin a sharadin su babu gardama.
A hankali ta nufi wurin abincin, ta zauna shima da kekenshi ya iso wurin, ya ɗan mike tare da bawa hannunsa karfi ya zauna a kujeran table ɗin.
Kallonshi tayi na wani lokaci kafin ta ce mishi. “Yasa ba zaka mai da cin abincinka kasa ba? Idan a kasa ne zaka fi samun nutsu. Amma shi hannun da kake daukar karfin kafar ka bashi zai iya gajiya, idan aka yi al’akari da shekaru wasu abubuwan zasu faru marasa dadi.”
“Hmm! Na saba da saman kawai a bar ni nayi yadda nake so!” Daga haka ya buga wani dan karfe sai ga kukun ya fito.
Shi ya shiga server ɗinsu.
Kamar wanda aka cillo shi ya shigo falon,babu sallama.
Kura mata idanu yayi ya nufe ta.
“Taso muje!”
Kallon fuskar Malik tayi babu wani matsalar kome abincinshi yake ci. “Taso muje nace!” Zare hannunta tayi tana me cigaba da cin abincin. “Ke taso muje!” Duban farfesun kaza Malik yayi ya kara mata. “Ci ki kara weight! Ina son mace me kiba kaɗan!” “Ni bana son kiba!”
“Ok ci!” Fisgota Shatima yayi ya ce mata.
“Duk abin da zaki ci daga hannunshi haramun ne, muje na baki kome da kike bukata!” Zare hannunshi tayi daga nata, tana kallon Malik.
“Duk abinda zaka bani, ba zai kai wanda nake da shi anan ba, ka tafi Malik nake son zama da shi!”
Cikin fushi ya ce.
“Tirsassata kayi ta zauna da kai?”
“Bai tirsassani ba, ni ce na ga dacewa haka!”
“Zeenobia kada kiyi abin da zai saka ki danasani, baki dace da shi ba. Shi ba mutumin kirki bane, idan kika juya bayanki wuka zai dabb’a miki, idan kika juya gabanki ya jima da cilla cikin Ukubar rayuwa. Kizo muje KE RABONA CE!”
Girgiza kai tayi tana faɗin.
“Kayi hakuri, zan zauna da shi.” Dukar table din yayi yana faɗin.
“Waye kai da zaka tirsassa mata!”
“Juyawa yayi yana kallon Zeeno.
“Taso muje babu abin da zai miki!”
Ruwa Malik ya sha, sannan ya ce mata.
“Idan zai iya biya na kudina,.kuje abinku idan kuma ba zai iya ba, ki ce ya fita ya daina min hayaniya cikin gidan domin bana son hauka!”…..
book 2 zai zo muku Whatsp da Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/10, 9:17 PM] Yan Mata: Volume:6 Choose Me or Him

Buga table din Shatima yayi yana faɗin. “How dare you, zaka ce na biyaka? An ci kuɗinka Malik anci kuɗinka kuma we shud see waye zai Malik Zeeno!”
Baya Malik yayi da kujeranshi ya ce mishi.
“Ba wani abu kuɗina! Zaka bani sai ka daina min haushe kamar jaki!” “Don’t insult me! Malik kada ka zage ni domin na fika mutunci a idanun duniya!”
“Waye kai?” Malik ya tambaye shi, “Nace waye kai? Kai waye?” Ya kuma tambayar shi a sanyayye. Amma daga yadda fuskarshi take murtuke zai tabbatar maka da cewa ranshi a b’ace yake. “Ni kake tambaya? Ni Khamis Shatima, mutumin da kowa yasan ban ketare iyaka ba? Bana bin mata bana bin maza. Ni ba makashi bane irinka,. Ni ba kazami ba ne me hada halak da haram! Kai wani ne da xaka yi alfahari?” Toothpick Malik ya dauka ya shiga sakace haƙoranshi. “Mtseeeeeew! Na zata wani Mashahuri gawurtaccen namiji ne, ashe kwailata ta fika cikar nasaba. Oya pay my money ka ɗauke ta ku tafi.”

“Kai Malik!” Ya shure ture keken guragu Malik ɗin da zai zauna. Garin rike keke ya fado akan kujeran, “wai meye haka ne?” Zeenobia ta tambaye shi, a hasale. “Me kike tambaya na? Ki rabu da shi kizo muje!” Ya fada yana shure kenan. Sake tare shi tayi tana faɗin. “Wai lafiyarka Boy?” “Lafiya ta lau, wannan kazamin mutumin nake so ya fita a rayuwarki! Macuci azzalumi!”
Shigowar Elbashir ya sami Malik zaune a kasa. “Subhanalillahi! Malik!” “Dauki Baby girl ku bar gidan nan!” “Ka da ka kuskura ka tab’a ta, domin idan na gama da nakasashrn nan zan dawo kanka!”
Janyo keken Zeeno tayi, cikin takaici ta ce mishi. “fadar da kake ba shi zai baka abin da kake bukata ba, don Allah ka kyale ni, ka je na gode!” Fisgota yayi yana faɗin.
“Billahi azim, babu dan iskan da ya isa aurenki.”
“Ka tafi da ita Bashir!” “Malik me kake nufi da Zeenobia? Ke dawo nan! Ko zab’a ko ni ko shi?” Baki daya bata taɓa cin karo da irin wannan masifar ba, hawaye cike a Idanunta ta ce mishi. “Ba da abun da zaka biya min kuɗinshi, da na salwantar. Sannan babu wata hanyar da tafi na zauna a karkashin ikon shi na zabe shi.”

“Keee! Zeenobia kin san waye shi?”
“Bashir ka tafi da ita!” Domin Malik ya fahimci, baki daya kunyanta shi Shatima yake shirin yi, jan hannun Zeenobia yayi tana kallon Malik da yake zaune a kasa yana kallonsu damuwa da tashin hankalin da ya hango a fuskarta ya sashi sake mata murmushin yana gyada kai. Ya kai mishi Mangari, sai dai kuma kafin hannunshi ya isa ga Malik yayi nasarar cika mishi toothpick din a tafin hannunshi, tare da murde hannun sai da ya durkusa, kuwa cikin fushi ya sakar mishi wani irin duka a gadon Baya, sai da ya sume.
Sannan ya ture shi, tare da jan kekenshi shi, ya koma kai ya zauna, cikin izza.

“Bindin Malik don Allah kada wani abu ya faru da shi, ka ga ya ture shi a ƙasa.”
“Malik zai ji da kome!”
“Ba zai iya ba, kana ganin shi ba kafa ba”
“Ranar da kika gudu a asibiti taya kika tafi asibitin? Kin kai Kanki ne?”
Girgiza kai tayi, tana faɗin. “Amma kuma.”
“Trust me, babu abinda zai faru.” Yadda yayi mata maganar sigar lallashi yasa ta gyada kai, yau ta ga lukutar masifa.
“Yanzu zabi yana hannunki, rayuwar al’umma charity House da kuma Maza biyu, idan kika bi ra’ayinki, rayuwar al’umma yana danger. Idan kuma kika zabi al’umma baki da case domin ko tsinke naki Malik ba zai barshi ya samu matsala ba.”

Baki daya ta shiga damuwa, haka suka isa gida wurin karfe uku na yamma, ta wuce cikin gidan, sai murna suke. Kai tsaye ta wuce ɗakinta bata iyawa kowa magana ba, haka suka yi ta binta da idanu.
“Allah ka ga zuciyata, bana son tsoho. Amma baki daya bawan Allah nan ya min bazata.” Ta fada tana jin kamar ta fasa ihu, kuma pride irin nata, ba zai saka tayi kuka ba, sai ta zauna a dakin shiru. Ammy da Abbas suka shigo Dakin, zama suka yi kusa da ita. “Me yasa kika koma haka? Malik ya miki wani abu ba ne?” Hawaye ne ya zubo mata,a hankali ta fashe da kukan da ta rasa waye zata gayawa tarkon da Malik ya d’ana mata.
“M
Ammy na shiga uku!” A rude Ammyn ta d’agota. “Me ya same ki? Malik ya miki wani abu ne?” Kai tayi tana faɗin. “Bai min kome ba.”taki gaya mata domin tasan matukar ta gaya mata gaskiya Ammy zata ce a bada gidan tunda suna da enough money da zasu iya sayan wani dan zama iya su!

“Kawai yace yana sona ne, ni kuma bana sonshi, amma ban san ya zan gaya mishi bana sonshi ba, domin yayi min tsofa!” Murmushi Ammyn tayi tana faɗin. “Ba shi kenan ba, Y’ata tayi goshi amma kin san da haka me yasa kika kwana a gidanshi anya Yar kunamar da na sani ne?” Wacce babu ruwanta da maza? Kada ki kuma kwana gidan wani namiji, duk da ba akan sonki da yake yi kike kuka ba, nasan sai dai akan wani abu na daban, idan har aka ne, tow ki daina kuka, Allah yana sane dake. Sannan idan wani abu ne ko gaya min In sha Allah ba zai gagara ba!” Tausayinsu ya kara cika mata zuciya. “Zimmmmm!” Taji wani irin kara, duba pepar bag din da Elbashir ya bata ta leka, waya ce sabuwa dal, wani kwali pink colour, a hankali ta ja kamshin turaren Shumukh ya daki hancinta.

A hankali ta shiga warware igiyar da aka rufe kwalin ta bude shi d’aga murfin tayi, tare da shaƙar kamshin shumukh, take dakin ta ya game da kamshin, “ikon Allah ji wani turare me shegen kamshi!” Kamar an cillota ta fado dakin. “Kai kutumalesi! Baby wannan kayan haka?” Karamin Alqur’ani ne pieces, izu goma goma. Sai jalbabba da counter. Su kenan kayan a cikin kwalin,domin kuwa kyauta ce ta musamman.

A hankali take kallon kayan, saka hannu tayi a jakan ta ciwo set na kayan kwalliya, sake baki yayi tana me zubawa a gaban Ammy da Hafsy. “Wani egen kika samo mana?” Juyar da kai tai tana faɗin. “Mayor Malik Menk Jordan!”
“Ahirrrrrrrrrrrrr;” ta rangad’a guda, “Don Allah nice me Miki kwalliyar biki!” Tab’e baki tayi, domin da sun san abin da ta faru ba zasu shiga farinciki haka ba, a bangaren hawaye ne yake zuba, ita tayi biyu babu. Babu ba saurayi matashi dan shekaru ashirin da takwas zuwa talatin ta kare a tsoho me furfura..bata san lokacin da ta fashe da kuka ba. Duk suka zuba.mata idanu domin ga abin dariya ga abin tausayi. Haka ya ci kukanta idan ta tuna cewa bayan tsofar baya tafiya akan kafarshi sai taji hankalinta ya kuma tashi, haka tayi ta kuka tana jin kamar wani abu ne yake yawo a ranta, suma gajiya suka yi da rarrashinta suka zuba mata idanu, duk abin da ya saka Zeeno kuka ai kasan ba karamin al’amari ba ne, amma yarinyar nan tayi ta kuka. Zuciyarta da shaidan suna kara ingizata. *Tsoho da furfura, nakasashr mara tafiya. Dan luwaɗi. Zai aure ki domin covering issues dinsa da siyasar shi.*
Yadda take kuka zaka rantse da Allah mutuwa aka mata, amma ina tsabar tashin hankali da damuwa. Kiranta yayi tayi har sai da ta gaji ta dauka. “Me kake so na maka? Ba ka ce zaka aure Ni ba, me kake so kuma?”
“Calm down! Idan kin huce an jima za a zai daukarki zamu fita shan iska!”
“Babu inda zani!” Ta fada tana kwalla.
“Karfe takwas da rabi bana buƙatar African time, ina bawa lokaci muhimmanci!”
“Malik don Allah ka kyale ni!”
“Taya zan kyale ki? Mrs Mayor! Gaya min taya zan kyale ki? Idan ba so kike duniya ta dauka barazana na miki ba!”
“Mene ne banbancin? Barazana na nawa kuma? Al’umma charity House yana karkashinka,sai yadda kayi da shi.”
“Yes na yarda da haka, amma kuma rashin zuwarki zai saka a fara yayyata gulmar da zai fito nan da wasu hours!”
“Malik!”
“8:30pm ina jiranki, rabona da fita yawo na manta so a ci gayu sosai!”
Kasa magana tayi wato Malik ya gama cin uwar rena mata hankali, cikin shashekar kuka ta ce mishi. “Babu inda zani!” Dariya yayi ya ce mata. “Ok Abbas ga Zeenobia!”
“Yan mata!” “Abbas ka tawo ka bar wurinshi.” “A’a gashi ya samu Baban Hibba an ba ni auren hibba!”
“Mua Baby ina jiranki, kada ki sake raina ya b’aci koda yake raina ba zai barci ba, zan zo na gaida Ammynku!”
Zabura tayi tana faɗin. “Malik me yasa kake min haka ne? Me yasa ka shiga rayuwata ka hana ni sakat?”
“Ina da naci a duk abin da na saka kaina. That’s all!”
Kwalla ne ya kara tuttulowa daga idanunta. “Allah yana ganinka, sai ya saka min!” “Daga taimako sai a nime yi min Allah ya isa da tattabatsinin!”
“Kai ka sani!”
“Tabbas ni daya na zan san yar kwailata!”
“Ni ba yar iska bace!” Dariya yayi yana faɗin. “Zan so ganin yadda kike kuka, sai kin fi haka kyau!” Yadda yaƙe zolayarta zaka ɗauka babu kome a ranshi, sai dai kuma haduwa da Zeenobia ya taimaka mishi wurin sauya shi sosai. Domin a da can ma bai da yawan sakewa. Balle yanzu da abubuwa suka canza, sai dai shi mutum ne me wanda ya san sirrin rayuwa da iya amfani da mutum domin cimma manufar shi a sassaukake.

Kashe wayar tayi baki ɗaya.

Shatima bar farka ba, sai wurin karfe biyar na yamma. Dafe kirjinshi yayi da yake shirin fashewa. Ya juya tare da kallon gefenshi Malik ne zaune yana karanta jarida. Ya kara kallon shi sosai tabbas murde shi yayi ya zuba mishi dundu a gadon Baya. Yunkurin tashi yayi kirjinshi ya amsa.
“Tsinanne kashe ni kaso yi? Kuma daga yau xan cire hannun jarina a kamfanoninka”
“Eh tow ina taya ka,murna kasan dai babu na biyu na a saka hannu jari a kasar nan. Karewa Ni nake da kaso mafi girma a kamfanin KJK!” Dafe kirji Shatima yayi tar da tashi zaune kamar zai hantsilo daga gadon. “Idan naso na karya kowa ina da wannan Powerful! Ina da karfin tsiya da zan rushe mutum daga sama, na san kome na kuma san halin kowa. Idan na ce zan mai da ka abokin gabana wallahi mafaka ba zaka samu a kasar nan ba, balle kuma a garin nan babu shegen da ya isa baka mafaka. Ban damu ba don ka cire hannun jarinka sam baka bani tsoro ba, sai dai ka sani Ni Abdul Malik bana cikin mutane masu tsoro da shakkar karyawa.

A duk lokacin da haka yazo min ina daukar shi, matsayin darasin rayuwa. Ka zata ban san shirinka da ka turo min auren Nadrah ba ne? Ni mutum ne da kafin ka iso min da bukatarka na san dalilin haka, da na amince na amshi auren Nadrah da yau an raba kome nawa an kwace ko? Hmmm kayi tunani da 6 dinka mana. Allah ba zai nakasani ya kuma hana ni hikima ba, domin da Abdul Hakim ana saka min da wallahi baka isa ba, Ni Abdul Malik ne shi yasa nake mulkarku ko kuna so ko baku so, ni sarki ne a garin nan. Bakin ciki,hassada, Kyashi, a jikinku yake duk yadda wani yafi ku sai kun adawa ce shi. Sai kun nuna mishi shi ba kowa bane, shi bare ne, bai san kan rayuwa ba. Na gaya maka da sassaukake murya ka nisanci Zainab idan kuma na kuma ganinka .” Lumshe idanunshi yayi ya bude shi tar sannan ya ce mishi. “Zan yake maka azzakarinka idan kana ganin karya ne bismillah ga fili ga me doki.”

Daga haka ya juya kekenshi shi, sai kuma ya ce mishi. ” Baka san me yasa Zainab ta ji haushinka ba? Ture ni da kayi sannan, ka kuma ture keken. Ni kuma naki kula ka, shi jarumi a gaban macen da yake son burgewa lusari ne, yana tadda jarunta shi ne a bayan Idanunta. ” Ya kai yatsar shi kanshi. “Ina lissafi da shekaru na, ni ba matashi bane, amma zan iya hawa skill matashi, ina abu na ne da lissafi da ace ka iya tow ba makawa ka gama da ita, kasan me naga bakinka yana rawa ka kiyaye abin da zai fito.”

Daga haka ya tura kekenshi shi, yana faɗin. “zaka iya amfani da kowacce hanya amma kan Yarinyar da na Zabe a daren da wata yake cikar shi, sai na manta da halaccin da ka min na kararaya kasussuwanka, sannan ta manta da girman abotar mu a tsakanin mu!”
Kafin ya saka kai ya fita, rintsa idanunshi yayi tare xa kiran Faruq, yaronshi ne ko nace drive ɗinshi. Shigowa yayi ya ce mishi. “Gani sir!”
“Ina wayata!” “Gashi nan!” “Murmusawa yayi ya ce mishi.” Ka tabbatar ka kira Zeenobia ka gaya mata, Malik ya min dukar mutuwa, ina kwance ban san inda kaina yake ba!”
“Ok sir!”
“Maza kirata!”
Ai kuwa ya shiga kiranta wayar bata shiga ba, “Yallabai wayar bata shiga ba!”
“Kira min Jalilah!” Kiranta yayi yana shiga ya mika mishi. “Jalilah! Kina ina Malik ya samu wata yarinya zai aura! Ke ya lalata miki rayuwa yaki aurenki, tow ki sani ni n janye auren da zan bashi na Y’ata ki san yadda zaki yi Yarinyar ta bijire mishi.”

Kashe wayar yayi bai bata damar magana ba, ya kira Lalla Salmah..
“Uwar wayo, tow Malik ya samu wata yarinya danya sharab, kuma ya ce ba zai auri yaran mu ba, sai ita yarinyar damar ku ce ni dai na hakura domin akan al’amarin ya dake ni,dakyar nake miki maganar nan!”
“Kana ina yanzu?”
“Ina asibiti ba lafiya an daure min bayana zuwa kirjina;”
“Innalillahi wacce shegiyar ya samu haka?”
“Wata yar jagaliya ce, akan Yarinyar zai iya kashe kowa.”
“Al’amarin yayi ƙamari ne haka?”
“Ya wuce yadda kike tunani! Lalla Salmah, idan na mutu ki rike min Nadrah kin san bata da uwa!” Don makirci ya kama tari, kamar tanshi zai fita, ya kashe wayar baki daya, yasan hankalinsu zai tashi.
Komawa yayi ya kwanta, yana sake wahalallen murmushi. Ko yanzu kasuwa ta watse dan koli ya ci riba, zai ga yadda Malik zai auri Zeenobia. Dariya ce ta kwace mishi, tabbas ya daku a hannun Malik, ya haɗa shi da matan nan, sannan ya koma gefe ya hada shi da Ita kanta uwar gayyar, Zai ga yadda zai escape daga sharrinsa dole Zeenobia ta zabe shi ta bar wani banza can. Sannan kafin nan zai san yadda zayi a sauke Malik a Mayor da karfin tsiya domin….
book 2 zai zo muku Whatsp da Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/10, 9:17 PM] Yan Mata: Volume:7 Primero Eatery
The best restaurants ne a garin Keivroto, gidan cin abincin da kudin table daya ya isa wasu iyalan cin abincin kwanaki shekara guda zuwa biyu, kafin ma wannan lokacin, ita kanta gidan abincin tun karfe biyu na rana aka rufe shi, tare da ɗaukar abincin da ya rage aka yi sadaka dashi domin Malik yayi odar gidan cin abincin baki daya na tsawon awa daya zuwa biyu.
An gyara wurin tare da kawata shi, da decorations masu daukar hankali kamar biki za a yi a wurin. Duk wanda y zo wurin za a maida shi a ce an rufe babu abinci wanda a ka’ida sai karfe sha daya ake rufewa, ba karamin kudi Elbashir ya kashe na kawata wurin ba.

Don haka sai da aka saka masu yar kid’a, irin cool music din nan, yadda kana gani zaka san an shiryawa zuwa wurin ne, na musamman domin wannan daren
A bangaren Malik kuwa, me gyaran fuskarshi ne yazo ya shiga gyara mishi fuska babu abin da ya bari sai yar kakkaurar gashin baki me zagaye da yar kasumba, itama an rage shi ya fito kamar dan matashi me shekaru arba’in a duniya, doguwar fuskarshi da gashi ya kawata shi,

Ana gama mishi gyaran fuska da aski ya shiga bandaki, yayi wanka, sannan ya fito daure da towel. Yana amfani da kekenshi, a hankali ya iso gaban closet ɗinshi, ya shiga ciki yana kallon kayan da suka dace da shi. Idanunshi ne ya sauka a kan wani expensive suit, Stuart Hughes diamond edition, dark maroon sai wani irin sheki yake me matukar daukar idanu.

Idanunn shi ne ya sauka akan boxes Calvin Klein, ya dauka tare da sakawa sannan ya tura keken ya Ciro kayan dake leken automatic ne, tana iya karawa mutum tsawo, yana gama daukar kayan ya shiga sakawa, sannan ya dauki takalmin shi. Da safa da duk abinda zai bukata ya nufi waje a can ya cigaba da sakawa. Yana gamawa ya dawo dakin ya agogo da zobenshi masu daraja, sai sandarshi wanda yake makale a jikin kekenshi. A hankali ya nufi wurin mirror ɗinshi, ya shafa man gashi na maza, sai ga gashin yana wani irin sheki har da ɗaukar idanu.

Haka ya fito ya nufi waje, koda ya ido falon sassanyar kamshin turaren imperial Majesty ya cika falon, juyawa Elbashir yayi ya sake baki yo ko zamanin samartaka shi bai wannan wankar ba, sannan ya san wannan suit din jikinshi ba kasafai yake saka su ba, sai idan zai yi baƙi na musamman. Yake saka su amma yau dake ya shirya haduwa da Zeeno shine hr da cancad’a kwalliya.
“Malik anya kai ne kuwa?” Cikin basarwa ya ce mishi. “What happen?” Gyada kai yayi yana faɗin.”not amma kuma duk kwalliyar ganin Yar kunama?”
“Me kake na gaya maka Bashir?” “Tsakani da Allah aurenta zaka yi?” Sunkuyar da kanshi yayi sannan ya d’ago ya kura mishi idanu ya ce mishi. “Ina son haihuwa ne, koda ace na mutu zata kula da abin da muka haifa, sannan ita daya ce ba zata bukaci raba dukiyata ba, sai dai daga ranar da na aureta zan daidaita kome da ita.”

“Malik ba a yabon dan kuturu, sai ya shekara arba’in da yatsu, sannan da kake ganin kamar duniya da dukiya basu dame ta ba, zata zo ta bukaci haka. Ni dai abin da nake gani kawai ka hakura da ita domin ga Jalilah da Lalla Salmah zasu iso gobe, ya zaka yi da su?”
“”Tunda na zaɓe ta, ba daina jin fargaban yadda kome zai zo min, amma ka sani idan ba kai ba waye ya gaya musu zancen Zainab;” girgiza kai yayi cikin damuwa ya ce mishi. “Wallahi ban tab’a daukar zancen ka na bawa wani ba. Malik baka yarda da Amana na bane har yanzu?”
“Baku nake tsoro Baz dabbobin da suke kirazanku nake tsoro, domin zuciyar mutum tafi gangan jikinshi illa!”
“Bana cikin masu irin wannan zuciyar, Allah zai nuna min lokacin da xan biyaka!”
“Hmmm! Muje ko”

Kamar ba zata shirya ba, sai da ta ci kukanta, ta koshi sannan Ammy ta shigo dauke da wasu jakuna ta mika mata tana faɗin. “Yanzu Abbas ya kawo min, wai inji Malik a kawo miki, zaku fita.” Sharrrrr hawaye ya zubo mata.
“Tow me na kuka kuma?”
“Ammyn tsoho ne fa?”
Murmushi tayi sannan ta ce mata.
“Amma ai kin kai aure ko za a barki ne kina kallon kowa ba dadi? Aure shine cikar mutuncin kowacce Y’a mace, na kira Hafsy ta gyara miki fuskar ki.”

Share kwallan tayi, tana faɗin. “Ammy kin yarda na je kenan!”
“Kayya ai yarda da nayi dake, ko cikin maza dubu kika kwana ba zan tab’a zarginki ba. Maza watsa ruwa ki fito!”
Hawaye ne sharrrrr suka zubo mata, haka ta shiga ban daki ta watsa ruwa, kafin ta fito Hafsy ta iso. Tana fitowa ta shiga fitar da kayan tana faɗin. “Durun uwa salatin maguzawa. ”
D’aga rigar tayi tare da fadar sunanshi. “Odette Square neck, midi dress!” Zaro wayarta tayi daga aljuhun rigarta ta ce bari na ga kudin rigar. Zeenobia Kinsan nawa kudin kayan?” “Kin san Allah, zan fasa zuwa!” Ajiye kayan tayi ta shiga tayata shiryawa har ta gama ta mata makeup, sannan ta shiga dauko dan kunnen Baroque pearl , stone wave, sai agogon Ferragamo women’se.
Haka ta saka, ta Ciro mata jakarta a cikin perpa bag din, a ledar shi.
“Allah ya saka ni a damshi. Jimmy Choo, Callie black suede bag and shoe.

Shirya tayi cikin nutsuwa ta kuma gyara mata fuskar ta sosai, sannan ta ce mata.
“Bani mayafinki tunda kayan red ne, zai dace da bakin mayafi sai na daure miki shi kamar turban ”

Haka ta dauko dan kwalin abayar ta mika mata, ta daura mata, shi yayi mata kyau, sannan ta dauko kwalin turaren Shumukh ta fesa mata. Kwankwasa kofar aka yi, “Yes!” “Elbashir ne Malik yana jiranki!”
Tashi tayi ya kalli Hafsy da ta ce mishi. “Okay yayi hakuri gata nan zuwa.”
A hankali ta karasa saka takalmin ta bar dakin makale da jakarta, ta nufi dakin Ammyn. “Ammyna na fit….” Sake baki tayi tana kallon Elbashir a falon Ammyn suna hira da Inna da Abbas. “Kai yar nan kinci sunarki sarauniyar girka me daraja, sai kin dawo.
Haka suka fito, daga dakin tana baya yana gaba, har wurin motar da Malik yake, phantom menace Ii, a hankali ya bude mata ta shiga, hango Malik tayi a hakimce yana wani baza hanci, kamar ta rufe shi da duka, wannan shi ne yake niman aurenta, wacce irin lalacewa tayi da zata kare da auren tsoho, dube shi don Allah? Wata zuciya ta hasilata.
“Tsaki tayi tare da dauke kai. Yaji zafin tsarkin don haka ya ce mata.
“Ko ba ni ba, kada ki kuma yiwa wani tsaki!”
A tsiwa ce ta ce mishi. “Idan nayi me zaka yi? Kashe ni zaka yi? Iyakaci ka saka a kashe ni!”
Domin ya bata haushi ya ce mata.
“Wai ai nafi karfin na kashe kyakyawar irinki, kawai abinda na sani zan cinye wannan kyakyawar bakin naki yadda gobe ma ba zaki kara min tsaki ba”
Rufe bakinta tayi, tana faɗin.
“Na shiga uku, ni ba yar iska ba ce, wallahi ban kai nan ba, rashin kunyata bata kai har nan ba”
“Idan har bata kai har nan ba tow wallahi a dai na min tsaki ko kuma sai na cinye bakin!”
Kauda kai tayi tana jin kwallan bakin ciki yana cika mata idanu. “Yau kinci abinci kuwa?”
“Ban sani ba! Idan kaji haushi ka daura min nace idan kaji haushi ka dura min!”
“Kayya saurin me kike? Nan wani lokaci zan dura miki abinci har da masu cin abinci anan dinki!” Ya nuna mata cikinta.
A firgice ta ce mishi. “Amma ai babu maganar ciki a sharadina?”
“Eh tow idan kika cigaba da gaya min maganar da ta miki, sai nayi koda karfin tsiya ce!”
“Innalillahi! Ubangiji ya min tsari da fyade yanzu kai baka ji kunyar cewa zaka min fyade ba?”
“Kina mata ta, meye a cikin don na miki fyad’e? Sunnar ma’aiki na gyara sai ma samun ladar da zan yi!” Toshe kunnanta tayi, tana jin kamar ta bude kofar ta fice da gudu, baki daya Malik ya goge mata yar karatun sallah.
“Dama haka kake?”
Tab’e baki yayi yana faɗin, “na wuce haka, me kike tunanin tsohon kasungurmin tuzuru zai aikata bayan haka?”
“Akwai mata irinka kaje ka same su mana why me?”
Shiru yayi kamar yana nazarin maganarta ya ce mata. “Gaskiya ba zan samu irinki ba, su duk sun tsufa ke kuma danya jagab ce!” Wani irin kara ta sake sai da drive ya taka.birki jin tayi shiru kuma Malik bai ce kome ba, yasa shi cigaba da tafiya.
Har suka isa wurin cin abincin, bata kuma yarda ta takale shi da magana ba, ta lura bakin shi bai da cikakken daraja, a bakin wurin cin abincin suka tsaya aka fitar mishi kekenshi, sannan ya fita a hankali. Ya zauna a keken kallonshi tayi wani malolon bakincikin ya kuma turniketa.

Ta wani haɗe rai, domin min har da Manager gidan Abincin suka tawo tarban su. Haka kawai sai take jin wani irin abu, wato daraja da girma yana tare da Malik ko yayya ka rabe shi, sai duniya ta mutuntaka, kamar su kwanta a kasa haka suke ta gaishe su, har suka isa inda zasu zasu ci abinciin.

….. Wurin babu haske sosai, da duhu suka isa wurin. Zama tayi tare da kallon shi. Shima tashi yayi a kekenshi ya zauna a kujeran a hankali yana murmushi.
“Kiyi hakuri, ki karbe ni a haka laluran shekaru goma sha uku da samun shi, ba haihuwa ta aka yi da shi ba.”
Duk da haushinsa da take ji, ta wannan bangaren sai taji baki ɗaya ya bata tausayi.
Ta bude baki zata yi magana, aka fara kida me taushi mara kara da sauti. Irin blue sounds me daukar hankali, ga sanyi me dadi a wakar, kallon yadda lokaci guda ta dan sake ranta, tsayawar da kidan. Wata dattijuwa ya fara kid’a piano, me ana amfani da gitta. Ga wani irin yanayi na fuskarta yanayin damina, iska me zafi zafi sanyi sanyi hade da kamshin kasa.

“Sannunku da hutawa!” Jerin yan mata, dauke da kayan abinciin aka shiga jera musu, Idanunta yana kan waje. Har suka gama shirya wurin. Sannan suka juya suka bar wurin. “Zainab!”
“Na’am;”
“Mu ci!”
A hankali ta dauki fork ta rike a hannunta, tana juyawa tana kallon shi. “Wannan yanayin yafi dacewa da Yaro Matashi ko?”
Hadiye yawu tayi tana kallon kasa, “ki ci zan duba al’amarin, idan da hali sai na rage yawan watanin zuwa wata biyar ba?”
Hadiye yawu tayi tana fad’in. “Wata biyar da gaske? Da gaske wata biyar kawai.”
“Baki yarda da abinda nace ba ne?”
“Na yarda mana”
“Tow ci abinci!”
A nutse ta fara cin abincin, tana sake murmushi tana kallonshi. “Kayi kyau!”
“Ai kin fini kyau”
“Hmmm ji wani wayo.”
“Bai kulata ba, sai ma cin abincin da yake tayi, itama tana ci a hankali. A hankali ta ajiye Fork ɗin. “Ki kara mana!”.
“Na koshi, bana cin abinci me nauyi da dare!”
“Ai gara ki fara ci, domin ina son kafin mu rabu, ki tara kumatai!”
“Hmm nafi son na rayu babu kiba sosai, domin ba zai min kyau ba……
book 2 zai zo muku Whatsp da Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/10, 9:17 PM] Yan Mata: Volume:8 behind the truel .
Ganin yadda take wasa da drinks din da aka saka musu ya ce mata.
“A matakin karatu me kika karanta?” Juyar da kai tayi tana b’ata rai kafin ta ce. “Diploma a business administration!” Kallonta yayi sosai sannan ya ce mata.
“Me yasa baki yi degree ba?” Watsa mishi harara tayi ta ce mishi. “Hala kaji a falo na girma, shima diplomar don kar a rena ni nayi, amma babu abin da zai saka ni abin da ban yi niyya ba.”
“Kinga kuwa ni degree na uku a fannoni daban daban, na farko akan course ɗinki nayi, na biyu akan tattalin arzikin kasa da na duniya, na uku akan siyasa da kabilanci. Yanzu ina dab da hada na hudu akan nazarin dan Adam!”

Tabe baki tayi tana faɗin, “hmmm! Tow me yasa baka yi karatu a cos daya ba, kabi ka bata lokacinka a kan kwasa-kwasai?”
“Ai ban gama baki labarin ba, ina da kwarewa akan!”
“Ka hana gaji da labarin digirin digirgir dinka, kai ko lahiranka baka tunawa sai aikin karatu da kashe mutane?!”
“Inji waye ya ce miki na kashe mutane? Eh na kashe su, sai dai Allah ya ce idan ba zaka iya hakuri ba ka rama daidai da abin da aka maka, ko ke da zaki bincika rayuwarki ta baya, Allah ne zai raba ki da mutanen da suka zalince ki.

Shi ɗaukar fansa ba kasafai ake bukatar shi ba, idan kayi hakuri zai wuce amma idan ba xaka iya hakuri ba ramawar yafi, duk da hakurin yafi ramawar alkhairi.”
“Tsakaninka da Allah baka danasanin kashe mutane?” Gyara zama yayi ya ce mata.
“Sam bana danasanin domin sun kashe min kowa nawa, sannan suka bani makami domin na daure kaina kina tsammani zan yafe musu?”

Kura mishi idanu tayi sannan ta ce mishi.
“Kana nufin kashe naka iyaye aka yi?” Gyara zaman shi yayi sannan ya ce mata.
“Ai shi ne cinikin rai, kuma Allah ya gani ban yafe musu ba, shi yasa na rama. Domin har gidan Yarin suka bini.”
“Kayi zaman gidan kaso?” Ta tambaye shi a tsorace. D’aga kafad’arshi yayi alamar Eh.
“Na shiga uku, kuma ka fito bayan shekara nawa?” Gyara zaman shi yayi yana faɗin. “Matsoraciya, na fito bayan shekaru ashirin da biyar!” “Kuma kana da shekara nawa ka shiga?” “Like 17 years!”
“Sha bakwai a tara da ashirin da biyar, shekaru arba’in da biyu!” D’age mata gira yayi yana faɗin. “Tow meye a cikinshi?” “Gaskiya i pity for you! A can ka haɗa duk digirorinka?”
“Eh a can nayi na farko da master! Na uku nayi shi a demark, yanzu ina yi nan Keivroto.” Gyara zama tayi tana faɗin. “Kuma kana zuwa class;” kallon yadda ta ɗan k’amk’ame jikinta yasa shi ɓalle botirin top din rigar shi ya janyo kekenshi ya zauna sannan ya matso har inda take. Ya ya daura mata rigar.
“Ko zamu tafi ne?” Ya tambaye ta,
Yatsina fuskarta tayi, sannan ta ce mishi.
“A’a ka bani labarin yadda kake atandin class!” Murmusawa yayi ya ce mata. “Zainab kenan.” Ya dan sosa goshinsa, sannan ya ce mata. “Ina karatu ne ta online, ba sai naje makaranta ba, bana buƙatar sai na shiga aji, amma idan lokacin Jarabawa yayi ina attending hall.”
“Yo ko da kudi zaka iya sayan jarabawar?”
“Ba dai ilmi ba, akwai masu saya amma yana da kyau, kayi karatun duk inda aka kai maka duka ka kare da kwarewa ba da baki ba.”
“Me yasa kake da kwarin gwiwa?” A hankali ya dauki kwalbar red wine ya zuba, sannan ya dauki cup din zai sha ta ce mishi.
“Wannan ba giya ba ne?” Dake ita normal juice aka kawo mata. Dariya yayi sannan ya ajiye cup ɗin ya ce mata. “Taya ina cikakken dan musulmi kuma bahaushe da ya fito kasar hausa na sha giya? Duk da mahaifiyata baturiya ce, amma bana fatar shan giya.”
Ya dauki kofinta ya zuba mata, kallonshi tayi sannan ta ce mishi. “Kada ka sani shan giya, bayan na hana harshena dandana na duniya, domin ina son naje na sha na lahira me masifar dad’i!”
“Allah ya baki hakuri, sha idan giya ne ki saka a kama ni!”
Kallonshi tayi, ya gyada mata kai dauka tayi ta sha, jin dandanon ba iri daya ba ne yasa ta ce mishi. “Hmm kuma yana da dadi!”
“Allah ko? Kika ce ana sayan ilimi?” Gyara zama tayi tare da saka hannunta dukkan biyu ta harde a Kirjinta. “Tabbas ana saya, ana saya da kudi ko da wani abu dai!”
“Gaya min, me ya faru?” Tura baki tayi tana faɗin idan na gaya maka, ba zaka ka min dariya ba.”
Murmushi yayi ya ce mata. “Duk abin da ya faru zan baki shawara, i by now we’re friends ko?” Gyara zama tayi, ta ce mishi.
“Dakyar na gama secondary school, domin a lokacin yara suka ganni kirana mahaukaciya suke, ko su kira me kashe mutane, na sha wahala a wurin mutane gashi ban san dangina ba, wancan gidan sune komi na, kuma nice kominsu. A lokacin na hadu da wata yarinya bayan na gama secondary school, lokacin da na shiga college. Ita take gaya min idan kana son pass sai ka bada cin hanci ko ka bari Malami ya kwanta da kai!”
“Kuma kin yarda kin kanta da Malamin?” Ya tambaye yana kasa da hannunshi, me dauke da cup ɗin, duk da na glass ne, karfin rikon da ya mishi ya janyo cup ɗin ya fashe a hannunshi. Girgiza kai tayi tana faɗin.
“Kullum nasihar Ammy na tsare mutuncina, sai dai na basu kuɗi. Ni bana cikin yan matan da suke bada jikinsu domin nasara, a lokacin na hadu da wani Malami shi kuma yace ba dan yi pass ba, sai ya kwanta da ni. Ni kuwa na tara yan daba suka mishi shegen duka.”
Ajiyar zuciya ya sauke, yana me sake fasashen cup ɗin, yana faɗin. ” Kin kyauta! A duk lokacin da mace ta bada kanta, domin faranta ran wani tow daga ranar na tsane ta.” Tura baki tayi tana faɗin.”ai ni ba yar iska ba ce.” Daga haka ta juyar da kanta.
“Bani hankychef a saman rigar nan!” Cirewa tayi ta mika mishi, ya ɗaure hannunshi, sannan ya ce mata.
“Naji VOGUE MAGAZINE sun cire hotonki a cover dinsu!”
“Hmmm! Dama ai ko basu cire ba, ni zan tafi har can na roke su, su cire hoton!”
“Saboda me yasa?”
“Saboda kazaman mutane da shaidanun bibiyar rayuwata suke, akwai wani mutum something Wazir yazo har da rungumata.”
“Kuma baki daki gaban dan iska ba?”
“Ai rikon bazata ya min, amma na mare shi. Ya ce zai dawo amma ni ma zan saka su Black su mishi mugun dukka!”
“Yawwa gara da kika kira min sunansu! A ina kuka hadu dasu?”
“A unguwar muka taso, Iyayen Black suna can wani kauye hari, sai Dundurosu a gaban kakarshi ya tashi iyayenshi sun rasu.”
“Sun yi karatu?” “Eh sunyi karatu suma diplomar ce, Black cos din mu daya. shi kuma Dundurosu ya karanci art ne!”
Murmusawa yayi ya ce mata. “Dundurosu yake meye sunan shi na asali!”
“Kabir haruna, sai Black Mas’ud, akwai Paul, ya tafi garin su wurin babanshi a can wani gari wai calaba;”
“Idan sun yarda sun amince, ki gaya min a waya shi Kabir zan tura shi Demark yayi aiki da kamfanin mu na can, shi kuma Black zan tura shi Fisto ina da babban gidan saukar baki ya rike a matsayin Manager, shi kuma Paul me ya karanta!”
“Shi aikin soja yake nima kuma har yau bai samu ba, shi ne aka ce ya kawo kudi, ya tafi garinsu kawo kudin.”
“Ki kira shi, ki ce mishi ya kawo takardunshi zan duba mishi.”
Kallonshi tayi dake ba zata iya shiru ba ta ce mishi. “duk me yasa kake ta basu aiki,domin na gode maka zan yi ba!”
“Nayi haka ne na raba ki da kowani d’a namiji da yake zagaye dake, ki rayu like princess! Ba kamar maza ba.”
“Ban fahimce ka ba?”
“Daga yau ni dake, mun fara soyayya kuma duniya zata shaida haka ne, shi yasa nake son duk wani namiji da yake rayuwarki na nisanta shi dake, domin kada ayi amfani da su wurin cutar da rayuwarki. Kawarki Hafsy ko? Hmmm! Na hadata da Elbashir shi me biyayya ne a gare ni ba zai ki ba, kasancewar ita ta fiki rawankai. Sone friends suna iya dawo da friend dinsu kasa ba tare da sun san da haka ba.”
“Taya zata dawo dani kasa?”
“Hmmm! Ta hanyar da baki zata ba, ba wai zarginta na ke ba, kudi shegen abu ne, babu abin da ba zai iya sakawa ba. Ban yarda ki fita ko ina ba, sai da umarnina.
Babu ke babu harka da yan sanda, babu ke babu fada a layi ko kasuwa, duk wanda ya tunkare ki, kalli can!” Ya nuna mata wani dogon gidan sama ya ce mata
” Dubi wuyarki!” A hankali idanunta ya kai kan jan danger din da aka yi points ɗinta.
“Rayuwarki daga yau, tana tare da ni ne. A duk lokacin da wani abu ya same ki, don take any action! My men there be with you, sannan wannan tracking devices ne, kada ki rabu dashi wanka ko ma meye kiyi da shi, da zarar any weapon ya tunkare ki, zai shaida min ko barci nake.”
“Duk me yasa haka?” A karon na babu adadi da yake jin wani irin tausayinta, ya janyota ta sake shiga hatsari sama da baya. “be a strong lady, as I know you. Kada tsoro ko kasawa ya sa ki fara feel guilty. Ba nace ina tare da ke ba?”
Gyada kai tayi, sannan ya cigaba da cewa.
“Amma ki sani ko ban kawo maganar aure ba, akwai mutanen da ba zasu barki ki rayu cikin salama ba, domin na san waye ni. Ina rayuwa ne cike da makiya, i hope kin fahimci Ni!” Gyada kai tayi sannan ta ce mishi.
“Hatta bindinka baka yarda da a shi ba?”
“Elbashir din ne bindina? Lallai yarinyar nan kin rena min Elbashir. Na yarda da shi dari bisa dari, kai dubu bisa dubu na yarda da shi. Idan kin ga Elbashir ya ci amanata tow wallahi wani abu aka mishi ni dashi ba. Har kwanan gobe Elbashir baya kwana a cikin gari sai a can Waterfall island. Na dawo nan ne kawai don ke!”
“Ni!”
“Yes domin an tab’a gaya min, matar da zan aura ita ce ajalina.” Ware idanu tai tana pointing kanta. “Yes kuma zaki zo ki canza min ƙaddarata! Tun daga lokacin da na ganki naji kece. Amma kuma ke ai cantract marriage zamu yi ko? Kuma babu zancen soyayya da tsoho!”
“Hmmm! Da nayi soyayya da tsoho gara nayi renon dan kwaikwaiyo.”
“Nima haka na gani!” Ya kalli agogon hannun shi ya ce mata.
“Muje mun ji dare!”
Kallon agogon hannunta tayi ta ce. “Sha daya saura!”
“Eh muje!” Haka suka fito garin ya fara sake iska me dad’i da sanyi. “Sai yaushe zaki kara bani damar mu sake haduwa?”
Tabe baki tayi tana faɗin.
“Wai! Ai ni ba zan kuma fita ba!”
“Ai shi kenan!”
“Mutumin tsibiri, na rike ka ko?” Murmusawa yayi, tare da bude mishi kofa ya shiga ciki.. itama kallonshi tayi tana faɗin. “Bindin malik kana murmushi mana, ka wani haɗe rai!”
Ta shiga tana kwantar da kanta, domin barci take ji, “ba zaki yi musu tsara ba?”
“Muje na gaji!”
“Jibi zan zo mu tafi shopping!” Juya kanta tayi tana faɗin. “Ka san me? Ni ba zan iya rayuwar nan ba, domin karya ce ire-iren waɗannan rayuwar!”
“Ni ne makaryaci?”
“No kai ban isa na kira ka haka ba, ni yar talakawa ce, wa ya sani ko Ubana dako yake kafin ya ciyar damu, kasan me? Irin wannan yanayin ga Yaran talakawa irina yana sawa ayi tunanin ko wani abu muka bada. Ƙarshe a ce kwadayi ya sani makalewa. Ina da gishiri ana bani manda!”

“Ko kina bada V ana baki I ba” kallonshi tayi.
“Kai amma baka da kunya;” ta rintsa idanunta, domin sai da tayi dogon nazari ta fahimci v da i……
book 2 zai zo muku Whatsp da Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/10, 9:17 PM] Yan Mata: Volume: 9 The trued behind illegal
Sai da suka iso kofar gidan ta fito shima ya fito, yana karewa unguwar kallo, sannan ya ce mata.
“Zainab baku da makaranta ne a unguwar nan?” Hararanshi tayi ta ce mishi.
“A matsayinka na Mayor me gari, baka san aikinka ba, babu asibiti babu makaranta, sannan kaga yadda unguwar take da manyan lambatu ka tambaye ni, kai abin da ka sani niman kudi baka san yadda rayuwar mutane suke ba, kada ka sake Allah ta tambaye ka, da hakkin talakawan unguwar nan!”
“Gaskiya ban kyauta ba, amma ai laifin ba Ni daya ba ne?”
“Na ka ne mana, kai ne shugaba kuma kai kake da hakkin sanin su waye suka zabe ka. Ni zan tafi na kwanta.”
“Na zata zaki ce dan gurgu muje ka taya ni kwana, sai na daka tsalle!”
Wani yatsuna fuska tai tare da juyawa, bata kuma cewa cikanka ba. Baki daya ta ta manta da jacket dinshi da ta rufa sai da ta shiga cikin gidan, Elbashir da wasu security suna leke-leke, saka yatsa Elbashir yayi ya ce.
“Ta shiga cikin dakinta!”
“Tana barandar ɗakinta!”
“Weldone ”
“Sir ta shiga!”
“Ok” ya dan dukka kaɗan ya ce. “Malik ta shiga ɗakinta.” “Ok, ina son nan da kwana uku a hada connecting Cctv footage din unguwar nan da master room dina. Sannan a saka Idanun akan motsi Shatima!”
“Kana zarginshi be?”
“Kula da kai bada sako.”
Shiru Elbashir yayi yana fadin, “kuma gaskiya ne, domin ya tunzuro Lalla salmah da Jalilah.”
“Kome aka yi da jaki sai ya ci kara, manta da su.”
“Hmmm! Kyale su, ina jiransu.”
Iya haka ya fada ya shiga motar, Elbashir ya nad’e mishi keken ya saka a bayan motar, suka bar unguwar.

Dakyar ta iya wanke fuskantar, ta cire kayan ta kwanta. Idanunta a rufe tayi addu’ar barc, daga nan barci yayi gaba da ita.
★★★
Washi gari
Lalla salmah ta shigo Keivroto da misalin karfe takwas na safe, bata tsaya ko ina ba, sai whiter town. Kai tsaye gidan Malik ta nufa. Wani abin dariya koda ta isa ku kwarjinin Malik ya hanata ko tari. Asalima sai ta shiga raba idanun tana sunkuyar da kanta. Malik yayi bala’in cika mata idanun.
Ai masu iya magana sun ce wargi wuri ya samu. Kuma hakan ce domin bata iya ko tari ba, Malik da ta kai sama da wata huɗu tana son ganin shi amma sai gashi a banza ta samu ganin shi.
“Malik dama nazo maka da wata magana ne.”
“Ina jinki;” ya fada hankalinsa yana kan tap dinshi.
“Wai ko zaka duba Maidah ce, bata da matsala.”
“Na riga na zaɓi wacce nake so, Don haka babu kome Allah ya bata wanda ya fini”
“Amma Malik wace ce haka ne Sa’a?”
“Wata marainiya ce daga cikin gari!”
“Marainiya kuma? Ba yar kowa ba?”
D’ago fararen idanu yayi ya zuba mata ya ce mata. “Dole sai Yar wani zan aura ne?” Girgiza kai tai, ya ce mata. “Kin ga kuwa bai zama dole sai nayi abin da zai faranta ran kowa ba, matukar raina zai min dad’i bana bukatar amincewar kowa da kowa, kin fahimta?” Ya kuma tambayar ta, gyad’a kai tai, ajiye tap din. “Ki nutsu akan goben yarki, bana son fitina da tashin hankali, i choice Zainab ne domin wani dalili na kashin kaina, don allow me to be angry!”
Gyada kai tai domin bata da bakin magana.
Ganin haka yasa ta mike tssm tare da mishi sallama.
Tabbas izuwa yanzu ta fahimci Malik ɗin da ta sani ba shi ne a gabanta, wannan sakakken Malik ne domin wancan babu ruwanshi maganar da zata fito bakinshi akan kuɗi ce ko harkan siyasa.
Amma wannan kiri-kiri ya gaya mata ya fara soyayya da wata yarinya ba yarta ba, sannan ba ita kanta ba, asibiti ta wuce wurin shatima da yake kwance ta ce mishi.
“Wai meye ya maka ne ka koma haka? Ya batun aurenshi da Nadrah!” Dakyar ya tashi zaune sai da Faruq ya taimaka mishi. “Hmmm! Batun aurenshi da Nadrah ai tuntuni ya rushe baki da labari ne? Nasan waye munafukin Elbashir ne. Don haka abin da zance ke ki jaraba hada shi da yarki mana!”
Zama tai sannan ta ce mishi.
“Malik ɗin da na gani yau, ba Malik ɗin da na sani ba ne, Malik ɗin da na sani babu harkan mace a gaban shi, amma yau da idanuna naga wannan Malik ɗin idanun shi naga much of love and affection!”
Murmushi yayi sannan ya ce mata.
“Exactly what I see, idan mutum ya taba yarinyar tabbas dukar mutuwa Malik zai yiwa mutum!”
Ajiyar zuciya suka cike da damuwa, can Lalla salmah ta ce mishi. “Hmmm ya kake ganin muyi tsayayya magana.”
“Kamar ya?”
“Mu ingiza Jalilah mana!” Kallonta yayi sannan ya ce mata. “lallai mata dole shaidan ya sallama muku, kaidinku tafi tashi.”
Juyar da kai tai tana faɗin. “ta wannan hanyar ne zamu turo yarinyar daga jikinshi. Sannan zamu dragging Jalilah itama. Yanzu zata iso nan da karfe daya na rana, zata sauka a gidana!”
“Allah ya kai mu!”
“Amin,amma kai meye matsalar da ya haɗa ku!’
“Yarinyar ina sonta, amma lokaci guda Malik ya juyar mata da tunaninta, sannan ya saka ta butulce min!”
“Kai fa yautai ne mugun tsuntsu ne, ka hango wani abun ne yasa ka nacewa yarinyar.”
“Gaskiya ne, yarinyar karama ce amma yar jagaliya ce, sai dai duk da wanan harkan tana da mugun kamun kai, kome nata a rufe yake, nayi kokarin nimanta da shashanci ya akan idanuna ta mari wani matashin mai kuɗi, shi kuma yayi alƙawarin sai yayi yadda yake so da ita, karshe na saka aka bi min shi har kasar shi, aka mishi kakkauran kashedi bayan sun karya mishi kafa da hannu, idan ya kuma zuwa gawarshi zata dawo ƙasar shi ba a gane shi ba.”
“Yanzu don wannan yarinyar kayi wannan aikin, na zata a film ake irn wannan aikin ashe har a duniyar zahiri ana aikatawa!”
Gyad’a kai Lalla salmah take, domin taga wanda ya ci ubanta a rashin mutunci. Kuma a haka aka samu wanda ya kwantar da shi, gyad’a kai tayi sannan ta ce mishi.
“Yanzu meye matsalar ka da Malik?”
“So nake na wargaza shi, na ruguza duk wani aikin shi na tukuru!”
“Ai kuwa ka dauki dala ba gammo, ruguza Malik ba sauki, domin babu hanyar da zaka iya ruguza Malik, babu shi har duniya ta tashi!” Inji Elbashir yana ajiye mishi kayan dubayya.
“Nazo nan ne, domin Malik ya bukaci haka, ka da zuwa na ya saka ku fara tunanin da wata manufa nazo. Lalla salmah har dake?”
“Ni kuma? Allah ya min tsari, kawai nazo duba shi ne da jiki.” Daga haka ta dauki jakarta tabar dakin,jan kujerar da yake gaban gadon Elbashir yayi ya ce mishi. “Zan baka shawara, a matsayin wanda ya fara zama da Malik. Ka sassauta kiyayyr da kake nuna mishi. Malik bai maka kome ba sai tarin alkhairi, wallahi idan ni ne kai ba zan yarda wani ya san meye matsalata da shi ba, tunda Malik ya rike hannuna, har kwanan gobe bana fatan ya sake ni, daga bayanka nazo amma yadda nasan Malik ko kai da ka sanshi tsawon shekaru albarka, don haka ina baka shawarar ka tuna me ka mishi ya juya maka baya?”
Shiru yayi sannan ya mike yana fadin.
“Indai akan Zeenobia ce, Malik ba zai ragawa kowa ba, yana da kyau ka san wace ce ita a rayuwar Malik duniyar shi yake son ginawa da ita;”
“Idan ka gama zaka iya tafiya, kare mara zuciya.”
“Duk abin kace daya ne;”
Daga haka ya juya ya fita,. Ba zai tab’a fahimta ba, ya barshi da halin shi, Allah yana ganin ya fita harkokinsu da Malik gashi ga Malik ɗin.
***
01:07pm
Jalilah ta sauka, Elbashir ya tafi daukota. Daga nan wani gidan Malik da yake cikin gari ya kaita. “Na kawo ki nan ne, domin Malik ya ce haka idan kuma sake kika biyewa Lalla salmah da Shatima kwabarki zata yi ruwa. Malik bai san kin zo ba. Ki gama kwanakin ki koma gida.”
Daga nan ya juya yayi tafiyar shi. Bayan tafiyar shi, ta kira Lalla Salmah, ta ce mata tazo maza. Kafin wani lokaci ta iso. Wanka Jalilah tayi, suka fita cin abinci. Suma gidan cin abincin da Malik ya ci suka je.
Can bayansu wata ta ce.
“Ke kin ga wani labarin da yake trending?”
Girgiza kai ɗaya tayi, “duba Mayor Malik Menk Jordan tare da wata yarinya suka ci abinci jiya anan gidan cin abincin.”
Kallon juna Jalilah da Lalla Salmah. Juyawa Lalla Salmah tai ta ce musu.
“Don Allah muga yarinyar?”
Mika mata suka yi, tayi zooming hoton Zeenobia bai fito ba. A saman hoton aka rubuta.
#girlfromgettoarea#keivrotoinhell#datingorbadside.
“Mika musu wayar” tana fadar haka ta mike daga kujerar suka fita a cikin gidan cin abincin. Kai tsaye ta ce. “Kai ni gidan shi;”
“Tow! Ai wallahi idan nice ba xan yarda ba zan yarda ba, ka lalata min rayuwa ka ajiye ni for while.” Haka tai ta zugata tana nuna mata ai Malik bai da amana, tunda yaci moriyar ganga shi yasa ya watsar da ita.
Ai da mutumin kirki ne d sun taru sun rufawa juna asiri.
Waye ya mutu waye ya dawo. Dakyar suka isa gidan, bata tsaya ta gama parking me kyau ba, ta fito daga motar ta shiga cikin gidan. Lokacin Malik yana tare da baki. “Ina maciyi amanar, bayan lalata min rayuwa da kayi ka ajiye ni for long time kana da zarar niman wata mace? Har kana da ikon auren wata mace? Tow wallahi sai duniya tasan abin da ka aikata ya bika kaji na rantse da Allah! Tun wuri ka gaggauta rabuwa da shegiya kwadayayyar yarinyar nan”
“Bashir yi min waje da mahaukaciyar nan” ihu ta shiga yi da tara mishi jama’a. Tare da fadar miyagun kalmai akan shi, kuma ta tabbatar da cewa sai ta yi taron manema labarai ta gaya musu abin da yake aikatawa.
Duk da baya son magana, bai wani ko dar ba. A wanan gaɓɓar Malik sam baya tsoro ko karya, abu daya ya sani koda maganar tafito mutanen da suke kewaye da Zainab zai yi wuya su barta ta juya mishi baya, don haka ya cigaba da tattaunawar shi. A bangaren ilimin da kuma cigaban al’ummar Keivroto City.

Bayan tafiyarsu yayi tsam yana nazari, kafin ya sauke ajiyar zuciya ya ce.
“Elbashir! Bana son al’amarin ya kai ga haka, amma Salmah da Shatima sai da suka kai ni bango!”
“Kayi hakuri zasu daina.” “Hmmm!” Ya
Fada tana sunkuyar da kanshi, asibiti suka nufa daga Shatima har Lalla Salmah babu wanda yace mata ka da ta tunkari Malik, kowannensu kawai amfani yake da ita domin biyan buƙatar ranshi.
Dake bata da lissafi, kawai ta shiga taron manema labarai.
Wurin karfe biyar na yamma, suka taru kofar asibitin, ta fito idanunta dauke da hawaye tana kuka, “Na tara ku ne anan ba don kome ba, sai dun a nima min hakkina.”
“A wurin waye?” Yan jarida suka tambaye ta,
“A wurin Malik Menk Jordan! Shekaru goma shatara ya lalata min rayuwa da sunan zai aure ni, ƙarshe ya buge da cewa na cutar mishi da Yarinyar da zai aura itama cikin yayi mata karshe ta haifa mishi yara biyu tagwaye.”
Kashe Cameras dinsu suka yi.
“Madam Jalilah! Wannan labarin ba zamu iya dauka ba, domin kuwa kema ana zargin ki da aikata miyagun laifuffukan safarra yara da mata. Ban ki Wannan labarin yayi trending a social media amma a zahiri babu haka. Amma kai tsaye an aika labarin. Wanda nasan gidajen jaridun mu sun tsayar da watsa shi duniya.”
“Babu me zarran tayani kwato hakkina?”
“Sai dai ki gwada sa’ar ki a internet, amma Malik ba kanwar lasa ba ne!”
Wato har abada tsoron Malik halittace ne a zukatan al’ummar Keivroto. Amma maganar gaskiya babu me zarran yakar shi, haka ne babu shi ba a haifi namijin ba, akwai maza.
Akwai mazaje.
Amma shi Namijin duniya ne,……
#500₦
#+234 703 513 3148
[9/10, 9:17 PM] Yan Mata: Volume:10 rumors
Al’amarin ya ta’azara Wanda ya shiga kunnen kowa da kowa, musamman alummar gidansu Zenobia, sakata suka yi a gaba da tambaya.
“Yar nan me muke a gari?”
Tun safe ake tambayarta har yanzu kalaman Malik yana yawo kunnuwarta. *Dole ki dauke kai kamar baki gani ba, dole wasu zantuttuka zasu yawaita, Amma magana daya zan gaya miki. Ki toshe kunnenki! Ina da darkside, alumma charity house yana hannunki think before take action!* Juya kanta tayi tana fadin. “Kunga ina da banbanci da ita, sannan matsalar Malik daban, alaƙar mu daban, don haka babu abinda ya dame ni da matsalarshi, kuma babu abinda ya dame ku da matsalarshi da fatan Kun fahimta.”
…”Amma magana daya ne, taya zamu zuba miki idanu ai Allah ya tambaye mu! Kina jin yan mata uku ya lalata, kice muyi shiru!”
“Inna indai Zainab tana sonshi ai ba aibu bane matsalar idan bata sonshi shine matsalar ko Zeey!” Gyada kai tayi tana sauke ajiyar zuciya. Domin Ammy ta kawo mata dauki lokacin da ya dace. “Amma dai, kin san illar abin da kike shirin turata?” Girgiza kai Ammy tayi sannan ta ce mata. “Bana jin zanyi na danama Alan zabin Zainab, ko akwai wani abu ne Zeey?” Girgiza kai tayi a karo na biyu, “Tow tashi ko wuce daki!” Mikewa tayi ta haura sama.

Tun da ta haura sama take safa da marwa, ita ba wai matsalarta da shi ba ne, a’a yadda al’amarin yake shirin juyowa, tana tsaye har yanzu Malik be kirata ba, which means abin da ake ta yayyatawa gaskiya ce, “tow me yasa bai kira ni ba?”
Ta kurawa wayar idanu. Kafin ta cillar da shi. Me yasa ake kiranta da Yar getto area? Bayan bata ga wani laifin haka ba, ai ita abin a jajjanta mata ne zata auri tsoho kuma nakasasshe. “Ya Allah! Sam baya tafia fa?” Ta fada kamar zata fasa ihu. “Taya na biyewa Amjad muka tabo abinda ya dame ni? Nima na cika shegen zakewa da iyayi mtsew !” Taja tsaki. Turo kofar dakin aka yi, juyawa tayi ta zubawa hafsy idanu. “Eh lafiyarta lau! Ok” ta katse kiran.
“An ce na duba kina lafiya?” Tsaki ta ja ta koma ta zauna. “Idan ya matso yazo da kafashi kuma wallahi fita zan yi!”

Daga haka ta wuce tare da daukar simple coat dinta ta saka tana fadin. “Haka kawai ya shiga rayuwata zai hana ni sakat!” Ta fuce tana mita amma maganar gaskiya rashin kiranta ya wanke kanshi yafi kome mata zafi.
★★★
Whiter town
Harkan gabanshi yake, kamar abin da yake faruwa baya cizon zuciyar shi, kokari yake ya forgot everything else, amma Ina abu daya yake yawo a ranshi Zeeno. Taya zata amshi thi situations? Taya zata amshi wannan al’amarin he thought da al’amarin bai kai haka ba, tow zai iya kare kanshi. Duk da Meeting yake tare da bayani amma Babu yadda zaka gane yana cikin damuwa sai Elbashir. Yana yawan lura yadda yake bayani, yana yana keeping heavy breathing, rabon da yaga Malik cikin irin wannan yanayin tun rasuwar Nuratu. Bai tsammanin haduwar Zeeno da shi zai kai matakin haka ba, da har zai boye damuwar a ranshi. Yana kallonshi har ya fita tare da kiran Hafsat ta duba mishi ita, kuma ta ce lafiyarta lau, sauke ajiyar yayi ya amso ruwa me sanyi, ya ajiye mishi.
“Thanks!” Malik ya fada.
“Ba kome!”
Yana tsaye, aka kira shi ya kalli Malik, Shima Malik din kallonshi yayi, a hankali ya fita daga dakin meeting din. Bayan ya gama wayar ya koma dakin. Lokaci zuwa lokaci yana kallon Malik. Har aka gama meeting din, bakin suka fita.
“Me ya faru da ita!” “Wai ta tafi bakin ruwa ne.”
“A motsa!”
“Zamu fita da Yara ne?”
“A’a ni da kai ai mun wadatar ko?”
Gyada kai yayi yana fadin. “Eh Malik amma naga kamar kana bukatar hutu!”
“Ka da ka damu, muje kawai.” Ya fada yana kallon agogon hannunshi. “Muje naga six tayi ma!” “Eh!” Haka suka fita har wurin mota, ya shiga tare da kwantar da kanshi, Elbashir shima ya shiga. Haka suka bar gidan, kwantar da kai yayi yana sauke deep breath, yana jin wani abu na mishi yawo a zuciyarshi.

A hanyar tafiyar ne, ya saka Elbashir su tsaya su karba mishi yar kamar scart, a wata yar karamar kwali aka nade shi. Aka saka a paper bag, Elbashir ya fito da shi, ya shiga motar. “Thanks!” Juyawa yayi ya ce mishi. “Malik babu godiya a tskanin mu!”
“Na fada dai!” A haka suka Isa har bakin ruwan, anan suka same ta zaune tana kallon ruwa, like she missed wani abu na daban, special for her only life. A can nesa da itama Zulfa ce zaune tana kallonta, ita Dake tana da raunanniyar zuciya kuka take. Har ga Allah tana son kanwarta sama da yadda take son kanta, sai dai a halin da Zenobia take gara su boye mata, akan su gaya mata wacece ita.
A hankali ya matsa kusa da ita sosai ya zauna. “Zainab i’m I hurt you?” Juyawa tayi ta zuba mishi fararen idanunta. Kafin ta janye saboda nauyin da idanunshi ya mata. “I’m i hurt you?” Murmushi tayi sannan ta ce mishi. “Waye ya gaya maka zaka iya cutar dani? Ni nazo nan ne domin shan iska shima iskar ba zan shaka cikin salama ba ne?”
“Waye ya Isa?” Juyar da kanta tayi tana fadin. “Zaka iya tafiyar ka.” A hankali idanunshi ya sauka akan kayan jikinta. Kasa kasa yayi maganar da dole sai da ta zabura tare da cewa. ” Anya kasan Allah kuwa?” Ta fada tana kare jikinta. “Eh mana, taya zaki fito daga ke sai riga da wando, sun kamaki. Sannan kin dauki wani rigar sanyi mara kauri kinsa. Salon ki saka dan tsoho aika-aika!” “Don Allah me yasa make zantuttukar da suka girme shekaru na ne?” Kai tsaye kamar ita ya ce mata. ” Ai naga hannu hagu ba bakon wanke duwawu ba ne, kuma nasan irin wannan maganar ai ba bakonki bane!” Tabbas Malik ya hasalata kuma yana son lallai yayi magana ne, amma taki cewa kome. Murmushi tayi ta ce mishi. “Hmmmmm!” Ta ja harufar.
“Zainab!” Kallonshi tayi for same seconds ta amsa mishi. “Na’am!” A hankali ya kai hannunshi Kan nata, “Nasan kin ji abinda ya faru!” “Sai aka yi me?” “I like your style!” Tab’e baki tayi tare da murgud’a shi ta ce. “Na tsani turancin nan Malik!” “Ina laifin ki kira ni da Mayor!” Juyar da kai tayi tana fadin. “Ban kira ba, wanna karon wani lokaci na tuna na kira.” Kallonta yake bai San yadda zai fara fadar ga yadda yake jinta ba, but she take everything from him.
“Za…!” “Malam Mayor! Idan da hali kayi….!” Kasa karasa maganar tayi, sakammakon yadda ya dauki ya daura mata abin a wuyarta yasata kallonshi. “Ki kula da sanyi, kuma idan da hali ki zo na sauke ki a gidan!” Hadiye yawu tayi tana sunkuyar da kanta. She never expect from him. Ganin yadda ta mutu da mamaki yasa shi. Murmushi ya ce mata. “Muje Mrs Mayor” jiki a mace ta mike, tana tafiyar kamar wacce kwai ya fashe mata a ciki,ya ce mata.
“Kin ga da Ina da kafa, daukarki zan yi Babu abinda ya dame ni da wannan tafiyar naki.!”
Shiru tayi bata iya magana ba, ita fa wallahi Malik yanzu Allah na tuba tsoro yake bata, ya koma wani irin mutum, abinda Zeeno bata gane ba, yanayin da take ciki Malik ya fita shiga, sai dai dukkansu gwanaye ne wurin hadiye damuwarsu a zauna lafiya. “Hmmm! Ba zaki gaya min maganar gaskiya ba” murmushi tayi sannan ta Isa wurin motat zata bude Elbashir ya bude mata, ta shiga sannan ya budewa Malik ma ya shiga ya dauki keken ya kai baya. “Muje kici abinci a gidana!”
“Na koshi!”
“Ni yunwa nake ji, muje ki dafa min abinci!” A hankali ta kalle shi, sannan ta ce mishi. “Ban iya girki ba” “hmmm! Malik ya gaji da cin abincin karti ya za ayi kenan?” “Sai yayi ai!”
“Okay muje!” Da sauri ta kalle shi zata yo magana ya ce mata. “Elbashir zai turawa Hafsat Muna tare.”
“Wani ya gaya maka wani abu ne?” “Sai dai yanzu zan ji a bakinki!”
“Hmm!”
Ita Zeeno lallai so take Malik ya fada mata abin da yake faruwa, shi kuma yaki yana son ganin reaction dinta, itama me shegen wayo taki nuna damuwarta. Haka yasa take ta ce mishi hmmm, Malik baya cikin irin mazan da zasu zauna ya ce zai gaya mata kome don kare kanshi, yafi son ta fara magantuwa shi kuma ya fahimtar da ita. Amma sai taki tayi shiru. Asalin shiru mara dadi.

Shi yasa yayi dabarar tafiya ita gidanshi ko zata sake a can yayi maganar da ita, sai dai har suka dauki hanyar bata kuma magana ba, asalima tafiyar suke tana sauke ajiyar zuciya kamar wacce taci kuka ta koshi, nan kuwa damuwa ce take dawainiyya da ita, tin daga maganar auren har zuwa yanzu, abin zuwa mata yake bazata. Har suka Isa gidanshi, sai da Elbashir ya bude mata ta fita sannan ya budewa Malik, suka shiga cikin gidan. “Malik dazu, Ramadan ya gaya min Jalilah tazo. Kuma tare da Lalla Salmah Amma ta tafi.” “Me yasa baka gaya min tuntuni ba? Me yasa baka gaya min Jalilah tana cikin gidan nan ba? Bashir kasan aikinka kuwa?”
“I’m sorry Malik!” Juyawa yayi ya kalleta, “muje!” Ganin yadda ya masifance Elbashir yasa ta kame kanta ina zata iya jarabar Malik. Idan ya fara masifa kamar Wanda ake Ingiza shi.
Haka suka shiga cikin gidan, Rai babu dadi. “Zo ki wuce dakina kiyi wanka da sallah kada ki sake ki fito kin ji ko?”
“Tow!” Ta fada tana wucewa hanyar d ya nuna mata, tunda ta shiga dakin. Ta sake baki. Domin kuwa abin da Malik ya guda shi ya faru, Jalilah ce a dakin. “Kece karuwar da kike bibiyar Malik?” Ita bata ce kome ba, sai ma juyawa da tayi zata fita ta ce mata. “Zo nan Dan ubanki, waye sa’arki Ina magana kina tafiya baki ji tsorona ba?”
“Ai ban San shi. Kin gane!” Daga haka ta saka kai zata fita, kwalbar turaren imperial majesty ta kwala mata, a baya daidai shigowar Malik dakin. “Ke wacce irin dakikiya ce?”
“Dakikai dai! Malik na ce dakikai dai! A shekaruna kamar ita, ka kwantar da ni karya na.maka? Waye yayiwa Nuratu ciki ba kai bane?” Wani irin kunya ce ta kama shi. Yayi fatan da yana iya tsayawa da kafarshi tabbas sai yayi kwallo da Jalilah. Abin karin takaicin yadda yake hango fushi a idanun Zainaba, “Koda na kwanta dake, ai sauran wasu na samu, ko karya ne!” “Karya ne! Na ce karya ne, blackmailed dina kayi, akan wani bukatarka, sake kallonshi Zeeno tayi, “amfani da ni kayi, domin biyar bukatarka kuma ai ka samu ko karya ne? Ai ka samu na maka karya ne? Malik ka zata ban sani ba ne? Ka zata ban san cewa tsafi kayi shi yasa ka kwanta da ni.” Kallon Zeeno tayi tare da fashewa da kuka ta ce mata. “Kin san ko ban haife ki ba, ni ba sa’arki ba ce ko? Ki gudu da kafarki domin kuwa sirrin dukiyar shi yana jikinki yana samun biyar bukatarka shi zai nimo hanyar da zai rabu dake, ba akaina ya fara ba.” Kallon shi Zeeno tayi, a hankali ya ja kafarta zata fita ya riko hannunta.
“Baki yarda dani ba ne?” A sanyayye ta ce mishi. “Me zance ce bayan abinda nake son ji daga bakinka, ta fada.” Sai tayi murmushi ta ce mishi. “Batun da yake tsakanin mu, yana nan wannan kuma tsakaninku ne zan tafi gida na gode da gayyatar!”

A hankali ta juya ta bar dakin, a zafaffe ya tura keken shi, ya bi bayanta. “Elbashir kaita gida!” Ya juya yana fuskatar Jalilah. “Ba zan miki kome ba, domin akwai lokacin da kunyar yarinyar zai hanaki sukuni har na karshrn rayuwarki!” Daga haka ya wuce ya barta nan. Har ga Allah ranshi yayi mugun baci bai San yadda zai yi ba, Amma ba damuwa bata da hankali zata gane bata da wayo lokaci na zuwa
*Ayi hakuri wayata ce ta lalace don Allah ayi hakuri 🥳🤩😁🧐*
500N
07035133148
[9/23, 1:53 PM] Yan Mata: Volume:11 fault
Tun da tafita taki yarda, Elbashir ya kaita gida, da kafarta take tafiya. A yau taji Ina da iyayenta SUNA raye, Ina da tana da Wanda zata gayawa damuwarta. Tana tafiya tana share kwalla. Domin kuka ne yake cikin karfinta. Suka fita daga unguwar bakidaya, shan gabanta Elbashir yayi ya fito ya ce mata.
“Ki shiga don Allah!”
Goge hawayenta tayi da bayan hannu, ta shiga motar tana jan hanci, idan ta tuna bata da hanyar da Alumma charity house ya tsira sama da sadaukar da rayuwarta, a hankali ta shiga sobbing, kamar ranta zai fita.

Bata iya shiru ba, kuka take sosai. “Bashir dawo da ita!” “A’a please kai ni wurin Abbashe don Allah?!” “Ka dawo min da ita nace!”
“Ok Malik” wani irin juya motar yayi tare da cillawa a guje, suka nufi whiter town. Har lokacin kuka take sosai. Ko da suka Isa, Elbashir fita yayi ya barta a motar, Malik ya zo ta wurin tukin ya zauna, yana kallon yadda take kuka. “Kukan me kike?” “Kawai idanuna ke ciwo!” “Don try me! Kukan me kike yi?” “Babu kome!” “Tow me yasa kike kukan?” “Me yasa ba zan yi kuka ba? Gaya min nima jikina kake bukata kamar nata?”
Kasa magana yayi ya zuba mata Ido, baki a sake. “Idan jikinki nake so, akan me zan kira aure akan kudina? Mtsew! Kika sake kawo min shirme sai na saba miki.”
Daga haka ya fita a motar, Elbashir ya zo ya tafi da ita gida. Tunda ta shiga gidan bata tsaya amsa maganar su ba, ta haura sama da gudu. Tun da ta shiga dakin ta fashe da kuka , tare da zama a tsakiyar gadonta. Ba kukan abin da ya faru a gidan Malik ba, tsoron kada itama yayi amfani da ita, sannan ya kwace su tashi two zero.
Dakyar tayi sallah, ta kwanta. Cike da mafarkin Malik ya kwace musu gida. Sama sama take jin ihun mutane, d’ago kai tayi aka doke kanta, da wani abu Wanda bata kuma fahimtar kome ba. Sai bayan wani lokaci.
Sama sama take jin maganar mutane, bud’e idanu tayi tana ganin dishi -dishi har ta fara ganinsu sosai. A hankali ta fahimci inda take, “ke kin tashi?” Kallonshi tayi sannan ya ce mishi. “Wani Dan shegiyar ne ya buga min abu a kai?”
Dauketa da Mari Jalilah tayi, sai da ta fadi can. Dake daure hannunta suka yi, inda ta fadi, akwai fasassun kwalabe, ga hannunta a daure, kenan babu yadda zata dauka. “Kai d’ago min ita mugu!” D’agota yayi yana fadin. “Hajiya na jima Ina cike da haushin shegiyar nan, dama kuma abinda nake so kenan na ci ubanta!”
Murmushi Jalilah tayi sannan ta ce. “ku gama da ita!”
“Kai dan daudu idan ka yarda kai namiji ne, ka kunce ni mana!”
“Ke har kina da abinda zaki iya!”
“Hmmm! Ashe ke ba mace ba ce? Ke lusara ce ashe rako mata kika yi, na zata zaki tsaya mu gwabza ne! Me rabo ta sace Malik! Sai gashi kin yi rashin wayo, kin kuma lalata alaƙarku!”
Marinta tai, sai da hancinta ya fashe ta ce mata. “Idan kina raye zaki yo tunanin akan Malik! Wai na tambaye ki, da gurguntaka kike bibiyar shi.” Daria tayi sosai sannan ta ce mata. “Ai kuwa ni kadai nasan abinda nake kwasa a wurin nan, hala bai gaya miki Ina dauke da Doggystyle gift dinsa ba.”
Jalilah bata san lokacin da ta kifeta da Mari ba, ita kuwa tayi ta Dariya, “kuma ki saka idanu Malik yana zuwa yanzu!”
Kiran wayar Jalilah, Lalla Salmah tayi tana fadin. “Ki bar wurin yanzu!” “Zan bar wurin sai na kashe yarinyar nan”

“Ki kyaleta domin Malik zai fusata. ”
“Wallahi ba zan kyale ta ba!” “Kai mugu, ku dauketa, ku sakata a cikin wancan randar, ku jefata cikin ruwa!” “Ka da ki fara abinda zai dame ki, ki kyaleta ta bar nan. Ni kuma tsakaninmu zan duba lamarin. Inji Malik da ya shigo wurin.
“Ba zan kyaleta ba, sai ka amince zaka aure ni.”
“Taya zan aureki? Bayan nayi alkawarin ba zan aure ki ba.”
“Akan meye?” Ta fada tana ihu, “Amma kasan kai ne ka fara lalata min jikina!”
“Na sani amma ai ba da gangan haka ya faru ba, ba a hayacina nayi haka ba. Please ki kyaleta domin bata san kome ba!”
“Ba zan kyaleta ba, ba zan kyaleta wallahi she deserves to death!” “Bata cancanci mutuwa ba! Please kyaleta babu ruwanta.” Hawayena zuba a idanunta, ta ce mishi. “Me yasa baka sona?” “Saboda na fahimci ba ni ne a ranki ba lokaci, akwai Wanda kike so, bayan batar iyayenki da na nimo miki danginki, ki kyaleta.”
“Me yasa ka kore ni? Bayan kasan ba zan iya cutar da Nuratu ba!”
“Zaki iya mana, tunda kika amshi aikin kashe ni Allah bai nufa ba. Shi ne kika kai ta wurin da aka tozartatta!”
” Ba dole ba, ba dole ba. Cewa kayi zaka aure ni Amma hankalinka yana wurin Nuratu. Cewa kayi idan na baka kaina zaka aure ni, bayan an gama kome kawai ka.juya min baya saboda abin da ya faru da Nuratu, kasan Nuratu bata gani sosai idan dare yayi kuma ni da kaina ba zan dauketa na kaita wirin da aka mata fyade ba, Amma ka gaza fahimta. Idan kace sa sakacina a faruwan lamarin na yarda, amma haka.kayi ta dukana har waje kana kirana karuwa, itama wannan yarinyar kasheta zan yi!” Ta doke fuskar Zeeno ta fadi can. A sume.
“Zainab!!!” Ya kira sunanta da karfi, ganin Zeeno kwance sai da jikinta ya sake kuma, bata tab’a kashe ko kuda ba, yau gashi ta duke mutum ya mutu hala mutuwa tayi yar da katakon tayi tana ja da baya, Koda ya Isa wurin sauka yayi daga keken ya zube a gabanta. D’agota yayi ya rungumeta yana girgiza kanta. “Hi baby girl wakeup, wake up gani tare da ke!” Ya girgizata sai da ta motsa, Amma ina ta tafi. Tab’a Bluetooth din kunnen shi yayi. Ya ce. “Bashir maza ku shigo ku kama kowa!” Haka kuwa aka yi, Bashir ya dauki Zeeno yan sanda suka kama ya daban. “Malik!” Jalilah ta kira shi da sauri. “Wallahi ban san zata mutu ba”
“Let me make it clear, har abada ba zan aure ki ba, kamar yadda na fada a baya tow yau ma ba zan tab’a aurenki ba! Kun jima baki kashe ta ba, Ina miki uziri ne

Sake baki tayi tana me kallonshi, “Malik ba zaka aure ni ba.” “Har abada kuwa.” Daga haka yayi tafiyarshi ta zube Kan gwiwarta, meye laifinta? Me ta aikata haka da ya saka Malik tsanarta har duniya ta tashi. Lalla Salmah ce tazo ta dauke ta. Tare da zugata kada ta yarda tayi hayar yan iska zasu tayata zanga-zanga. Duk da bata so ba, domin tana ganin Babu abinda zai saka Malik waiwayarta, Amma kuma kulafuncin da take da shi akan Malik ba na wasa ba ne, ta dauki ahawarar Jalilah.
★★★
Menk Jordan world cares,
Aka kai Zeeno, wacce bata san waye akan ta ba. Sai da aka yi ta mata karin ruwa, a lokacin Dr wardah ta kuma tuna musu aikin da ya dace ayiwa Zeeno.
Sai can dare ta farka, ganin ta a gadon asibita ya sakata yunkurin tashi. Amma ya maida ta. “Relax!” Wayar dakin ya dauka ya ce. “she a wake!” Sannan ya ajiye wayar yana kallon yadda ta tsura mishi fararen idanunta. “Sorry kin ji!” Juyar da kai tayi tana fadin. “Ina take?” “Wa kenan?” “Matar nan?” “Mahaukaciya dai ko?” Shigowar Dr wardah ya sa bata bashi amsa ba, cikin girmamawa ta gaida Malik, sannan ta wuce wurin Zeeno ta gama dubata, sannan ta cire mata karin ruwan, “zaki iya wanka ko a na taimaka miki!” “Zan iya!” Haka ta fada sannan ta mike. “Wardah ki turo nurse biyu, da pad!” Sai lokacin Zeeno ta lura da abinda ya faru da ita, komawa gadon tayi ta kwnta yaki yarda ta kalle shi, rufe idanu tayi tam,taki budewa “Mayor ko zaka fita ne?” Murmushi yayi sannan ya ce mata. “Ok!” A hankali ya tura keken shi, ya fita ajiyar zuciya ta sauke a hankali ta bude idanu. “Dodonki ya fita.” Bata ce kome ba, har Dr wardah ta fita suka shigo da nurse biyu da pad din. Da taimakawarsu tayi wanka ta gyara jikinta, ta fito ta samu Inna da Ammy sai Abbas da Black, Malik na gefe yau ya Kara yarda Zeeno a rayuwarsu wata duniya ce, musamman Abbas da yana ganinta ya fashe da kuka, yana fadin. “Sai na kashe matar sai na kashe matar.”
“Ni fa ban san me ya faru ba?” Zeeno ta fada, tana amsar abincin da Ammy ta mika mata. Kallon Malik tayi tana fadin. “Ammy sake zuba min.!” Ta sauka a gadon ta nufi wurin shi, mika mishi tayi tana fadin kaci. Kallon kwayar idanunta yayi, tayi maza ta juya tare da nufar gadon, ba karamin burge Ammy tayi ba, domin kuwa Zeeno irin mutanen nan masu iya kashe Kansu, su raya wani.

Sai da ta koma ta zauna Ammy ta mika mata, bai da niyyar ci Amma saboda ta kawo mishi, mikewa Ammy tayi ta ce.
“Inna zo mu Dan zaga cikin asibitin!”
Gyada kai tayi, zata fita Abbas ya mike xai bi bayansu. “Zo ka zauna” “a’a zan tafi wurin Hibba ne” murmushi Malik yayi domin kuwa ya yaba da dattakon Ammy.
Suna fita ya turo kekenshi wurinta, ya zuba mata Ido.”me yasa kika zuba!” Dauke kai tayi kamar bata ji ba. “Yarinya!” Kallonshi tayi na dan wani dakikai kafin ta ce.”Ci abincin ka.” Daga haka ya cigaba da cin abincinta. A nutse ya kai faten waken da yaji ganye da hanta, ya kai bakin shi. “Hmmmmm! Garnish yummies!” “Baya cikin ladabin cin abinci, ana magana!’ gyada kai yayi ya cigaba da ci. Da sallama Lalla Salmah ta shigo. “Amin wa’alaikumun Salam” Zeeno ta amsa mata. Shatima ya biyo bayanta, “Zee Baby! Me ya faru da ke?” Ya shigo a rude, ajiye abincinta tayi magana suka had’a idanu da Malik, kwarewa tayi, Malik ya mika mata ruwan da yake cikin gora. Sai da ta sha. “Kiyi a hankali domin kaidin evil eye’s.” Yadda Malik ya hade rai, baki daya kowa ya shiga hankalinshi, musamman ita kanta Zeeno yadda ta kame kanta, ciro hanky’s yayi ya goge mata a bakinta, “na gode!” “No need!” Sai da suka gama cin abincin a tare, ta mike zata ajiye plat din, ya amsa yayi ya ajiye mata, ya tura kekenshi ya dauko mata dankwali, ya mika mata.
Koda ta daura, kallonta yayi yaga yadda take Dan motsi na shanunta suna motswa, a kaikaice ya kalli Shatima. Yaga yadda ya mata kuriiiii da idanu, cire top dinsa yayi ya rufa mata, yana fadin. “Daga yau kada na kuma ganinki babu hijab.” A hankali ya juya tare da kallonsu. “Ba zaku tafi ba ne? Ai gaisuwar ta Isa haka!” Ya fada yana wani hade gira. Idan da bata labari aka bata ba zata yarda ba, Amma yau da ta gani a idanunta, ta yarda Malik bala’i ne. Bai rufe baki ba, suka cikawa bujensu iska. “Mtsew! Sun wani zubawa matan mutane idanu, haba sai kace makafi ko yau suka fara ganin mace ni bana son haka. Kuma ai duk laifina ne shi yasa ”
Ita Kan bata kula shi ba, domin ta lura da yadda yake jin rigima aran shi.
*Ayi hakuri wayata ce ta lalace, don Allah! Ayi hakuri 🥳🤩😁🧐*
500N
07035133148
[9/23, 1:53 PM] Yan Mata: Volume:12 Injection
Duk yadda taso kadaici Malik ya hana. Asalima sai ya hana kowa zama da ita, idan ba Abbas ba, domin shi daya ne kawai yaƙe zama da ita su sha hira. Kuma abin da ya fahimta, maganar Jalilah yana damunta idan ta zauna zata yi shiri ta dinga tunani. Haka yasata jin wani kamar idan ta cigaba da mu’amala da Malik tow akwai matsala, don haka ta fara tunanin hanyar da zata yakince Malik, don haka ta cigaba da bin shi da idanu, kuma abin da yake d’aga mishi hankali kamar shiru nan da take tana bin shi da idanu. A cikin kwana biyu, shima tafiya ta kama shi zuwa kasar Malawi akan kasuwancinshi, ya bar Elbashir.
Duk da ya bar Amanarta a hannun Elbashir, amma rashin yarda irin na Malik sai da ya kara da Abbas da Inna domin ya gane tsohuwar tana da mutunci da kamun kai, yasa shi sake mata amanar Zeeno.
Ya bar garin da kwana biyu, Jalilah ta dira asibitin. Inna ta fita sayo goro, shi kuma Abbas bai zo ba. Iya Zeeno ce ita ɗaya a dakin. Turo kofar da aka yi ta d’ago kanta. “Zeenobia Nas Hadejia ko?” Dauke kai tai bata ce mata kome ba, harinta take ta shigo ta shaƙe ta, ai kuwa tana zuwa gabanta tayi wani tsalle ta shaƙe wuyarta, sosai domin cike take da haushinta.
“Kin azabtar dani don baki san wace ce Ni ba.” Cikin fisgar numfashi ta ce mata. “na ji labarin cewa kin shiga cikin mutanen da suka damfari Malik ko nawa ne kudin na biya domin san da shi ya miki dabaibay”
Ture ta zeenobia tayi ta ce mata. “Fita ki bar min daki!” “Ki gaya min meye alaƙarki da Malik?” Murmushi yayi sannan ta ce mata. “jeki tambaye shi!” “Ba zaki gaya min ba kenan!”
“Idan naki akwai abin da zaki iya min ne?”
Murmushi Jalilah tai, ta ce mata. “zan saka ki faɗa!” “Fice min a daki!” Ta faɗa tana sauka a gadon, tashi Jalilah tayi tana faɗin.”zan fita name da tsanani!” Ta fice Zeeno ta koma ta zauna, can nurse ta shigo dauke da magani da allura, ta ajiye tun ganin fuskar Nurse din babu rahama yasa Zeeno share ta, ta kauda kanta tare da zame rigarta. Ai kuwa ta mata allurar. Sannan ta bata kwayar ta sha.

Tana fita ta ɗan kishingida ta kwanta, tare da lumshe idanun ta. Takai minti ashirin a wurin kafin ta bude idanunta, duk da bata shan kwaya amma yau tana jin kamar allurar da aka mata akwai kwaya, domin kuwa idanunta a rufe amma take ganin jiri. Koda ta bude Jalilah ta gani zaune ta daura daya akan ɗaya. “Gaya min, meye alaƙarki da Malik!”
Yadda bata niyyar magana ba,haka bata kulata ba. Karshe da Jalilah ta matsa barci ta kama yi, sai da ta mari cinyarta ta bude idanunta. “Meye alaƙarki da Malik?” “Abin da kuka yi da kuruciyarki muke da shi, nayi laifi ne?”
“Kina sha’awar mutuwa ne?” “Waye ya gaya miki Ina tsoron mutuwa?” “Tow gaya min mene ne a tsakaninku?” Dariya ta saka sannan ta ce mata. “idan kika iya biyana miliyan ɗari huɗu zan iya gaya miki gaskiya!” “Me zaki yi dasu?”
“Malik zan biya kuɗin shi!”. “hmm sai me?” “Zai fasa aurena!” “Kin tabbatar!” A matukar buge ta sauke kanta, kafin ta d’ago shi tana faɗin. “Idan kina ganin karya ne, ki tambaye shi mana!” “Kwanta ki yi barci zan baki kuɗin ke kuma ki fasa aurenshi!” “Malik dole ka zama nawa, idan ka ji labarin bata raye ai aurena dole ne kayi!”
Haka kawai tana fita, taki yarda ta sanarwar Lalla Salmah, domin duk cikin su da Shatima babu wanda yake bata shawarar tabi kome a sannu, sai a gaggauce. Koda Inna ta dawo ta samu tana kwance, amma kuma ba irin normal barci ba, gyara mata kwanciyar tayi. Ta cigaba da barcin wanda take yin shi a mugun wahale.
Idan ka ganta, dole zaka dauka barci take nan kuwa karfin maganin ne yake kassara lafiyarta. Kafin zuwa dare jikinta yayi wani irin pale. Abin da ya dame Dr Wardah kenan, ita d wasu Drs suka tsaya a kanta. Al’amarin ya da ya d’aga hankalin Elbashir yaki gayawa Malik, karshe wayarta ma kashewa yasa Ammy tai. A lokacin da abin ya faru, Shatima yazo lekenta ya ji labarin abin da ya faru, mara lafiyar Malik tana cikin halin ƙaƙanikayi.

Dakin tsaro ya wuce tare da basu umarnin, su bincika mishi su waye suka shiga dakin. Can kuwa sai ga lokacin da Inna ta fita, kawai sai ya dauke babu alamar wanda ya shiga. Abin ya dame shi. Bai ce kome ba, ya fita kai tsaye gidan Lalla Salmah ya wuce. Koda ya isa ya samu Jalilah, yana isa kanta ya shaƙe wuyarta. “Me kika yiwa Zeeno?wallahi idan baki gaya min ba, sai na saka an kashe min ke, keeeeeeee! Wallahi kiyi fatan na kashe ki domin Malik avin da zai miki sao yafi nawa Muni. Me kika saka aka mata!”
“Ciniki muka yi da ita na saya kuma ta sayar min sai nayi laifi?”
“Ke wacce irin mara imani ce? Da zaki sayi rayuwar ta?” “Kaga Shatima sake min wuyata, ta sayar na saya, so me ya rage? Alamari ne na cinikin rai ban ga dalilin d’aga min hankali ba, don haka kayi tafiyarka, ko ka kashe ni ba zata dawo ba, ka bini a hankali, ina son Malik ya zo da kafar shi ya ce zai aure ni, sai na gaya musu abin da za mata.”
“Har sai yaushe zata kai?”
“Zata iya kai wata guda, jininta yana tsotsewa ana kara mata, sannu a hankali hantarta zai fara kumbura, kodarta ma haka. Kafin sati biyun farko za a ta saka mata jini da ruwa yana karewa. Har sati biyu. Bayan sati biyu ne organ na jikinta zasu fara lalacewa. Kasan mene ne a jininta? Zazzafar alluran mutuwa ce da aka hada da miyagun sinadarai. Maza Malik ya tawo nan, ya mashi aurena……
Wata ta samu matsala ne, amma in sha Allah daga yau xan koma yadda nake typing……
book 2 zai zo muku Whatsp da Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/23, 1:53 PM] Yan Mata: Volume:13 Jalilah
ZINNIEE’s SECRET
(One stop shop for a new sensation)

Kina Neman kamshi mai sanyaya zuciya❓
Shin kina Neman kamshi da dada❓
Ko kuwa kamshi mai ratsa zuciya kikeso❓ko Kayan gyaran jiki kike nema dry skin ne dake ko hard skin tabbas kinzo inda za’a share maki kukan ki

Tabbas Zinniee’s secret ya gama da damuwarku Ina mata masu aji mace mai aji ai Sai da gyara .tabbas Zinniee’s secret sun gama da damuwarki Hajiya ta.

Zinniee’s secret sun tanadar muku Kaya kamar……
Room freshener
Toilet spray
Bed spray
Dish wash
Mopping mist
Kai har ma da
Feminine wash
Akwai
Glowing soup dinmu mai kyau da inganci.
Glowing cream
Face cream da kuma body scrub

domin samun dadadan Kayan kamshi.da Kayan gyaran jiki maza garzayo Zinniee’s secret
Zinniee’s secret DUNIYA ne !!

Zaku iya yi mata magana a wadannan kafafan sadarwar kamar su—IG-@Zinniee’s secret
TIKTOK@ Zinniee’s secret
Ko ku tuntube su a wannan number 08080840567 za kuma ku iya mata magana ta hanyar Watsapp da wannan number.
Zinniee’s secret suna nan a kano Hadeaja road Kano state.

Zinniee’s secret one stop shop for a new sensation.

Zinniee’s secret got u covered,a trial will convince you.
_________________________
Zuba mata idanu yayi yana kallon ikon Allah, domin bai zaci haka daga gare ta ba. “Kika ce Malik ya zo nan ya aure ki? Kika ce Malik ya zo nan? Lallai Jalilah baki san Malik ba. Ganin shi kike yi, akan wannan yarinyar wallahi sai kin mutu ba tare da kin shirya ba, Malik bai tab’a rashin nasara ba, shi nasara ya sani.”
“Shatima kenan, ai shi yasa na yi amfani da yarinyar domin ita ce kwarin gwiwarshi. Kuma da kake ta min ihu ka fita ka bani wuri.”
Daga haka ya mike ya bar falorn yana kallonta. Duk rashin mutuncinta babu wanda zai iyawa. Lokacin da ya isa Asibitin ganin yadda aka hana kowa shiga inda yake yasa shi komawa gefe, ya zauna yana kallon shige da ficcen shi, ganin Elbashir yana waya da Malik yasa shi mikewa ya nufi bayan Elbashir ya fauce wayar ya saka a kunnen shi. “Mata nawa kake son su mutu domin ka? Malik itama yarinyar da babu ruwanta ka janyota cikin wannan masifar kenan? A duk inda kake ka kawo ko kazo ka samu gawarta.”

Kashe wayar yayi ya wurgawa Elbashir, sake kira Malik din yayi ya ce mishi..”me ya same ta?”. Hadiye yawu Elbashir yayi ya ce masa. “Bamu san me ya faru ba, kawai tun da ta fara Barci ata farka ba, sai fatarta yayi wani irin haske.”
“Jalilah!! Gani nan zuwa.” “Malik amma”
“Kada ka damu, rayuwarta yana da muhimmanci!” “Saboda kana sonta!” Kashe wayar yayi.
A gaskiya jikinta yayi laushi, don haka ko awa biyu ba ayi ba, wani likita dan kasar China ya iso asibitin daga gista Malik ya gayyato shi, tare da wasu kwararrun yan team suka iso akan lokaci.
A wannan karon abin ya dami kowa na Al’umma charity House, domin har ga Allah basu tab’a ganin lukutar masifa irin wannan ba sai yanzu, zuwan likitocin ya taimaka sosai, musamman shi Dr Xingi Wung. Tare da yan team dinsa suka fara shawo kan laluran.

Kusan kwana suka yi, yayinda Ammy ta kwana tana gayawa Allah samuwar Zeeno. Ba karya wani irin kauna take nunawa Zeeno, domin kuwa kamar yadda take yiwa Abbas addu’a haka take mata ba dare ba rana, kwana likitocin nan suka yi tsakanin lab da dakin Zeeno. Har washi gari abu daya suke, shigowar Malik cikin asibitin ya kara saka hankalin mutane shiga jikinsu, domin baki daya aka shiga kama tun daga leburorri har masu shara da Nurses a cikin asibitin. Umarni daya bada, sannan aka wuce can inda ake zubar da shara, aka fara binciken kwalbar alluran.
Wasa wasa kafin karfe biyu, Dr Xingi Wung ya fito yana share goshinsa, “Dr ya take?” “Da sauki, za a iya farkawa kowani lokaci.” Sannan suka shiga takawa da Malik wanda yake kan keke. “Kasan me duk wanda ya haɗa mata wannan maganin ba yana nufin ta mutu ba ne, sai dai kuma akwai hatsari sosai. Domin zai iya shafar ƙwayoyin halittar jikinta, kama daga ƙwaƙwalwa, hanta, huhu, ko koda, na gaya maka haka ne domin ka fahimci girman lamarin, gashi nan samfurin jininta,mun tura can cibiyar hada maganinka da take Desa sun ce nan da kwana uku zasu turo!”
. “Me yasa sai kwana uku zata farka, me yasa ba zata farka yau ba!” “Ba zai yiwu ba, koda ta farka, zata iya samun tab’in hankali ka ga kenan an yi bq ayi ba.” Sabon jinya ya kuma samuwa, gara a barta ayi hakuri!” Gyada kai yayi yana jin babu dad’i. Bayan sun gama magana da shi, ta wuce dakinta. Dama yasan haka zai iya faru a koda yaushe. Amma bai zaci farmakin zai kai haka ba.
A lokacin da aka kamo masu aiki a asibitin, kawo mishi su aka yi ya zuba musu idanu, rike camera yayi yana kallon su. ” Na saka wannan abin a cikin dakin domin nasan tabbas haka zai faru, amma ba san daga ina za a farmake ta ba, idan kuka dake naga fuskar ɗaya daga cikin ku, abin da zai faru ba zai muku kyau ba!” “Munji
Shigowar Ammy da mutanen gidansu. Yasa shi juyawa yana me jin babu dad’i. Shiga dakin suka yi Ammy ta tsaya suka yi magana, wanda jikinshi yayi masifar sanyi. “Ayi hakuri haka ba zai kuma faruwa ba, a gafarce ni da sakacin da nayi da rayuwarta.” Girgiza kai tayi tana me wucewa dakin. Kiran Elbashir yayi ya mika mishi camera din, “A duba min.” “An gama!” Daga haka ya koma dakin, kallonta yake kamar ya cire ciwon ya mai da shi jikinshi. Juya kekenshi yayi ya bar dakin, a bakin kofar ya hadu da Shatima.
Bayan awa guda, Elbashir ya dawo dauke da laptop, ya saka masa video matar da suka shigo da Jalilah, har ta mata allurar tare da duk hiran da suka yi da Jalilah. Akan lokaci aka fara niman matar, a cikin asibitin bata nan, ya kuma bada umarnin a nimota a duk inda ta shiga. Jalilah kuwa, Malik bai kuma bin ta kanta ba. Ya ajiye mata

“Duk macen da ka haɗa hanya da ita, sai an nime kashe ta? Na kasa fahimtar shin tsafi kake ko kuma.” Kura mishi idanu Malik yayi ya ce masa. “duk yadda kace daya ne!” Daga haka, bai tab’a jin b’acin rai sama da yau ba, don haka ba tare da ya nuna musu haka ba, domin kuwa yana son Zeeno ta farka sai ya dauki matakin da sai ya girgiza su.
A cikin kwanaki uku, da a za a gwada jininshi ya haura ya kai dubu, Allah da ikonshi ranar da dare ta fara farkawa. Ammy tana zaune akan abin sallah. Shi kuma yana waje domin a cikin kwana uku nan barci baya iya runtsawa. Mikewa Ammy tayi tana kallonta.
“Zainaba?” Ta kira sunanta. Jin muryan Ammy ya shigo dakin. “Ta farka ne?” “Eh!” Daukar wayar dakin yayi ya kira likitan da yake aiki a daren, tare da Nurse suka zo aka fara bata agajin gaggawa. Tare da mata allurar barci, idanunta yana kan Malik ta lumshe.
“Sir in sha Allah, gobe zata farka da yardar Allah. A kula da masu shigo mata.” Ajiyar zuciya ya sauke yau kimanin kwana uku rabonshi da barci, juyawa yayi ya nufi daya daga cikin dakunan da suke ɓangaren vip aka gyara mishi. Ya shige ya kwanta. Ya samu Elbashir yana zaune yana ta famar aikinshi. “Mutanen tsibiri na ajiye ka, gobe ba sai ka kwana ba. Ta farka.” “Alhamdulillahi, Ubangiji ya bata lafiya. Juliet ta rayu, Romeo sai a a kula da ita, yanzu ya batun kasuwanci.” Shafa kansa yayi yana kallon kofar waje. “Ikon Allah! Jama’a kuzo yau Malik yana jin kunya.” Mikewa yayi daga kekenshi ya koma gadon, ya kalli Elbashir. “Bani wani abu me zafi ba sha, yunwa nake ji.” “Ikon Allah na zata soyayya zaka ci:” daga haka ya mike ya fara kokarin hada mishi coffee.

“Ina Jalilah?” “Tana can na saka an rufe ta. “Ka nima mata ticket ta bar kasar nan, bana son na cutar da ita.” “In sha Allah! Ai halin da take ciki ma abin tausayawa ne domin yau kwanta uku ko ruwa bata sha ba. ” “Ka kyauta!” Ya amshi coffee din a babban mug, ya fara sha yana kallon Elbashir ɗin. “Duk da bana tsoronsu sai dai alaƙar da yake tsakaninmu yana bani tsoro, Bashir ka gaya min gaskiya kana kanta ko kaima dama kake jira ka kashe ni?” Murmushi yayi ya ce masa. “Lokacin da aka ce min Babanka ya kashe mahaifina, nayi fatan kafin na hadu da kai na kashe ka, amma yadda ka taimake ni bayan turo ni aka yi na kashe ka, karshe da aka ga ban iya samun nasara akanka ba, shi ne sune suka zo kashe ni, Malik a ranar da ka taimaka min na farfaɗo na ji zan iya kare ka da dukkan zuciyata na rantse da Allah ina masifar jin ciwon yadda kake nuna min baka yarda da ni ba ” yana kai aya ya mike zai fita. “Kada ka ga laifina yadda khamis ya sauya yasa nake ganin kamar kowa ma zai iya sauyawa!”
“A’a Malik ba kowa ba, ba zan tab’a sauyawa ba.” Yana gama fadar haka, ya dauki jacket dinsa zai fita domin yaji haushin Malik sosai. “Dawo ka zauna dan uwana, kada ka ga laifina nima abin da na ga yana faruwa ne!.”
“Don Allah ka daina zargina!”
“Na daina!” Ya faɗa, sai kuma ya fashe da dariya yo abun bai mishi dadin faɗa ba a bakinshi. Haka suka yi ta hira kafin Malik ya ce. “Idanuna akwai bashin barci, ina jin barci ne!” “Kwanta ka huta!”. Kwanciyar yayi shima, Elbashir ya zauna ya cigaba da kula da tsaronshi kamar yadda shima ya hana idanun shi barci ya kula da Elbashir ɗin, tow me zai yi mishi don ya cutar da shi bayan shi rayuwarsa ya sadaukar saboda shi. Ya kuma taimakawa danginshi da dan kanwarshi..
Sai da barcin Malik din yayi nisa, ya tashi ya rufa mishi bargo, sannan ya juya ya koma ya kwanta, barci ya dauke shi a saman kujerar.
5:15am
Malik ya ri ga Elbashir farkawa, don haka ya bar Elbashir ɗin ya rintsa, sai biyar da sha biyar ya farka yana kallon Malik!
“Me yasa baka tashi ne ni ba?”
“Saboda na ga kana bukatar hutawa ne!” Wucewa ban daki yayi, tare da alola ya fito, lokacin Malik ya koma saman keke ya zauna. Yana azkar duk da ibada, sai dai yadda yake niman kuɗinsa yasa ba a ganin yawan ibadanshi.
Sai da garin yayi haske Elbashir ya koma kujerar ya kwanta, ya koma domin cewa Malik. “Ni babu inda zan taka, ka kare yawon shigar da soyayyarka ni sai na gama barcina!”.
“Wai meye nufinka da Hafsah?”
“Gaskiya kake son na gaya maka, ko nayi shiru?”
“Kai dai ka zama ɗan iska!” “Na yarda kaho ne a kaina.” “Ina jin ka!” Malik ya ce masa. “gaskiya yarinyar tayi, amma kuma .”
“Amma kuma me?”
“Tayi kankanta, sannan bata da tsawo, ina da zaɓi a kan macen da nake so, da doguwa ko bata da fasali zan tafi da ita.”
“Allahu ya shirya ka.
“Allah ya kyauta, sai ka cigaba da dakon doguwa irin Zainaba!” Daga haka yayi kwanciyar shi.
★★
Tun da Elbashir ya dauke Jalilah ya kawo ta, wani gida ya rufe kome yayi tafiyar shi, bata kuma ganin shi ba, kusan bai wawayeta ba, har yau babu ruwa babu abinci, babu kome tun tana dauka yanzu zai zo, har ta daina saka ran da ta wuni da yunwa da ƙishirwa kamar zata mutu, haka ta kwana, washi gari ma haka, babu ruwan. Dole ta fara tunanin anya ba kashe ta za su yi ba, domin ba ruwa ba abinci.
book 2 zai zo muku Whatsp da Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/23, 1:53 PM] Yan Mata: ZINNIEE’s SECRET
(One stop shop for a new sensation)

Kina Neman kamshi mai sanyaya zuciya❓
Shin kina Neman kamshi da dada❓
Ko kuwa kamshi mai ratsa zuciya kikeso❓ko Kayan gyaran jiki kike nema dry skin ne dake ko hard skin tabbas kinzo inda za’a share maki kukan ki

Tabbas Zinniee’s secret ya gama da damuwarku Ina mata masu aji mace mai aji ai Sai da gyara .tabbas Zinniee’s secret sun gama da damuwarki Hajiya ta.

Zinniee’s secret sun tanadar muku Kaya kamar……
Room freshener
Toilet spray
Bed spray
Dish wash
Mopping mist
Kai har ma da
Feminine wash
Akwai
Glowing soup dinmu mai kyau da inganci.
Glowing cream
Face cream da kuma body scrub

domin samun dadadan Kayan kamshi.da Kayan gyaran jiki maza garzayo Zinniee’s secret
Zinniee’s secret DUNIYA ne !!

Zaku iya yi mata magana a wadannan kafafan sadarwar kamar su—IG-@Zinniee’s secret
TIKTOK@ Zinniee’s secret
Ko ku tuntube su a wannan number 08080840567 za kuma ku iya mata magana ta hanyar Watsapp da wannan number.
Zinniee’s secret suna nan a kano Hadeaja road Kano state.

Zinniee’s secret one stop shop for a new sensation.

Zinniee’s secret got u covered,a trial will convince you.
_________________________

Volume:14 Reasons.
Dakin Zeeno ya leka ya samu Inna tana tsokanarta. “Gawa taki rami!” “Kai Inna!” Ta faɗa tana shan kunun alkama, yadda ya turo kekenshi zuwa dakin ya zuba mata idanu. Dauke kai tayi kamar bata ganshi ba, ya ce .”Hajiya Inna barka da safiya.” Murmushi Inna tayi tana amsa mishi da cewa. “Barka dai, wai tsaya Malik idan son Yar kunama kake, ranar juma’a a daura aure, na gaji da ganin gamsheshen tsoho irinka yana sintiri akan yar jinjira irinta.”
Tsabar maganar Inna ya zo mata bazata bata san lokacin da ta furza da kunun da ta kurba a fuskarshi ba, kashe mata idanu yayi sannan ya juya ga Inna ya ce mata. “Hajiya Inna ai bazata ba zaki bani yar jikallenki bane, amma tunda kin yi magana ranar juma’a sai a bani ita, ni kuma na bada goro da alewa irinta al’adar bahaushe da shuwa arab. ” Ya karshe maganar yana kafeta da idanun. “Ni ba zan aure shi ba” sake baki Inna tayi tana faɗin. “Yau naga bakin ciki, yar Hajiya Inna ma da ya ce min zaki min bakin cikin da haka? Tow ahir dakin. Da kike kwance a nan ce miki aka yi kin tsira ne? Ai shine rufin asirinki, a waje za a iya cutar dake amma a cikin gidan shi sai inda karfinshi ya kare.

Ja’ira a ranki ba murna kike, kin zamu mijin nunawa sa’a amma kin wani kare da boyewa a ranki, ai kawai kazo ayi maganar bata yara da mata ba ne ta manyan maza ne, ” tana gama fadar haka ta bar dakin.” “Me yasa ba zaki aure ni ba?” “Saboda nima bukatarka zaka biya a kaina, idan ka samu yadda kake so zaka shafe babina.” Dariya ta bashi cikin sigar tsokana ya ce mata. “Kuma haka ne, idan na gama yadda nake so watsar dake zan yi na kuma niman wacce bata kai ki ba ”
“Allah ya min tsari da aurenka, wallahi tun wuri kada ka fara tunanin hanyar aure na”
“Ai ba iya tunanin nake ba, yadda zan mallake yar kwaila baki ɗaya nake ta nazari ”
“Kana da son zuciya.” “Eh a wurinki na koyi son zuciya, amma kin san me duk abin da zaki fada ba zai bani haushi ba, domin nan da kwana uku, kin shige daga cikin gidana.”
“Ai ba auren Allah da Annabi ba ne. Auren kwangila ce!” “Ai duk aure aure ne, tinda an karanto siga” “ni fa bana son auren nan, wallahi! Domin ba zan yarda kayi tsafi dani ba.”
“Bokana ya gaya min na nimo mace, yar siririya yarinya fara masifaffiya mara hakuri, idan na kawo ta aka yanke bakinta kudi xan samu na mahdi ka ture!” “Kai ko kunyar fadar abin da kake baka ji?” “Tow tsaya me yasa baki sona?” Shiru tayi tana kallonshi kafin ta ce mishi. “Saboda kana da budurwan zuciya!” Shafa kanshi yayi, tare da kallon yadda ta sunkuyar da kai kasa taki yarda su hada idanu. “sai me kuma?” “Hmmm!” Kawai ta ce matsawa gabanta yayi da keken ya zuba mata idanu ya ce mata. “kalle ni kika ce ba zaki aure ni ba kawai don ina da budurwan zuciya?”
D’ago kanta tayi ta kalle shi, kafin ta ce mishi. “Ni ka tafi bana son ganinka. Kuma bana son aurenka ka rabu da ni, idan kuma rayuwata kake so sai ka dauka ka huta, amma ba zan auri tsoho irinka bayan ga sa’o’i na, suna auren matasa ba.
A cire maganar wasa kai ina zaka kai ni? Ai matar nan tayi gaskiya ban da son zuciya ina zaka kai ni? Sannan idan ba kwadayin irin na Yaran talakawa irina ina zan kai ka? Ina son ka gane auren irina takura ne, ka je ka nemi wata yarinyar amma ni bana son aurenka!”
“Idan an daura sai ki mutu shi ne, karshen kiyayyar da zaki nuna mishi, kina tsammani zaki gaya mishi magana ne a Kyale ki, tow a hir ɗinki, kada na kuma jin kin mishi rashin kunya, aurenki da Malik an gama, ranar juma’a domin ta haka ne za a nunawa makiyanku a shirye kuke!”
“Amma Ammy gurgu ne!” Wani irin kallo Ammy ta mata, sannan ta ce mata. “Idan gurgu ne kece kika halicce shi?”
“Ni dai ba zan auri tsoho irinshi ba”
“Age is just a number, kyautatawa da sanin ya kamata shi ne shekaru, don haka kul na kuma jin kin ce tsoho ko wani nakasa, aure babu fashi.” “Ni dai aka min auren dole na mutu ba yarda zan yi ba, domin fatalwa zan yi na addabi wanda ya aure ni.” Ta faɗa tana wani hararan Malik, d’akka mata duka Ammy tayi tana faɗin ” Allah ya shirya ki, ki bar sakaci don Allah kayi hakuri yarinta ke damunta.” Murmushi yayi bai ce kome ba, ya bar dakin.

Wasa wasa Malik ya hana a sallame ta, duk da taji sauki, amma fir ya hana ta bar asibitin. Gidan da aka Ajiye Jalilah.
Tayi wani irin laushi, ya zuba mata idanu kafin ya ce mata. “Na barki ki tsira da mutuncinki amma kin gaza fahimtar haka, Tunda nace zan auri Zainab nasan dalilin da yasa na ce zan aure ta, amma kika gaza fahimtar haka. Domin ture dake a jikina Lalla Salmah da Shatima suka miki tarkon da kuka fita aka yiwa Nuratu fyade. Amma a duniya baki da masoya sama da su, lokacin da nayi hatsari na san ke aka fara biya ki zuba min guba kika ki, wannan dalilin ne ya saka har kwanan gobe kike da kima a idanuna. Ai wancan ranar ban yi niyyar tozartaki ba, kece kika bukaci haka.

A yanzu ma dama ce a gare ki, Dangin mahaifinki da mahaifiyarki, suna garin gere na garin Borno Maiduguri. Ba zan ce miki wani abu ba, amma ita yarinyar da kike kokarin cutar da ita yar Yayarki ce Ummu, idan kin so ga dama bindiga ce, ki je ki kashe Zeenobia domin ni. A wancan ranar da kike tsammanin na kwanta sake, ban yi abin da kike tsammani ba, domin babu wanda a cikin zuri’a na ya lalata yar wani, Shatima dai da kike ganin wani ne, shi ne wanda ya aikata miki kome.

…. …… “Lalla Salmah da take zuga ki, bata gaya miki me yasa take ingiza ki yarta ce take buƙatar na aura, idan kika ture Zeeno a jikina, ai dole kece ke kuma sai ta san yadda zata ture ki. Kenan dukkanku baku da alkibla, idan kin so ki bar ni na auri Zeenobia idan baki so ba, kofa a bude take ki kashe ta. ” Sannan ya tura kekenshi shi zai fita ta ce mishi. “Me yasa tuntni baka gaya min yar Yayata ba ce?” “Saboda zuciyarki ya makance da son zuciya, idan na gaya miki tunaninki bana son alaka dake ne, me zao saka na tsaya bata lokaci na akanki? Saboda ita na miki uzuri. Ba don kome ba, akwai Yar uwarta Yar sanda ce tana falo xata kula dake ki koma gidanta da zama, amma ki kame kanki a matsayin Uwa kike a wurinsu, surukar Malik Menk Jordan!”
A hankali ya fito falon, ya samu Asp Zulfa da Elbashir. “Ki kula da ita.” “Yes!” Ta faɗa tana sara mishi. Har zai tafi ya ce mata.” baki tambaye ta ba?” “Hmm wai naga tunda tana tare da kai, tana cikin koshin lafiya. Na ziyarci asibitin sau biyu. Idan Yasir yazo zamu kara zuwa, domin yace ma tsahirta zuwa ganinta.”
“Gaskiya ne, kema ba don kakinki ba da ba zaki kai wannan lokacin ba, ki kula da mutanen da kika mu’amala da su, duk nasan har yau kina kallona a matsayin makiyi, nima har yau binciken mutuwa Nasr Hadejia nake ”
Bata amsa mishi ba, sai dai kuma tayi shiru har ya saka kai ya fita Elbashir yana biye da shi. “Malik yanzu ya batun Lalla Salmah sa Shatima!”
“Ita Lalla Salmah, dawo da ita zamu yi daga majalisa, shi kuma Shatima board zasu cire shi daga matsayinshi.”

“Alhamdulillahi! Karshen azzalumai yayi!” “Eh haka ne, amma kuma tow Allah ya sa mu dace” “Amin Ya Allah!” Daga haka suka shiga.a cikin kwanaki da ake maganar za ayi aurensu, wato da Zeeno biya ta tashi hankalinta. Sai da tayi yunkurin cutar da kanta, amma aka samu nasarar mata Allura, dole aka d’aga lokacin domin ta kwantar da hankalinta, wannan abin yana faruwa ne, sakamakon yadda Shatima yake hure mata kunne, tare da bata misali da ina Jalilah? Malik ya batar da ita. Don haka haka ya gaya mata kada ta sake ta auri Malik bai da Qualitys din da ya dace ta aure shi. Domin ta sani rayuwarta tana cikin hatsari. Wannan dalilin yasa aka ajiye batun auren don tace matukar aka aura mata Malik gudawa zata yi ko ta sha guba kuma ajiye maganarta domin ba zata yi wasa da abin da tayi niyya ba. Wannan dalilin ba karamin ciwo yayiwa Malik ciwo, domin daga hakan tayi ta fadar abubuwan da ya haɗa su, A bangaren Ammy bata wani damu can ba, domin kuwa Malik shine daidai da Zeeno, sannan shi ne kawai zai zauna da ita babu cin mutuncin ko gori. Sannan babu wanda zai kyamaceta, amma baki daya ta lalata wannan sa ran. Shi yasa shima Malik shima daukar mataki, ya kuma ki fita harkanta. Domin yana fita harkanta Media zasu samu hanyar yayyata karya da gaskiya akansu.
Ba tare da jin kome ba, Malik ya shiga hada Meeting, da duk masu ruwa da tsaki na party ɗinsu. Ba a san yadda Lalla Salmah ta jiyo labarin ba, a masifar guje ta tawo, domin wanke kanta, tun safe take son ganin Malik, amma yana Meeting da board members na party ɗinsu. Sai bayan Azhar ta samu ganin shi, inda ta zubea gabanshi tana kuka tare da faɗin. “Don Allah ya mata rai, ya rufa mata asiri, ta san tayi laifi amma duk abin da ya faru, bata da masiniya Shatima ne ya shirya. Wallahi bata san kome ba, ko abinda ya faru da Nuratu shirin Shatima ne ya saka Jalilah cikinshi domin wanke kanshi, ita kanta Jalilah bata san da haka ba. Don Allah ya rufa mata asiri idan ya cire ta a matsayin assamblywoman za a mata dariya, sannan abin kunya ce a gare ta. Waye ya mutu waye ya dawo.

“Ki je zan nime ki.” Dakyar ta mike domin Malik ya girgiza yan hanjinta. A wannan karon ba karamin razanata yayi ba, iya abin da ya faɗa kenan da shirinsa, amma ta haukace ina kuma shi Shatima, koda yake Malik bai san shirin Shatima ba, shima kuma Shatima bai san shirin Malik ba. Don haka lokaci guda aka fara samun mummunar takun saka, ita kan Lalla Salmah, an dakatar da ita a majalisar domin karar da Al’ummar da take wakilta suka yi,. Idan ka ganta kamar ta yi hauka. Gefe guda an soke visa dinta, kawai kokari take ta koma matsayinta. Amma tayi rantsuwa sai ta ga bayan Zeeno domin ita ya saya masu Malik.

Satin Zeenobia biyar aka sallame ta, a asibitin. A lokacin Nadrah ta dawo daga Demark saboda abin da yake faruwa, a cikin kwanakin taso ganin Zeeno amma Allah bai nufa ba, domin kuwa ana gyaran unguwarsu Zeeno, Malik ya dawo da ita estate dinsa da yake bayan whiter town, ana kiransa da great town.
Sannan bai yarda a ranshi zata koma unguwar ba, domin yasan Shatima yana nimanta a ruwa a jallo, shi kanshi Malik tun da suka koma great town, ya saka Abbas dauko mishi wayarta ya cire layin ya bashi ya maida mata, yasan zugata ake, kuma ba daga mutanen gidan ba, sannan ya yanke hanyar da zata ganshi, ita ɗaya ya katse alaƙar shi da ita, Amma Ammy da Inna kan, shirya musu tafiya Umra yayi, bata sani ba. Ita kuma ya hana su gaya mata, sam bata san da tafiyar ba, sai a ranar da safe suna karyawa ta cewa Inna.
“Inna wai yaushe zamu bar gidan nan ne? Na gaji gara na koma inda nafi wayo!” Tabe baki Inna tayi ta ce mata. “Auzubillahi minna shaidanun rajim! Allah ka mana tsari da musu mana baki cikin da hassada.”
“Ikon Allah, Inna nice shaidaniyar?” Murgud’a baki tayi, ta ce mata. “Da yau Abbas mace ce, ai ba zai watsawa Uwarshi kasa a idanu ba, ya ce ba zai auri Malik ba, haka zai karba ya kuma yi biyayya amma sai kika nuna mata ba ita bace ta haife ki, ba ta isa ya saka ki aurenshi ba, Zainaba sai ki zuba ruwa a kasa ki sha mutumin da kika tozarta ya biya mana umra!” Sake baki tayi tana kallon Ammy sa ta fito hannunta dauke da ludayin miya ta ce. “A’a Inna ita fa Baby ta fasa auren ne, domin tsirar da Al’umma charity House, kamata yayi mu yaba mata!”
“Wani ya ba mata? Nace wani yaba mata? Yarinyar da ta watsa mana kasa a idanu ai kallonta nake kawai, sai anyi magana tazo tana narke fuska. Ai wallahi kin bani mamaki,yo ko mahaukaci tace ki aura kya kwantar da kai ki aura balle kuma mutum irin Malik me dinbin daraja!”
” Ammy me yasa baki gaya min kina son na auri Malik ba?” Murmushi tayi sannan ta ce mata. “Ai idan na miki bayani ba zaki gane ba, zaki ga kamar dole muke miki!”
“A’a Ammy da ko duka na kika yi zan fahimta. Amma abin da Inna ta faɗa ya min zafi, don baki haife ni ba sai nace baran miki biyayya ba, wacce Ni? Ban sani ba amma kin rike ni da gaskiya kamar kece kika haifan, Ammy na amince a daura auren na amince a daura aurena da Malik idan zai saka ki farin ciki na amince.”
Dariya Ammy tai, sannan ta ce mata. “A’ Zainaba idan baki so ai an shiga uku, gara ki samu wanda zaki so shi kamar kanki amma banda Malik, na san dai da ina da ya mace ce da dole na bashi ita.”
Ta faɗa tana dariya, domin kamar ta faɗa ihu. “Ammy wallahi na amince!” “Kin amince a aura miki ki kashe kanki, babu wannan zancen a bar shi kawai.” Ta rasa yadda zata yiwa Ammy bayanin na fahimta ta amince. “Ammy na amince fa!”
“Zaman aure da Malik zaki yi, ba da ni ba idan har aka damu matsala tow haushina zaki ta ji har karshen rayuwarki”

“Ammy ki fahimta mana ni na amince zan auri Malik yau ba gobe ba, domin kaina na kuma tabbatar miki ni yar halak ce ba wacce ta san halacci!” Gyada kai Ammy tayi ta ce. “Inna kinji ko? Kada gobe ta ce na zalunci ta.” “Ina jin ku, sai ki kira Liman da kawu ayi magana ta manya!”
Bata son ta nuna karayarta amma maganar gaskiya, bata shirya auren Malik ba, ta kowani fuska amma babu yadda ta iya. Wurin karfe daya na rana, aka ta taru har da Malik aka tambaye ta, ta ce ta shirya kallonta yake kawai, because bai zaci haka daga gare ta ba.

Kuma yasan tunda ya ce zata yi auren, akwai abinda ta shirya Zeenobia bata da kirki a idanun shi tunda ta fadi, ba zata aure shi ba, don yana da abin da yake bukata ne yasa ya nace idan ma tsafi ne ya je can ya nemi wacce ta dace da shi ba ita ba. Yasa shi jin babu dadi shi yasa ya ajiye ta a gefe guda, ya daina shiga harkanta. Duk da babu sauki daina ganinta da yayi ba karamin azabtuwa yayi ba, “Zainab kika ce kin amince zaki auri Malik, shin dole aka miki?” Kanta yana kasa, ta kasa d’ago kanta ta ce musu! “Na amince!”
“Kin amince ka da daga baya kice an kware ki, Gara ki fadi Gaskiya.”
“Na amince!”
“Jama’a kunji ta ce ta amince ko?”
“Eh munji!”
“Alhamdulillahi!” Daga nan suka saka.mata albarka, suka fita har da shi Malik. Karfe uku da rabi, aka shaida auren Malik Menk Jordan da Zainab Muhammad Nasr Hadejia! Akan sadaki me daraja, asalin danyen gold wanda ba a tacce shi an rage mishi Quality ba. Kafin karfe biyar magoya bayan Malik sun shirya yar karamar walima, wanda ya janyo hankalin mutane domin wasu dan niman suna live aka daura a social media.

Shatima da yake cikin tashin hankali, sai ganin bikin yayi jifa yayi da wayar shi, ranshi yayi masifar b’aci, shiru yahi yana jin wani irin bakinciki yana yana cika zuciyar, Me Malik yake nufi? Yasa an dakatar da shi, sannan ya cire mishi hannun jarinshi a kowani branches na Kamfanin shi, sannan ya saka an kama jiragen dakon kayanshi haka bai ishi Malik ba sai da ya saka aka ajiye shi a gida a matsayin ladabtarwa sakamakon rashin zuwan shi, lokacin da aka nime yazo ya kare kanshi……..
book 2 zai zo muku Whatsp da Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/23, 1:53 PM] Yan Mata: ZINNIEE’s SECRET
(One stop shop for a new sensation)

Kina Neman kamshi mai sanyaya zuciya❓
Shin kina Neman kamshi da dada❓
Ko kuwa kamshi mai ratsa zuciya kikeso❓ko Kayan gyaran jiki kike nema dry skin ne dake ko hard skin tabbas kinzo inda za’a share maki kukan ki

Tabbas Zinniee’s secret ya gama da damuwarku Ina mata masu aji mace mai aji ai Sai da gyara .tabbas Zinniee’s secret sun gama da damuwarki Hajiya ta.

Zinniee’s secret sun tanadar muku Kaya kamar……
Room freshener
Toilet spray
Bed spray
Dish wash
Mopping mist
Kai har ma da
Feminine wash
Akwai
Glowing soup dinmu mai kyau da inganci.
Glowing cream
Face cream da kuma body scrub

domin samun dadadan Kayan kamshi.da Kayan gyaran jiki maza garzayo Zinniee’s secret
Zinniee’s secret DUNIYA ne !!

Zaku iya yi mata magana a wadannan kafafan sadarwar kamar su—IG-@Zinniee’s secret
TIKTOK@ Zinniee’s secret
Ko ku tuntube su a wannan number 08080840567 za kuma ku iya mata magana ta hanyar Watsapp da wannan number.
Zinniee’s secret suna nan a kano Hadeaja road Kano state.

Zinniee’s secret one stop shop for a new sensation.

Zinniee’s secret got u covered,a trial will convince you.

Volume:15 New Life
Shi lamarin aure da ban mamaki yake, koda wasa Malik bai tab’a kawo aurenshi nan kusa ba,tunda Zeeno ta botsare sai gashi a lokacin da bai zata ba, yar renin hankalin nan ta amince zata aure shi kome mutum yayi hakuri zai ga nasara.

A bayan an tashi walima, mutane dayawa kiranshi suke suna mishi Barka da arziki, domin sai yanzu ya gwangwaje. Bayan an watse Shatima kiranshi a waya yana dariya. “Wai kai sai yanzu zaka yi aure? Hmmm bayan yarinyar da zaka aura ba sonka take ba, sai dai zan iya tayaka murna, amma ka saka a ranka sunan aurenka hoto idan kana ganin karya ne, a shiga dakin amarya lafiya.” Murmushi Malik yayi ya ce masa. “Na gode sosai, amma ni ba kwadayayye ba ne irinka. Duk fitinata ina da iyaka, shi yasa na kame mutuncina, na gode.” Daga haka ya kashe wayar.

Bayan wani lokaci, yana tare da duk ma’aikatan gidan, da ya tara musu. “Ba sai na gaya muku na samu damar yin aure. Don haka zan rage ku masu aiki a cikin gidan. Elbashir zai tattauna da ku, don haka zaku iya tafiya.” “Mun gode, Allah ya baƙu zaman lafiya.”
“Amin Ya Allah!”
B
Kasancewar auren yazo da wurwuri ga tafiyar su, Ammy da Inna Umra. Yasa ana daura auren, suka mika ta cikin gidan Malik, tare da Hafsy. Wurin karfe biyar suka bar gidan har da Abbas, ya rage daga ita sai Hafsy. Daurewa kawai Zeeno take, domin kuwa kuka take son yi, sam bata shirya auren Malik ba, Ammy ce ta mata abin da ba zata tab’a wulakantatta ba, har dare suna cikin gidan, abincin da aka kawo ma, tab’awa kawai tayi sama sama.
A bangaren Malik kuwa, wannan shine target ɗinsa na farko, dama ita yake ya dabaibaye ta, daga nan zai samu damar cin Uban Amjad. A daren ranar ya dira a KJK Mansion estate, tare da kwararrun Yaranshi gwanayen harbi daga wata iya duniya. Ai ko lokacin da Jalilah ta shiga cikin gidan, wuta aka tasar a gidan yaki ya cika ko ina, haka yasa baki daya suka kasa gane kome, da taimakon wannan device din hannunta aka gano inda take.

Don saj da ta sace Zeeno aka fahimci an fasa kofarta, don haka Malik ya kudiri aniyar ta gama zaman gidan, duk wanda zai kawo mata hari tow tare zai kawo musu hari, domin yana tare da ita yanzu kuma babu me iya ratsa shi ya isa gare ta.

Diran da suka yi, ba karamin bata kashi aka yi ba, domin kuwa sai da aka kai ruwa rana kafin ya samu damar cabke Amjad a wulakance. Aka wurga shi a bayan mota, a lokacin Khuldu Jahid Khan ya fito da burgan shi, ya nufi Malik. “Idan na sake kara taku, danka yana new York, ka fahimci abin da zan aikata” yadda yayi maganar ya matukar buge shi, me yasa Malik ya masifar sanin kome na shi? Waye yake basa Malik sirrinshi haka?

Haka ya juya tare da bari aka fita da Amjad, kai tsaye bai kai Amjad office din yan sanda ba, amma ya gaya musu yana hannunshi domin yasan za a iya kashe shi.
Can waterfall Elbashir ya wuce da shi, ana zai zauna kafin Malik ya nutsu. Basu shiga cikin gidan ba, sai karfe daya na dare. Duk da yaso ganinta amma sai ya kyaleta. Ya wuce dakinshi yayi wanka tare da yin Sallah nafila ana godiya ga Ubangiji. Sannan ya kwanta, ya huta gajiya.

★★
“Zulfa ko zaki tuntubi Malik ne zan koma Demark babu abinda zan yi anan!” Hankalin Zulfa na kan wayar da suke ta d’ago kai ta ce mata. “Ok zan gaya mishi.” Ta cigaba da wayarsu. “Kaga Yasir ba zan iya ba, kawai tunda ya tuntube ka, ka daure ka gaya mishi gaskiya Baby tayi aure saura ni. Nima ina bukatar gidana inda zance nayi aure na huta.”
“Idan kin amince na tura ayi auren mu, domin ni nayi renonki kuma babu dan banxan da zai aure min ke!”
“Yasir akwai son kai cikin lamarin ka, gaskiya ni ba zan aure ba! Shekaru nawa ka bani?” “Goma mana, goma sha daya Malama don haka ki daina wani cewa ba zaki aure ni ba, kin ganin dan fari kyakkyawar namiji, idan kina tunanin ba zan iya dake ba, tambayi matata sau nawa nake zuwa mata a dare.” Kashe wayar tayi tare da blocking din shi, domin kuwa zai iya yanko mata wani maganar.
“Aunty Jalilah kika ce na gayawa Sir Malik zaki koma Demark ko?” “Eh!” Ta faɗa, “tow shi kenan zan gaya mishi idan an Allah ya kai mu gobe in sha Allah!”
“Amma me yasa ba zaki auri wanda yake sonki ba?” “Tare muka tashi, bayan rasuwar iyayenmu, shi ya saka min kwadayin niman hakkin iyayen mu, ya ce ba zamu samu ba, sai mun kasance yan sanda ta haka zamu iya binciken abin da ya faru, tow amma kuma ni babu zance aure a raina da shi,nafi son na samu babba me dan hankali domin Allah ya gani na rena Yasir, shi ba kato ba siriri da shi kamar tsinke, ga matar shi ni ba zan iya kai kaina damu ba, kin san larabawa da zafin kishi.”
“Ina ruwanki da kishinta? Idan kina son shi kawai ya ajiye batun kishin matarshi face your relationship, ba ita ba mijin bai san kishin matarsa ba ne? Indai ya sani tow naki a wane? Babu ruwanki da zancen ta, tunda ya nuna yana sonki, da gaske yasan me yake yi ne. Ki fuskance shi ku shirya gobenku. Shi yasa wasu matan auren, suke ganin kamar karuwai na yiwa mazajensu asiri, akan Malik naji zan iya kome. Shi yasa nake ta hauka amma idan na wani ne iya ladabi da biyayya xan yi na kwace shi koda ba zan aure shi ba. Ki kula sosai, yana sonki sauƙin kai da girmama shi yake bukata.” Shiru Zulfa tai tana jin yadda Jalilah take magana tare da gaya mata yadda zata cafke Yasir Aswad Yemini. Ita Zulfa bata iya magana ba sai sauraren abinda take faɗa.
***
Tun bayan sallah asuba, da suka komal barci, basu farka ba sai wurin sha daya na safe, wanka suka yi kowacce ta shirya tsaf. Kallon Hafsy Zeeno tayi ta ce mata. “Ba dai kina shirin tafiya ba ne?”
“Uwar me zan miki?” “Babu kome!” Shigo musu da abinci aka yi, suka karya, duk da tea Zeeno ta sha, a hankali ta ce musu. “yanzu yan dabata sun watse?” “Eh ai dama rashin abin yi ne yasa suke tare dake, yanzu kuwa Malik ya basu aikin yi waye zai bata lokacinsu a wani dabanci?”
“Ka da ki zage ni mana!” “Allah ya baƙi hakuri!” Daga haka tayi shiru. Abin gwanin ban tausayi, lokaci guda tayi wani zuru-zuru kamar ba Yar kunama ba, kallon Hafsy da take cin abinci, tana gamawa ta ce mata. “Kin ga don Allah bani wani abu na kunshe sauran snack din nan”

Duba akwatinta tayi ta ciro mata wani leda, ta mika mata ta kwashe kome tas. “ke gidanki ne idan baki ci ba, Mayor zai baki a baki, amma ni fa? Gara naje da abuna.” Kokarin danne kukanta tayi, har Hafsy ta mike zata tafi, kawai bata san lokacin da kuka ya zo mata ba. Ta rungume Hafsy, tana shashekar kuka. “Sai yaushe kuma?” Ita kanta Hafsyn kuka take, haka suka yi ta kuka, sai da aka buga kofar suka rabu, Malik ya shigo tare da kallonsu. “Me yasa kuke kuka?” “Babu kome!” Mika mata wata paper Bag yayi ya na tura kekenshi izuwa gabanta. Riko hannunta yayi ya ce. “muje a raka ta ko!” Haka suka rako Hafsy waje, tana kuka itama Hafsy na kuka. Har zata shiga mota ta juya da sauri ta rungume Zeeno.

Kuka suke dakyar Elbashir, ya janyeta ya saka ta a motar, ya rufe tare da jan motar suka bar gidan, shima Malik fisgo Zeeno yayi ta faɗa kan cinyarsa, ya cigaba da tafiya da ita, sai kokarin sauka take amma bawan Allah nan ya saka fuska.
Ita kuma ganin mutanen yasa zata kwace kanta, har suka shiga falon. Ya tsaya sannan ta sauka. “Ki daina kuka, yau gidan akwai baki da zaki yi, so me zaki girka musu?” “Ai na gaya maka ban iya girki ba”
Fisgota yayi ta faɗa kanshi. “Na sani, ki gayawa chef zai miki kome.”
Ya rike ta sosai, janye hannunta tayi zata mike, ya ce mata. “Kin san wancan sharadin ya rushe, yanzu zamu sake kafa wani ne.” Yayi maganar bakinshi a daidai wuyarta. Jikinta ne ya dauki rawa, domin tun da take bata taɓa shiga irin wannan yanayin ba. Ganin yadda jikinta yake rawa, a hankali ya kai bakinshi kunnenta, “ina da zafi, kuma ina son karban yanayina. Kafin zo miki a mutu!” Yadda yake maganar, a cikin kunnenta yasa ta rike shi gam.
“Don…. Allah… K…a b….ari” ta faɗa a rarrabe, tana rike rigarshi. “Zan bari sai kin daina min magana anyhow;” gyada kai take tana rike shi, a hankali ya zagaye hannun shi a bayanta, tare da mannata da jikinshi. “N….a…. ce n….a j…i” murmushi yayi yana kallon yadda jikinta yake karban sabon yanayi, haka kawai yaji a ranshi. Yana kokwanto a kanta.
Domin ya kara zaburarr da ita, ya kai harshen shi, kunnenta. Wani irin tsumma jikinta yake, bata san lokacin da ta sake mishi kuka ba, domin al’amarin ya sha kanta. Rike shi tayi gam tana juya kanta, bai fasa wasa da kunnenta ba.
Hannunshi ya tura cikin rigarta, ya shiga wasa da tender boons dinta, baki daya ta narke a jikinshi, idanunta a rufe gam. Tana jin wani abu na yawo a kanta. Bata taɓa shiga irin wannan yanayin ba, gara idan ta gama Mp tana jin wani irin matsanancin sha’awa, shima ba wai koda yaushe ba, amma yau abin da malik yake mata yasa ta, jin take like bata raye domin yawo take a cloud, hatta numfashinta, tana ganin kamar niman izinin Malik yake kafin ya fita.
Juya kanta take tana son ya daina, amma bawan Allah nan, sai kara kamkameta yake yana cilla ta cikin wani mugun yanayi. Dakyar ta rike kanta tana jin wani irin abu kamar zata mutu, mararta kuwa kamar zata sake fitsari take ji. A hankali ya zare hannunshi yana kallon yadda ta daina ko numfashin kamar matacciya.
Murmushi yayi ya ce mata, “kin ga zaki karya ni, dama gurguntar da ake min gori kullum!” Shafa kansa yayi yana kallon yadda take zaune. So take ta tashi amma ta kasa, domin kafarta kamar ba a jikinta yake ba, dakyar ta mikewa kafin ta kuma zubewa a jikin shi. “Idan ba zaki iya tafiya ba, na kai ki dakinki!”
Bata iya magana ba, domin numfashintq da baya fita a daidai. Haka ya taba remote na keken ya shiga tura ta, har dakinta bakin gadon ha isa sosai, ya zuba mata. “Kin ga tashi kada ki karya min kafa!” Dakyar ta mike, ta faɗa gadon rub da ciki. Gyara keken yayi ya tashi ya koma gadon.
“Gaya min! Me yasa baki son aurena?”
Juya mishi baya tayi, tana jin wani irin zummmm a jikinta, magana yake amma ta kasa bashi amsa, a hankali ya kai hannun shi ya juyo da fuskarta, suka kalli juna ya ce mata. “Bude idanu muyi magana.”
“Kace auren wata biyar zamu yi? Sannan babu wanda zai tab’a wani, a idanun duniya zamu nuna muna aure. Don Allah ka daina tab’a ni, idan ka cigaba mutuwa xan yi dakyar nake numfashi…….”
book 2 zai zo muku Whatsp da Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/23, 1:53 PM] Yan Mata: ZINNIEE’s SECRET
(One stop shop for a new sensation)

Kina Neman kamshi mai sanyaya zuciya❓
Shin kina Neman kamshi da dada❓
Ko kuwa kamshi mai ratsa zuciya kikeso❓ko Kayan gyaran jiki kike nema dry skin ne dake ko hard skin tabbas kinzo inda za’a share maki kukan ki

Tabbas Zinniee’s secret ya gama da damuwarku Ina mata masu aji mace mai aji ai Sai da gyara .tabbas Zinniee’s secret sun gama da damuwarki Hajiya ta.

Zinniee’s secret sun tanadar muku Kaya kamar……
Room freshener
Toilet spray
Bed spray
Dish wash
Mopping mist
Kai har ma da
Feminine wash
Akwai
Glowing soup dinmu mai kyau da inganci.
Glowing cream
Face cream da kuma body scrub

domin samun dadadan Kayan kamshi.da Kayan gyaran jiki maza garzayo Zinniee’s secret
Zinniee’s secret DUNIYA ne !!

Zaku iya yi mata magana a wadannan kafafan sadarwar kamar su—IG-@Zinniee’s secret
TIKTOK@ Zinniee’s secret
Ko ku tuntube su a wannan number 08080840567 za kuma ku iya mata magana ta hanyar Watsapp da wannan number.
Zinniee’s secret suna nan a kano Hadeaja road Kano state.

Zinniee’s secret one stop shop for a new sensation.

Zinniee’s secret got u covered,a trial will convince you.
Volume:16 Briden Monster
D’agota yayi yana kallon yadda jikinta ya mutu likis,”kina son na daina?” Sharrr hawaye ya zubo mata, domin abin da Malik yake da yatsunta tunda tazo duniya babu wanda ya taɓa mata haka, dakyar ta ja shashekar kuka tare da zare hannunta, ta ja dakyar ta koma kuryan gadon. Ta haɗe kai da gwiwa. Shi kan mamaki take bashi, komawa kekenshi yayi ya bar dakin, stiret dakinshi ya wuce, bai tsaya a ko ina ba, sai ban daki, ya sauka akan kekenshi, ya cire wayarshi ya cilla kan keken, jan wani igiya yayi rufa me dumi ya shiga zuba mishi kai.
Cizon fatar bakinshi yayi ya sakarwa kanshi ruwan, yana zuba kamar me. Amma babu wani cigaba, kashe me dumi yayi ya sakarwa kanshi na sanyi, amma babu wani abu, dole haka ya fito ya kure sanyin Ac ya koma yana me cire kayanshi. Dan janta da yayi a jiki ya saka shi jin wani irin dumi yana ratsa shi, shiga cikin closed Dinshi, side din Jallabiya ya bude, ya ciro wani Morocco jallabiya, ya saka sannan ya fito. Rage karfin ac din yayi ya koma gadon shi ya kwanta.
Kiran Elbashir yayi, yana dauka ya ce masa.”Ya gaya maka inda kudina yake?” “A’a bai gaya min ba, ina fatar da ya gaya min.”
“Tsoronshi kake ji ne, da ba zai gaya maka inda kudina yake ba?” Kamar ya rusa ihu ya ce mishi. “Malik zai faɗa idan baka yarda ba, zan zo na kai ka sai ka ji.” Duk da ba wani magana me zafi ya faɗa ba, amma kuma kwarai Malik yaji haushin kalaman Malik. “Baka da hankali be zaka gaya min magana?” “I’m sorry Malik..” “sorry for yourself! Idan ka sake na hadu da shi, sai dai Uwarshi ya haifi wani!”
“Kayi hakuri!” Katse wayar yayi yana huci.

Kwanciyar shi yayi, yana duba wayar. A hankali barci yayi gaba da shi. Itama Zeeno barci ta sha, tana farkawa wanka tayi da alwala ta gabatar da sallah Azhar, tana idarwa ta duba a cikin kayanta, ta saka riga da wando, sai hula da top har gwiwarta. Gyara fuska tayi ta saka kwalli a idanunta. Ta fito falo babu kowa can tsakiyar falon ta je ta zauna tana me. Fitowa me girki yayi ya gaishe ta.
“Ma, ina ta jiran ki fito baki fito ba, me za a girka?” *Yau muna da baki!* Maganar Malik ya fado mata. “Ayi fried rice and veggies chicken. Sai abin da bLota a rasa ba.”
Gyada kai yayi yana faɗin. “Ok Ma” ya juya zai tafi ta ce mishi. “Ko zaka yi da wani abin sha?”
“Ok Ma!”
Kwanciyarta tayi tana sauke ajiyar zuciya, Malik ya shigo falon yana kallota, wani hade rai tayi tana wani dauke kai. Yana zuba ya kunna tv yana kallon labarai. Wayar shi tayi kara. “Ok ku shigo!” Ya faɗa yana kallonta, sai wani cika take tana batsewa, dariya yayi a kasan ranshi. Allah ya gani shi ba matashi bane balle ya ce zai iya rike kanshi, shi dattijo ne shi yasa bai sake ya lalata tsufanshi tun daga yarantar shi ba. Tana zaune a wurin aka bude mishi kofa, yan mata da sama ne. Suka fara shigowa da kayan. Suna dubawa a falon har izuwa gaban Zeeno.

Kafin wata gogaggiyar mace ta shigo, tana murmushi. “Barka da hutawa Mayor!” “Barka dai Madam Zakiya!” Murmushi tayi ta kalli Zeeno ta ce mata. “Amaryanmu!” Yake Zeeno tayi, tana satar kallon Malik. Bata san shi ita ma yake kallo ba, ko da ta ɗan waiwaya suka yi idanu biyu da shi kauda kanta tayi. Cike take da lots of curious. Yadda yake wani abu ita kan tsoro yake bata. Shafa kasumbarshi yayi yana mata wani irin kallo, da sauri ta dauke kai. “Zakiya ya kwana biyu?”
“Alhamdulillahi! Na gode da choose mall din mu” “ita zaki godewa!” Ya faɗa yana kallon Zeeno, yake tayi ta ce. “A’a ba sai ta gode min ba” sai da suka gama bude kayan sannan ta ce mata. “Ma ko zaki duba gayan?” “Yanzu wadannan kayan na meye?”
“Zamu yi baki an jima ne yasa aka kawo kayan da zaki saka.” Kallon shi take baki sake. “Ma zamu iya shiga ki sauya kayan.” Haka ta mike kamar doluwa ta bi yan matan, ta shiga saka kayan tana fitowa, yana zab’a. Sai da taji kafarta ya fara mata ciwo ta saka kayan karshe, wani Iran gown ne me had’e da hijab yaji stones, kin fitowa tayi ta zauna abinta a dakin tana matsa kafarta kasancewar ta saka hill ne a kayan. Tana zaune ya shigo yana kallonta. “Kin yi kyau! Ashe yar kwaila ta wuce a kira ta da kwaila Masha Allah. Madara kenan!”
Da sauri ta kare kirjinta, tana faɗin. “Bana son haka billahi!” Murmushi yayi ya matsa gabanta. “Kin san me? Wata rana da kanki zaki bini na sha ni kuma nayi ta ja miki class.” Kamar ya fasa kuka ta kare kirjinta. “Ni bana so!” Ta faɗa tana kare kirjinta. “Me kike so nayi?” Share shi tayi tana faɗin. “Ban sani ba, ka fita ka barni.” “Babu inda zani!” Ya faɗa yana murmushi. “Ni bana son haka!” “Ni ina son haka. !” Kasa magana tayi ya mike zata bar wurinshi ya taka mata gown ɗin. Faduwa zata yi ya riko ta. Ta zauna akan cinyarsa. Hannunshi ya kai ya zagaye kugunta.
“Me yasa baki so?” Ya sumbaci kafadarta. “Mayor!” Ta faɗa tana son tashi.”kin san me? Bana son kina min haka.” “Me na ma…..” Hannunshi ya kai kirjinta, bata san lokacin da ta zille ta mike tsaye tana faɗin.
“Dama sune damuwarka? Dama ai ta gaya min bukatarka zaka biya ka watsar da ni! Idan da don shi ne da ka gaya min na baka a waje ka kyale ni. Ka sani duk abin da kake ba zan tab’a baka kaina ba!”
Tabe baki ya ce mata. “So what? Ni tsafi zan yi da kirjinki na bawa dodona bayan na gama sha, idan yaso kika mutu sai na kara auren, itama ya mutu na kara auren haka zan ta aure na zama Dodon Amare!”
“Allah ya min tsari, ba iya ni ba har da sauran Amaren!” “Amma sai na shanye madara na.” Mikewa tayi ta bar shi, A wurin tana hararanshi. Kamar ya fashe don dariya domin kuwa ta masifar bashi dariya musamman yadda take nuna yarintarta.

Fita yayi daga dakin, sai da ta gama uzurinta, ta fito ta cire kayan tana kokarin duba wani riga mara hannu ya kutsu kai domin dai bai rufe kofar ba, daga ita sai pink pant, sai bra irinshi da sauri ta tsalla ihu tare da rarrumar rigar ta shige ban daki, wanna karon kan dariya ayi sosai. Yaki fita a dakin yana jiranta, har bayan minti ashirin bata fito ba, dole ya fita ya bar dakin. Shiryawa tayi ta fito dake lokacin la’asar tayi, ta fita zuwa falo ta samu baya nan, kitchen ta leka ta samu ana kan abincin. Sannan ta juyo da niyyar komawa dakinta, kawai suka yi kicibis. “Babbar mace an fito ne?” Ya tambaye ta yana murmushi. Kin d’ago kai tayi. “Ai oho kina nufin baki magana ne, tow shi kenan” daga haka ya matsa ta wuce, shi ba yaro ba ne kuma ba waliyi ba ne. Sannan ba mahasumi ba ne da zai ga mace ace kamfanin sadarwan shi bata dauki chaji ba. Ta gama guje gujenta yana kallonta.
Haka suka yi ta wasan boya har dare yayi, bayan Isha bakin suka iso . Manyan magidanta ne da matansu, har su sha biyu. Tsabar kishi irin na Malik har dakin ya biyota bayan sun tarbi bakin ya shiga duba mata wani abaya ya mika mata. “Bana son ki kara saka kayan nan matukar ba iya ni dake ba ne!”
Bata rai tayi tana me saka abayar, kallona yayi ya mata. “kin ajiye mazaunai kamar agwagwa ba dole ki tashi kaina ba!” Da sauri ta juya tana kallonshi, d’age mata gira yayi yana fadin. “Ce miki aka yi ni matashi ne? Koda bana cikin jerin matasa amma jini na yafi nasu tafasa. Don haka a kiyaye kada a lalata min tarbiyya!” Gyada kai tayi bata kuma kula shi ba. Domin da gaske Malik ya fi ƙarfinta. Yana magana kamar wanda ake zura mishi magna dama haka yake ko yanzu ne yake da magana haka? Haka suka fito falon suka samu ana ta hira matan da mazajensu. “Sannunku kunsan sabon ango yadda yake, shi yasa ban dawo da wuri ba, Madam ki mana jagora kan table din ki mana.”
Murmushi tayi ya ce musu. “Bismillah!” Ta koma bayan Malik tana tura mishi keke, fuskarta a sake. ” Madam da fatan yau zaki cika min cikina da abinci, yo Ina sabon ango dole na ci me nauyi!” “Ai sai na baka da na yau da na gobe, domin ka cika cikinka” haka suka yi ta hira da raha, har table din abincin, aka shiga zama. Daga yadda ta ga suna kasa kasa tun da suka fito ta fahimci ba karamin girman Malik suke gani ba. Don haka itama ta shiga rigar nutsuwa, har suka gama cin abincin, ta mike ita da mata shida suka nufi falon sama. Suna barin wurin Daya daga cikin bakin ya ce. “Yallabai muna tayaka murna auren da kayi.” Murmushi yayi yana goge gashin bakinshi ya ce musu. “Na gode!”
“Hmm! Malik dama Malik akan Lalla Salmah ne, ayi hakuri a d’aga mata kafa. Al’amarin yayi mata tsauri!” Shiru yayi yana sauraren su. Har suka gama magana bai ce uffan ba, sai dai yana binsu da idanu ne. “Yallabai baka ce kome ba, kayi hakuri tayi kuskure. Amma a d’age mata takunkumin yayi mata tsari ba zata kuma ba.
“Shi kenan zan duba lamarin!” “Mun gode!” Daga haka ya kira suka yi yar hira sannan suka tashi zasu tafi, ta hannun Malik suka mata kyauta da tukwaici. Kiran matansu suka yi, a tare suka sauko tare da Zeeno. Bayan sun fito ta shiga dakinta. Ta sauko musu jakunan kayan nan, ta basu da turaruka. Har suka rabu da dadin rai. Mutumin da ya zo da batun Lalla Salmah ya dawo yana me cewa. “Amarya don Allah ga yallabai nan, ki saka baki ya dawo mana da Lalla Salmah, tayi danasanin abin da ya faru ayi hakuri.”

“Ba kome, ya wuce.” Ta faɗa tana kallon Malik, kauda kai yayi yana me cewa. “Ku gaida gida.” Ya musu sallama, saboda dare ya fara nisa don har goma ta wuce. Suka juya cikin gidan, a ranshi yake jin yau zai fara gwada lafiyarshi domin yana da burin cin amarcin shi me lasisi.
Table din ta wuce ya shiga hada kayan, tana murmushi domin taga sun ci abin sosai. Shigowar Lalla Salmah a hargitse ya sata sake flat a kasa tana binta da idanu. Gaban Malik ta nufi ta zuba gwiwarta tare da fashewa da kuka. “Malik ka gafarce ni, Nadrah tana asibiti she committer suicide.” Bai san lokacin da ya nufi hanyar waje ba, ya manta da wata Zeeno. Tun tana saka ran ganin shi da suka fita har ya hakura ta zubawa kofar idanu. Haka ta kwashe kayan ta nufi kitchen ta gyara gidan tsaf sannan ta dawo falo tana zaman jiranshi, duk da tana son kiranshi amma me zata ce mishi?
A can asibiti kuwa, ba karamin wahala suna sha ba, kafin ta dawo duniyiyyar rayayyu. Kiran Elbashir yayi yaji wayar a kashe, haka ya hakura, sannan ya nufi wurin zama ya zauna yana tambayar Lalla Salmah”me ya faru?”
“Tunda honorable jafar ya gaya min cewa kace sai kayi nazari, ya ce Zata tafi ta bar min duniyar ma sai nayi yadda nake so da shi. Matukar ta rayu a gidanka zata dawo da zama, ban san ya zan yi da Nadrah. Na yi kokari na fahimtar yanzu kan bata da ikon zuwa wurinka. Amma yarinyar nan taki tunda nace maka an tsige ni ta ce matuƙar ban dawo da matsayin,sai hm kashe kanta zatayi me yasa take haka , nasa kai nawa laifi amma ita yake fushi da ni, na kasa fahimtar me damunta. Don Allah Malik ya zauna kafin na koma wurin da nake aiki kayi hakuri, ba zan kuma ba.
A can gida kuwa, zaman da Zeeno tayi sai ta baka tausayi domin kuwa ta gama zaman jiranshi. Amma har wurin karfe sha biyu. Abin tausayi bata taɓa sanin haka mata suke jiran mazajensu ba, idan suka futa daga cikin gidan, ganin haka yasa ta mike ta bar falon ta tafi dakinta, tayi wanka ta kwanta, daga ita sai towel. Ta kwanta tun tana jiranshi har ta kai barci yayi gaba da ita.
. …. Malik bai dawo gida ba, sai karfe hudu na asuba, lokacin da ya shigo ya hango ta kwance towel din ya zame daga kirjinta….
book 2 zai zo muku Whatsp da Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/23, 1:53 PM] Yan Mata: Volume:17 change’s
Wucewa dakinshi yayi, ban daki ya shiga ya watsa ruwa sannan ya dauko kayan barci ya saka, kafin ya koma dakinta ya nufi bakin gadon ya haura yana me kwanciyarshi a bayanta. Kanshi ya daura a gadon bayanta, ya tura hannunshi ya tura ya rungumeta.
Sannan ya sakalo daya hannun ya kara rungumeta, duk da ya so yan mata ya latsa wasu. Tunda yaji wani wa’azi na cewa sai ayi da matarka ko yarka ko kanwarka ko bangon gidanshi ya hakura da niman mata.
Sannan yadda yake cikin nadamar yar abin da ya haɗa su da Jalilah. Babu karya yayi rayuwar shan minti da kai, ba don kome ba sai na daya babu me mishi fada,na biyu babu me gaya mishi gaskiya. Na uku yana da kudi sun hana shi hango kuskuren haka, sai ranar da aka yiwa Nuratu fyade. A ranar ya tsani mummunar alaƙa..
Daura kanshi yayi a bayanta yana kara jin nutsuwa a ranshi, wai duk wannan na shine ba na kowa ba. A hankali yake tunani har barci ya fara fisgar shi, aka kira sallah farko. Tashi yayi koma dakinshi. Ya nufi masallaci. Itama tashi tayi ta zauna tana shako kamshin turarenshi ya shigo dakin ne? Ta tambaye kanta, ganin babu me bata amsa, yasa ta shiga ban daki yayi ya alwala ta fito tana me sauya kaya, ta gabatar da sallah asuba, tana idarwa ta jima tana azkar. Kafin taga gari ya fara sha, ta cire rigar ta haura gadon ta kwanta bayan ta maida wanda ta cire dazun.
Malik bai shigo gidan ba, sai karfe shida da minti hamsin da daya, yana shigowa dakinta ya shigo ya samu ta fara Barci. Cire jallabiyar jikinshi yayi ya rage daga shi dai gajeren wando. Ya kwanta a bayan, tare da shiga cikin duvet din ya janyota jikinshi yana shafa hips dinta
A hankali yayi sama da rigar jikinta, tare da zubawa dan pant dinta, idanu shi babu abin da yaƙe burge shi kamar yadda duk wani kayan da zata saka a ta ciki suke kasancewa masu haske. A hankali ya kai hannunshi saman cikinta yana motsawa,da sauri ta riko hannunshi. Zuciyarta kamar zata buga. Tsabar tsoro da firgici bata san lokacin da ta zabura zata sauka ba. Ya matseta gam sannan ya sakar mata zazzafar numfashinsa a wuyarta. Tsigar jikinta ne ya wani bala’in mikewa. Ya juyar da ita suna facing juna. So yake ya ga yadda take daukar al’amarinshi. Fir taki tsayawa, sai da ya sakar mata wani mugun ƙarfi tare da matseta da karfin tsiya, “Malik ka sake ni! Ban shirya aurenka ba, ka kyale ni nai tafiya ta ko kuma na fara gudunka!” Yasan zata aikata amma wannan ba matsala ba ne, duk inda zata shiga zai lallubuta. A hankali ya kara matseta ai kuwa suka shiga kokuwa ita, bata tab’a kawowa yana da wannan karfin ba, domin kuwa da hannu daya ya matseta tayi ta kokarin kwance kanta, amma ta kasa dole ta hakura. Sakar mata karfi shi yayi ya haura samanta tare da janye rigar barcinta sama ya cire tare da yasarwa can.

“Don Allah kada ka min haka!” Girgiza kai yayi ya ce mata.” Bani da zaɓin da ya fi haka, ko tausayawa shekaruna. Ki dube ni da idanun rahama, ni ma ɗan adam ne ko bar ni na rayu dake!”
“A’a bamu yi haka da kai ba, wallahi bamu yi haka da kai ba. Don Allah kayi hakuri kada ka min kome!” Bai saurare ta ba, ya kwanta sosai jikinta. Zamewa yayi kaɗan ya kifa kanshi a kirjinta. Shi daya yasan wani irin wuta yake ruruwa a jikinshi. Wani bala’in kaguwa yayi ya ji shi duniyar ta amma kuma yadda take magiyar ya saka shi jin kamar ya hakura da ita baki daya. Amma wata zuciya tana kara nuna mishi fa’idar murkusheta. Cakfe na fulaninta yayi ya shiga mata mahaukacin tausar da yasa dole tayi ta sake tagwayen ajiyar zuciya. A kai a kai. Tare da jan numfashi kamar me cutar asthma. Baki daya ya hanata sukuni. Wani irin damkarsu yake yana jin kamar baki daya duniyar shi daya ne Ka bashi wannan aikin, wani azabtuwar da jininshi yake, da tafasa yasa shi kasa jure mata, ya birkita mata lissafi. Tare da d’ago kafarta yana kallon yadda baki daya tayi wani irin laushi, ita kanta bata jin tana cikin duniyar zahiriyya, zare pant dinta yayi tare da kai hannunshi, yana motsa jikinta yadda ya mishi. I cant wait ko yayya ne ba xai jira ba. Yadda yake murza ta yana kara tabbatar mishi ita din tana cikin irin matan da yake so, ya sashi kara susucewa yana kara jin wani bala’in kaguwa ya yi kome da ita, da dan hasken rana da ya fara haska dakin, ya hango fuskarta da take jan numfashi kamar zata mutu, bakin shi ya kai kan nata. Ya shiga mata wani deep kiss wanda ya kara zaburarr da ita ta shiga bankare mishi tana wani irin motsin da yasa illahirin jikinta rawa suke, a hankali ya kai hannunshi ya zame box dinshi. Ya gyara kwanciyar shi a kanta, duk ya sakar mata nauyin shi. A hankali ya cigaba da sumar da tunaninta. Kafin cikin hikima ya d’ago kafarta daya, tare da karanto addu’ar saduwa da iyali. Wani irin dauke wuta yayi. Bai san lokacin da ya sake ta ba, ya mai hannunshi ya rike ya ji ta kwanta shiru, kamar an tsoma ganyen shayi a ruwan zafi, a tsorace ya janye daga jikinta.
Ya dauko wandon shi, ya kalli yadda gaban wandon ya jike, rike abin yayi ya jijjigata yajita tayi shiru (😂🤣) baiwar Allah bata san halin da ake ciki ba, shi kuwa babu shiri ya kwanta tare da juya mata baya, yana kara matse abar amma ina Alqur’an tayi shiru. Da fa har harbin iska take a wandon shi, wani irin bala’in mikewa tayi tana yin nishi kamar zata fasa wandon, ko minti biyar ba ayi ba, da yaji wani haniniyarta amma ace yar banxan aba ta koma tayi barci. Kamar bata cikin halittar jikinsa. Wani irin zufa ne ya karyo mishi. Bai san lokacin da ya mike tare da janyo kekenshi zai saka rigarshi da yake kan keken, ya juya yana kallon yadda take kwance. Ya d’aga mata hankali zai kuma tafi ya barta wannan ba adalci ba ne. Tow me zai mata? Komawa yayi ya rungumeta. Yana shafa bayanta. Yana kara jin wani wani bala’in tausayinta.zuciyarshi babu dad’i, ya shiga ya motsa na shanunta yana kara matseta. Abin mamaki sai ga abin ta kuma tashi kamar wacce cajinta y kare ana jona shi da wuta ya dauka yadda yake murzata yasa ta kuma fadawa sabon yanayin da yafi na baya. Hannunta ya kai tare da daurawa kan abar, ai kuwa ta kuma nishi abar.

Ruwa na sauka kamar ba gobe, yana kara jin wani irin bala’in nutsuwa. Sake gwadawa yayi yaji kome ya tsaya sama da na baya, bai yarda ya tsaya ba. A hankali ya samar mata da nutsuwa. Ta hanyar wasa da ita kamar hauka. Kafin ta ji ta sake ajiyar zuciya, tana matse kanshi. Domin bata cikin hayacinta. Sai da ta ji hankalinta y dawo jikinta kafin ta bude idanunta ta ga nononta a bakinshi yana kallon kwayar idanunta, bata san lokacin da ta fasa ihu ba, tare da ture shi ta fado daga gadon ta wuce ban daki tumbur.

Duk da halin da yake ciki, bai hana shi dariya ba. Domin tayi bala’in bashi dariya nan ta gama mikewa tana nishi da kamkameta shi. Yana gama dariyarta ya tuna halin da yake ciki, da sauri ta wuce dakinshi. Zama yayi cikin abin wankan yana sauke ajiyar zuciya. Baki daya ya cika ruwan dumi yana jin yana gani tare da sauraren yadda ruwa yake cika mishi abin wankar, ga abinshi a kwance yana kallonshi ya kwanta kamar an yi ruwan sama an dauke, yana kwance kamar danyen nama.
Tunda yake bai tab’a shiga tashin hankali irin na yau ba, sai da yaji zai iya amma ashe ba zai iya ba, me ya kai shi auren yar mutane da yasan haka ne, tow da bai fara ba, duk wacce zata zauna da shi babu kamar Zainab. Tana zaune da shi ne ba don dukiyarshi ba, sai ma karfi da yajin da ya nuna mata. Domin yasan ya takurata ainun ya kuma hanata sakat.

Itama a bangarenta, wanka tayi tana zaune cikin abin wankar kallon yadda bakin boons dinta suka mike, a hankali ta kuma shiga cikin ruwan tana sauke ajiyar zuciya. “Ba zan kuma barin ya shigo min daki ba, kawo ya zauna a dakinshi.” Ta faɗa tana hararan gefe da gefe kamar tana ganin Malik ɗin.
Haka yayi wanka ta fito, sai dai wani abu da ya shiga damunta, kirjinta. Ba halin ta matse ciwo suke mata abinka da rashin sabo. Dakyar ta saka rigar tana fatan kada su takura mata, lokacin da ta fito wanka ta duba gadon, kamar anyi wasan dambe, bedsheet din ya mugun yamotsewa.
Ga duvet can gefe, pant dinta a yashe can, rigarta a saman side bed, da sauri ta shiga tsinci kome tana juyawa. Zaune yake akan kekenshi..kin yarda ta kalleshi tayi ta juya mishi baya.
Tura keken yayi ya riko towel din. Da sauri ta juya. “Don Allah kada ka min tsirara!” Sake baki yayi yana kallon bakinta. Jan towel din yayi tayi maza ta rike. “Ni dai nace kada ka min tsirara!” Fisgota yayi daga ita har towel suka faɗa kanshi, a lokaci guda suka fadi dukkansu biyu da towel din. “Don Allah meye haka?” Ta tambaye shi, kamar zata yi kuka. Shafa fuskarta yayi yana kallon yadda take kokarin mikewa.”are you okay?” Tashi tayi ta koma bayan kekenshi wai ita zata d’aga shi, amma haka ta kasa. “Zo nan!” Ya mika mata hannu, dakyar ta daddage ta d’ago shi. Tana tura baki, abin dariyan shine babu towel din ko rudewa tayi ko kuma wani abu can sai da ya cilla mata towel din ta ce. “na gaji da ganin kwaila tsirara!” “Wayyo!” Ta faɗa da karfi tana kare kirjinta. “Aikin kawai naga kasar” da sauri ta juya ya ce. “Wai suma mazaunin ba laifi!”
Wato Malik ko, sai da ya manna mata hauka, sannan ya bar dakin wani abin mamaki ya manta da Nadrah da Uwarta. Baki daya ita Zeeno ce a gabanshi, ita ce a idanun shi.
Wunin ranar yana cikin kunci, amma idan ya kalleta baya sanin lokacin da dariya take kama shi, wayar shi tun daren jiya ya kashe, tunda suka karya. Taki yarda su sake haɗu. Shi ma idan ya je dakinta kin yarda take su haɗu.
***
Tun Lalla Salmah tana tsammanin zuwan Malik, har ta cire ranta. Tasan shi mutum ne da yake masifar kaunar Yara, domin ko lokacin da Nadrah take yarinya, ba karamin kauna yake nuna mata ba, shi yasa da abin ya faru ta kira shi, idan har Malik ya yafe mata ta koma matsayinta, hmmm.

Har can la’asar kafin ta kira Elbashir ta gaya mishi halin da suke ciki. Don Allah ya duba mata Malik, haka ya tawo gidan ya samu Malik yana cikin nishadi. Sai da suka koma gefe, yake gayawa mishi sakon Lalla Salmah. “Na sha’afa wallahi domin tun jiya wayar a kashe, take ban kunna ta ba.” Ya nufi dakinshi ya sauya kaya, sannan ya leka Zeeno ya same ta fara Barci. Juyawa yayi ya fita can ya tafi dakinshi ya rubuta mata.
_Zan leka asibiti duba Nadrah sai na dawo! Na gode sosai da bani yau ɗinki da kika yi, Ni kuma xan tabbatar na baki gobe na_
*MMMJ*
A hankali ya bar dakin, ya kawo mata sakon ya ajiye mata bayan ya sumbaci hannunta. Murmushi yayi yana girgiza kai. Wato babu abinda ya kai kuruciya dad’i. Bata iya rudewa ba, baki daya take kome da zuciyarta. Dariya yayi ya saka kai ya fita. Suna nufi Asibitin, shi kan Bashir bai zauna ba, tafiyar shi yayi domin haka kawai yake jin haushin yadda Lalla Salmah take wani kuka tana cewa. “Idan yarinyar nan ta mutu ban san ya zan yi ba, zunubina ya haifar min da haka, ina zan saka rayuwata?” Duk da yasan halin Malik amma sai yake ganin kamar wani abu ne can ake son cimma ba rashin lafiyar ba. Da zai tafi Malik ya kalle shi. “baka ga halin da take ciki ba ne?” “Na gani Malik, amma ai ba wani babban al’amari ba ne, kowa ma na iya shiga halin da yarinyar take ciki, infact da ka koma gida, ka bar yar mutane a can zai fi kyau da zama anan!” “Ka da ka gaya min maganar banxa, kai a ranka Zaka ji dadin haka?”
“Malik kaidin mace zan tuna maka” daga haka ya juya ya tafi, shi tun shekaranjiya rabon shi da Malik, so yake su sake sa juna wani bai shigo musu ba, amma ina shaidaniyar matar can ta shiga jikin Malik ta yadda ba zai gane ba.
Tun da ta farka barci, bata ganshi ba, ta sake tayi ta harkan gabanta, har wurin karfe biyu tayi sallah ta dawo Falo, abincin ma a falo taci kiran wayarta aka yi aka gaya mata tana da baki. Ta ce su shigo. Tunda suka shigo kusan matan wancan gidan ne, har da Yaran. Shiga kitchen tayi ya ce a dafa musu abinci me sauki sannan ta dauki tire ta shiga fito musu da kayan ciye-ciye kafin kace me ta cika musu gabansu da shi aka shiga hira. “Ina mai gidan yake?” Murmushi tayi ta tuna da sakonshi. “Akwai yarsu da bata da lafiya, tana asibiti ya tafi dubata daga can zai wuce wani wurin.”
“Allah sarki! Allah ya bata lafiya!”
“Amin!” Nan suka cigaba da hira har aka yi Sallah la’asar suka yi sanan aka kawo musu abincin, suka ci. Hira sosai suka yi bayan la’asar sosao suka bar gidan ta saka aka mai dasu gida zuciyarta cike da kewarsu.
Koda ta dawo gida kiran Ammy ne ya shigo mata, tana jin muryan Ammy ta kashe wayar ta kira su. Aka kafa hira. Tana jiyo muryan Inna tana cewa. “Abulle gani gaban dakin Allah ina roka muku Allah ya baƙi, haihuwar yan biyar lokaci guda!”
“Amma dai tsohuwar nan bata da imani haihuwar biyar sai kace akuya!” Nan suka shiga hira da Ammy, “Ya ina kuna lafiya da Malik?” “Lafiya lau Ammy,” murmushi me sauti Ammy tai, Allah ya gani bayan Abbas da mahaifinshi da iyayenta. Karfin Addu’arta Zeeno tayiwa. Ta mata addu’ar Allah ya zaunar da ita Allah. Ya kare ta da mugun ji da mugun gani. Don haka ta basu damar su more juna na kwana biyu kafin ta kira su. Bayan sun gama wayar ta kashe.
Wasa wasa sai ga Malik har goma na dare bai dawo ba, haka jiki a mace ta koma dakinta, ta kwanta tare da saka key ta ture dakin ba zata bar shi ya kuma shigowa ba, yazo ya hanata sakat. Amma kuma abin mamaki har barci yayi gaba da ita bai dawo ba, don yasan matukar ya dawo zai buga kofar dakin. Amma shiru dake bata san lokacin da ya dawo jiya ba.
Yau ma kamar jiya Malik bai bar asibitin ba, sai goshin asuba ya dawo…..
book 2 zai zo muku Whatsp da Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/23, 1:53 PM] Yan Mata: Volume:18 Maidah Sheikh
A matukar gajiya ya dawo, don ko dakinta bai leka ba. Asalima yau masallaci ya nufa. Shi kansa bai san me yasa ya damu da ciwon Maidah ba. Sai dai yana shiga wanka yayi ya gabatar da sallah asuba, daga nan yayi kwanciyar shi. Baiwar Allah bata san me yake faruwa ba, sai sha biyu na rana ya fito, ta nime abin karyawa, daga ita sai wando boom shot na jeans, da yar vest iyakar shi kirjinta. Ta zuba abincinta ta wuce daki da shi, tana murnan yau babu me damunta, don haka ta cigaba da harkanta sai karfe hudu, ta ga ya fito daga dakinshi. Lokaci ta sauya kaya doguwar rigar Bahrain gown, me dogon hannu an zagaye shi da net, rigar iya gwiwarta ya tsaya, hadiye yawu tayi abin da ya faru jiya ya dawo kanta, wani yarrrrr taji bata san lokacin da ta rintsa idanunta ba. Har yazo inda take ya ce mata. “Ke idan baki ga mutum ba, baki iya nimanshi a waya ba ne?” Dauke kai tayi tana faɗin. “tow kai da ban kiranka ba, me yasa ba zaka kira ni ba?” Shiru yayi yana kallonta kafin ya ce mata. Shiru yayi domin bai da abin faɗa, har ga Allah tafi shi gaskiya da bata kira ba, sai ya kira sai ya sha’afa baki daya.

Yau ma abin da yasa bai fita da wuri ba, don yana da aikin da Elbashir ya tura mishi ta email ne, kuma ya gaya mishi ya bar mishi sako, haka da Elbashir yayi yana nufin Malik ka da ta fita ne, shi yasa ta tsare aikin ya dawo mishi da su, ya ce yana fama da ciwon kai. Amma kuma dake Lalla Salmah ta shirya tsiya, baki daya taki barin Malik ya nutsu, ta kira shi ya kai sau dari, bayan ya gama aikin wanka yayi. Ya cigaba da wasu ayyukan,yana waya da Elbashir. Domin dai Elbashir hana shi fita yayi. Sai yanzu ne ya samu kanshi. A sace ta je kallonshi suka hada idanu da juna, dauke kai tayi tana mamaki taya yasan tana kallonshi. “Yarinya nasan kina kallona” har ta bude baki zata yi magana aka kira wayar shi. “Ya jikinta dai?”
“Da sauki zance kenan, ina ganin kawai zan fita da ita ne, ka saka baki a bude min visa na ne, na gayawa Mahaifinta yaki daukar wani mataki a kai!” Yaji matukar tausayin Lalla Salmah. Don haka ya ce mata.
“Ok bari nazo” daga haka ya kalli Zeeno. “Zan fita saura kada ki kira ni!” “Ai dama baka ce na kira ka ba, kuma baka bani number ka ba, ai kome ciiniiki kuke don haka nima biyana zaka yi!”
“Hmm! Ok bani account ɗinki!”
“Tura baki tayi, tana faɗin.” Na gaji da zaman gida fita xan yi?”
“Allah ya baki sa’ar fita!”
“Gaskiya na gaji” share ya yayi, tare da barin dakin yana jin babu.

Tunda ya tafi asibitin ko minti goma bai yi ba, Maidah ta farka. Tunda ta ganshi ta fashe da kuka, ita bata son ganin Uwarta. Itama ta shiga kuka. “Ni kawai ki fita ko na mutu!” Jin haka yasa ta ficce tana kuka. Rarrashinta Malik ya shiga yi yana bata hakuri, da nasiha.
“Dadi tunda ta iya cutarka ya waye ba zata cuta ba? Don Allah ta daina zuwa wurina.” Yadda ta birkice yasa Malik cewa. “is okay! Ba zata dawo wurinki ba, shi kenan?” Hawaye ne ya zubo mata tana kuka. Fitar Lalla Salmah, kiran likita tayi aka duba Maidah, bayan an gama nurse suka taimaka mata tayi wanka, shi kuma ya fita ya ce mata. “Tunda akwai wurin abinci, ga katina ki amso mata abinci da abin sha, tunda babu wanda ya kawo muku!” “A’a za a kawo yanzu!” Jinjina kai yayi, ya zauna sai da nurse din ta fito ta gaya musu ta fito itama. Lokacin da ya shiga dakin, ya sha mamaki domin kuwa a madadin ta saka kayan jinya na asibitin, sai gashi ta saka wani irin rigar barci, har yana iya hango kirjinta, da na fulaninta, dauke kai yayi bai kuma kallonta ba, saboda idan wannan ganin yake so, yayi tow ya baro a gidanshi.

Haka Lalla Salmah ta kawo abincin, amma taki yarda ta zuba mata sai Malik ne ya zubo musu. A lokacin ba karamin mamaki yayi ba, domin kamar ta shige jikinshi. Don ma yana taka mata birki ta hanyar tsare gida. Ganin yadda yake dauke kai yasa ta ɗan nutsu, har ta gama cin abincin. Koda ta gama magani ta sha, suka yi ta hira a hankali har barci ya ɗauke ta, ya ja mayafi ya rufe ta yana kallon yadda take barci sai lokacin Zeeno ta fado mishi. Ya fita daga dakin ya kira ta. Ganin Maidah a wannan yanayin ya d’aga mishi hankali.
Sai da ya kusan tsinkewa ta dauka, tana faɗin. “Waye ne?” “Dodon Amaren ne!” “Hmmm! Tow sai kaita cinye su ko” “kina lafiya?” “Lafiya lau!” “Baki tambaye ni mai jiki ba” “Kaso na tambaye ka jikinta ne?” Shiru yayi yana mamakin meke damunta? Ya daure ya ce mata. “Ok meke damunki?” “Babu kome ai hanani fita kayi” “idan shi ne kuwa, kada ki saka kafarki a bakin kofar fita domin zan bata miki rai!” “Hmmm!” Daga haka ya kashe wayarshi. Kallon Lalla Salmah yayi ya ce mata. “Tunda tana barci bari na tafi na dawo!” Bata so Malik ya tafi ba, kamar ta fasa ihu.

Bai zame ko ina ba, sai gida yana shigowa ya same ta a dakinta kwance tayi rub da ciki tana kwance. Jin karar rufe kofar yasa ta juyawa. Hadiye yawu tayi tana kallonshi! “Tow me ya dawo da kai?” “Gaya min ni da gidana, akan me ba zan dawo lokacin da ya min ba?” Shiru tayi ta juya mishi baya. “Kin manta da yarjejeniyar mu ne, babu rashin kirki?” Tashi tayi ta zauna. “Ni Allah ya gani na ce bana son aurenka! Taya zaka addabi!” Karasawa yayi wurinta ya tsaya a gabanta. Saka hannu tayi ta rufe bakinta. “Kika ce me?” “Ni dai gaskiya ka rabu da ni!” Kayan da ya fita ya barta dasu a jiki sune har yanzu. Kallon yadda take zaune yayi, kallonshi tayi ta ga ya kura mata idanu, da sauri ta kare kirjinta.
“Malik meye haka!” “Jeki ban daki ki jika jikinki kizo!” “A’a wallahi ba zan jika jikina, na kama mura ba!” Fisgota yayi tare da rungume ta, “ni dai ka kyale ni, ba zan zauna da tsoho ba” d’agota yayi yana kallon yadda take kokarin dauke fuskarta zata mike a jikinshi. Hannunshi dukka biyu ya kai bayanta, a hankali ya zuge zip din rigar da sauri ta kalle shi. Hura mata iskar bakinshi yayi. Ta dauka kai tana kokarin mikewa ya kuma rungumeta. Kamar zata yi kuka a hankali ya shiga lasar gefen fuskarta.
Cikin wani irin zukudi da son lallai yaji yadda take, “Ni dai ka kyale ni” a fisge ta yi maganar, bai san lokacin da ya shiga bi da ita kamar zai cinye ta ba, tare da sumbatar ko ina na fuskarta. A hankali ya sauka a kan bakinta, ya shiga mata wani mahaukacin kiss, amma yarinyar nan bata respon ba, asalima yakince shi tayi tana me faduwa can. “Nace maka ba zan aureka ba, ka gane mana ni kai ne bana so. Ka rabu da ni, ka daina min wadannan abubuwan bana so! Na haɗaka da wanda ya halicce ka, ka daina tab’a ni.”

“Hakkina fa?” “Ni bana sonka, da na baka shi gara na mutu sai ka amsa da gawata!” Yadda tayi maganar ya shi kura mata idanu. Ranshi ya b’aci amma sai ya danne. “Me yasa baki sona?” Shiru tayi tana jin kamar ta fasa ihu. Ita bata so ma ya zauna kusa da ita, domin sakata yin wani abu da bata shirya yin shi yake. Tayi auren nan domin Ammy ne, kuma Alhamdulillahi. “Kai kace auren mu kawai suna ne, akan me yasa zaka karya alƙawarin da muka dauka?”
Murmushi yayi tare da juyar da kekenshi ya bar dakin, dakinshi ya shiga, ya zauna tare da kurawa wayarshi idanu. Bude drowe dinsa ya dauki robar maganin shi ya watsa a bakinshi.
Sai da ya sauya kaya, sannan ya koma asibiti, tunda Lalla Salmah ta ganshi ya sauya kaya ta san wancan yar jagaliyar ta saka shi yayi wani abu da ita, kamar ta rufe Malik da suka, haka ta yi fuska.
A hankali ya leka dakin yaga Maidah tana barci, sannan ya dawo suka dan tattauna.
Yau ma, a asibitin ya kai har karfe uku na dare, sannan ya koma gida. koda ya isa gidan dakinta ya shiga ya samu tana barci, komawa dakinshi yayi, ya rage kayan jikinshi yayi wanka, tunda ya fito yake jan hancinshi, domin mura da ya kwaso. Kwanciyar yayi domin maganarta yana yawo a kanta, shi yasa bai wani bukaci ganinta ba.
Washi gari da sassafe ya nufi asibitin, bayan ya saka chef yayi mishi abincin na musamman ya tafi asibitin. Bata ganshi ba, kuma bata damu da ta ganshi ba sai da suka kusan kwashe sati guda ranar asabar. Ta fito tana son leka Al’umma charity House, ta nufi dakinshi. Bugawa tayi ya ce Mata. “Yes!” Tura kofar tayi ta hango shi a tsakiyar gadon shi. Ko ina a hargitse. Wani mahaukacin kunya ne ya kamata. Inda take raye tsaf, inda mijin da take aure kamar dakin wasan Yara. Bata mishi magana ba, ta shiga kwashe kayan dakin. Tana gyara tare da hada na haɗawa.

Tana gama tattara dakin, idanunta ya sauka a kanshi ya zuba mata idanu. “Me kike bukata?” “Idan na gama gyaran dakin zan gaya maka!” Ta nufi ban daki, ta gyara sannan ta fito tana kallonshi. “Me yasa ba zaka gaya min a gyara maka dakinka ba?”
“Saboda take na sallame su, ke kuma kin ki mu fahimci juna shi yasa na bar dakin a haka!” Gyada kai tayi sannan ta ce mishi.”Ai auren mu, bai da wani fa’idar mu gina shi da wani abun da ba lallai ya kasance ba, idan muka rabu zamu wahalar da juna.”
“Ina jinki me ke tafe dake?”
“Zan tafi al’umma charity House ne!”
“Ba zaki ba.”
“Amma me yasa kake min haƙa!”
“Saboda ina son kwanciya dake ” ya faɗa mata kai tsaye, sai lokacin ta lura daga shi , sai polo shirts da dan boxes.
Dauke kai tayi tana jin kamar ta rusa ihu. “don Allah ka bari naje an yi haihuwa ne zanje barka!”
Ture laptop din yayi ya ce mata. “Kofa a bude take, maza tawo sai ki tafi duk inda yayi miki.”
“Yanzu ba zaka bar ni don Allah ba, sai na sadaukar da jikina.” Banza yayi mata ya cigaba da aikinshi. Kamar tayi fushi amma dai ta tuna ba zai tab’a barinta zuwa ba. “Malik ni fa ban tab’a yi ba, wallahi ban tab’a irin wannan yanayin ba, wahala yake bani don Allah kayi min, sama sama.”
“Ai ko minti biyar ba zamu kai ba” ya faɗa yana cigaba da aikinsa. “Shi kenan” ta faɗa kamar zata yi kuka. “Zo nan” ya bude mata hannun. “Kafin kizo cire kayan!” “A’a ba zan iya cire kayan ba, kawai kayi da kayan a jikina sai ba fita.” A ranshi ya ce. “Yarinya zaki cire da hannuki” haurawa gadon tayi, ya ture laptop din gefe. Ya bude mata hannun. Ture hannunsa tayi ta koma saman gadon, ta zauna, janyota yayi ya matseta da jikinshi. Bakinshi ya kai dokin wuyarta yana lasa, har zuwa kunnenta. Bata san lokacin da ta zabura zata mike ya kuma rike ta, ai kuwa jikinta ya shiga rawa, juyata tayi tare da kurawa fuskarta idanu. Bai san lokacin da ya kai hannunshi fuskarta, tare da lallubar tun daga fuskar ta har zuwa kirjinta ba.
Wani irin bala’in kiss da lasheta yake yi, yana jin kamar ya hadiye ta, jan zip din rigar yayi kasa, ya fita bata sani ba. Push-up bra dinta ya kurawa idanu, hannu ya kai ya ɓalle shi….
book 2 zai zo muku Whatsp da Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/23, 1:53 PM] Yan Mata: Volume:19 guest.
Tun daga kanta har zuwa kirjinta, yake haukata, kamar zai cinye ta. Wani zazzabin karfi da muradi yake ji na kara taso mishi, bai san lokacin da ya damketa ba, domin yana jin kamar wani abu yana yawo a kanshi. Kanshi ya daura a tsakanin kirjinta, ya shiga murza kowani na shanun. Ita kan ba zata iya tantacce me take ji ba, abu ne da yake sabo a wurinta, ko wancan karon da ya faru na shanunta ne yayi ta azabtar da ita da ciwo, yau kan da alamu, sun dauki sakon Malik, domin ita kanta bata san lokacin da ta biye mishi ba, suka shiga haukata junansu da wani irin zazzafar kauna, ita kanta bata san lokacin da take biye mishi ba, sai dai wannan karon kamar farkon faruwar kome, domin sai da ya kai yana jin motsin lafiyarshi, amma kuma yana zame wandonshi, yaji kome ya tsaya cak.
Da sauri ya mai da wandon, amma ina wannan karon ma babu wani respon domin taki daukar wuta balle chaji, ita dai yarinyar da ya d’agowa hankali ita ya samu yayi ta, murzata yana kara matseta, sai da ya ga jikinta yana rawa, ya kyaleta. Yana rungume da ita, a bangaren Zeeno kuwa gani take ai iya wannan shi ne auren, kwantar da ita yayi a kirjinshi tana sauke ajiyar zuciya, kanta na daidai kirjinshi. Tana jin yadda zuciyar shi yake bugawa, lumshe idanun tayi tana jin abin har tsakiyar kanta. D’ago ta yayi a hankali ya kalli fuskarta, a hankali ya kama fatar bakinta yana tsotsa. Ba zai ce ga yadda yake ji ba, amma abin da daure kai. Haka yana lura da ita har barci yayi gaba da ita. Sannan ya ajiye ta, ya nufi ban daki wanka yayi ya fito ya shirya, ya nufi ban daki.

Bata farka ba sai wurin karfe biyu. Wanka tayi ta nufi dakinta. Da hanzarinta ta bar gidan. Tare da nufar cikin gari. Tsabar ta samu sake bata dawo gidan ba sai bayan isha. Ta tawo da Chu-chu, dakin Malik ta leka ta ga baya nan, sai ta wuce na ta, bata yi tunanin kiranshi ba.

Har wurin karfe goma tana zaune, Chu-chu tana barci, ganin ba zai dawo ba yasa ta shiga ban daki tayi wanka, ta kwanta. Tare da tunanin dama haka yake baya dawowa da wuri ko kuma yau ne bai dawo ba. Har barci ya ɗauke ta bata san kome ba, kuma tun bayan fitar ta Elbashir ya zo aka ce mishi basu nan. Ya tambaya yaushe ta fita aka gaya mishi, Malik fa? Suka ce ai yakai sati idan ya fita baya dawowa Sai dare, wani bin asuba. Shiru Elbashir yayi, ya koma da isha da ya dawo aka ce tana ciki, ya ce Malik fa suka ce bak dawo ba, don haka koma bai shiga ba, yayi parking ya zubawa Sarautar Allah ido. Yana son ga da gaske ne Malik baya dawowa gida sai tsakiyar daren.

Abin mamaki yana wurin zaune a cikin motar har karfe biyu da arba’in da tara, Malik ya dawo. Bude motar shi yayi ya nufi motar Malik. Don ranshi yayi mugun b’aci, budewa yayi ya shiga suna kallon juna. “Ai kai ba yaro ba ne, don haka gobe xan zo muyi magana;” ya bude motar ya fita, Malik bai kawo kome a ranshi ba, suka shiga cikin gidan.
Yau kan yana son ya kwanta a jikinta, don haka yana shiga cikin gidan. Dakinta ya wuce sai dai kash, ganinta dauke da Yarinya yasa shi juyawa ya koma dakinshi.
Da safe, tana idar da sallah asuba. Ta fita tare da hado kayan tea ta ajiyewa Chu-chu. Tana idar da sallah ta haɗa mata abin karyawan ta sha, sannan ta koma suka kwanta.
*01:30am*
“Na gaya maka Malik, duk abin da ya fito bakina zan gaya maka, ai na san dole zan iso wannan matakin amma ba zan tab’a lamuntar ka zalunci Mareniya ba, me ta maka? Akan me zaka na tsalleke matarka kana zuwa zaman jinyar Yarinyar da Uwarta take son ganin bayanka?”
“Bashir ina ruwanka da ni? Gidana ne i have right da zan tafi ko yaushe na dawo ko yaushe. Ina ruwanka da ni?”
“Ok shi yasa kake dawowa tsakiyar dare ko da asuba? Shi yasa kake yadda kaso don tana gidanka? Aurenta kayi ko alfarma ka mata? Gata nan aurenta kayi ko alfarma ce kayi mata? Batun Maidah ta dawo gidan nan bai taso ba”
“Gida na ne, ina da ikon kawo duk wanda ya min, kuma ka fita daga cikin harkan gidana!” Daga haka ya nufi hanyar waje. Bata san meke faruwa amma ganinsu kowannensu ya dauki zafi yasa bata iya cewa kome ba. “Zan ajiye maka aikinka zan koma wurin ahalina! Domin na gaji da makotaka da zububinka ba zan iya daukar zunubin marainiyar da bata san wacece ita ba;” daga haka ya ajiye mishi takardun a tsakiyar center table. Ya juya ga Zeenobia. “Kiyi hakuri!”
Daga haka y bar gidan, akan idanun Malik ya wuce abinshi. Sai da yaji ran shi ya b’aci, taya Elbashir zai bishi da kafar shi zai dawo. Tun daga ranar bai kuma jin duriyar Elbashir ba. Da gasken gaske Elbashir yayi fushi.

Kwana uku tsakani aka sallame Maidah, kai tsaye gidanshi Lalla Salmah ta kawo ta. Kafin wannan ranar, tana kwance ta ji ana ta buge buge dake ta maida Chu-chu gida. Fitowar da tayi ta ga dakin da yake kusa da na Malik ake buge bugen. Bata kawo kome ba, ta leka gyara ake a dakin don haka ta juya, da safe da suka hadu tunda zuwa yanzu ta fahimci baya kwana a gidan, a hankali ta koma daki ta cigaba da kwanciyarta. Haka a cikin kwanakin aikin. Ranar da zasu zo gidan da safe ya biyo ta dakinta ya ke gaya mata. “An jima Maidah zasu zo, ita da Uwarta wancan dakin da yake gaban nawa zata zauna.”
Cikanka bata ce mishi ba, ya gama maganar shi zai fita ta ce mishi. “Amma kasan ma gaji da zaman jiran maka gidanka? Zan koma rayuwata ta baya, idan tazo sai ta cigaba da kula da kai.”
Kallonta yayi ya ce mata. “Kishina kike?” Dariya yayi sannan ta ce mishi. “Allah ya kiyayye nayi kishinka, yadda ban sonka ba bana fatan na soka”

Wannan abin ya bashi haushi, don haka ya zuba mata idanu. Izuwa yau da su Maidah suka zo gidan, tana zaune a falo suka shigo suna hirar su, alamar farin ciki da jin dadi. Ganin Zeenobia yasa su shan jinin jikinsu. “Sannunku!” Ta faɗa rai a sake. “Yawwa!” Lalla Salmah ta amsa mata, rai a b’ce domin ta tsani ganin Zeenobia.
Daki suka wuce dake ya gaya musu. Suna shiga uwar ta cewa Yar. “Zama ba naki ba ne, dole ki shiga jikin Malik. Ki nutsu ki fahimci yadda zaki kwace shi kada ki dake ta fahimci kinyi nisa sai an fara maganar aure na gaya miki. Ina son ki mishi yadda zaki raba su.”
Ita kan Baiwar Allah bata san kome va, haka suka gama kulle kullensu. Suka fito suna kallonta a wulakance.
Koda Maidah ta dawo, shiga kitchen tayi ta shiga bada umarnin abin da za a girka a kaiwa Malik office, domin ta shirya tsaf zata kore Zeenobia. Ita kam Zeeno bata wani damu ba, domin Malik din ba damunta yayi ba, balle har ta saka a kanta.
Wannan yasa baki daya ta bar falon ta koma dakinta, wurin karfe biyu na rana aka kaiwa Malik abinci, bayan Maidah ta tabbatar da inda yake, bata yarda ta ce mishi ita ta saka ba, domin da ta kira shi a shagwabe ta ce mishi. “Dadi kana iya?” “Ina office!” “Ok dama na kira naji lafiyarka ne. Kuma za a kawo maka abinci!” Bata bari yayi magana ba ta kashe wayar.
Ana kai mishi abincin, abokan shi da suke tattauanawa suka zata abincin amarya ne, don haka ko sakawa a bakinshi bai yi ba, suka cinye abincin.
Kafin ya dawo an mishi tuwon shinkafa miyar ugusi da yaji nama da ganda, stockfish, dryfishi. Da zallar namar rago. Tunda Zeeno ta fito ta ga a tare suke aikin da Chef bata ce kome ba, ta koma gefe ta hada tea da Cookies, ta fita sam bai dame ta ba, har bayan isha da ya shigo gidan ya same tana zaune. Ta sha kwalliya kamar me zuwa party. “Sannu da zuwa dadi! Ya aiki?” A ranshi bai yi na’am da ita ba, amma don ya saka Zeeno ta zo gare shi ya ga ya samu opportunity da zai ga yadda zata dauki sabon relationship dinsa da Maidah.
Sai dai a wannan gaɓɓar ya fadi, domin Zeenobia bata cikin mutanen da suka bar matsalar su har wani ya sani, shi yasa koda ya wuce bai ganta a falon ba, sam bai yi tunanin kiranta ba, ya amshi jakarshi ua shige dakinshi. Yana watsa ruwa ya fito ya nufi wurin abinci. Maidah ta zuba mishi, ya tunda ya saka abincin a gaba Zeeno yake son gani bata fito ba,haka yayi ya hadiye abincin kamar yana cin guba, sai da ya kusan gamawa ta fito tana, latsa wayarta tana sanye da 3qrts. Kanta babu dankwali, kitson da tayi kalaba ce, ya sauka har bayanta. Daya ta mishi ta sake yar murmushi ta ce mishi. “Kawo ya aiki?” Daga haka ta wuce kitchen. Ta hado tea ta dawo falon ta zauna, baki daya tunda ya ganta ya susuce. Cire hannunshi yayi cikin abincin ya wanke, sai da ya goge sannan ya nufi dakin karatu da yake falon. “Dadi inzo na tayaka hira ne?” “No ga Auntynki kuyi da ita.” Ya saci kallon Zeeno a ranshi yana mamakin halinta.

Haka suka zauna bayan ya bar falon, Zeeno ta kira Hafsy suka shiga hira. “Ke akwai abinda zan kawo miki, na je wani gida kwalliya ake hirar abin shi ne na saya miki zaki sha ko?” “Eh tow bari na gani ko!” “Ke ance na jin dadin aure ne, ina son ko gwada ne ko dagaske!”
“Ke!!!” Ta mike tare da nufar dakinta, ta lailayo asharia ta ruga mata, ta ce mata. “Bana son iskanci ba zan iya bawa wannan tsohon jikina ba, na gaya miki!”
“Wallahi sai na gayawa Ammyn idan ta dawo ”
“Ke wasa nake miki!”
“Yaushe kika fara wasa ban sani ba?”
“Kinga wallahi wasa nake, don Allah kada ki hada ni da ita zata ga kamar ba biyayya na mata ba, sannan ki fahimta wallahi ba zan iya bashi kaina ba ne. Da kunya na bashi kome daga gare Ni! Don Allah kada ki gaya mata.”
“Ban tab’a sanin ke wawuya ba ce sai yanzu, Zeenobia wallahi baki da hankali baki daya, hakkin aurenshi kike hana shi. Lallai Allah sai ya kama ki, kuma kika mutu a wannan yanayin wuta zaki wuce.”
“Hafsy!”
“Dalla yi min shiru, kamar tasan Allah zan zo ki gaya min illar abin da yake jikinshi? Shugaba ne guda, wallahi idan nice ke mike kafa zanyi nayi ta haihuwa da shi.”
“Amma ya zanyi?”
“Ki tafi wurinshi, hala ma a dakinki kike kwana?”
“Hmm!”
“Na shiga uku, Zeenobia baki tunanin wata ya kwace miki shi?” “Tow ance miki Ina sonshi ne da haka zai dame ni?”
“Sakarya kawai, sai kiyi ai!” Ta kashe wayarta don haushi. Duk da Maidah tana bakin kofar, ta saka kunnenta. Murmushin mugunta tayi, “Mu zuba mu gani waye zai yi nasarar mallakar Malik Menk Jordan!….
book 2 zai zo muku Whatsp da Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/23, 1:53 PM] Yan Mata: Volume:20
Zama Zeeno tayi, kanta ya daure bata san me zata yi ba. Yadda Hafsy ta ce zata gayawa Ammyn gara tazo. Kiranta tayi tana faɗin. “Don Allah Bestie ki kawo min zan sha, wallahi ba zan kuma ba”
“Shi kenan jibi zan zo kin sansu Ammy suna hanya wata sati?” “A’a bata fada min ba” “Ok xan zo mu gyara musu part dinsu.”
“Kina nufin a nan zasu zauna?” “A’a bai gaya miki baa gama musu gyaransu ba ne?” “Nifa ban san kome ba!” “Ina zaki sani wawuya kin mai da kanki baya, wallahi kika sake Malik ya samo wacce ta fiki hankali da sanin ya kamata kin rasa shi kenan.” “Ji ki da wani shirme!” Ta fada tana dariya, domin kuwa tasan bata son Malik baya ga dalilin da zai saka ta ji haushinsa ba don ya nime wata mace.
Haka suka gama wayar asannan ta kwanta, a nan barci yayi gaba da ita. Can wurin karfe ɗaya. Fitsari ya matseta, ta nufi banɗakinta. Tana fitowa ta ji sautin tv.
Kugi cikinta yayi alamar yunwa, a hankali ta nufi hanyar waje. Maidah da Malik ne a falon, wai suna kallo. Kawai sai ta dauke kai ta wuce kitchen abinta, ta haɗa tea domin shi ne abin da ko mutuwa tayi ya farka zata hada ta sha bata wahala ba. Ta haɗa da cake da ta gani a kitchen din, ta fito falo ta zauna tana me kallon tvn itama. Wani station ne suka saka 365 kuma da alamu ba a jima da farawa ba. Kallon Film din tayi ta tuna sun tab’a ganin shi da Hafsy. Kai hannunta yayi ta dauki remote din, kafin ta kashe received ɗin tare da wani irin haɗe rai ta ce mishi. “Ina ga a matsayinka, na uba wannan Film bai da ce da kai ba, balle a matsayinka na me rikon Yaran wasu.” Sai a lokacin abubuwan da yake mata suka shiga fado mata, wani irin rintsa idanu tayi tare da girgiza kanta da ƙarfi. Bata san lokacin da ta nime kwarewa ba, ta mike zubur mike tare da nufar dakinta. Tana shiga Malik yana biyo ta,
“Me kazo yi?”
“Ina son ki bani labarin Film din can?” “Kai ina ni yunwa nake ji!” “Fa sai kin bani labarin film ko kuma na kunna na gani a dakinki!” “Sai kayi kuma” ganin ba zata bashi hadin kai ba, ya nufeta da sauri. Garin ta gudu, ta kware a karo na biyu da tea din, zama tayi tana tari.
“Sannu!” Ya shiga shafa bayanta yana mata sannu. Ganin haka yasa ta jinjiga kai tana kokarin mikewa, ya kuwa shammaceta ya daurata akan cinyarta. “Ki kulani don Allah!” “Kai jinjiri ne da zan baka nono?” Sama yayi da rigar jikinta. Yana shafa kirjin. Buge hannunshi yayi yana faɗin.”ki bar ni na more sadakina!” “Ni dai bana so!” Hannunshi baki ɗaya ya daura a fuskarta yana faɗin. “Me nayi miki? Ko kina so na gayawa Ammyn ne kina bani wahala?” Ware idanu tayi, tana faɗin. “Idan ka gaya mata, mutuncina zubewa zayi”
Dariya ta bashi ya ce mata” tow gaya min ya zan yi?”
“Hmmm! Ka ga dai ni waɗannan abubuwan ciwo suke min, ranar da kayi min dakyar na saka riga. Haka ma na ranar ban iya daura towel ba a saman shi!” Bakin shi ya kai kunnenta yana faɗin. “Basu saba ba ne, idan suka saba ba zasu miki ciwo ba! Ki bari nayi.” Shiru tayi kafin ta rintsa idanunta.
Duk abin da suke Maidah tana jin kamar ta fasa ihu. Tana tsaye tana jin yadda Malik yake kome, idanunta sun yi jajjur. Komawa dakinta tayi ya kasa zama ta kasa tsaye. Har wurin asuba. Malik da yar kwailarshi kuwa, yau ma ba karamin hadin kai ta bada ba, domin shi kanshi ya sha mamakinta, abin da bai sani ba, jikinta ya fara sabawa da abin da yake mata, yadda dan tab’awa idan yayi take jin haka a ranta, har bata son ya daina tab’a ta. Sai dai a bangarenshi kan babu wani cigaba, abu ya tsaya cak kamar wanda aka haramta mishi kulawa da kome.
Kusan a jikinshi ta kwana, a karon farko a rayuwarta, duk da sauran kwanan da suke ba kamar wannan ba, an samu body contact, wanda ya kara effect ɗinsu ba su sani ba, ga Malik za a iya cewa ya sani amma ga Ita gimbiya sai a hankali.
— Washi gari babu wanda ya fito daga cikinsu, sai karfe daya na rana, domin sake yi suka yi bayan sallah asuba da suka. Ya kuma matseta, haka da wurin karfe sha daya sai da ya kuma hargitsa mata lissafi, sannan ya samu sauki wai shi a tunaninshi.kada shin sauke hakkinta.

Abun karyawa yana ajiye, har an gama na rana basu fito ba,.daki ta koma ta kira Lalla Salmah tana kuka. “Maama yarinyar nan makira ce, da zarar Dadi ya ganta bai da nutsuwa sai ta bar wurin.”
“Listen to me, abinda zaki lura anan Malik yana sonta ne sosai, don haka ki saurari abin da zan gaya miki da kyau!”

“Kina tsammanin haka zai tafi daidai Maama?” “In sha Allah!” Daga haka suka ajiye hiran. Lokacin da Malik da Zeeno suka fito wasai fuskarsu. Haka suka sha hira suna karyawa.
Wunin ranar Malik ya ki fita ko ina, yana zaune a gida, sai dai har ga Allah ya gagara Manta Elbashir, sai yanzu yake jin.babu dadi amma ya share kamar bai wani damu ba.
***
Demark
“Kuma kawu da ka zo nan, ka bar shi cikin makiya adalci ka mishi? Gaskiya kawu baka kyauta ba, nasan yallabai Malik baya Abu sai da hujja. Ka koma yana da dalilinsa!” “Bai da hujja! Yarinyar da yaƙe aure ta sanadin Malik ta manta da kome nata, ta sanadin Malik aka kashe iyayenta, me ya kama yayi? Sai ya dauke kome a kanshi y zauna da ita, amma ya taso ya kwaso Lalla Salmah jikinshi.”
“Duk da haka, ka kyale shi ka bi a hankali akwai dalilinshi nayi haka!”
“Taya zan bi a hankali? Yarinyar tausayi yake ba ni, yasan sarai idan ta fahimci wacece ita ba zata barshi ba yasa yake mata haka, ba zan iya ba.”
“Tow yanzu fushi kayi ko kuma barin Malik kayi?”
“Duk ɗaya nayi, na bar shi da fushin?” Kallon shi Adnan yayi baki sake, sannan ya ce mishi, “Kawu wani lokaci, na kan kasa gane kai da Malik waye me fahimta. Shima nan wani lokaci yayi fushi ya bar maka Keivroto yanzu kai ma ka bar mishi Keivroto. Sai kuyi ta yi tunda ku ba yara ba ne.”
“Kai ni sa’anka ne? Sai na sab’a maka, dismissed” ya nuna mishi hanyar waje. “Ka da ka manta yarinyar da kuka cillata cikin tashin hankali, saboda muradinku Allah ba zai bar ku ba” Yana gama fadar haka yayi gaba abin shi. Tsaki Elbashir yayi yana kanshi kamar zai cire.
***
Keivroto
Suna zaune a falo, Maidah ta rike kanta tana yar zabura kaɗan, “Lafiya kuwa?” Zeenobia ta tambaye ta, dake Malik yana dakin karatu, nazarin wasu ayyuka yake, bai san yadda suke ba. Mikewa tayi zata wuce dakinta, ta yanki jiki ta fadi tare da fasa ihu me mugun ƙarfi, tana faɗin”Wayyo Allah na, zasu nan zasu tafi da ni?” Tana ja da baya,kallon wurin tayi bata ga kowa ba, ta kai hannu zata rikota ai kuwa ta fasa ihun da sai da security guard suka shigo gidan, Malik babu shiri ya fito dakin karatun.
Aka rufa a kanta, ita kan Zeenobia bata tab’a ganin tashin hankali irin na yau ba, don haka tayi ta binsu da idanu. Kafin wani lokaci Maidah ta hargitsa gidan, dole aka wuce da ita dakinta, a can tayi ta faɗa Malik yana mata addu’ar da tazo bakin shi. Yau yake jin kewar Elbashir. Har asuba yarinyar nan ta hana Malik fita, karewa a wurin suka kwana, su uku. Da assussubar fari, Lalla Salmah ta dira a gidan.
Aljanun suna ganinta, suka fara magana. “Wayyo Allah! Gara da kika zo da wuri kafin a kassara mana godiyar mu, Keee fita kafin mu shanye jininki, alugunguma munafuka. Karuwa wacce ta zubda ciki babu iyaka, fita kafin mu tona asirin kika saka a binne kawarki zasu zo ta kawo miki maganin da zaki mallake Malik!” Shiru tayi ta fara gurnani. A hankali Malik ya riko hannun Zeenobia ya fitar da ita zuwa dakinta. Sai da ya shigar da ita sannan ya zuba mata idanu, zma tayi a bakin gado jikinta babu kwari. Sunkuyar da kai tayi, zagin da aka mata yake yawo a kanta. Wani irin d’ago kanta tayi, suka kalli juna idanu cikin idanu, da sauri ta rintsa idanunta, a hankali jini ya fara saukowa daga hancinta. Mikewa tayi yayi ya saurin fisgota ta faɗa, jikinshi wani azzababen rawa jikinta yake, idanunta ya rufe. “Relax! Ina tare da ke, ai ya gaya miki na yarda da ke, me yasa zaki razana? Idan ma duk kinyi haka ai don ni kika yi ko? Ina sonki. Show then you love me! Tell then how you love me! Kada kiyi faɗa a kaina, kaina Please ban yarda da ire -iren wadannan abubuwan ba. Ya Isa haka!”
Tura kanta tayi kirjinshi, tana kuka a hankali, har barci yayi gaba da ita. Kara rungumeta yayi suka koma gadon. Har g Allah a nan ya manta da Salmah da yarta. Basu farka ba, sai karfe goma na safe shima wayar Malik da yake ta kara ne a falon. Tana jikin a nade sai barci take. A hankali ya cire rigar jikinta, ya ɓalle botirin rigarshi yana jin fatarta a cikin nashi. Kara rungumeta yayi. Yana goga mata hancinsa a dokin wuyarta.
Zare jikinshi yayi ya shiga wanka, a dakinta. Sannan ya fito ya nufi dakinshi yayi Sallah sannan ya shirya ya kuma fitowa, a wurin cin abincin ya samu yar karamar wasikar Lalla Salmah.
*Malik ban ji dadin, abin da ya faru ba. Na mai da Maidah gida ta karasa jinyarta*
Ajiye wasikar yayi ya koma, dakin wurin Zeeno ta fito wanka tana saka hijab zata yi Sallah ya ce mata. “Maidah ta tafi!” “Allah ya bata lafiya!” Daga haka ta taddata kabbara. Tayi sallanta. Tana idarwa ta sauya kaya ya fito cin abincin. Suna cikin cikin abincin, sai ga Maidah kamar an korota.
“Dadi! Ban san me ya faru ba kawai na farka na ganni a gidan Maama don Allah ka ce kada ta kuma tafiya da ni.”
“Babu kome.” Ya nuna mata hanyar dakin. Wasa wasa, Maidah ta sako Zeenobia a gaba da iskancin da aljanun karya. Idan ta gama zaginta zata buge da barci. Idan kuma dare ne babu wanda ya isa rintsawa. Rashin barci ua haifawa Malik hawan jini domin ko kebewa yayi Zeeno zata fara ihu da hauka.

Duk Zeeno ta zama abin tausayi,domin idan ta fara haukar ita kanta Zeeno bata isa tayi barci ba, tayi.ta ihun a kira Zeeno. Wannan abin ya dami Malik don haka dole ya kira Sayyada Quddisiya ya gaya mata abin da yake faru. Ba tare da sanin Zeeno ba. Domin ya gayawa Maidah zasu tafi Demark. Amma bai gaya mata har da Zeeno ba. Ta kira Uwar ta gaya mata. Ita kuwa ta haɗawa yarinyar kayan gyaran jiki ta ce. “Na san halinsa ki bashi duk abin da ya bukata!”
“Tow!! Ana gobe zasu tafi ne, Hafsy ta zo. Tunda ta zo ta ga Zeeno zaune tana gyangyadi. “Ke ko mun samu Baby ne? Kin san gobe su Ammy zasu zo?”
Tashi tayi tana murmushi, duk ta lalace ta ce mata. “amma ba iya Saudiya suka tsaya ba?”
“Sun tafi Dubai hada kayan auren Abbas ne, meke damunki?” Gyara zama tayi ta fara bata labari, kallon Zeeno take kamar ta rufe ta da duka. “Amma ban tab’a ganin banza sakarya irinki ba. Kina zaune ana shirin rabaki da mijinki? Wannan sharrin makirci ne fa. Ba Aljanu ne suke damunta?”
Shiru tayi tana kallon Hafsy. “Ba zaki gane ba, sai ya tashi a gabanki.” Kamar jira take Zeeno ta fadi haka ta fara zuduma musu ihu, ke kuwa Hafsy da iskanci ta zafi wayar chaji ta nufi waje, tana kwance a kasa sai burgima take, Allah ya bawa Hafsy sa’a ta shiga zane ta, ai tuni ta qare ta fara ihun niman taimako. Ita kuwa Hafsy cewa take. “Yasarkumu zarkkukka, maza fita kafin na kona ka da ayar Allah!” “Wayyo Allah na, wallahi nice Maidah”
“Kece Anya kuwa?”
” Ba dai Maidah ba, Aljana Julka ce bari na cire ta don ubanta me rantamemen kai!” Sai da ta mata likis, sannan suka kyaleta. Murmushi Zeeno tayi ya ce. “Sayyada Hafsah ga Aljanu dai sun fita ya zamu yi kenan?” “Idan kina da barkono ko garin barkonon dauko a jika mata yayi wanka sauran a nimo abin turaren wuta a mata hayaki muje kafin ta farka a barci!”
Suna fita Maidah ta tattara ta gudu, bata yarda ta tsaya ba, balle yan iskan yara su kasheta.
Lokacin da ta isa gidan, ta samu Shatima da Lalla Salmah. Mikewa Uwar tayi tana tambayarta. “Waye ya miki haka?” “Wadancan Yaran! Wallahi duka suka min” ta fada cikin kuka. “Kin yarda yarinyar she meant to Malik? Duk yadda zaa raba su, ba za a yi nasara ba. Har saka nayi a rufe min shi, kada yayi kome da ita amma kin ga aikin bai yi tasiri ba, don haka dole yau na fatauci Malik har lahira! Su kashe shi su dauko min ita.”
“Ina ganin haka duk ba yi bane, amma dole muyi kashe muraba da dukiyar shi!”
“Duk inda yake a cikin gidan na basu aikin farautar shi, a kashe shi a yanko min kanshi. Khuldu Jahid Khan shima ua bukaci na kashe Malik, shu’iba ma haka har kuɗi suka saka min sun bani kafin alkalami. Ni kuma nace su hada Malik da yarinyar su kashe domin ko sun kawo min ita ba zata yi min amfani ba.”
“Ina Elbashir ya tafi!” “Ya rabu da Malik tuntuni!”
“Kai wannan abin ya min dadi! Zamu iya Daurawa Elbashir ɗin”
“Wannan shi ne shirina!”
Sun jima suna saka yadda zasu kashe Malik, kafin suka ajiye maganar daren yau. Zasu kashe Malik.
***
A bangaren Zeeno kuwa, aikin abincin suka yi da Hafsy. Har yamma , dake zata kwana a gidan ne, Malik ya ce a’a ta je gida. Su Ammyn ma ba yau zasu dawo wata sai wata sati suna can Demark.
Aikuwa Zeeno taji haushi bana wasa ba domin taso su kwana da Hafsy su tashi akan aikinsu.
Wani irin abu take ji, kamar an tsoma ta a cikin ruwan sanyi haka yasa baki daya , bata da kuzarinta. Ga uban faduwar gaba. A can waje kuwa Malik ya sallame kowa yana ce musu cin dare zai yi tafiya don haka su koma gida zai nime su.
Wannan shirin ba iya Shatima yayi ba, shi kanshi yayi shirin akansu, shi yasa ya janyo Lalla Salmah jikinshi………
book 2 zai zo muku Whatsp da Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/23, 1:53 PM] Yan Mata: Volume:21 Villains
Malik ya kware a iya jan makiyanshi jikinshi, ya kuma basu abinci yana tatsar gubansu. Domin yasan matuƙar suka shiga jikinshi, definitely zai san kansu. Kuma ya samu. Tun kafin Amjad Fahad su shiga jikin Zeeno ya fara nimanta, ya kuma san cewa dole ita zata iya shiga aikinsu shi yasa da tazo kai tsaye ya amshe ta, ya kuma saka mata sharadin aure a tsakaninsu. Daga Lalla Salmah da Shatima yasan cewa idan ya nime Auren Yaransu, aka yi kudirin su shine yaransu kwana ɗaya a gidanshi ranar na biyu su maka shi a kotu.
Shi kuma sai yayi musu wayon kin yarda da auren Yaran, na farko Nadrah wacce lokacin da ya ganta yana da interesting akanta, lokacin bai sake ya bar ta ba, sai da yasa mata wayar wani pen dinsa a jakarta wanda lokacin da ta isa gidan ya ji, yadda Shatima yake son ya shammace shi, ana auren ko kwana uku ba ayi ba, ya mallaki rabin dukiyarsa.

A bisa tsarin kasar, matukar mace ta ce ba zata zauna da kai, dolenka idan zaka saketa ka raba dukiyarka biyu, a bata rabi shi Malik ba fitar dukiyar ba ce matsalarshi, hannun wanda zata faɗa ne baya fatan haka, shi yasa ya ki maganar auren a tsakaninsu da yaransu, koda Zeeno tazo yasan tabbas zata zo domin ya jima yana nimanta. Ba iya shi ba hatta Zulfa da Yasir Aswad Al Yemini.

Tun bayan rasuwar iyayensu, yayi kokarin niman Zeeno amma bai zame ta ba, Yasir da Zulfa ya samu ya mai da su wurin danginsu, amma Yaran suka ki zama dole ya dawo dasu Keivroto tare yi musu alkawarin nimo musu Zeeno.

Har zuwa hatsarinshi da yayi fatan da ya hadu da Zeeno, ya kaita wurin Yan uwanta. Dake Yasir ya fi Zulfa wayo. Ya taso da mugun tsanar Malik domin akan kunnenshi ya sha jin tashin hankali da iyayensu suka shiga. Sai da ya gama secondry school. Ya tafi jami’ar da Malik ne ya dauki nauyin shi, a lokacin ya shiga binciken motsin Malik, da abubuwan da yake faruwa, yana gama jami’a yayi joining Police academy. Inda ya fara nazartar abubuwan d suka shafi binciken. Ba karamin wahala yasha kafin ya iya gano wasu bakin zaren munakisar da aka yi na wani case din dan kasar China da Malik ba. A lokacin sai da aka yi wata biyar ana bincike kafin aka kama mutanen da suka kashe dan china da sunan Malik, wannan ya wanke zargin Malik wato rigar shi ake sakawa ana kashe mutane, kwarai a lokacin yayi aiki da Malik ba na wasa ba, domin yadda ya dinga bin didigin Malik da gayyatar shi, yasa Malik yayi ta saka shi yana haduwa da manyan har ya kai matsayin da yake na AIG a tsakanin shekaru Ashirin da tara a duniya.
Wannan kenan.
Yadda take ta juyi, tana jin wani irin bala’in tashin hankali yasa ta mikewa zata fita, wutar gidan daukewa. A hankali ta soma jin wani irin motsi me mugun rikitarwa. Duk wannan abin da ake baki daya Malik yana kallonsu ta cctv. Har dauke wutar, sai da ya kirga yawansu. Kuskuren da yaso aikatawa barin Zeeno ita ɗaya a cikin dakinta. Haka ya shiga bi ta wasu hanyoyin gidan, sai da suka shiga asalin falon gidan, sannan suka ji waka a bayan sun. Juyawa suka yi tare da kai harbi. Suka ga yar karamar Radio ce ta MP4.
“Sako ya shigo, Malam Malik Menk Jordan me kake bukata a wannan lokacin?” MP4 ya tambaye shi, daga bayansu ya ce mata. “Malam Rebecca wuta za a bude musu!” Juyawa suka yi, suka samu baya nan, sake juyawa wurin MP suka yi, suka samu yana tsaye. “Sako ya kammala!” Kafin kace kwabo an bude musu wuta, karar harbe – harben ne ya kidima Zeeno ta fadi can kasa, ashe wasu sun biyo ta window dakinta, suka fasa glass din window suka shigo.
Zare idanu tayi ganin yadda suka saka mata bindiga a kai, tare da riko gashin kanta, suka fito da ita, suna haska torch. ” Ka sake baka dakatar da Harbin nan ba, zamu kashe ta!” Hasken gidan ne ya kawo, tana tsaye suna rike da kanta, dukar kafarta suka yi, ta durkusa. “Ku kyaleta tafi, ni ku min abinda kuke so”
“Ai mu baki dayanku aka ce mu kashe ba zamu tab’a kyale ku ba.”
“Wannan shine kuskuren da zaku aikata, matata bata san kome ba.”
Ya faɗa yana kallonta yadda take kallonshi. “Ka mana shiru!” “Tow ku kyale ta”
“Munki kyaleta!”
“Kuskuren da kuke aikatawa fa ba zai kaiku ko ina ba?” “Dama ai mu akan kuskuren muke. “Malama Rebecca duba adadin fitar numfashinsu!”
“Sako ya amsu!”
Kafin su fahimci me yake faru, hayaki ya cika falon, a lokacin ya saka abin zukar iska a hancinshi. Ya mike a hankali ya daga kan keken, idanun Zeeno kamar zai fado kasa, tana mishi wani irin kallo. Kafin ta ankara daga ita har mutanen sun fadi sunammu. Koda yake ita kafin ta daina hango shi, ta ga yadda yake takawa, cikin Isa da jin kai irin na gogagun marasa mutunci. Yana isa wurin da mazukin iskar ya saka mata a hancinta. Sannan ya ɗauke ta suka bar gidan, daya daga cikin motar shi. Ya sakata a gaba, snnan ya bude motar y zauna.
Yana shiga ya danna bleutooth, a hankali ya ce. “Malama Rebecca. Ruftar da gidan. Kada a samu wata shaidar ina raye”
“Malam Malik Menk Jordan, sako ya amsu!”
ba tare da bata lokaci ba, ya bar gidan, Haka ya rubta cikin karkashin kasa, a daren ya wuce bakin taku, aka saka motar shi a cikin wata kwantena, ya dauki matarsa suka shiga wata jirgin, tare da barin ƙasar. Koda zai dawo sai ya gyara shirinsa da matarshi domin yadda zai ci amarcinsa a nutse.
Tunda ya kwantar da ita ya kira likitan jirgin, ya fara dubata tare da saka mata ruwa, sannan ya shiga yayi wanka ya fito sannan ya dawo ya kwanta a gefenta. Yana kallon yadda take barci Bayan saka mata ruwan da aka yi. Bata farka ba sai da gari ua waye, har haske rana yana lekawa ta dakin sannan ya bude idanu tana kallon cikin dakin. A hankali ta sauka a gadon, ta ga wani kofa, bude kofar tayi ta ga banɗaki, wanka yayi tana me lumshe idanun kafin abin da ya faru ya shiga dawo mata. A razane ta zauna dabas a kasa. Kafin ta mike tana me yin alola. Ta fito ganin abin sallah a shimfide yasa ta nufa, tayi sallah.
Tana idarwa Malik yana turo kofar dakin, hannunshi dauke da tiren, ja da baya tayi tana faɗin. “Innalillahi!” Murmushi yayi mata ya ce mata. “Kin razana ne?” Ya d’age mata gira biyu yana murmushi. Yana matsawa gabanta, ya ja da baya. “Wayyo Allah mugun ji mugun gani Allah ka kare ni da gani” ta faɗa tana ja da baya.
Ajiye mata abincin yayi yana faɗin. “Oya zoki ci!” “Na koshi!”
“Ok haka ma yayi amma ki sani, yau zan amshi hakkina!” Ware idanu tayi tana faɗin. “Wallahi ba zan iya ba! Ni dama tausayinka nake ji, yanzu kuwa na daina tausayinka tunda da lafiyarka.”
“Wallahi sai kin bani hakkina kaji wani wayon banza,” haka suka yi ta jajjyayya, har yayi nasarar cafketa. Saka ihu tayi tana faɗin. “Don Allah kada ka min haka wani, wallahi ƙaddara ta kawo ni rayuwarka,. Idan ka yafe min xan fita.”
“Na ji zaki fita sai kin bari na haihuwa da ni ko daya ne, baki ga na tsufa ba ne”
“Wayyo Allah na, wallahi ni yar karama ce ba xan iya haihuwa ba ” saka bakinshi yayi a kunnenta. “Idan kika haifa min yara masu irin idanunki sai ki tafi a binki”
“Ai ko masu kama. Da ni ba zaka samu ba”
“Ai kuwa nasan wacce tafiki kyau zaki haifa min”
“Don Allah ka kyale ni!” “Idan na ki fa?”
“Ni dai wallahi ba zan iya ba” abin dariya haka yayi ta zolayarta, dakyar ya samu ta ci abinci, sannan ya ciro mata wani kayanshi ya bata. “Ina zan kai wannan jamfar?” “Sakawa zaki yi.” Ya faɗa yana mata dariya, wato sai yanzu ta ƙara gane Malik yana da barkwace da zolaya sosai ga babu abinda ya dame shi kai tsaye yake magana, yana daga cikin mutanen da basu dauki kai da wani damuwa ba, shi dai idan zaja mutuntatta shi bai da matsala. A cikin kwanaki uku da suka yi ya kara musu shakuwa, tunda ya fahimci ita din matsoraciya ce ya gaske. Domin da zarar ya ce yana son wani abu zata fara zaro idanu. Shi yasa bai sake niman kome ba, yayi kokarin koya mata yadda zata shiga jikinshi,
*Kuyi hakuri bamu da wuta ne*
book 2 zai zo muku Whatsp da Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*[9/23, 1:53 PM] Yan Mata: Volume:21 Villains
Malik ya kware a iya jan makiyanshi jikinshi, ya kuma basu abinci yana tatsar gubansu. Domin yasan matuƙar suka shiga jikinshi, definitely zai san kansu. Kuma ya samu. Tun kafin Amjad Fahad su shiga jikin Zeeno ya fara nimanta, ya kuma san cewa dole ita zata iya shiga aikinsu shi yasa da tazo kai tsaye ya amshe ta, ya kuma saka mata sharadin aure a tsakaninsu. Daga Lalla Salmah da Shatima yasan cewa idan ya nime Auren Yaransu, aka yi kudirin su shine yaransu kwana ɗaya a gidanshi ranar na biyu su maka shi a kotu.
Shi kuma sai yayi musu wayon kin yarda da auren Yaran, na farko Nadrah wacce lokacin da ya ganta yana da interesting akanta, lokacin bai sake ya bar ta ba, sai da yasa mata wayar wani pen dinsa a jakarta wanda lokacin da ta isa gidan ya ji, yadda Shatima yake son ya shammace shi, ana auren ko kwana uku ba ayi ba, ya mallaki rabin dukiyarsa.

A bisa tsarin kasar, matukar mace ta ce ba zata zauna da kai, dolenka idan zaka saketa ka raba dukiyarka biyu, a bata rabi shi Malik ba fitar dukiyar ba ce matsalarshi, hannun wanda zata faɗa ne baya fatan haka, shi yasa ya ki maganar auren a tsakaninsu da yaransu, koda Zeeno tazo yasan tabbas zata zo domin ya jima yana nimanta. Ba iya shi ba hatta Zulfa da Yasir Aswad Al Yemini.

Tun bayan rasuwar iyayensu, yayi kokarin niman Zeeno amma bai zame ta ba, Yasir da Zulfa ya samu ya mai da su wurin danginsu, amma Yaran suka ki zama dole ya dawo dasu Keivroto tare yi musu alkawarin nimo musu Zeeno.

Har zuwa hatsarinshi da yayi fatan da ya hadu da Zeeno, ya kaita wurin Yan uwanta. Dake Yasir ya fi Zulfa wayo. Ya taso da mugun tsanar Malik domin akan kunnenshi ya sha jin tashin hankali da iyayensu suka shiga. Sai da ya gama secondry school. Ya tafi jami’ar da Malik ne ya dauki nauyin shi, a lokacin ya shiga binciken motsin Malik, da abubuwan da yake faruwa, yana gama jami’a yayi joining Police academy. Inda ya fara nazartar abubuwan d suka shafi binciken. Ba karamin wahala yasha kafin ya iya gano wasu bakin zaren munakisar da aka yi na wani case din dan kasar China da Malik ba. A lokacin sai da aka yi wata biyar ana bincike kafin aka kama mutanen da suka kashe dan china da sunan Malik, wannan ya wanke zargin Malik wato rigar shi ake sakawa ana kashe mutane, kwarai a lokacin yayi aiki da Malik ba na wasa ba, domin yadda ya dinga bin didigin Malik da gayyatar shi, yasa Malik yayi ta saka shi yana haduwa da manyan har ya kai matsayin da yake na AIG a tsakanin shekaru Ashirin da tara a duniya.
Wannan kenan.
Yadda take ta juyi, tana jin wani irin bala’in tashin hankali yasa ta mikewa zata fita, wutar gidan daukewa. A hankali ta soma jin wani irin motsi me mugun rikitarwa. Duk wannan abin da ake baki daya Malik yana kallonsu ta cctv. Har dauke wutar, sai da ya kirga yawansu. Kuskuren da yaso aikatawa barin Zeeno ita ɗaya a cikin dakinta. Haka ya shiga bi ta wasu hanyoyin gidan, sai da suka shiga asalin falon gidan, sannan suka ji waka a bayan sun. Juyawa suka yi tare da kai harbi. Suka ga yar karamar Radio ce ta MP4.
“Sako ya shigo, Malam Malik Menk Jordan me kake bukata a wannan lokacin?” MP4 ya tambaye shi, daga bayansu ya ce mata. “Malam Rebecca wuta za a bude musu!” Juyawa suka yi, suka samu baya nan, sake juyawa wurin MP suka yi, suka samu yana tsaye. “Sako ya kammala!” Kafin kace kwabo an bude musu wuta, karar harbe – harben ne ya kidima Zeeno ta fadi can kasa, ashe wasu sun biyo ta window dakinta, suka fasa glass din window suka shigo.
Zare idanu tayi ganin yadda suka saka mata bindiga a kai, tare da riko gashin kanta, suka fito da ita, suna haska torch. ” Ka sake baka dakatar da Harbin nan ba, zamu kashe ta!” Hasken gidan ne ya kawo, tana tsaye suna rike da kanta, dukar kafarta suka yi, ta durkusa. “Ku kyaleta tafi, ni ku min abinda kuke so”
“Ai mu baki dayanku aka ce mu kashe ba zamu tab’a kyale ku ba.”
“Wannan shine kuskuren da zaku aikata, matata bata san kome ba.”
Ya faɗa yana kallonta yadda take kallonshi. “Ka mana shiru!” “Tow ku kyale ta”
“Munki kyaleta!”
“Kuskuren da kuke aikatawa fa ba zai kaiku ko ina ba?” “Dama ai mu akan kuskuren muke. “Malama Rebecca duba adadin fitar numfashinsu!”
“Sako ya amsu!”
Kafin su fahimci me yake faru, hayaki ya cika falon, a lokacin ya saka abin zukar iska a hancinshi. Ya mike a hankali ya daga kan keken, idanun Zeeno kamar zai fado kasa, tana mishi wani irin kallo. Kafin ta ankara daga ita har mutanen sun fadi sunammu. Koda yake ita kafin ta daina hango shi, ta ga yadda yake takawa, cikin Isa da jin kai irin na gogagun marasa mutunci. Yana isa wurin da mazukin iskar ya saka mata a hancinta. Sannan ya ɗauke ta suka bar gidan, daya daga cikin motar shi. Ya sakata a gaba, snnan ya bude motar y zauna.
Yana shiga ya danna bleutooth, a hankali ya ce. “Malama Rebecca. Ruftar da gidan. Kada a samu wata shaidar ina raye”
“Malam Malik Menk Jordan, sako ya amsu!”
ba tare da bata lokaci ba, ya bar gidan, Haka ya rubta cikin karkashin kasa, a daren ya wuce bakin taku, aka saka motar shi a cikin wata kwantena, ya dauki matarsa suka shiga wata jirgin, tare da barin ƙasar. Koda zai dawo sai ya gyara shirinsa da matarshi domin yadda zai ci amarcinsa a nutse.
Tunda ya kwantar da ita ya kira likitan jirgin, ya fara dubata tare da saka mata ruwa, sannan ya shiga yayi wanka ya fito sannan ya dawo ya kwanta a gefenta. Yana kallon yadda take barci Bayan saka mata ruwan da aka yi. Bata farka ba sai da gari ua waye, har haske rana yana lekawa ta dakin sannan ya bude idanu tana kallon cikin dakin. A hankali ta sauka a gadon, ta ga wani kofa, bude kofar tayi ta ga banɗaki, wanka yayi tana me lumshe idanun kafin abin da ya faru ya shiga dawo mata. A razane ta zauna dabas a kasa. Kafin ta mike tana me yin alola. Ta fito ganin abin sallah a shimfide yasa ta nufa, tayi sallah.
Tana idarwa Malik yana turo kofar dakin, hannunshi dauke da tiren, ja da baya tayi tana faɗin. “Innalillahi!” Murmushi yayi mata ya ce mata. “Kin razana ne?” Ya d’age mata gira biyu yana murmushi. Yana matsawa gabanta, ya ja da baya. “Wayyo Allah mugun ji mugun gani Allah ka kare ni da gani” ta faɗa tana ja da baya.
Ajiye mata abincin yayi yana faɗin. “Oya zoki ci!” “Na koshi!”
“Ok haka ma yayi amma ki sani, yau zan amshi hakkina!” Ware idanu tayi tana faɗin. “Wallahi ba zan iya ba! Ni dama tausayinka nake ji, yanzu kuwa na daina tausayinka tunda da lafiyarka.”
“Wallahi sai kin bani hakkina kaji wani wayon banza,” haka suka yi ta jajjyayya, har yayi nasarar cafketa. Saka ihu tayi tana faɗin. “Don Allah kada ka min haka wani, wallahi ƙaddara ta kawo ni rayuwarka,. Idan ka yafe min xan fita.”
“Na ji zaki fita sai kin bari na haihuwa da ni ko daya ne, baki ga na tsufa ba ne”
“Wayyo Allah na, wallahi ni yar karama ce ba xan iya haihuwa ba ” saka bakinshi yayi a kunnenta. “Idan kika haifa min yara masu irin idanunki sai ki tafi a binki”
“Ai ko masu kama. Da ni ba zaka samu ba”
“Ai kuwa nasan wacce tafiki kyau zaki haifa min”
“Don Allah ka kyale ni!” “Idan na ki fa?”
“Ni dai wallahi ba zan iya ba” abin dariya haka yayi ta zolayarta, dakyar ya samu ta ci abinci, sannan ya ciro mata wani kayanshi ya bata. “Ina zan kai wannan jamfar?” “Sakawa zaki yi.” Ya faɗa yana mata dariya, wato sai yanzu ta ƙara gane Malik yana da barkwace da zolaya sosai ga babu abinda ya dame shi kai tsaye yake magana, yana daga cikin mutanen da basu dauki kai da wani damuwa ba, shi dai idan zaja mutuntatta shi bai da matsala. A cikin kwanaki uku da suka yi ya kara musu shakuwa, tunda ya fahimci ita din matsoraciya ce ya gaske. Domin da zarar ya ce yana son wani abu zata fara zaro idanu. Shi yasa bai sake niman kome ba, yayi kokarin koya mata yadda zata shiga jikinshi,
*Kuyi hakuri bamu da wuta ne*
book 2 zai zo muku Whatsp da Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/23, 1:53 PM] Yan Mata: Volume 22: T Water Town
Da sassafe aka samu labarin mutuwa Malik, wanda yaja hankalin yan jaridu kasar baki daya, babban abin tambayar ina gawar Malik. Balle na Zeeno abin da ya masifar d’aga hankalin mutane. Lokacin da Shatima yaji labarin abin da ya fara yi, shine kokarin mamaye duk wani abinda yake na Malik sai dai abin takaici bayan an gama ihun mutuwar Malik na tsawon kwanaki uku, ya gane cewa Malik ya gama kashe shi da ranshi, inda ya wallafa wani faifen video na cewa. Idan aka ji labarin mutuwarshi a tambayi Shatima Khamis.

Wannan abin ya d’aga hankalin Shatima. Domin koda aka fara binciken kafin a kai wani kwamiti, daga Shatima har Lalla Salmah, sun bar ƙasar. Tabbas suna cikin damuwa da tashin hankali. Haka yasa koda aka ta nimansu ba a same su ba, Yasir Aswad Al Yemini shi ya kara uzura wutar binciken sannan suna guduwa, ya shigar da labarin ga shugaban kasa, aka saka duk wanda ya ga Shatima da Lalla Salmah, a bude musu wuta.
★★★
Water Town.
Wani gari ne da yake gaban Keivroto ta gabashin garin, mutanen garin masunta ne, sana’ar kifi suke yi, a koda yaushe suna samun bakin masu yawon bude idanu. Garin da gidajen garin a cikin ruwa suke, kuma suke rayuwarsu lafiya lau.
A lokacin da suka isa garin, ba karamin burge Zeeno yayi ba, suna sauka gidan me garin kauyen suka sauka. Yana ganin Malik yayi ta murna, “wannan wacece Malik?” “Matata ce!” Ya bashi amsa yana kallon Zeeno. “Tow gaskiya zata zauna amma dai sai mun kai ta, wurin ruwa me albarka ya tabbatar mana kuna son juna kada a kawo mana iftila’i da bala’in.
“Tow!”
Vow water, ruwa ce me matukar zurfi da wasu irin tsotsa, aka wuce da Zeeno matukar matar aure ce,idan an saka babu abin da zai faru ruwan da kanshi zai turota waje. Idan ba matar aure ba ce tsutsar cikin ruwan zasu makale mata, har sai an bata maganinsu. Kallon Malik Zeeno tayi zata yi magana, aka wuce da ita kai tsaye wurin suka tafi suka wurgata. A matukar razane tayi kasar ruwan, haka ruwan yayi rimi da ita, kafin ya watsota waje!” Mutanen wurin sunyi believe matukar ruwan yayi maka irin wannan uwar watsin ba karamin mahaukacin kaunar abokin zamanka kake ba. Kallon juna suka yi. Ya ga yadda take kokarin fitowa, riko hannunta yayi yana me daukarta yayi, suka wuce masaukinsu.
“Amma kasan haramun ne yarda da irin wannan abin ? Gaskiya sun kusan kashe ni da raina!” Ta faɗa tana zare idanu. A hankali ya zare kayan jikinta. “Me yasa kike boye min yadda kike sona?” Tura baki tayi tana faɗin. “Ni na gaya maka ina sonka ne?” Sama yayi da rigar jikinta, he can’t wait ya cigaba da kallonta haka, tunda ya tabbatar tana masifar kaunarshi, kawai ba zata fada ba ne. Shegen zurfin cikin nan nata.
Cire rigar jikinshi yayi ya watsar can. “Mayor ni fa ban shiryawa wannan lamarin ba.” Ta faɗa tana zare idanu. Kamar zata gudu. Cak yayi yana kallonta,.”sai yaushe zaki bani hakkkna!” “Tsoro kake bani!” “Allah ya dace ki ji tsoro ba ni ba” daga haka ya shiga binta da wata masifaffiyar kiss da yasa ta, dole mika wuya, suka shiga kashe junansu kamar bazu kyale juna ba.
Ganin tsayuwar zata gagare shi, bai san lokacin da ya zube a saman bed din da ita. Suka shiga kashe ƙishirwan junansu, wasu abubuwan da Malik yake mata, bata tab’a sani ba. Ko wuka aka daura a wuyarta ba ta san da su ba. Amma yau baki daya tana hannunshi yau sai yadda yayi da ita. Har zuwa yanzu bai shi al’amar wani abun shi zai dauke ba, sai da ya kai makurar da ba zai iya hakuri ba, ya karanto addu’a a daidai kunnenta. Duk ta fita hayacinta, bata da cikakken fahimtar duniyar da take, a hankali ya shiga bin ta a hankali, bakiɗaya hankalin shi ya bar gangan jikinshi ne, lokacin da ya isa duniyar da bai zata ba, shi a haka kallon wacce ta san wani abu na rayuwar waje ba, ya rud’e iya rudewa, ya gigice fiye da tunanin mai tunani, shi kanshi bai tab’a sanin zai kai matakin hakan ba, Baiwar Allah kuwa, wani irin karfi ne yazo mata suka shiga kokuwa da ita, ko yayya ta turee shi, sake shigewa jikinta yake, haka ysa tafashewa da wani irin kuka me bala’in ƙarfi, don tunda take a rayuwarta bata taɓa shiga wannan halin ba.
“Don Allah don Allah! Kayi hakuri ka barni akwai zafi!” “Kiyi hakuri ba zan iya kyale ki ba” nutsata yake yana kara jin wani irin abu yana yawo a kanshi. Yummmm yana kara jin wani abu akanta, zuciyarshi cike da kaunarta. Tausayinta da wani irin shauki yake ji. Wani abu yake fisgarshi, kara nikata yake kamar an bashi nikar masara, ya kasa hakuri ya kasa janye kowacce kofa na tausayawa shi kanshi a daidai wannan lokacin ba zai ya gane abin da yake faruwa ba. Domin kanshi yayi mugun daukar zafi, wani azzababen rawa jikinshi yake, domin ya gama fahimtar duniyar da yake raye, daban da duniyarta. Shi yasa ya mata kaca-kaca yadda shi kanshi ko bindiga aka daura mishi ba zai kai labarin abinda ya faru ba. Amma yasan ya gwangwaje amarcinshi.me tsada da jin dadin rayuwa. A hankali ya koma gefe yana sauke ajiyar zuciya. Asalin tausayi ta bashi.
Janyota yayi ya rungumeta yana girmama yadda, ta iya kame kanta ba tare da ta sayarwa kowa mutuncinta ba, yana jin saukar ruwan hawayenta a jikinshi amma baki ɗaya ya kasa rarrashinta. Sai kara matseta yake, a hankali ya mike, ya nufi ban daki sai da yayi wanka ya had’a mata ruwan zafi, sannan ya dawo ya dauketa cak, ya kaita cikin bandakin ya sakata a hankali, zabura tayi ya kuma maida ita, wani irin kuka ta saka mishi. Ya rungumeta yana shafa bayanta cike da tausayinta. Wani irin tausayinta yake ji, ba karamin tausayinta yake ji ba, kuka tayi ta yi yana kara matseta, idanunta sunyi luhu-luhu, bude ƙafafuwanta yayi ruwan ya shiga sosai, sannan ya d’agota ya ƙara. Cireta ya kuma tara ruwa, ya sakata wani malalacin kuka ta sakar mishi. Tana tuttutre shi, murmushi yayi ya ce mata. “Sorry yan mata na” dakyar ya lallabata suka fito, bayan tayi alola suka hi sallah Azhar da la’asar, sannan ya nimo mata abincin. Bata iya ci ba, sai ruwan zafi ta kwanta kafin wani lokaci zazzaɓi ya rufe mata, shi kanshi shiga duvet din yayi ya lullube su, suka kama barcin a tare.
Basu farka ba, sai karfe bakwai na dare, shi ya fara tashi yayi wanka, har lokacin a gajiya yake, alwala yayi ya fito ya gabatar da sallah, sannan ya koma kanta ya saka ta tashi ya surka mata ruwan zafi, ta shiga tayi wanka, ya nimo mata abincin da zata ci, kaɗan ta ci ta sha body pain. Sannan ta koma ta kwanta, jikinta yayi mata tsami, ita kanta bata ganewa jikinta har zuwa asuba domin bata yi barcin kirki ba, Malik ya hanata barci da jagwalgwalo son ranshi .

Da asuban kuwa tana idar da sallah, ta shige bargo bata kuma farkawa ba, sai karfe daya na rana, lokacin ya fito ban daki daure da towel. Zuba mishi idanu tayi tana kallon tarin kwanjin da ya tara? ” Me yasa ka boye gaskiyar ka bayan lafiyarka lau?” Sake towel dinshi yayi, da sauri ta ja bargon ta rufe kanta, shiga cikin bargon yayi yana faɗin. “idan ban yi haka ba, taya zan tantance makiya na? Rufe idanunki na miki bayani!” Janye rigar barcin yayi, a hankali yake kara matseta, yana kara lallubar . Kafin ta ce me ya jefeta cikin wani sabon yanayi, me wuyar fahimta, ba tare da tunanin kome ba, ta kuma mika wuya, Malik kuwa ya fara kokarin bin hanyar, a lokacin ne ta fahimci Allah da girma yake. Domin kuwa fama mata ciwon da yayi. Wannan karon kuka tayi ta mishi tana yarfe hannu, sai da ya mata bulala sannan ya kyaleta suka kuma sabon wanka.
Ai kuwa ranar yaga tashin hankali, domin jikinta yaki bata hadin kai ko tafi bata iyawa, daga kwanciya zai kwanciya, ga zafin bala’i idan taje fitsari da zazzaɓin da ya saukar mata kamar zata yi hauka. Haka Malik yayi ta lallabata, aka samu me likita yayi mata allura da karin ruwa.
A hankali kwanakin tayi shi a matukar galabaice, domin ba karamin wahala ta sha da jikinta ba, sai da suka shafe kwanaki takwas sannan suka bar garin, kai tsaye Demark suka wuce. Wanda tun da suka baro garin, jikinta ya kara yin sanyi. Malik yaki barinta ta huta, from morning to night, around ko ina ya sameta baya zuwa mata da sauki. Yanzu haka ya gama turmusata, tana kwance a bakin gado, shi kuma ya zauna. Daure da towel duk ta fita hayacinta. Tausayinta da kaunarta suna kara cizon ranshi. Ya mike yana gyara zaman towel ɗinshi, ya karasa wurinta. Yana gyara mata kwanciyarta.
A hankali towel dinta ya zame, hadiye yawu yayi. Ya kai hannunshi saman cikinta. Bude idanu tayi a gajiye zata yi magana ya hade bakinsu. Hannunshi dukka biyu a na fulaninta. Murzata yake yana kara jin wani abu na kwasarta. Kuka ta fashe da shi, duk da bakinta yana cikin nashi bai hanata jin kamar zata mutu ba, lokacin da yake ratsa babban kwamitin sabis dinta, rike damtsenshi tayi. Tana zare idanu domin ya kashe ta a karo na biyu a cikin jirgin, yana shiga ya kara matseta. “Thank you!” Ya fada a zafaffe, yana kara nutsata yana juya kanshi.

Kamar ba zai daina ba, gashi ko saunawa zai yi baya gaji da ita, baya iya barin ta haka yasa baki daya. Sai da ya haɗata da jikin gadon, yana aikin son ya samu kanshi, ita kan zubewa tayi a jikinshi. Hancinta yana zubda jini. Sakamakon gajiya da yanayin rashin hutun da bata samu.
Babu shiri suka kara saurin tafiyarsu na tsawon kwanaki goma sha biyar, suka shiga Demark a kwanaki tara.
Tun kafin su isa aka kira asibitin da ya dace a ganta, aka musu booking. Suna isa motar asibitin ta dauke su, har asibitin. Abin tausayi, hancinta sai zubda jini yake, ana zuwa da ita ba tare da wani bata lokaci ba, suka fara shirin mata aiki, domin kare lafiyarta da rayuwarta.
Kiran Adnan yayi ya gaya mishi, halin da ake ciki, akan lokaci suka tawo shi da Elbashir domin da gaya musu aka yi ba su yarda ba, ga Malik a Demark.

Sai da suka rasa inda zasu saka shi, Sayyada Quddisiya da suka bata labarin Malik yana raye, itama tazo da su Wahida da Wahiba suka tawo tare,anan suka zauna ana ta jajjnta halin da ake ciki, Kallon Malik Yan biyu suka yi. “Dadi dama kana tafiya?” Murmushi yayi ya rungume su. “Ina tafiya mana!” “Dadi shine baka gaya mana ba”
“Kun ga ku bari, musan halin da second Mommy dinku take ciki ko?” Gyada kai suka yi, har wani lokaci. Elbashir kunya ta hana shi magana, sai da aka kai yamma a asibitin suka yi sallalolin ranar, wurin karfe biyar na yamma.
Aka turo ta a gadon, tana kwance kamar matacciya. “Alhamdulillahi!” Duk suka furta suna bin bayansu, har dakin da zata zauna, kasancewar Malik yayi amfani da takardun shi na kasar, don haka suka karbeta babu bata lokaci.
Zama yayi tare da saka hannunshi cikin nata, yana jin wani irin kaunarta me cika zuciya da kewayenta. “Allah ya baƙi lafiya!” “Amin Ya Allah!” Ya furta yana shafa kanta, kamar zai yi kuka he love her. Kawai ya rasa yadda zai yi bai ki a cire ciwon daga jikinta a saka mishi ba, sumbatar goshinta yayi, yana gyara mata zaman abin lullubuwarta.
“Zata kai yaushe kafin ta farka?” “Ban sani ba, domin aikin ujila aka mata.”
“Allah ya bata lafiya!” “Amin!” Shigowar nurse yasa suka zuba mata idanu. Cikin girmamawa ta ce musu. “sir likita nason ganinka,
book 2 zai zo muku Whatsp da Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/23, 1:53 PM] Yan Mata: 24 I’m not king, I’m king maker

Kura mata idanu yayi yaga yadda ta koma can kuryan dakin, sai jikinshi yayi mugun sanyi. Zama yayi yana faɗin. “Zainaba meke damunki?” Dauke kai tayi tana haɗe rai ta ce. “Wani mutum nake son na nime. Ban san a ina nake ba yanzu?” Shiru yayi jikinshi yana kara yin sanyi ya ce mata. “waye haka mutum?” “A wani gari nake yanzu?” “Kina Demark ne!” Yayi shiru yana kallonta. “Zai kai mu yaushe, mu koma Keivroto?” “Zai kai mu wata biyar, domin sai kin warware, me zaki yi a can!” Cikin salon yan jagaliya ta ce mishi. “Akwai tsohuwar gaba ce nake son naje na kaddamar da shi.”
“Wani irin tsohuwar gaba?” “Mutumin da ya kashe min iyayena zan je nima joha ko waje na manta amma zan tafi fisto ne binciken ahalina!” Bai tab’a shakkar wani ya san gaskiyar waye shi ba, amma yau kalaman Zeeno ya karya mishi zuciyarshi. Tsoron kada ta rabu da shi ya bayyana a cikin idanunshi. Bai tab’a zaton zai zama fool akan soyayya na, sai ga shi ya zama mara amfani. “Baki rike sunanshi ba ne?”
. “Idan da na rike sunanshi zan gaza gaya maka ne? Ban san sunan mutumin banza ba!”
Hadiye yawu yayi yana kallon yadda take wani, rangaji tabbas Zeeno da ya sani dama can suna da wata a kasa, amma kuma tana dai rage mishi wani abu idan ya kira sunan Ammy. “Tow shi kenan! Zo mu kwanta!” Ya janyota zai rungume ta. Ta dauki wukar da ta yanka fruit. “Kada ka sake ka tab’a ni!” Hadiye yawun bakinshi. “Zainaba meye matsalarki ni mijinki ne!!”
“Wannan matsalarka ne, bana sonka tab’a ni. I hate that!”
Riko hannun wukar yayi yana faɗin. “Ban san me nayi ba, amma baki daya na fuskanci sauyin ƙaddara daga gare ki, I’m sorry Ina sonki. Ba zan iya rabuwa da ke ba” ya rungume ta a hankali. Daura kanta yayi a kirjinshi. Tana jin bugun zuciyarshi. D’ago kai tayi tana kallonshi kafin ta ture shi. Sake riƙe ta yayi yana tambayarta. “Meye nayi mara kyau? Soyayyarki ce bata min adalci ba ko me nayi?” “Fansar kashe iyayena zan tafi na dauka, kana da halin kai ni ko yau ne!”

Girgiza kai yake yana faɗin. “No Zeeno! I can’t, ba zan iya ba. Na kawo ki nan don mu huta ne ban kawo ki don na ƙara mai dake ba, ki tuna saboda ke na bar kome na tawo nan” “Ni? Tow waye kai?” Kamar an watsa mishi ruwan zafi yaji tambayarta. “Me yasa ka dame ni? Me yasa ka shiga rayuwata?” Rike kanta tayi tana jin abu me dumi yana zuba ta hancinta ta ce mishi. “Me yasa ka dame ni?” Da sauri ya koma bayanta ya rungume ta, tana jin bugun zuciyarshi, a hankali ya juyar da ita, tare da riko hannun, sakewa yayi ya cire rigarshi ya fara goge mata hancinta. “Zan gaya miki waye ni idan har kin amince!” Yana gama goge mata jinin ya shiga sumbatar bakinta, tare da ƙoƙarin goge mata hadda. Wani azzababben kewarta da yake yi, yasa shi kara matseta. Yana kara jin wani, abu na taso mishi. Jikinta ne yayi sanyi, ta kara rungume shi. Tana sauke ajiyar zuciya. Izuwa yanzu zuciyarta tayi na’am da lamarinshi, bai tab’a nimanta a irin wannan yanayin ba, ko bai tab’a jin ya nimeta ta wani yanayi ba, amma yau sai da ya danganta da jikin wall na dakin, sannan ya shiga wani irin sauri-sauri yana me kara jin wani bala’in kaguwa akanta, sai da ya rungume ta gam, sannan ya shigeta da karfi. Ajiyar zuciya suka dauke once. Yana sumbatar habbarta. “Kin fahimci waye ko na cigaba!” Rungume shi tayi tana me daura kanta a kafadarshi. Hada kafafunta tayi a bayanshi ta makale shi. D’ago kanta tayi ya shiga lasar wuyarta har zuwa fuskarta. “A tsawon watanni da kika dauka baki da lafiya, hakuri nayi banyiwa shukata ban ruwa ba, a yanzu zan juye kome na kara tuna miki ni naki ne baki ɗaya ba zan iya cutar dake ba!” Ya fadi haka yana matse bom-bom dinta, sama yayi da rigarta ya shiga matse na shanun da suke kara haukata shi yana jin kamar yayita ihu, juyawa yayi da ita ya zauna a bakin gadon. Ya shiga juyi a tsakanin su, yana kara jin wani irin shauki. Musamman yadda take wani deep moaning da groan kamar ranta zai fita. Wannan nishin yana.daga cikin abin da yake kara mishi confidence. Shi daya yasan yadda yake jinta, shi.daya yasan me yake bukata a jikinta, don haka baya ji ybaya gani yake zungureta. Yana shiga da fita a ko ina na jikinta, ji yake kamar kome na shi ya ƙare, akanta amma ba sai iya rabuwa da ita. Ba zai tab’a rabuwa da ita ba. Ko zata na yankar namar jikinshi ne kuwa yana makale da ita, ba zai taba rabuwa da ita ba, she meant to only him, don haka zai ta shiga cikin rayuwarta kafin ta gano waye shi, ya gama fahimtar da ita tsantsar kaunarshi.

Ba zai d’aga kafa ba, ba zai d’aga hankalin ba, amma zai zame mata kamar kaska zai addabi rayuwarta har sai ta fahimce shi. Zai matsa mata da soyayyar shi yadda ba zata tab’a tsare mishi ba. Zai ta bibiyar rayuwarta har sai ta ji ta gaji da takura mata tayi accepting dinshi ai yasan, ba shi ya kashe iyayenta ba, taya zai addabi kanshi da damuwa. Zai yi farin ciki idan har ta gane matsayinshi a ranta. Zubewa suka yi a gadon. Tana kwance a jikinshi. Tayi masifar laushi sai ajiyar zuciya take tana me juya kanta. Haka yake fatan a koda yaushe ta gane shi jarumi ne ba lusari ba.
Ta fahimci shi na musamman ne, ta gane bayan shi babu wani namiji. A hankali ya janyen ta daga jikinshi yana shafa bayanta, barci me nauyi ne yayi gaba da ita, shima ya shiga ban daki yayi wanka ya fito ya shirya cikin kananun kaya, sannan ya koma saman restchair ya zauna yana sauke ajiyar zuciya. Kallonta yake yana kara jin gajiya. Amma baya jin zai iya rabuwa da ita.
Sai yamma likis Zulfa da Yasir suka iso gidan, tana zaune a dakin kamar mayya domin bata son shiga harkan kowa a gidan tun da Malik ya gama nikata, ta farka a barci take zaune a wurin. Dakatar tayi wanka shima dai da ya kamata da nufin zai mata, shi ne tayi tana. Sanye take da riga da skirt, sai hula da ta saka. Tana wurin kamar me tunanin wani abu. Turo kofar yayi Zulfa tana biye da ita. Ta zuba mata idanu. “Zeezeen Abba!” D’ago kai tayi tana kallon Zulfah. Kafin ya dauke kai tana kallon can gefe. _Ki Zulfah dawo ki ɗauke ta, ki bisu Zeezeena_ karar wayar Zulfah yasata razana tana kalle-kalle! Ta tashi zata gudu, ya riko hannunta. “Ina zaki?”
“Zanje Abbana ne, zasu kashe shi!” Ta faɗa da karfi tana rike shi, rungumeta yayi tana ta kokuwar kwatar kanta, amma ta mata riko me kyau, kuka ya saka tana me kwantar da kanta. Komawa yayi da ita cikin dakin ya kwantar da ita, kusan ma tare suka kwanta, tana ta kuka. “zan je na kashe mugun da ya kashe min Abbana, akan idanuna suka kashe min Abbana!” Kara rungumeta yayi yana faɗin. “Zamu kama su insha Allah” ya faɗa yana shafa bayanta. A hankali barci yayi gaba da ita. Sai da ya saka mata pillow a bayanta sannan ya fito waje, ya zauna yana kallon Zulfah itama kuka take. “bata tuna da mu ba!” “Zata tuna da ku, ki daina kuka ai da sauki tunda ta fara tuna wancan abin da ya faru!” Ya faɗa yana cigaba da tafiya kitchen, ruwa da juice ya kawo musu, sannan ya ce musu. “Dole mu kama waɗanda suka aikata wannan abin a gurfanar da su, Nayi magana da matar da ta zauna a wurinta ta ce min, Zainab tayi fama da trauma na tsawon shekaru, tare da karfin harsashin kanta, wanda ya kara mata karfin gaske, Zainab tana bukata kulawa da janta a jiki.

Ta haka ne zai saka ta fahimci cewa ta rayu da mu. A wani lokaci da ya wuce. ” Sosa goshinsa yayi yana faɗin. “And dole a bude file din shakaru goma sha uku baya, ta hana ne zamu goge abin da ya faru a kuma bankad’o gaskiyar da take rufe.”
“Kana nufin sabon bincike za a fara?” Yasir ya tambaye shi.
“Yes!” Ya faɗa tana shan ruwa, Ya zubawa Zulfah idanu. “Na samu labarin kina digging case din file din yana hannunki.”
“Ya zamu yi da ma’ikantan tsaro?” “Zanji da su!”
“Yan majalisar kasa da zartarwa, majalisar koli na shugaban kasa, dole sai mun samu haɗin gwiwan su!” “Ku bar min kome a hannuna. Zan ji dasu.”

Shiru suka yi, kafin suka mike a tare, “zamu tafi yallabai!” “Ok” ya mike tare da raka su. “Kafin ki bar garin nan, make sure kin kuma zuwa kun gana da juna, tana bukatar wani a tare da ita, kamar nata.” Gyada kai tayi tana faɗin. “Zan zo insha Allah!” Daga haka suka mishi sallama, komawa ciki yayi ya shiga dakinshi, kayanshi ya bincika sannan ya ciro wayar karama ce, ya kira wani layi da shi. “Mr Haris Jabir!” Daga can aka ce mishi.” Malik Menk Jordan! Kana ina ne? Ƙasa ta hargitse da tashin hankali!” Murmushi Malik yayi sannan ya ce . “Zan dawo kowani lokaci, amma a bawa mutane na izinin fara binciken mutuwar Aswad Al Yemini da Nasr Hadejia. Zasu iso kowani lokaci!”
“Malik zan yi murabus, idan aka gama binciken. Kai sai ayi nominate dinka a matsayin PM!” “A’a Mayor din ma, zan ajiye muku ni i’m not king im king make, na zabi wanda nake so,na ajiye wnada bana so. Keivroto nawa ne, nawa ne Keivroto!” “Malik duk yadda kace”

Daga haka ya kashe wayar, ko Mayor ya karba ne, domin cusawa Khuldu Jahid Khan haushin ya rasa kujerar da ake ganin kamar gadon shi yayi, ya hana shi. Ya kuma kafa daula babba wanda kowa zaiso ya kasance shi daya a wurin, Allah ya bashi arziki, ya bashi karfin iko. Uwa uba yana da makiya son ranshi, me ya rage mishi? Babu don haka zai sake shiga filin dagga ne domin Zeenobia ba don kanshi ba. Daga ranar da aka samu labarin yana raye daga ranar ko ina makiyanshi bayyana zasu yi, yana son haka ya gansu suna nufar shi. Yana kara mishi shaukin da jin dadi.
Don haka ya shirya tsaf, ya tura da sakon cewa. *A saka live zan yi magana a Keivroto baki daya*
_An gama!_ aka turo mishi. Daga haka ya ajiye wayar, sallah magariba yayi da isha, sannan ya koma dakin ya tashe ta. Tayi sallah. Bayan ta idar ya dauko sweatcoat ya saka mata, ya daure mata shi, sannan ya riko hannunta ya daura mata mayafi. “Ni bana son haka!” “Zan yi haka domin ina so!” “Auren wata biyar ne next month zamu rabu kada ka manta da wannan” gyara mata mayafin nayi. “ba zan tab’a danasanin rabuwa da ke ba, domin nasan ina sonki, kuma zan amshi kasa ko gazawa daga gare ki. Amma ba zan tab’a sake ki ba wannan shi ne alkawarin da na dauka miki.”
“Tow Ni nace bana sonka!”
“I’m sorry baby you too late, ina sonki muje muci abinci!”
“Ka ajiye ni kana biyan bukatarka da ni, ka ajiye ni kana yadda kake so da ni ka kyale rayuwata ko na baka mamaki!” “Babu mamakin da zaki bani, domin yarjejeniyar mu Ammyn ta wargaza shi, aurenmu fresh ne babu cantract!'”
“Zan kashe ka kuwa!” Tab’e baki yayi yana faɗin. “Thank God Mayor zai mutu a hannun matar da yake masifar kauna!”
“I hate you!” “I love you!” Wuce shi tayi zata tafi ya dawo da ita, da karfi. “Ashhhhhh!” Ta rike cikinta, saboda karfin fisgota da yayi……🤔🙄🥺 Me haka yake nufi wani abu yana min Dillin dillin 🤔 Happy weekend 🌸🥳
book 2 zai zo muku Whatsp da Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/23, 1:53 PM] Yan Mata: 25 pregnancy
Karfin fisgota ya janyo mata kullewar mara, tare da jin bugun zuciyarta sauri-sauri, rike shi tayi tana jin wani irin zazzaɓi tare da bugun zuciyar lokacin guda, bata san lokacin da ta rungume shi ba. “Are you okay?” Ya tambaye ta, juya kanta tayi tana kara rike shi gam, zufa yana karyo mata. “Ci…ki…na” ta faɗa dakyar tana rike shi, kasa magana furta kome yayi ya ɗauke ta cak, ya wuce ciki da ita, kwantar da ita a kujera yana me zama kasa. “Meke damunki!” “Kasar cibiyana, ya daure?” Ta faɗa tana cizon fatar bakinta. Riko hannunta yayi ya ce . “Ko muje asibiti ne?” Juya kai tayi ta rasa meke mata dad’i, komawa yayi ya kuma shiga dakinta, kafin ya kuma fitowa, ya dauke ta cak suka fita daga gidan. Wani irin tausayi take bashi, domin baki daya ta kasa magana, sai zufa take. Ganin yadda zaman ya gagareta yasa shi kwantar da sit din. Yana mugun gudu, har suka isa asibitin. Daukarta yayi yana kiran “Doctor!!!” Yana rungume ta ita. Da sauri suka nufe shi.
“Ina likita?” Ya kuma kara kwala musu kira, da gudu suka turo gadon, aka kwantar da ita. “Me ya same ta?” “Oh she’s bleeding.” Suka faɗa da sauri aka nufi emergency room da ita, “what’s going on?” Ya tambaye su a fusace, “Calm down! ” Suka dakatar da shi, da sauri wasu nutsu biyu suka fita, can suka kuma dawowa da blood bank, suka shiga cikin dakin da aka.kwnatar da ita, Kiran Elbashir yayi a waya, “Bashir!” “Na’am Malik lafiya?”
“Zainab ba lafiya!” “Gaskiya ta cika ciwo” “Jini take zubarwa!” “Subhanalillah, gamu nan zuwa!” Ya kashe wayar yana kallon yadda suke kaiwa da komowa. Yana zaune ta daura daya a kan daya, ya dunkule hannunshi ya saka a.kasar habbarshi.

Har su Elbashir suka iso, yana zaune he shock, suna zaune likitan ta fito, tana yarfe hannu. Mikewa Malik yayi yana kallonta, ya kasa magana baki daya. “Sir mun bata bedrest, damuwa da gajiya idan da hali, a dan rage yawan sexual affairs da ake, a dan bawa cikin lokaci yayi kwari. Idan kana son ganin yadda zuciyar Baby yake bugawa sai mu shiga ka gani amma daga uwar har Yaron,suna cikin koshin lafiya.” Ƙasa motsi yayi, bakin shi yana rawa ya ce. “She’s pregnant?” Ya fada kamar me tsoron a ce karya ne babu cikin. “Yes!” Ƙasa yarda yayi ya kalli Elbashir ya ce. “Kaji Zainaba tana da cikina wai cikina ne? I gonna be a Father!” Wani irin abu yake ji, dama haka uba yake when aka yi gaya mishi ana dauke da babynshi, ko kuma shi ne yake jin haka, kasancewar ya tsufa bai haihu ba.
“Alhamdulillahi!” Ya furta jikinshi yana rawa, jikinshi yana kerma kamar zai tashi sama. Ganin yadda ya gigice da farin ciki nurse din ta kuma sake kara mishi wani ta hanyar kaishi dakin ya ganta. Sannan ta kuma mata wani scanning ɗin tana faɗin. “The baby is weak, saboda abubuwan da uwar take fuskanta na damuwa. A kyale uwar ta huta Babyn zai samu kulawa na musamman!” Gyada kai yake yana kara kallon Zeeno.
“Thank You doctor!” Murmushi yayi yana kallonta. Baki ya kasa rufuwa, kalmomin da zai amfani da su na godiya sun yi ƙaranci a bakin, zama yayi ya gaban Zeeno tare da kai hannunta a gefen fuskarshi. “Zainab i love you!” Ya furta a hankali yana kara jin wani irin kaunarta, ga ta dauke da babynshi. Barci take sosai. Shigowa dakin Ammyn tayi tare da Sayyada Quddisiya, dai Zulfah da Jalilah. “Wai ciki ne da ita?” Zulfah ta tambaye su.
“Ba wai bane cikin ne da ita, tana da da cikin Malik!” Kallon Zeenobia tayi tana ta barci kafin ta ce musu. “Ina mamaki baby sister da ciki!” Ta faɗa tana dariya, irin abin y zo mata bazata. “Ba a mamaki da ikon Allah, kome zai yi domin tabbatar da ikonshi.”.
Dake dare ne, dole wasu suka tafi, Malik kan sai da suka yi da gaske, ya saka kai ya tafi. Karfe biyu na dare ta farka. Tana jin yunwa. Kallon Ammyn tayi tana kan abin sallah. “Ammyn!” Ta kira sunanta a hankali, juyawa tayi ta kalle ta, kafin tayi magana Malik ya danno dakin,ashe bawan Allah nan bai tafi ba, cire ruwan yayi ya ɗauke ta cak. Kallonshi tayi sannan ta maida kanta kirjinshi. Shafa fuskarta yayi lokacin da suka shiga ban daki. “Likita ta ce ban da aikin wahala!” A hankali ta cire pant dinta, ta zauna tana fitsari. “Ni kan ka fita zan yi pupu!” “Tab’a na fita garin nishi ki fitar min da D’a?” Bata fahimci me yake nufi ba, don ta fahimci ba zai fita ba.
“Malik fita don Allah!”
“Wallahi bani fita! Ki ja min masifa.” Haka kuwa ta gama fitsarin, ta mike zata gyara zaman pant dinta, yayi maza ya gyara mata. “Bana son janyowa kai masifa, don Allah babu ruwanki da yin kome ni zan miki na gaya miki.”
Gyada kai tayi, domin bata da karfi, suna fitowa ya ajiyeta a gadon. “Me zaki ci?” Komawa tayi da baya ta kwanta tana lumshe idanunta. “Ina son kunun alkama, da kosai!” Kallonta suka yi daga shi har Ammyn. ” A ina zamu samo miki wannan kayan?” Murmushi yayi ya ce mata. “za a samu bari na fita.” Haka ya fita cikin daren ya shiga yawo, yana niman any African restaurant. Kamar yayi hauka, dakyar ya hadu da wasu yan Ghana, ya sayo kunun. Kafin ya iso yayi sanyi. Koda ya zo ya samu tayi barci, rike abincin yayi yana kallon yadda take barci.
“Ammyn bari na jira a waje!” Ya fito ya zauna yana kallon mutanen da suke shige da ficce. Har wurin karfe biyar na asuba . Kafin ya nufi wani karamin masallaci yayi Sallah ya dawo ya samu bata farka ba. “Malik ko zaka tafi gida ka huta ne?” Girgiza kai yayi..”tow ni ya zamu yi, kwana kayi baka yi barci ba, kuma ka ce ba zaka ka kwanta ba.” “Shi kenan zan tafi zan dawo karfe sha daya in sha Allah!” “Allah ya kai mu” daga haka ya fita, itama Ammyn ta kwanta ta huta, sai wurin goma na safe suka farka, shigowar Wahida.
Matakin farko da Zeeno ta fara fuskanta shi ne, yawu yaki tsayuwa a bakinta, da farko ta zata rashin brush ne, sai da ta wanke bakin ta fito ta gane ba daga bakinta ba ne, a’a wani yanayi ne na daban da ta tsinci kanta a ciki. Kunun da ya kawo mata, Ammyn ta nuna mata, taba gani nmta fara yunkurin amai.
“Sannu kin ji!” Gyada kai tayi tana kallon kular da Wahida ta zo da shi. Budewa yayi ta ga arish, soyayye sai farfesun kifi. Dakin ya dauki kamshi. Sai dai me madadin taji kamshin sai ta fara jin kamshin ta cika mata hanci ta fara yunkurin amai. “Ikon Allah. Haka zamu yi da kai bawan Allah? Ba zaka bar yarinya ta ci abinci ba?” Hawaye ya zubo mata, tana son cin abinci amma ba hali, a irin wannan halin Malik yazo, yana zuwa ta fashe da kuka. “Mayor!”
Kamar ya kanta ya haye kanshi, ya riko hannunta. “Babynbaby me kike so?” “Yunwa nake ji.” Ta faɗa muryanta yana rawa. “Me za a kawo miki?” “Baby duk abinda aka kawo min zan ci”
Gyada kai yayi ya fita can dai gashi da fruit. Ya wanke mata, sannan ta fara cikin apple, tana kallonshi. Sai da ta cinye tass sannan yayi gyatsa. “A kara min!” Mika mata avocado yayi, ta shiga ci tana lumshe idanunta. Har ta cinye, tunda ya gano abinda take so. Shi kenan ya samu sauki idan ya fita zai kawo mata apple da avocado da ayaba. Sam bata gajiya da cinsu. Kwana uku a jere tana cin apple da avocado da ayaba, ai kuwa a ranar na hutu yana shigowa ta ce mishi. “kai mai da shi bana son shi, grapes nake so, ba pink din ba, green din nake so”
“An gama ranki shi dade” ya fita da shi, can sai gashi ya kuma dawowa dauke da grapes.

….. Zama yayi yana ciro plat ya fara kokarin zuba abincin yana kallonta. “Ko a sallame mu,mu koma gida ne?” Girgiza mishi kai tai tana faɗin.”Wurin Ammyn zan wuce;”
“Hmmmm! Ba zan iya ba!”
“Don Allah” ta faɗa a marairaice, girgiza mata kai yayi. A haka suke ta hira har ta gama, “Mayor! Ka zuba min nima ya ji miyar sosai.”ta jima bata ci abi cikin ba, na yau kuwa taji ance Mama Jalilah ce tayi, har da soyayyen planter. Haka ya zuba mata, tana tana tsoron kada tayi amai.

Har ta gama bata ji amai ba, sai ma jin dadin girki. “Mayor abincin yayi dadi ko zaka kara min!”
“Kada ki min amai”
“Ba wani amai da zan yi, please kara min.
Haka ya kara mata, taci ta koshi. Sai dai kuma tana gama cin abincin, ta fara yunkurin amai. Haka ya dauko mata kwanon aman tayi sosai. Har sai da jikinta yayi laushi, kwanciya yayi tan nishi.
Wasa wasa sai da Zeeno t kwashe wata biyu d sati Uku, kafin aka sallame su.

Gidan Sayyada Quddisiya aka kaita, a ranar taga soyayyar da bata taba gani ba, wani irin nutsuwa take ji, amma ta gefe guda bata yi na’amar da cikin jikinta ba. Ranar da take da kwan biyu da dawowa ya zo ai mata. Kiri-kiri ta ce mishi. “Ni da zaka taimaka min a zubda cikin nan gaskiya ban yi na’am da shi ba.” Kura mata idanu yayi ya ce mata. “Idan kika ce baki son gani na yarda. Amma idan kika yi wani tunani mara tushe akan cikin, sai na baki mamaki! Ina son abuna, halataccen jini na ne a kasar maranki!”
“Bana son shi, cire shi zan yi bana son shi ba zan.tab’a haihuwa da kai ba.”
Ta faɗa da karfi tana ihun da ya ja hankalin kowa na gidan, “na gaya maka , ka raba ni da shi ko na sha magani mu mutu baki daya da cikin! Ban shiryawa zama da kai ba!”
Sake baki yayi yana kallonta idan wani ya ce mishi zata yi mishi haka, ba zai yarda ba amma yadda take mishi a akan cikin yasa shi zuba mata idanu. “Ok kiyi duk yadda ya miki!”
“Zaka sha mamaki kuwa wallahi ba zan bar shi ba” takaici ya sa shi barin dakin bai shirya ba, domin ranshi ya masifar barci, ya tsani kayan haushi…..
book 2 zai zo muku Whatsp da Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/23, 1:53 PM] Yan Mata: 26-
Dukkansu suna falo ya fito, bai saurari kowa ba yayi tafiyarshi, Elbashir ya rufa mishi baya. Tunda ya shiga motar yake cirra kamar wanda zai tashi sama. “Kayi hakuri!” “Ba kome!” Ya faɗa yana cigaba da cire, tabbas lalacewar bata kai da Zeeno zata mishi haka ba.

“Kayi hakuri ka mata uzuri” murmushi yayi ya ɗauke kai yana fadin.”Muje ka ji” “Ok!” Daga haka suka yi tafiyarsu. A can kuwa baki daya aka rasa me mara fada, ita da laifi ita da kuka. Mikewa Zulfah tayi ta tsaya a bakin kofar tana faɗin. “Kukan uban me kike? Idan kika sake wani abu ya kuma samun cikin wallahi ni zan tsayawa Malik da gayya kika zubda cikinki. Wawuya mahaukaciyar banza” a fusace tayi yunkurin mikewa ta ce mata. “Dan ubanki tashi zaki yi ki zubda cikin? Idan shi ne ya rage miki a duniya fa? Idan kin so ki zubar yar iska jaka, wallahi sai na gayawa Hajja Mama iskancin da kike mishi wawuya kawai”
“Eh nayi din!” Ta faɗa da karfi tana ihu, “mahaukaciyar banza” daga ta fita ta bar bakin kofar, haushi ya cikata, ba abin ta zane ta, ta zane cikin jikinta, domin ko wannan ihun da take, jini ne ya fara zuba. Don bakin hali bata fada ba, sai da ta fara jin qarfinta ya fara karewa ta shiga niman a gajin mutane, ko kafin a nimo Malik ta suma yafi a kirga, domin ba karamin jini ya zuba mata ba. Lokacin da suka isa asibitin bata ma san waye a kanta ba. Haka suka yi ta kokarin tsayar da jinin. Dakyar ya tsaya. Zuwa lokacin ran Malik kamar ya ficce a jikinshi don b’acin rai. Da aka ce za a mata karin ji, kin yarda yayi a saka mata wani ya bada na shi aka.saka mata, bayan ya huta na tsawon awa hudu, suka koma wurin likitan. “Sir cikin yana nan, amma watanin ya koma baya, sannan yawan damuwar da take shiga yasa jinin ya zuba, amma kome ya daidaita. Cikin a kula da shi domin munso mata wankin cikin sai muka samu yana bugawa bai mutu ba, don Allah a kula da lafiyar uwar da dan cikin!”
“Mun gode!” Elbashir ya furta yana me fita Malik ya bi bayanshi. “Yanzu ya zamu yi da ita?” Elbashir ya tambaye shi, yana kallon dakin da take. “Ina ga a kyaleta da zancen cikin, matukar ta san cikin yana raye a jikinta, zata iya zubawar”
“Haka shine mafita!” Don haka suka samu su Ammyn da maganar a bar batun cikin a barta da halinta, duk suka amince aka zuba bata idanu, sai da ta kwashe kwana uku tana kwance kafin ta farka, a lokacin ta ga dakin da take ciki. Lumshe idanunta tayi tana son tuno abinda ya faru, a hankali ta tashi zaune, jikinta babu kwari ta kalli bakin kofar babu kowa, komawa tayi ta kwanta tana jin wani irin rashin karfi, turo kofar nurse tayi. “Har kin farka?” Gyada kai tayi tana kallon matar da uniform. Sai da ta gama mata tambayoyi kafin ta fita ta can sai ga ta tare da su Ammyn. “kin tashi Zainab?” Gyada kai tayi tana kallon su. Brush da toothpaste ta kawo mata, sai ruwa a kofi ta bata, tana sha kaɗan. Bayan ta wanke bakinta. “Ammyn yunwa nake ji!” “Tow bari na baki abincin ko” hada mata tea tayi, sai doya da kwai, ta fara ci a hankali. Tana kallon Ammyn. “Ammyn babu su Abbas ne?” “Eh yana tare da Black sun fita!” “Hmmm! Dama Black yana nan yaki zuwa inda nake.”
“Tow waye zai zo inda kike? Bayan kin san halin da kike ciki? Kawai kowa yana gudun abin da zai janyo ki ci zarafin Malik ne yasa kowa ya kama gabanshi.” Daga haka Ammyn ta fita, tabarta ita ɗaya a dakin kamar mayya, taji haushin Malik ta kara kamata, ko da Ammyn ta koma dakin ta samu ta gama har tayi wanka. “Ammyn cikin yana nan kuwa?” “Cikin da kika ce baki so ne za a bar miki? Cewa kika yi baki san cikin waye yake da zarar cewa a bar cikin a jikinki? Shi yasa da aka bukaci wanke shi na ce e ai baki son shi a cire shi, kada ki farka ki mutu bayan ana sonki.”
Wani irin kaunar cikin ya tsarga mata, ta ware idanu waje. “Ammyn kuka ce a wanke cikin?” “Eh yo me kike so muyi? Muce a bari ki ji haushin mu?” Fashewa tayi da kuka tana faɗin. “A ƙalla a jira a ji ra’ayina, nima ina da hakki akan cikin sai a wanke mishi shi?” Girgiza kai Ammy tayi tana faɗin. “Abin da kike bukata ne aka miki sai ya zama laifi?”
“Baki son cikin an zubda laifi ne? Cewa kika yi baki so me za a miki da shi? Kin ga rayuwarmu nan tana da muhimmanci, kowa tattalin abin da yake da shi yake, amma e cewa kika yi zaki watsar da shi, don haka kiyi addu’a Allah ya kawo wani idan kina so!” Yadda take kuka kamar da gaske cikin ya tafi yasa Ammyn tsammanin ta nutsu, don haka ta kara mata da nasiha, ko zata kara jin nutsuwa a ranta, har na wani lokaci. Tunda Ammy ta tafita take kuka tana jin wani bala’in kaunar Babynta, as a mother she never protect he own child, Babyn da baby ruwanshi. Bai dauki hakkin kowa ba, amma tayi curse dinsa har ya mutu tun bai zo duniya ba, ta zubda shi. Haka tayi ta kuka tana karawa.
Koda nurse tazo, ta ga halin da take ciki allurar barci ta mata domin jininta yayi mugun hawa, dole barci yayi gaba da ita, lokacin da Malik ya ji labarin yazo har dakin tana barci. Yana ganin yadda bakinta yake motsi. Ya kai kunnenshi.
“Na gaza ceton yarona, na gaza zama uwa!” Abinda take nanawata kenan har barcin yayi nauyi sosai. Daga nan ya koma ya zauna, tare da riko hannunta ya daura a saman cikinta. “You never give up! Har yau ke uwace, laifina ya shafe shi natural and pure love kikewa little Malik” ya sumbaci goshinta yana shafa kanta a hankali yana kallon yadda duk ta lalace, dama ba auki ne da ita ba, sai kuma ta kara figewa.
Tashi yayi ya bar dakin, yana kallon Elbashir. “Jirgin yaushe muke da?” “Jirgin karfe goma na dare, saboda yanayin Keivroto akwai yanayi mara kyau.”

Kallon agogon hannunshi yayi, yana me jingina bayan shi da bango. “Me yasa take damuwa da rashin kare Yaron?” “Saboda tana sonka, tana son abin cikinta, shi yasa take kuka kamar yadda take sonka take sonshi.” “A’a ba sona take ba, kawai na mata dole ne dolen da na mata, yasa take jin haushina da cikin. Har take ganin a matsayinta Na uwa ta fadi da ta gaza kare dan danta.”
Shiru Bashir yayi yana mamakin, yadda Malik ya sauya baki daya, tun daga ranar da suka fara ganin Zeenobia tun ranar Malik yake cewa ya samu mace. Wacce babu ruwanta harkan gabanta yafi mata kome. Ashe ba haka ba ne, ashe ita nata goben daban. Na shi daban. “Bashir ka daina tunani!” “Malik idan ban yi ba me zan yi? Yarinyar nan ta sauya maka rayuwa daga yadda na sanka. Ta saka ka zamo wani irin mutum a cikin al’umma. Malik be yourself ka dawo hankalinka mana” Murmushi yayi yana tafiya a hankali yana biye dashi. “Kasan meye banbancin mu da kau?”
Girgiza kai Bashir yayi, ya juyar da kanshi yana kallon waje. “Ina sonta, kuma ina soyayya. Kai kuma baka soyayya baka san meye soyayya ba, shi yasa da kasan meye soyayya ba zaka ga laifina don na biye mata ba, sai mq tausaya min da zaka yi. Idan har mace ta kai namiji wata duniyar da bai tab’a isa ba, yana mata uzuri a duk abin da zata mishi. Bashir kayi aure ka gane me nake nufi!”
“A’a Malik ba zan iya ba, yarinyar da bata wuce sa’ar hanjin cikina ba, tana min yelling ballata zan yi na kai gidan uwareta.”
“Ba zaka iya ba, ko ni da can baya aka min abinda Zainab tayi sai yanke mata harshe, amma a yanzu lafiya lau sai ma tausayi take bani!”
“Allah ya kyauta, amma ba zan yarda da auren yarinya karama tana min tsawa ba” dariya Malik yayi ya ce masa. “Ai na yafe mata, abin da zata min da wanda na sani da wanda ban sani ba, da wnada zata yi gaba na yafe mata baki ɗaya. Bana fatan Allah ya kamata da laifin da ta min, bari na gaya maka wani sirri! Ban sani ba ko lafiyarka tayi rauni ce, amma idan kana son gyara shekarunka da tsufarka, ka auri budurwa wacce kome nata yake tsaye, zaka more rayuwa. Zaka kuma gyara kaifin haddarka faɗin Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama ne, ba fadar Malik Menk Jordan ba!”

Shiru Elbashir yayi, yana sauraron shi. Can ya ce. “Kana ganin na nimo auren Hafsah kenan?” “Idan har zaka iya ka nima mana, ai zaka ji dadinka ne” suna tafe suna hira, har suka isa gidan Sayyada Quddisiya. Da Wahiba ya hadu ta ce mishi. “daga wurin wancan mahaukaciyar ka dawo?” Ya rasa yadda zai yi da ita, domin jin haushin Zeeno take. “Daadi wurinta ka tafi?” “Wahiba me yasa kike haka ne?” “Me yasa ba zan yi ba? She driving Daadi crazy!” Ta fada kamar zata yi kuka. “And ta zubar da dan uwanmu, kin san da Daadi ya gaya min she’s pregnant hatta kawaye sai da na gaya musu, second Mommy she got baby for us! Akan me ba zan tsane ta ba!” Ta faɗa da karfi tana kuka. “I love my siblings tun ban ganshi ba, na.ji ina masifar kaunarshi.” Rungume ta Malik yayi yana shafa bayanta, “Sorry my twins, kukan ya isa haka, kin ji zan tafi Keivroto ku kula da ita, please ban da fushi da rashin kunya she still my wife!” Cikin kuka da ihu ta ce. “Ka sake ta mana! Dole ne sai ka zauna da matar da bata dace da kai ba. Akwai masu sonka mu ma muna sonka.” Zaunar da ita yayi sannan ya ce mata. “A matsayina, mahaifinku dole na nime macen da zata kula da damuwa ta, babu kyau kadaici shi yasa na kawo ku nan, idan kome yayi daidai zan ce ku dawo wurina a Keivroto;”
“Daadi kayi hakuri” murmushi yayi yana rike hannunsu, gani yake kamar Nuratu ce a gabanshi, gani yake kamar yana tare da ita. Rungume su yayi baki daya yana mai da kwallqr da ta cika mishi idanu. “Ban da rigima da faɗa.” Haka yayi ta jansu da hira. Sannan ya bar su, ta tafi wurin Sayyada Quddisiya da take kitchen, ya zauna a kujeran da yake fuskarta ya ce mata. “Anne zan tafi na barku da aiki don Allah a duba lamarinta!” “In sha Allah babu abunda zai kuma faruwa, sai alkhairi.”
Haka suka yi ta hira tana mishi nasiha, sannan ya shiga ya dauki kayanshi suka bar gidan, da kasar baki daya.
A can asibiti su Black, Abbas, Adnan da matarshi sun hadu a can asibitin. Sai can dare suka bar asibitin. Wayarta ce a hannunta, tana chatt da Hafsy sai dariya take mata tunda ta bata labarin cikin da ya zube.
*Ke Yar kunama, yaushe har aka yi abin haka da sauri, sau nawa aka yi da har kwallon ya faɗa raga?*
_Ke dai banza ce, na gaya miki mun yi kusan wata biyu a wani garin ruwa kuma ai a lokacin anyi ya fi sau biyar, tun a hanya na fara rasa isasshen lafiyata._
Dariya ta saka har da emoji. *Da gaske an yi ya fi sau goma kenan?*
_Mahaukaciya! Ba zan gaya mikin ba_
Dariya hafsy ta saka tana gaya mata. *Allah kin bani dariya, wato daga dauke ki sai aka yi abin da Sayyadi yayiwa Nazneen! Daga nan sai labari ya sha banban ko?*
_Ke bana son iskanci wace ce Nazneen da Sayyadi?_
*Banza labarin novel din Addah Ramlat nake gaya miki*
_Allah ya kyauta wallahi na zata wani abun arziki ne_
*Allah abin arziki ne, ke dai da baki karanta hausa novel!*
_Zan rufe data na, tunda na zaki min taaziyar Babyna!_
*Allah ya sa me ceto ne ya baƙi na mora, zan saya miki littafin kina so ko baki so?*
….
______
*Kuyi hakuri da abin da yake, nima ba son raina ba ne. Amma zan kokarta mu tafi yadda ya dace, idan kuma kuna son ayi rushing mu gama shi nan da kwanaki idan zaku iya hakuri labarin yana nan kan domin yanzu muka yi tsakiyar rigimar Zeeno da Malik na gode sosai*
book 2 zai zo muku Whatsp da Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/23, 1:53 PM] Yan Mata: 27
*Mtsew!* Ta tura mata tsaki, murmushi ta turo mata, sannan ta ce mata. _Allah ya shirya ki_ ta faɗa tana dariya. *Allah ba abin wasa bane, Yarona na rasa fa? A matsayina Na uwa kin ji yadda nake ji kuwa? Sai yanzu na fahimci irin kaunar da nakewa cikin!* _Koma mene ne ya wuce Allah ya baƙi na mora_ haka suka yi ta hira tana jin kuka yana taso mata, domin son da takewa cikin ƙara samun matsuguni a ranshi. A hankali ta sauka daga gadon ta nufi waje, bayan ta saka hula da sweatcoat. Tana jin kamshin tutaren Malik. A bakin can wurin zaman masu son ganin likita ta zauna, tana shafe kwalla. Tana wurin wasu couples suka fito da Babyn rungume a kirjin Uwarshi, uban yana tallafe da uwar, sai wani rawan jiki yake akansu. Ko abokansa ne da yan uwansu, suna haba haba da Babyn.
Haka kawai take jin kadaici, a hankali kuka ya kwace mata, me yasa bai kuma zuwa ya ganta ba, ko yayi fushi da ita ne? Cikin shashekar kuka ta d’ago kai, yana tsaye rike da sweatcoat dinshi, ya zuba mata idanu, da sauri ta mike, da wani irin sassafar ta isa gare shi, bude mata hannun yayi ya shiga, tana sake fashewa da kuka. Rungume ta yayi yana faɗin. “Sorry!” Rungume shi tayi tana shashekar kuka. “Zan tafi Keivroto ne, nayi missing flight shi ne dawo!” Kara rungume shi tayi tana kukan!” A hankali ya dauke ta cak ta zuba hannu a kafadarshi, tana sauke ajiyar zuciya. Bayan ta kura mishi idanu. “Kayi hakuri ba da gayya na zubda cikin ba.” “I knew that!” Ya faɗa a hankali, yaba zuwa ya kwantar da ita a saman gadonta. “Me yasa kika fita a wannan sanyin?” “Kana jin haushina ne?” Yake yayi yana gyara mata zaman lullubi, “baka ce min kome ba!” Kallonta yayi, na wani lokaci kafin ya ce mata. “Me zance?” Ya tambaye, kasa tayi da kanta tana jin kuka na zuwa mata. “Malik!” “Shiii ya isa haka, kwanta ki huta!” “Ina son babyna!” Kura mata idanu yayi dominya lura rigima take ji. “Wani baby bayan wanda ya zuba?” “Ina son wani ne!” Murmushi yayi ya ce mata. “Allah ya kawo masu albarka!” “No Ni yanzu nake so” wayar shi ce tayi kara, murmushi yayi a hankali ya nime wuri ya zauna. Ya fara waya, daga yadda yake wayar ta fahimci da mace yake, fashewa da kuka tai, ta zo ta fisge wayar ta buga shi da bango. Durkuswa tayi ta shige jikinshi. “Me kike so?” ” Ka dai na waya da wata a gabana” kara rungumeta yayi yana shafa bayanta. “Kince baki son cikin, me zaki yi da shi?” “Haka kake so na zauna cikin kadaici? Nima ina son abokin hira, nima ina son wanda idan baka nan zai zame min abokin hira!” Jan hancinta yayi yana faɗin.”idan muka rabu, sai ki haifi wani. Kin ga yanzu kin lalata min waya.” Wani irin kuka ne ya kwace mata tana kallon shi.
“Ni babyna nake so, idan yaso ka tafi ma kada na kuma ganinka!”
“Me yasa baki sona?”
“Bana sonka babyna nake so!” “Ok zan tafi idan ban dawo ba,me zaki yi?” “Zan fara sabon rayuwa zan manta da kai!”
“Shi kenan babyna ya tafi sai kiyi hakuri!” Rigima sosai ta saka ita dai ya nima mata baby, ya rasa yadda zai yi da ita baki daya bata gane yadda yake danne kanshi, amma taki fahimta. A hankali ya janyota jikinshi yana shafa bayanta, har ta fara hamma. Daukarta yayi ya daura a saman gadon. “Ina zaka gudu kaje, bayan baka gaya min yadda zan samo babyna ba”
“Zan yi tunanin inda ake sayar da Babyn sai a sayo miki!” Ya faɗa yana Sosa mata kai, a hankali barci yayi gaba da ita.
Kwantar da ita yayi, yana shafa fuskarshi. Ya koma ya zauna tare da daura daya akan ɗaya, yana kallon yadda take barci a dan takure. Tashi yayi ya kara dumin dakin sannan ya koma ya zauna yana me cigaba da kallonta. Yana zaune a wurin aka buga kofar, “Yes!” “Malik na kawo maka abin rufuwa ne!” “No muje gidan kawai!” Ya tashi yana me zuwa gabanta, sumbatar goshinta yayi yana shafa kanta. “Kina tare da babynki, hala kafin ki san da zaman shi hankali ya kuma shiganki” daga haka ya bar dakin, a daren jirginsu ya wuce Addis Ababa, domin jinkirin da aka samu, yasa shi dawowa asibitin.

Washi gari da wuri Ammyn ta zo asibitin, ta shiga dakin tana kallonta yadda take barci. Bata tashe ta ba har zuwa wani lokaci kafin ta farka, tana kallon Ammyn. “Ammyn ina yake?”
“Wa kenan?”
“Mayor mana” ta faɗa tana sauka a gadon, tana nufar ban daki, wanka tayi da brush, sannan ta fito dakin, ta zauna ta fara cin abincin.”Ammyn zan iya sallah? Na ga jinin ya tsaya.!” “Eh zaki iya sallah!” Ta faɗa mata, tana cin abinci. Idanunta yana kan kofar dakin. Tana nazarin yadda zata kuma samun wani cikin ne, daga nan sai ta rabu da Malik. Wani bahagon tunani da ya shige ta, shi yasa ta kudiri a ranta yau yana zuwa za a sallame ta, ta kuma kunna data ta shiga tambayar Hafsy!
*Hafsy wai an ce daga lokacin da aka yi bari, ana kuma samun wani cikin ne?*
Sakon ya tafi ya bada al’amari ya shiga ba a duba ba, sake tura mata wani tayi tana faɗin.
*Bana son iskanci ki bude sakona*
Nan na shiru, ganin sai jera mata ashar take bata duba ba, kawai ta shiga kiranta.
“Ke bana son bura uba, uwar me kike da ba zaki duba sakona ba?”
“Aiki nake ba wasa ba, please be having yourself, an gayyace ni wani aiki ne!”
“Ki bar aikin zan biya ki sama da abin da zasu baki. Duba sakona!”
“Gaskiya ba zai yiwu na duba wayar ba, domin kwalliya nakewa yar command sojojin Keivroto, ki taya ni godiya Malik ya min hanya ta hannun wannan Baturen abokin shi?”
“Kuna dating juna ne!”
“Hmmm bayan gaya miki ba, kawai dai na gaya miki abin da na sani ne.”
“Banza kawai ki duba sakona don Allah!”
“Ok bani minti ashirin zan duba!” Ta kashe wayar, ita kuwa Zeeno kamar ta shiga ta wayar tayi ta zubawa wacce akewa kwalliyar mari, tayi tsaki ya fi sau dari. Agogon wayarta da agogon dakin akan idanunta suke bugawa, kamar zata fasa ihu.
After like 20mins sai ga ta a Whatsp,
_Babban magana! Wai ma me ya faru har aka rasa cikin?_
Nan ta shiga bata labarin abinda ya faru, sannan ta tura mata, emojin kuka tayi tana faɗin.”ina son babyna ne!”
Murmushi Hafsy tayi tana faɗin.
_Yarinya you too late!_
*Bana son iskanci, ki gaya min ya zanyi?*
_Gaskiya na gaya muku_
*Babu wata hanyar da za abi ne?*
_kinga Zeeno wallahi ban sani ba, Malik ya fi ni sanin hanyar da zai kuma dirka miki wani cikin_
*Tun jiya da ya zo o ya sani barci, ban kuma ganin shi ba*
_Ba dole ba. Cewa kika yi baki son ganin cikinshi ya burge ni me shegen taurin kan tsiya_
*Kai Hafsy!*
_Mtsew_ ta rufe datar bayan ta tura mata sakon. Wasa wasa lokaci yayi tafiyar ba zata da zata kai ka inda baka zata ba, domin kuwa kwanaki sunyi ta haurawa har aka samu sama da sati sannan aka sallame ta, a lokacin ta kara yarda Malik ya tafi abinshi. Ranar tayi kuka for God sake, ta ji babu dad’i. Abu goma da ashirin ga Wahiba rashin mutunci take mata. Da bakaken magana, wannan abin ya dami Zeeno. Da ta gaji da mata rashin kunyar, ta mata duka biyu sai da ta suma, Sayyada Quddisiya bata yi magana ba, domin itama tayiwa Wahiba faɗa, amma taki ji, dake yar gata ce, ta kira Malik tana gaya mishi abinda ya faru. Shiru yayi kafin ya ce mata. “na san halinku daga ke har ita, Zainaba vata saurin hannu sai ka kure ta, sannan bata cin zalinka don tafi ƙarfinka, Anne ta fada min yadda kike mata rashin kunya, she’s my wife bana son rashin wayo da reni, idan na kuma ji zan sab’a miki!”

Kuka ta saka ta kashe wayar, kiran Wahida yayi ya ce ta kaiwa Zeeno, tana wance tayi sallama tare da mika mata wayar. “Second Mother, Abba yana magana!” Amsa tayi ya saka a kunnenta. “Maman Yara, naji anyi hukuncin!” Kuka ta saka masa tana karawa, taki magana. “Meke damunki?”
“Shi ne ka tafi ka bar ni?”
“Tow ya zanyi? Na bar abubuwa dayawa, kuma don ke na bari ba don kaina ba, farin cikin da na fara samu kin hana ni, likita ya ce a barki,ki huta shi yasa kike rigima damuwa ta miki yawa?”
“Ni yaushe zan kuma samun Babyn? Kullum sai nayi mafarkin ina bawa babu abincin shi, ga marana ciwo yake min.”
“Ciwon mara kuma?”
“Eh mana!”
“Ok Adnan zai kawo likita ta duba ki?”
“Ni bana son magani Alkur’ani kawai zata min.”
“An gama gimbiya!”
Haka suka sha hira sosai, kafin suka ajiye wayar, can yamma sai ga Adnan da likitan, ita tazo ta dubata, dake Malik ya gaya mata kome, bata gaya mata kome ba, magani ya bata, sannan tayi musu sallama, kiran Malik ya shiga wayarta.
“Dr ya kika ganta?”
“Tana lafiya, cikin ya fara kwarine, shi yasa maranta yake ciwo, da zarar ya kai wata biyar zuwa shida ciwon zai ragu, idan bai ragu ba, dole mu cire mata shi a 29 to 30weeks.domin ina jin bugun zuciyar Babyn yana yawa.”
“Allah ya sa mu dace, amma ita uwar tana lafiya?”
“Eh tana lafiya.”
Nan suka tattauna, kafin suka yi sallama ya kira Zeeno, ta fara mishi rigima ita ice cream zata sha yasan yadda zai yi da ita wallahi. Kiran ya katse ya kira Adnan, ya gaya mishi. Ya kirata ya gaya mata, kaya ta dauka zata saka, tayi ta kokuwa da kayan, karshe wandonta a iya cinya ya tsaya, bata san lokacin da ta kira shi tana kuka.
“Kuma me kike so?”
“Kayan sunki shiga ne?”
“Shi ne na kuka?”
Shashekar kuka ta ja, tana faɗin. “Kawai ba gaya maka ne, kayan sun ki shigana”
“Ki saka abaya mana!”.”Ni bana so ne!”
Ta faɗa tana kashe wayar ko sauraron shi bata yi ba, ta kira Hafsy tana kuka take gaya mata, kamar sun hada baki da Malik suka ce ta saka Abaya, kuka sosai take har da shashekarta.
Kafin ta ciro abayar tana hararanshi. Bra ta dauka zata saka, domin ta kwana biyu bata saka ba, ai kuwa suna de basu san da wannan zancen ba. Hawaye na zuba mata, ta dauka tana cusawa da zafi ya ishe ta wurgi tayi da shi, ta dauki abayar da hafvest ta saka sannan ta fito tana kallonsu. Kamar ba zata shiga motar, babu wanda ya bita, domin ta koyi bakin hali. Bata gayyaci kowa ba, tayi tafiyarta.
Haka suka jido kayan kwalama da makulashe,ta wuce daki da wasu wasu ta bawa atika ta saka a frij, sannan ta wuce dakinta, apple ta zauna tayi ta ci tana lumshe idanu, kamar ta cinye da yatsunta.

Kiran Malik tayi tana gaya mishi. “Kunna data ki nuna min na ganki!”
Kunna wayar tayi tana nuna mishi kome, sannan ta juyar da Wayar tana kallon fuskarta. Wani munafikin kalli yake mata kasa kasa, tayi kyau fatarta ta murje idan ya fahimta har da shi a masu takura mata, kirjinta yayi bala’in d’aga mishi hankali, fatarta tayi kyau wai wani glowing take. Kamar daren goma sha huɗu….
book 2 zai zo muku Whatsp da Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/23, 1:53 PM] Yan Mata: 28- “Me kike ci kika zama ƙatuwa haka?” Ya tambayeta, yana kallon yadda ta zauna a wurin kamar kayan wanki. Tura baki tayi tana fadin.”Ba wani katancin da nayi kawai baka gani ne!” Sosa goshinsa yayi yana faɗin. “Kuma gaskiya ne,bana gani sosai. Amma, cire min wannan abin na ganki da kyau!” Kallonshi tayi sannan ta ja mayafi ta rufe kirjinta. “Da nace maka ina son baby tafiya kayi baka kula ni ba” dafe goshinsa yayi yana faɗin. “Na manta ne, amma kuma ina son naga yadda zan iya baki wani Babyn babu matsala!” A ranshi yana see mamakin wannan haukar na Zeeno ga ciki a jikinki kina niman wani cikin, salon da yana nan, suna rigima da junansu.
A hankali ya kura mata idanu, shiru yayi idanunshi yana ɗaukar saken fatarta. Har ga Allah Zeeno bata gane mijinta take haukar son Kasancewa da shi ba, shi yasa take damuwa ya mata wani cikin, kurawa kirjinta idanu yayi yana faɗin. “Good girl! Gaskiya na yarda kina son Baby! Zan saka Adnan ya saya miki ticket zaku tawo dasu Ammyn kinji.”
Gyada kai tayi tana faɗin. “Hmm! Ni dai yau nake so?” “Kin ga in sha Allah jibi!” Kamar tayi kuka ta ce mishi. “Tow shi kenan!” Ta faɗa tana yada kai. “Sorry kinji!”
“Tow!”
Kashe wayar tayi, tare da sakawa a fly mode, sannan ta wuce ban daki. Ruwa ta sakarwa kanta, sai da tayi wanka ko zata ji sauƙin ganinshi da tayi. Zama tayi a bakin gadon kamar wacce ta rasa kome nata.
***
Keivroto
Zaune yake yana kallon hotunan da ya dauka, suna wayar. Hotunan ta ne. Juyi yake a kan kujerar office dinshi, yi mishi kyau matuƙa amma yana gudun kada ta zo a samu matsala, wayar shi ya dauka yayi baya da kai yana kiran Adnan. “Kayi musu booking jirgin asuba!”
“An gama yallabai!”
A hankali yake kara zooming hoton yana murmushi, yar siririya tayi kiba! Ya faɗa a ranshi, yana kara jin kaunarta.
Al’amarin rigima da bude file din kisan iyayensu aka bude, bincike ake yi kamar akwai wani abu da ya alakanta haka da gwamnatin kasar na da. Haka yasa Malik ya kuma bude wuta, sai an yi.
Haka yasa ake farmarka shi, duk da baya son wani abu da zai shafe ta, amma yadda take nuna tana bukatar ganinshi yasa shi. Sawa a mata booking. Kiran Elbashir yayi yana faɗin. “Zainab zasu shigo da Ammyn Abbas. A bawa airport tsaro sama da baya.” “Malik a hakura da zuwanta, Hafsy ma tana karkashin kulawarmu balle Zainaba da kasan shegen taurin kanta kamar na karamin jaki;”
Wani irin dariya Malik ya saka yana faɗin. “Bashir Matata ce take da taurin kai, kamar a jinjirin jaki?”
“Malik waye bai san halin taurin kanta? Sannan Ammyn da Abbas su zauna, kafin kome ya lafa. Ita tsuntsuwar soyayya sai ta zo.”
“Yawwa Yallabai Bashir!” Kashe wayar yayi yana dariya, kiran Adnan yayi ya gaya mishi ya cire sunan Ammy da Abbas, ya turo Zeeno. “Tow yallabai!” Ya kashe wayar.
Shigowar wani sako, yasa shi dubawa. “Kamar yadda na rasa Y’ata wallahi sai na saka ka rasa kome Malik, hakkin mutuwar Maidah yana rataye a wuyarka”
Kiran layin yayi, yana faɗin.
“Lalla Salmah! Kashe Nuratu da kaita wurin Khuldu Jahid Khan da Shu’iba, turo Jalilah ta hana ni auren Zainab, ko kawo Maidah ta saka min gida on hell ko? Duk basu isa hujjar da zai saka ki gane kawaici da kunyar da na miki ba? Kizo Keivroto babu me tab’a ki.”
Ya faɗa yana murmushi, sannan ya koma kujerarshi yana murmushi.”mutanen da ba yarda dasu, sune masu shirin su yake ni akan gaskiyaida na san nike da ita!”
Kiranshi aka yi, ya ɗauka. “Maciyi amana, fasiki makashi sai na tabbatar da rabaka da kowa sannan kayi mutuwar da gawar kare sai ta fika daraja!”
“Khamis Shatima! Tow dai Allah ya baka sa’a zance ba”
“Kai Malik karshen ka yazo!”
“Allah ya sa muyi kyakkyawar karshen!” Ya fada yana dariya, domin da haka ya dace da shi.
***
Demark.
Da wuri ta shirya, domin Adnan ya gayawa Ammyn an soke tafiyarsu, dama tasan Keivroto babu lafiya, don haka ta saka Zeeno a gaba da faɗa. “kin san halin da ake ciki a inda zaki je kuwa? Shima da yake namiji da gaske yake kokuwa da rayuwarshi balle ke, da yanzu ba da ba ne, ba zaki iya kare kanki ba, balle wani da baki san da zaman shi ba”
“Kai Ammyn tow ni yaushe zan girma? Nayi kewar Keivroto ne fa, nake son zuwa na ga mutane su ganni!”
“Zainab mijinki kike kewa, a wannan yanayin da kin hakura ya gama magance matsalar gabanshi zai zo gare ki ”
“Ammyn!!” Ta kira sunanta kamar zata yi kuka.
“Don Allah ki daina faɗar haka kada ki hanani zuwa don Allah.”
Ta fada idanunta yana kawo ruwa, “Maman Abbas, kyaleta mu da muke bukatar zuwanta, yau ta ce zata da kafarta Allah ya tsere ya kuma kai su lafiya. ”
“Shi kenan Inna, wai dama saboda yanayin ta ne, amma Allah ya kiyaye hanya ba”
Gyada kai tayi, tana zama kusa da Inna. “Gaskiya matar nan ba zan so ki mutu da wuri ba.” “Saboda rayuwata a hannunki take ba, don kaniyarki.”
Dariya Zeeno tayi tana me wucewa dakinta, da idanu suka bita. “Zan ga ranar da Yarinyar nan zata yi hankali. Abu a jikinka baka gane ba sai yaushe zaka gane!”
“Yarintar fa! Idan ba yarinta ba, me zak saka haka? A yanzu cikin ya fara kwari dakyar take zama dakyar take tashi amma haka bai saka ta fahimci yanayin da take ciki ba.” Inji Sayyada Quddisiya.
Murmushi suka yi, daga tafiyar Malik zuwa yanzu wata uku kenan, lokacin da cikin ya damu matsala yana wata wata uku ba don ya damu matsala ba, cikin watansa shida da wasu kwanaki kenan, yanzu kuma ya koma baya, ko don abin da ya faru ne cikin ya saka mata kiba kamar an hurata, sannan duk wani wurin sharholiya na jikinta ya kara girma da cika.

Ita tana ganin kamar kiba tayi, bayan cikin ne yasa haka.
A hankali ta gama kwashe kayanta, sannn ya koma ta kwanta. Shiru a yan kwanakin nan, sai ta ji cikinta kamar ana yawo ko ana motsi, ita ta gaji da yiwa nurse bayani tana cewa lafiyarta lau. Wancan karon da Dr Helin tazo ta gaya mata cewa tayi normal ai wani lokacin organ na cikin mutum yana haka. Shi yasa ta share bata kuma magana ba, amma gaskiya har yanzu abin yana mata wannan yawon.
Dake a duniya bata da wanda take saukewa mitarta, a zauna lafiya sai Malik don haka ta kira shi kamar zata yi kuka ta ce mishi. “Mayorrrrrrr!” Sai da ya sauke ajiyar zuciya sannan ya ce mata. “ina jinki babyna!”
“Mayorrrr! Wani abu yana motsi a cikina?”
“Ikon Allah kuma Helin ta duba?”
“Ina ta duba ni, kullum sai su ce organ dina ke motsi.”
“Ok idan kin zo sai na kai ki wurin Dr Saddika ta duba baki”
Aikuwa ya biye mata suka sake zama sakarkaru, dama can sakarya ce bata sani ba, amma zuwa yanzu Malik ya kara girmama sakarcinta da shirmenta.

Ya kuma biye mata tana kara, sakalce mishi. Ba zuwan Zeenobia ba ne, bai zama dole ta iya daukar wasu al’amarin. Don haka har suka isa airport tana waya da shi, sai da suka kusan tashi ta kashe wayar ta saka a fly mode.

—–
Tunda suka ce mishi ta taso, ya tattara suka koma airport. Domin ya san zata sauka da safe ne, don haka ya tare a airport ɗin, zuwa yanzu an mishi txt na barazanar za a kashe ta. Ita da abin cikinta. Da ya hanata zuwa zata ga kamar bai sonta ne, amma yanzu da ya barta ta tawo yasan koda wasa ba zata sake yarda ta cusa kanta a hatsari haka ba. Aiki kawai ake ana leke leke. Yana zaune idanunshi a kan kofar da matafiya suke fitowa. Dan kishingida yayi, barci ya dauke shi.
“Mayor!” D’ago kanshi yayi ya kalli yadda ta jike cikin jini har yana d’iga. Nuna mishi hanyar da ta fito tayi, Elbashir ya hango kwance cikin jini! “Har mutane nawa zasu mutu domin ka!”
A firgice ya farka, Elbashir ya gani zaune a gefenshi. Mikewa yayi ya kallon kofar da shi kanshi Elbashir din, wayar shi ya ciro tare da kiran Commander na sojojin kasar, akan a turo musu sojoji.
Sannan ya kashe wayar, ko minti ashirin ba ayi ba, suka iso. Fuskar shi a hade ya ce musu. “Ku tafi da shi!” “Malik me nayi ?” “Ku tafi da shi kawai”
“Malik gaya min meye nai maka!”
“Ku bashi abinci, ya ci ya koshi. Sannan a rufe shi a idan zai huta yana fama da cutar hauka ce, idan ya ga mata masu ciki farmakarsu yaƙe. ”
“Malik!” Ya kira sunanshi kamar zai tashi sama, haka sojojin suka tisa keyarshi. Tare da barin airport ɗin, ajiyar zuciya Malik ya sauke. “Ba zan yarda ka mutu domin ni ba!”
Yana ganin yadda aka tusa shi cikin motar, sannan Commander Keivroto ya kira shi. “Me yasa ka saka aka kama shi. ”
“Bana son na saka rayuwar mutanen da suke kusa da ni a matsala ne. Shi yasa don Allah a kula da shi, zan kula da nan ɗin.”
“In sha Allah!”
Daga haka ya cigaba da kula da zuwan Zeeno, wurin karfe biyu na rana, jirginsu ya sauka. Idanunshi yana kan fitowar mutane, idanunshi ne, ya sauka a kan Zainaban shi, tana tafiya a hankali, tare da yatsuna fuska sakamako gajiyar da tayi, kafaffunta sun kumbura, da sassarfa ya isa wurin kafin ta iso, bude mata hannu yayi ta shiga ta. Tana sauke ajiyar zuciya. Kar’ar harbin da ya cika wurin yasa aka musu zobe, tare da kare Malik da ita, ware idanu tayi kamar zata fashe da kuka. “Me haka yake nufi?”
“Rayuwar da nake ne yanzu, muje!” Wayar shi tayi kara, dauka yayi yana rike ta. “Ka duba wuyar matarka, ba fa kai kaɗai ka iya wannan wasar ba!”

Duba wuyarta yayi yaga jini na zuba. “Shatima! Kada ka sake ka tab’a min mata da yarona. Domin yanzu haka Nadrah tana Cyprus tare da kanwar mahaifiyarta, tana cikin hotel din da aka kama ta, sannan tana sanye da bikini skyblue. Sai kanwar mahaifiyarta tana sanye da bakaken kaya, tana cikin swimming pool, kayi kokarin dakatar da ita daukar ruwan da yake gefenta, ko kuma a kira ka domin binciken taya aka yi yarka da kanwar mahaifiyarta suke tu’amali da miyagun kwayoyi!.”
. Ya kashe wayar, tana kallonshi. Har suka fita. “Me haka yake nufi?”
“Ba matsalarki ba ne, muje gida.” Radadin da take ji ne ysa ta shafa wuyarta, “Jini!” Ta fada a firgice, tana rike wurin. Daukar hanky dinshi yayi ya goge mata, yana cewa.
“Kasan halin da ake cikin ka sani na zo?” Zuba mata idanu, kafin ya ce mata. “Tow ya zanyi?” Bata san lokacin da jikinta ya fara rawa ba. “Ke!” Ya daka mata tsawa. “Ki kula da kanki, cikin jikinki kike son mu rasa shi?” Ware idanu tayi, tana rike hannunsa. “Ciki ne a jikina!”
“Shi yasa nace ki bari kome ya lafa, sai ki zo kin ga gashi nan, zaki saka mu cikin tashin hankali. Ban damu na mutu ba, amma please ki kula da cikin kinji!”
Ya faɗa yana sumbatar goshinta, kwantar da kanta tayi tana sake ajiyar zuciya. “Me yake faruwa ne?”
“Wani dan karamin rigima ne yake faruwa, idan na magance zan miki bayani!”
Kwantar da kanta tayi tana sauke ajiyar zuciya, wani irin bala’in tsoron kada wani abu ya tab’a babynsu. Har suka isa gidanshi me cike da sojoji da yan sanda.
“Sannu kinji!”
“Yawwa! Ina Uncle Elbashir!”
“Sawa nayi aka garkame min shi, domin kada wani abu ya same shi!”
Zillo da cikinta yayi ta rike hannunshi. “What?” “Wani abu ya juya a cikina”
Rungume ta yayi yana dariya, “Babyn mu ne yake murnan ya hadu da Daadinshi” kwantar da kai tayi, tana tuna bayanin matukar ta fahimci tana dauke da cikin Malik zata rabu da shi. Kallonshi take,
“Me ye?”
“Ka hakura da abinda yake faruwa, mu tafi wani wuri mu rayu! Ko na tafi da Babyna!”
“Me yasa baki son zaman lafiya?”
“Taya zan zauna a nan kayi sanadin rasa cikin jikina? Idan har da gaske kana son mu, ka bar kome kazo muje mu bar wannan duniyar da abin yake cikinshi, mu yi tarbiyyar Yaronmu!”
“Anan aka fara, anan zan karkare shi ban miki wannan soyayyar da zaki juya ni!”
“Malik ka bar wannan rayuwar mu tafi wani wuri!”
“Babu inda zani dama kin zo ne, kin zo ki d’aga min hankali ne?”
“Ba zaka zo ba kenan?”
“Kema kin san baki yi wannan isar ba.”
Ganin da gaske ba zai yarda ya hau ra’ayinta ba, yasa ta Fara faɗa.
“Zan zauna da kai, daga lokacin da wani abu ya faru wallahi zan aikata abinda zai wargaza ikonka!” Ta wuce bata kuma magana ba. Sako Shatima ya turo mishi.
*Da alamu Zainab bata san kai ka kashe mata iyaye ba, wannan shine numberta.*
Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/23, 1:53 PM] Yan Mata: 29-. Ji yayi kanshi ya dauki matakin wani irin zafi. A gefe guda ya kura mata idanu yayi, duk yadda yake bukace da ita, ya watsar da ita domin ba zai kuma bin ta kanta ba, ba zai dauki reni daga mace ba, duk kaunar da yake mata. Don haka ya dauke kanshi daga kanta, yayi alƙawarin ba zai bukace ta ba, ba zai nime ta mishi wani abu ba. Haka yasa baki daya ya kame kanshi sama da can baya. Kafin dare gari ya dauka an kaiwa Mayor da matar shi hari a airport. Wurin karfe tara Elbashir ya shigo gidan yana bin Malik da kallon banza. “Kayi hakuri! Tsoro nake kada wani abu ya same ka!”
“Shi ne zaka kulla min sharri?” “Idan akwai abin da ya fi sharri my friend zan maka domin na kubutar da kai!” Zama yayi ya cilla mishi wayarshi. “Sakon Shatima!”
*Idan kana tare da Malik sai ya maka butulci, yanzu ma gashi ya saka an kama ka, ka haɗa hannu da ni!*
_Bana hada kai da maciyi amana!_ Elbashir ya tura mishi, “nima ya turo min number Zainaba!” Zunkud’ewa Elbashir yayi kamar zai fado kasa. “Yana nufin zai gaya mata ne?” Murmushi Malik yayi ya ciro wayar Zeeno yana nuna mishi. “Na dauke wayar lokacin da take jarabarta da ta saba, yanzu haka na cire layin yana kan wayata, na mai da mata daya layina da babu kowa a kai.”
Shiru yayi yana kallon yadda Malik ya kware a kowani fuskar. “Amma da zaka yi film sai ka samu Oscar awards.”
Girgiza kai yayi yqna faɗin.”ba haka ba ne, ina fama da ita da wani rikicin ne, taya zan kuma barin wani abu ya kunno min kai? Ina son magance matsalar mu, shi yasa na dauke wayar a jakarta tana can tana jin haushina.”
“Allah ya kyauta!” Daga haka suka tsinke da hira. Jama’a Madam tunda ta shiga dakin shi, tayi wanka da sallah, ta tsaya a gaban Mirror tana kallon cikinta, da ta gaji ta koma ta zauna hannaunta biyu akan cikinta, tana murmushi ta manta da abinci da zarar cikin ya motsa zata tab’a wurin.
A hankali yunwa yayi ta damunta, ita da abin cikin, ganin Malik bai shigo yasa ta mike tana me nufar hanyar waje daure d towel. Allah yasa shi yake fuskar kofar fita Elbashir ya bata baya, ganinta daure da towel, tana gyara rikon da tayiwa towel din yasa shi daka mata wani irin tsawar da sai ta ta juya da mugun sauri, tana me fashewa da kuka. Shi kanshi Elbashir sai da ya firgita. “Lafiya?” Jikinshi yana rawa ta nufi cikin gidan, ya same ta a durkushe tana kuka. “Da kin sake kin fito Elbashir ya ganki wallahi da na makantar da shi, ke wawuyar ina ce? Zaku futa daga ke sai towel?”

“Tow ba yunwa nake ji ba! Tunda nazo hanci abinci ba, baka kawo min abinci ba ka bar ni a daki Ni ɗaya!” Shiru yayi yana kallonta, sai kuma ta bashi tausayi yasan bata iya kome ba, nufar wurin kayanta yayi ya bude jakar, ya shiga ciro mata kaya dakyar ya samu wata gown mara nauyi da takura, ya saka mata. Idanunshi yana kan kirjinta. Janye idanunshi yayi ya nufi hanyar waje, tana bin bayanshi. Yana zuwa ya nufi kitchen dake a falon yaƙe. Daga falon kana hango abin da ake yi, ya fara bude firji ya sauko kwai shida. Da indomitable.
Ya daura ruwa, ya daga mata guda biyu. Saura hudun ya ciro kayan miya, green pepper, red pepper, carrot, chicken breast. Ya fara yanyankawa sannn ya saka a wata yar ƙaramar turmin karfe. Ya saka namar ya dake shi tass, ya juye a wankakken frypan.ya d’iga mangyada ya daura akan wuta, yana ya tattara yankakkken kayan miyar ya zuba a cikin frypan din, ruwan da ya daura na tafasa taliyar indomitable ya rage karfin wutar ya saka taliyar yana kallon yadda take hadiye yawu.
A ran shi ya ce. *Kamar da gaske, nan kuwa tafi kowa fitina!* Yana soya kayan miyar ya juye namar ya saka yar gishiri da sinadarin dandano, ya zuba garin citta, kanumfari da garin tafarnuwa ya nuna mata curry ya ce mata. “Kina so ko na bari?” Lumshe idanu tayi tare sa gyada kai, a hankali ya zuba kadan, take kitchen da falorn yq dauki kamshi. “Allah ya tona asirinka, wato girki kake don mugunta shine har sa daka tsawa na dawo nima zan ci!” Ban za yayi mishi yana fadin. “Yawwa ka duba can akwai key din dakin da yake sama, mu zamu zauna a kasa, ka zauna na wani lokaci muga yadda zamu shawo matsalar!”
Sannan ya koma ya cigaba da aikinshi, dole ya kara indomitable din, ya juye na farko ya daura wutar na biyu, ya cigaba da aikin namar shi na nuna ya fasa kwai a wani bowl, ya zuba kayan kamshin indomitable ya kada sannan ya zuba akan sauce na naman nan, ya zauna yana motsawa har ya nuna ta rufe a hankali.
Dauko flat yayi yana faɗin. “Yanzu zaki ci kinji!” Gyada kai tayi, bude firji din yayi ya dauko aya, kankana, apple, da sauran kayan fruit ya markade mata su, ya juye mata bayan ya tacce. Sannan ya dauko parsley leaf ya tsinke guda biyu masu kyau bayan ya juye abincin, sannan ya zuba mata miyar a gefe, ya saka mata ganyen nan a saman abincin yakawo gabata ya ajiye mata.
“Oya digging!” Yatsuna fuska tayi tana faɗin. “ban tab’a cin girkin namiji ba!”
“Karya kike domin duk girkin da kika ci kafin muje Keivroto Chef yake yi.”
Tura baki tayi ita ya ƙaryatatta, haka ta cinye abincin, bayan ya gama nasu da Elbashir. “Uncle Elbashir abincin nan yayi dadi, matsalar yayi citta ne dayawa.”
“Ke kin san waye Malik kuwa?” “Maza antaya lomarka, akwai wanda ya zai bada labarin Malik bayan ni ne?”
Girgiza mata kai yayi yana faɗin. “Elbashir sai Shatima.”
“Ni fa?”
“Hmmm! Lokacin muna gidan yari, shi yake dafa abincin gidan tare da Chef!”
“Aha ashe kun jima da Chef din”
“Sosai mana” kamar abin arziki ta zauna ana hira da ita. A ranshi ya ce kafin an jima ta birkice, can ta fara hamma. A hankali ya isa gaban ta, ya dauke ta cak.
“Nayi nauyi fa!”
“Eh ba laifi kan sai flour, ya sa baking powder. Ya kada sai da ya hadu sosai ya fara soya mata a nonstick. Yana zubawa ya koma gefe ya dauko wani karamin tukunya ya zuba sigar ya diga lemon tsami, ya bar shi ya narke sosai, sannan ya kashe wutar, ya barta, ya cigaba da soya fancake yana ganawa ta ce mishi. “Me kake yi ne?”
“Abu ne ina zuwa!” Ya bata amsa, sannan ta nufi wurinta da kayan ya ajiye mata.
Ta zauna tana kallonshi. “Ka sani jin kamar da ban fito ba!” Tun da kuruciyar shi yayi fatan zama kamar mahaifinsa, wurin yiwa mace hidima.
Cigaba da aikinshi yayi ta zauna a kasa ta ware kafa, tana kallon tvn. Kallonshi tayi tana jin wani abu yana yawo a jininta da jikinta,dakyar ta hadiye yawu. Ta koma ta zauna sai da ta cinye ta matsa jikinshi tana jin dumin jikin shi.
Yana sane da ita, musamman yadda take kara shige jikinshi. Janye ta yayi yana faɗin. “Kin ga ni ina fama da basir!” Sake baki tayi ta ce. “Basir!” “Eh!” Kamar tayi kuka haka yake ji, don haka ta kwanta a jikinshi tana kuka kamar wacce aka zane ta.
Dakyar ya lallabata, har tayi barci ba don kome yaki ba, sai don ba mamaki gobe ta narka mishi rashin arzikin, shi mutum ne da yake da mugun taka tsantsan akan mutane ba kowa yake sakewa jiki ba, shi yasa lokacin da ya fara jin ya aureta yayi tunanin haka. Yan matan yanzu basu da kunya, kuma abin da ya guda kenan kada ta rena shi, ya za ayi taga girmanshi har da furfuran. Yayi wanka a gabana dole renin ya kara ta’azara.
A hankali ya nufi dakinta da ita, ya kwantar da ita zai mike ya janyo shi ya ɗan sunkuya. “Ka kwanta a nan”
*Tab’ gobe ki karta min rashin mutuncin!*
“Ina aiki ne idan na gama zan dawo” ya fada mata haka, don ta kyale shi. Yana futa ya sauke ajiyar zuciya, Bashir ya samu ya saka Påñçäkęš a gana yana ciki a hankalin shi kwance.
“Kai dai wata rana sai ka samu wanda ya zuba maka, shinkafar bera a abinci”
“Ya kyauta min! Don bakin hali ina cewa kullum abincin waje muke ci tunda matarka tazo ka daina mana oda sai dai muce na hannunka”
“A da bana tsoron abin da zamu ci, amma a yanzu Shatima niman cutar da makusanta na yake taya zan bude ciki na ci abincin waje.”
“Kai kuma kana tsoron kada mu mutu ko? Bayan ko a kan idanunka ne mutuwa zamu yi balle a bayan idanunka.”

“Kula da kai yafi bada sako, da na ji zafin wani Gara na kiyaye daga kaina.” Haka suka yi ta hira har dare ya raba, sannan suka yi sallama, Bashir ya koma sama, shi kuma ya kashe wutar gidan baki daya, ya haura can samar gidan ya shiga dakinshi na musamman. Computers ne da manya manyan wall TV, na ilahirin titunan garin ne .
Sai wani karamin computer, wanda yake da shi na musamman. Abu ya saka a kunnen shi. “Ya yarinyar take?” “Suna lafiya da kanwar mahaifiyarta!” “Ubanta ya san ina bibiyarta, don haka ka kula sosai.”
“In sha Allah”
Daga haka suka ya rufe laptop din, yana kallon airport ɗin da kuma yadda aka samu maharan. Wayar da ya samu a dakin ya kira wani layi ya ce masa. “ka tafi titin Nelson Mandela, akwai wata bakar Prado. Ka tabbatar min idan ka ganshi ka turo min number motar!”
Bayan kamar minti ashirin, aka sake kiranshi. “Eh na gani, me za ayi?”.
“Ka bar wurin, zan gaya maka yadda zaku yi;”
Daga haka ya cigaba da wasu binciken, shigowar Lalla Salmah yasa shi murmushi, yayi ya ce a ranshi. *Kin kyautawa kanki! Sharrinki zai biki*
Haka ya gama latsa wayar,ya tura musu.
“Kada ku tsaya,kama Shatima ko Lalla Salmah. Ku barsu halinsu zai kama su.”
“Yes sir” fita yayi daga cikin gidan ya kunce wasu masufaffun karanunkan da ya kiwota su da fushi. Suka samu wuri suka boya.
Sannan ya koma dakin Zeeno ya samu tana ta barci, burge shi tayi ya wuce tare da rufe mata kofar. Ya dawo Falo ya kwanta.
Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/23, 1:53 PM] Yan Mata: 30- baki ɗaya barci kaurace mishi yayi ya tashi zaune yana jin wani abu yana motsa mishi ranshi a kan cikin Zainab ɗin. Murmushi me sauki yayi, burin ana gama wannan hayaniyar ya saka Zulfah da Jalilah a gaba da ita ya kai su garin danginsu. Ta haihu a can shima kuma ta koma kano ya ga nashi dangin amma ina ta lalata mishi tsari. Yana zaune a wurin yake nazarin yadda zai bullo mata, domin kuwa baya son wani abu ya a taba ta, ko ya shafe ta.
***
Shatima..
Shi ya dauko Lalla Salmah, yana faɗin. “Na san halinsa sarai, koda yake zuwa yanzu bai san mun shigo ba.”
“Malik din ne bai san mun shigo?” Garin yayi corne kawai ya daki wani me mashin, suka fadi can. Komawa gefen titin suka yi. Suka fito ganin mutumin ya tashi tare da cewa. “Wash! Da sauki zaku iya tafiya, ku dai ku kula da hanya.”
Daga haka ya koma wurin machine din da abokinsa, suka bar wurin. “Yan shaye shaye ne!” Suna barin wurin Shatima ya bisu da idanu. Kafin ya koma cikin motar shi da Lalla Salmah. Suka fara tafiya har sun kusan isa gidan da yake boye.

Motarsu ta bi ta kan abu, take tayar motar tayi wani irin kara, tare da kwacewa a hannunshi. Dakyar yayi ta tafiya yana kokarin sun isa gidan da yake. Amma motar taki bada hadin kai. Dole suka fita tare da Lalla Salmah, suka shiga gudun ceton ransu. Koda suka isa gidan a gajiye suka isa suna haki. *Ku kula da hanya!* Abin da ya dawo kan Lalla Salmah kenan ta ce mishi. “Na gaya maka Malik yana sane da motsin mu, amma kace a’a.”
“Tow taya zan karya miki zuciyarki da zancen Malik, kawai manta da shi amma dole na dauki mataki akan shi.”
Haka suka kwana rai babu dad’i, Washi gari suka tashi domin su fara tunanin yadda zasu cutar da Malik.
Sai dai maganar gaskiya, ba Malik ba ne ya kai musu barazana, idan zai yi ba zai musu da rayuwarsu ba, tab’a abin da suke so yake. Ya gaya musu yana tare da wane.
Ko ita Lalla Salmah, bata san cewa Malik yana sane da boyayyen sirrinta ba, shi yasa take ganin kamar ai bata da wani abu wanda Malik bai sani ba.
Abin da ya faru Shatima ya saka aka musu haka, domin kuwa ya kara cusawa Lalla Salmah ta yarda cewa Malik yana farautar rayuwarsu.
Yaran da suka buge da da saninshi, yayi haka domin ta kara yardan cewa Malik ne, a ta kowani fuska yana son ya lalata alaƙar Malik da kowa.
Tana fitowa taga fitar daya daga cikin Yaran, kafin ya isa yayi tafiyarshi. Ganin yadda take leke ne ya ce mata. “wani abu kike nima?”
“Ina yaran nan da muka buge su jiya, na ga kamar ya shigo gidan nan ne?”
“Kin ganshi ne?”
“Kwarai da gaske na ganshi, kada Malik ne ya turo shi ya mana wani abu?” Ganin yadda take nuna tsoronta a fili yasa ran Shatima b’aci..
“Malik kike tsoro? Bayan gani a gefenki!” Kallonshi tayi sannan ta ce mishi. “Ko ƙarƙashin ƙasa ka shiga, Malik yana iya binciko ka, balle kuma a sarari ni fa shi yace idan ina da zarar hana shi kome na shigo Keivroto kana tsammanin ba zai iya kome ba ne don kare gefenshi?” Tayi maganar ranshi ya kara b’aci ya ce mata.
“Babu abin da zai iya miki, ina tare da ke. Sannan ki daina kiran shi a gabana, matuƙar ina nan babu wanda ya isa kiran Malik.”
“Hmmm! Kana nufin kawai don ina tsoron Malik sai ka da na kira sunanshi? Bayan nasan cewa kai ma karfin hali ne, da zaka ganshi sai ka sake fitsari a wando ka saka a nimo wannan yaron domin Malik be ya saka shi aiki.”
Duk yadda yaso ta manta da Malik ta tsaya su mishi taron dangi taki, don dole ya kyaleta yana me gaya mata duk inda ta shiga bata tsira ba. Domin Malik yana bibiyarsu. Haka yasa ta fara tunanin hanyar da zata cusawa Malik tashin .
Ba tare da shawara da Shatima ba, ta kira taron manema labarai.
Wuce shi tayi tana me daukar wayarta domin kiran yan jarida, yq fisge wayar yana faɗin. “Akwai kawar matarshi nasan zuwa wani lokaci Matar shi zata so su haɗu, zan saka miki number ta, ki kirata ki ce mata don Allah zaki bata sako ta bawa Zeenobia sai ki tura mata, idan yaso hanyar farko da zamu samu Zeenobia ta fito, so nake na kasheta daga ita har cikin jikinta, yadda zan dasawa Malik bakin cikin da bai isa ya kashe mu ba. Daga haka zai kyale mu, ko ya tattara ya bar kasar ko ya gudu baki daya!”
“Amma me yasa baka gaya min tun farko ba? Da nasan da haka yaushe zan tsaya taron masu nimam labarin da bai zama dole su amshi labarin ba, amma kanka a yana ja!”
“Gashi saka min! Number ta!”
Wayarshi ya ciro ya saka numberta, sannan ya koma ya zauna yana gaya mata. Yadda matukar suka girgiza mata ƙwaƙwalwa da wanna labarin sai taji gara ta kashe Malik.
“Idan kuma bamu samu nasarar kashe ta fa?”
“Idan bamu samu nasarar kashe ta ba, zamu yi kokarin raba shi da ita, ni kuma ta wannan bangaren zan tafi na nimo soyayyarta, bayan na kashe cikin jikinta nasan ko ban yaki Malik gaba da gaba ba, Zeenobia zata yake shi, har dai ta ga ta kai shi kasa. Daga nan zan saka ta, niman a raba dukiyarshi biyu a bata rabi.”
“Eh tow idan tana son cikin jikinta fa?”
“Amma dai ban tab’a ganin mara tunani irinki ba, bayan na gaya miki yadda za ayi idan tana son cikin ba laifi ai, sai na taya ta so, na kaunaci dan na cusa mishi tsanar Malik. Mu ga yadda zai ji idan ya rasa uwar da Yaron.”
“Wai wai! Amma wallahi kacika makiri, tow ni meye makomata a garin nan?”
Shiru yayi domin shi duk tsarin shi bata ciki, bata cikin tunaninshi balle har ta shiga tsarin benefic da wani abu da zai samu a tare da Malik, murmushi yayi ya ce mata.
“Zan tabbatar da Party a sauke Malik a baki matsayinsa.”
“Kana nufin daga yar majalisar kasa zuwa Mayor? Gaskiya matsayin yayi min kaɗan. Ka duba dai a bani koda ministan harkokin mata da yara ko, wani matsayin amma wannan Mayor fa?”
A ranshi kuwa yasan za ayi haka, don haka ya ce mata.”saurin me kike yi ki kwantar da hankalin. Zaki isa wurin ai”
***
Tun asuba, ta fahimci ita ɗaya ta kwana a dakin don haka, ta mike zaune tare da nufar ban daki tayi wanka da alola, sannan ta dawo dakin tayi sallah. Tana addu’a ta ji kamshin abincin ya sakata bata idar ba, ta nufi waje, tana zuwa ta same shi yana aikin jan kujera tayi ta zauna, tana hadiye yawu. “Kin tashi?” Gyada kai tayi tana kallon abincin, a nutse yayi ta jera mata, yana cewa. “Zan fita kada ki tafi ko ina, ki zauna a gida, ki duba firji akwai duk abin da zaki bukata kafin na dawo. Please kada ki fita ko kofar gida ne?”
“Gaskiya haka zan zauna ban fita ko waje ba? Ni ina son ganin Hafsy ne!” Share ta yayi yana cigaba da aikinshi, har ya gama sannan ya nufi daki yayi wanka ya sauya kaya, sannan ya fito ya same ta. Zama yayi ya fara cin abincin. Bashir ya sauko ya zauna shima. “Uncle Elbashir ka tambaye shi me yasa ya ce kada na fita?”
“Saboda lafiyar cikin jikinki idan ta ni ne , da ya bar ki a can Demark ki karaci shirmenki” shiru tayi tana kallon Elbashir da yafi Malik daukar zafi.
“Zan fita sai dai na mutu, da abincin.”
“Aniyarki ta bi ki!” Ya faɗa yana daukar abincin.
“Zauna ka ci anan!” Komawa yayi ya zauna, yana cigaba da cin abincin. Nad’e hannunshi yayi a kirjinshi. “idan kika gama Hafsah zata zo yayi miki?”
“Zan fita wurin gyaran jiki da kai!”
“Zasu zo su miki har gida.”
“Tow ni haka zan zauna ban fita ba!”
“Duk yadda kika gani daya ne, amma babu wanda ya isa ya barki ki bar gidan nan. Koda kuwa da wasa ne.”
Ran Elbashir ya ɓaci sosai, don haka ta cigaba da cin abincin yana gamawa Malik ya ce masa. “Ka saka a kawo mata Hafsah ta zauna sa ita kafin kome ya dawo daidai.”
“Kana nufin ta dawo nan da zama?”
“Eh!” D’ago kai tayi zata mishi wani magana yana zuba mata idanu, da sauri tayi kasa da idanunta. Mikewa tayi zata bar wurin ya ce mata. “Idan kika tashi zan baki mamaki! Ni ba sa’anki ba ne da zaki mai dani sakarai. Ni ban yi kama da lusarin da zaki na juyawa son ranki ba, ji gaya min me kike bukata, ba haka kawai kika zo nan ba, gaya min me kike buƙata?” Ya daka mata tsawa, ƙasa motsi tayi tana kallon tea din gabanta, wanda hawaye yake d’iga cikin cup ɗin.
“Gaya min me kike so na miki?” Ya faɗa da murya me amo. Rikicewa tayi da kuka. “Malik!”
“Bar ni na goge mata abinda take ji aranta!”
“Idan na rabu da ke,zan iya moving on, kafin ki zo rayuwata ina rayuwa lafiya babu abin da ya faru. Suddenly bayan zuwanki babu abin da ya canza. If you’re think that saboda cikin jikinki zan zama sakarai you think wrong! Ba zan tab’a beg you da ki zauna da ni ba, domin ko baki zo ba, shirina ne na mai dake wurin dangin mahaifinku.” Saka hannun yayi cikin rigar shi. “Wannan shi ne takamarki! Tun kafin na ganki tun bayan gaya min kina da cikina na ajiye a raina zaki bukaci rabuwa da ni! Don haka nan da sati zan mai daki wurin dangnki. Zan iya zama da mace mara kamun kai da hauka, amma ba zan zauna d macen da bata san darajata ba.
Kaf abokan gabana, sun san ba ni da sauki amma ke kin same ni don na baki fuskar da zaki min yadda kike so, na raga miki ne don Amanarku da mahaifinku ya bani da baki isa ki min rashin hankali na kyale ki ba! Tun kina haukar ki nake bibiyar ki balle yanzu da kika zama me lafiya. Cikin jikinki idan kin so ki gaya mishi ina sonshi rashin mutuncinki yasa na hakura d ku, idan kin so ki gaya mishi na mutu wannan matsalarki ce.”
“Malik yarinya ce!”
“Ba yarinya ba ce, tasan me take yi, ta san me take ji, ta kwaso jiki ta biyo ni domin tana bukata ta, bata biyo ni don ta fahimce ni ba. Ni bana cikin mazan da mata zasu juya. Allah na tuba ko asiri ake yi bana cikin mazan da zai kamasu, domin na tsare addinina da ibadana, baki isa ki min kome ba.
A duk inda zan shiga bana fasa niman taimakon Allah akan kome, ke har kin isa ki min renin hankalin? Bari ki ji da kyau bana daukar reni kuma bana rena kowa, duk wanda kika ji muna takun saka tab’a ni yayi idan bai tab’a ni ba, bana tab’a shi don haka baki isa ba wallahi!”

Daga haka ya mike zai bar falon, Elbashir ya ce masa. “Me yasa ka mata haka a gabana, idan jininta ya hau fa,?”
“Jininta ba zai hau ba, domin tana kuka da bata kuka ba zan gaya mata magana ba, tayi kukanta ya ishe ta.”

Ya bar su a falon, yayi tafiyarshi. “Har ga Allah baki kyautawa. Malik yana sonki amma haka kike ta bashi wahala ban san yadda zan gaya miki ba. Amma ki kula sosai Malik ba abin yarwa ba ne an jima za a kawo miki Hafsy!”
Yana fita gidan su Hafsyn suka tafi aka daukota, tare suka dawo ya koma ciki ya dauki kayan Hafsy ta same ta a daki tana barci. “Lafiya yan mata, saura wata guda azumi! Me kike shiryawa mutanen Al’umma charity House…”
Wayarta ce tayi kara, dauka tayi ta ce .
“Waye?”
“Eh nice ga Zeenobia nan.”
Shiru tayi sai.kuma ta mika mata wayar.
“Yan mata amshi ana son waya dake…….
*Waye zai mutu? Waye zai rayu! Marubuci shi ne Ubangijin labarin shi😁🙄*
Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/23, 1:53 PM] Yan Mata: 31-
“Waye?” Murmushi tayi ta ce mata.
“Mayor!”
“Ba zan amsa ba.” Abin ya bawa Hafsy mamaki kuma tasan yana jinsu. “Ki amsa mana me yasa kike haka ne? A gabana kike nuna rashin girmama Mijinki idan wani ya mishi haka zaki ji dad’i? Wallahi kin bani mamaki sam baki da wayo. Mijinki kike abu kamar baki san darajar shi ba, ai na zata soyayyar da ya nuna miki zai ci albarkacinsshi, gaskiya ba zan iya zama da ke ba, zan koma gaba iyayena yanzu na fahimci dalilin da yasa Abbana kin tarayyata dake ashe baki da hankali ne sam. Yana tsoron na dauki halinki Gara da ban zauna a tare da ke ba.” Tana gama fadar haka ta nufi wurin kayanta zata dauki jakarta, aka bude kofar dakin. Malik ne tsaye rike da wayar a hannunshi.
“Kada ki bar gidan nan, har sai na bukaci haka kin ji!” Gyada kai tayi tana ajiye jakar, ya kalli Zeeno da take zaune tana kuka. “Idan ta gama kukan ga masu gyaran jikin sun zo!”
“Tow!” Hafsy ta faɗa, tana me kallonta. “Kiyi shiru ba inda zani!” Hafsy ta gaya mata, “tow meye laifina kowa sai haushina yake ji!” “Laifinki daya, mijinki ya sauke duk wani nauyin da yake kanshi, ke kuma kin gaza sauke nauyin da ya dace, hakkin girmama shi, dole ne dole ki mutuntatta shi, a gaban uban kowa. Da ana yiwa wani sujada don girmamawa da Allah ya umarci mace tayiwa mijinta, amma me yasa ke ba zaki girmama shi ba? Malik bai da matsalar kome, idan akwai abin da yake jin tsoro ya faru da shi kece yake gudun wani abu ya faru dake.
Bake ba, hatta ni da iyayena Malik ya saka idanunshi akan mu, balle ke da kike uwar danshi.”
Cikin shashekar kuka ta ce. “Tow don Allah me yasa yake guduna? Jiya farkawa nayi na samu baya dakina, wurin waye yake kwana?” Sake baki Hafsy tayi tana kallonshi, kafin ta ce mata. “Wannan kuma laifinki ne, kin ga Zeeno a ajiye maganar son rai, mijinki yana gudun ki sake mishi gwiwa ne ya sa yake gudunki. Taya ma za ayi jiya ki ɗauke hanya ace babu abin da ya hadaku na kewar juna! Akwai abin da kika mishi wallahi!”
“Wai kawai nace ya bar kome mu bar garin nan ne fa!” “Lallai fa, tow ai lamarinki akwai matsala wallahi. Tow sai ya biki dake shi kaurar mata ne ba? Sai ya biki don bai da abin faɗa, namiji ne fa ba ragon maza ba, ki gyara alaƙarku domin yana shirin mai daki Nigeria ce, baki san halin su ba, Baba Abbanki da Umminki, idan kika je waye zai tararaye ki kamar kwai? Waye zai kula dake kamar yar kwai, kin ga wani lokaci muke wasa da Opportunity din mu.”
“Tow ya zan yi?”
“Haka zaki bude zuciyarki, ki amshi mijinki! Kin ga tashi muje a gyara miki jikin sosai!”
“Tow!” Ta mike tana me nufar ban daki ta wanke fuskarta, sannan ta dawo dakin suka fito a tare, a wani Falo na daban aka sauki mutanen, zama tayi suna ta gaisheta. Tana amsawa daga nan suka yi shiru ana hada kayan gyaran gashi da na jikin. Suna gamawa biyu suka zo gabanta suka fara duba gashin kanta, aka warware kalabar. Sannan suka shiga tage gan a hankali tana gaya musu. “Kuyi a hankali akwai ciwo akan bai gama warkewa ba”
“Tow ma!”
A hankali suka dauki wasu mayuka na regular suka shafa akanta, sannan suka saka mata wani hula. Sannan suka bata wani riga ta shiga ban daki ta sauya, ta kalli cikinta da ya dan fito. Ta fito, aka fara gyara mata jiki, ana mutjeta. Mutum biyu suna hada lalle baki da ja, an fara tun karfe goma. Kafin karfe biyar sun gama kome tass ta fito shar amarya ga lalle ga gyaran jiki. Sai kamshi take tana kara jin wani iska yana shigar ta. Bayan tafiyar mutanen ta shiga kitchen bisa jagorancin Hafsy suka fara girki, wanda aikin Hafsy ne. Ita banda daba da jagaliyanci me ta iya. Bata iya kome ba.
Haka suka gama tuwon shinkafa miyar kuka, suna saukewa su Malik suna shigowa. Ruwa da juice suka basu. Kafin ya riko hannun Zeeno yana faɗin. “Hmmm! Hafsy baki mata yar fantin nan da yake mai da mace aljana ba, maza a karasa aikin na biya kuɗin da hujja!” Murmushi suka yi, ta riko hannunshi suka. Shiga dakin su. Idanun Elbashir kur akan Hafsyn bai san me yasa yake son dumb dinta ba, amma maganar gaskiya ta hadu. “Me kwalliya ba za a raka ni ba ne?” Da sauri ta d’ago kai ganin yana kallonta yasa tayi masa ta sunkuyar da kai tana kokarin danne kunyarta.
“Ok sai an daura zaki taya ni wanka?”.da sauri ta wuce falon da suka yi kwalliyar nan. Ta rufe kofar yana me jin kamar ta nutse. A can kuwa dakin Malik yana sane yaki yarda yayi wani abun da zai saka ta fara gwara mishi kai, ya wuce ban daki zai tara ruwa ya samu ruwan yana taruwa domin tana hada mishi ruwan ne, ganinshi a bayanta, yasa ta juya. “Sannu da ƙoƙari!” Ya fada yana matsawa daga gefenta. “Guduna kake?”
*Zata fara!* Ya fada yana kallon yadda take raurau da idanu. “Me zan miki!”
“Na gaji! Marana ciki yaƙe”
“Gaya min gaskiya zan baki mintin maza, kina kewar abin ne?” Dunkule hannun tayi tana dukar kirjinshi, tare da bubuga kafarta a kasa. Janyota yayi ya haɗa da jikinsa. “Gaya min me maran yake yi ni kuma zan baki magani!” Yayi maganar can ƙasar kunnenta. “Hmmm ciwo yake min! Sai naji ina son kwanciya a jikinka!”
“Ok zo muyi wanka” a hankali ya zamar mata da rigarta kasa. Ita kuma tana cire mishi botirin rigarshi. “Gyaran gashin yayi fa!” Ya faɗa yana sumbatar wuyarta. Tana cire rigar ya sake a kasa, takai hannu zata cire belt din ya tayata. Tana kai wandon kasa, ya riko hannunta ya daura kan wurin.
Da sauri ta cire hannunta. Murmushi yayi ya ce mata. “Ni dai a tab’a min” kunya tasa babu shiri ta rufe fuskarta da kirjinshi.
“Maganar gaskiya a kula ni!”
Ya kai hannu yana me fitar mata da shi, yana faɗin. “Kamar yadda ake min rashin kirki, shima a mishi kirki.” Ƙasa motsi tayi domin abubuwan da yake mata kamar ba shi ba, wani irin kunya ta kama ta, shi bata kama shi ba.
Cak ya dauketa ya sakata a cikin ruwan suka shiga wanka, koda yake ba wankar aka yi ba, shi ne ya janyo ta jikinshi. Amma maganar gaskiya a tafashe yake kamar zai fasa ihu. Duk yadda yaso ta mishi wani abu, kasawa tayi domin wani irin kunya ya hanata yin kome, shi kuma.wayayyen mutum ne da yake son harkan karuwanci.
lokacin da sukq gama wankar ya ta riga shi fita, don haka ya fito babu towel, sake baki tayi tana me dauke kanta a kanshi.
“Kalle ni!” Kin kallonshi tayi, ya janyota jikinshi. “Wallahi ba zan iya kallonka ba ”
“Ni ina son haka, ina son karuwanci. Ina son mace da ta iya karuwanci, wacce bata kunya ko shayin kome! Don Allah ki min karuwanci shi nake so”
. “Ba zan iya” ta faɗa kamar tayi kuka, shiru yayi yana kallonta, sannan ya ce mata. “Shi kenan kada kiyi kuka.” Ya nufi wurin kayanshi, kasa kasa ta kalle shi, sannan tai maza ya rufe idanunta.
Haka suka fito rai ba dadi, bayan sun ci abinci shi kan kaɗan yaci ya shiga aikin gabanshi, Hafsy ce ta kaiwa Elbashir na shi, tun da ta kai bata fito ba. Har wurin tara. Tana can Elbashir yana matseta, ganin Zeeno tana gyangyadi, Hafsy ta fado mishi rai, da sauri ya haura sama. Tun kafin ya bude kofar yaji muryanta tana kuka sama sama, shi kuma Elbashir sai nishi yake yana rokonta don Allah ta bari ya shiga na zai yi release ba. “Hafsah!” Ya kira sunanta da karfi, dole Elbashir ya sake ta, ta rarumi kayanta ta saka jikinta yana rawa. Ta bude kofar kamar munafuka.

Ta fito, ya rasa me zai mata ya wuce takaici daka mata tsawa yayi ya nuna mata hanyar kofar Zeeno. Shiga dakin yayi ya same shi yana kokarin maida wandon shi.
“Ka bani mamaki, idan kana son aure ai ba zan hanaka ba, asalima kai ne ka nuna baka bukatar auren me yasa zaka lalata mata gobenta? Kai babu me zarginka amma ita har karshen zuriyarta sai ya tab’a. Me yasa? Kada ka kuma min haka domin zai fusata nayi maka abin da zai dame ka.”
“Kayi hakuri Malik wallahi ban san ya aka yi ba, ban tab’a kusantar zina ko sai yau don Allah kayi hakuri wallahi shaidanan.”
“Kada ka sake ka ji!” Gyada mishi kai yayi, fita Malik yayi ya samu Zeeno a inda ya barta sai zare idanu take.
“Kira min Hafsy!” Tashi tayi ta shiga daki, ta ji muryan Hafsy na kuka, buga ban dakin tayi, tana faɗin. “kizo yana kiranki!”
Bata amsa.mata ba, ita kan fitowa tayi wurin Malik ta zauna, tana son tambayar shi, yaƙi bata fuska. Lokacin da Hafsy ta fito kuwa rufe idanu yayi ya ci mutuncinta, tayi ta kuka, sannan ya ce ta shiga dakin Zeeno ta kwana. Daya dakin da yake gefen na Zeeno ya shiga ya kwanta, kamar mayya ta shiga dakin, tare da kallon kome na dakin kamar nata, amma wannan kamshin imperial majesty yake tashi a dakin.

Zare rigar jikinta tayi, tana me shiga ban daki, ta fito daure da towel. Tasan idanunshi biyu. Don haka ta koma bayan shi ta kwanta, tana sauke ajiyar zuciya. Sakala hannunta tayi tana faɗin. “me ya faru ne?”
“Babu ruwanki!”
“Tow!” Ta fada tana sauke ajiyar zuciya, shi kuma kirjinta ne da yake dauke da dumi yake fisgarshi. Ya juya a hankali ya rungume ta. Sumbatar goshinta yayi yana jam mayafi zai rufeta.
“Ni ba zan yi barci ba!”
“Ok kiyi gadina.”
Wani sakaltacen kuka ta saka mishi, babu shiri ya shiga wasa da kowani gurbi me dauke da anntenal sadarwan jikinta, ba tare da ya shirya haka ba, ya shiga bin jikinta da wani irin kulawa tare da ajiye kome a bangaren muhallinshi, Malik yayi kewarta wani boyayyar ajiyar zuciya, yake saukewa a lokacin da mahad’a rayuwarsu. Ya haɗe da juna, wani gigitaccen yanayi me fisgarwa tare da tafiya da al’amarin juna, shi ya shiga ratsa kwakwalensu.

Yayinda zukatarsu ya kai kololuwar mannewa juna, gaggarumin chemistry, wanda babu wahalar solve da solution, hatta theory sai da suka solve shi, a wata duniyar da biology da Physics bai isa samun mafakar siyasa ba, shi kanshi Malik baya konkwanto akwai sirri na musamman a tare da ita, musamman mace me juna biyu. Yayi hakurin kai zuciya nesa da ya iya sarrafa muradinshi, inda yayi ta gurzanta a yanayin da bata isa fahimta ba, sai har an fahimtar da ita, ya kai matsayin da kusan a tare suke sauke wahalallen numfashi, zuciyarsu tana beating a tare, kaunar da take jibge a zukatarsu tana kara samun mafakar siyasa. Basu an karar ba, sai da garin ya kara sanyi da wani irin duhu me fitar da labarin dare, sun kai matakin da dole suka hakura da junansu. Yana kara rungumeta.
Yana jin saurin bugun zuciyarta, Hakazalika tana jin bugun nashi, kara narke mishi tayi tana jin wani abu na zuba a jikinta,yayin da take jin wani suuuuumm a kasarta. D’ago kai tayi ta kama habbarshi ta shiga tsotsa.
Dama yayi tunanin haka, gajiya ta mata yawa ba takai yadda yaƙe tunani ba, kara rungume ta yayi ya shiga, mata aikin karfi wanda yasa ta zare idanu, tuni ta fara sake abun da ya jima yana damunta. Tana sauke ajiyar zuciya, jikinta ya sake kamar bata numfashi…..
*Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/23, 1:53 PM] Yan Mata: 32- dakyar ya lallabata tayi wanka, suka kwanta. Wani irin gajiya ce ya taru mata, barci me nauyi yayi gaba da ita, bata san wani duniya take ciki ba, sakamakon shi da ya kasa rintsawa. Idan har zata cigaba da bashi kulawa haka, yasa rayuwarshi zata fi haka sauyawa, amma yarinya ta haɗa mishi jagwal, rungumeta yayi ya baya, suka cigaba da barcinsu. Da asuba ma dakyar ta tashi bayan ya shirya suka bar gidan, domin wanka yayi ya shirya cikin shigar kamala.

Abin burgewa haka ma Elbashir, a tare suka shirya, shi shaddar shi fari sol. Suka nufi gidansu Hafsy. A nan suka yi Sallah asuba, ana idarwa aka daura auren Elbashir da Hafsy. Duk da ba a samu labarin akan lokaci ba, amma kuma an taru a masallacin, mutane dayawa sun yi murna domin ana daura auren suka shiga rabon kuɗi. Kafin suka shiga wurin Mahaifiyarta, suka gaishe ta sannan suka fito. Gidan suka dawo suka saka Hafsy da Zeeno a gaba. Aka kai su gidan su Hafsy, Mahaifin Hafsah kuwa don jin dadi kamar ya rungume Zeeno, don murna.kamar ya kwantar da kai ta hau kanshi. Dake basu san me ke faruwa ba, don haka aka saka su a duhu.
“Mama lafiya kuwa?”
“Aunty Hafsy kin zama amarya yau!” Kallon juna suka yi, suna masu maida hankalinsu kan Adi, “kamar ya?” Dariya yayi yana fitar da sabin kudi, ya cigaba da cewa. “kun ga wannan mijin Aunty Zeenobia ya raba mana, bayan an daura auren Aunty Hafsy da Uncle Elbashir!” Ya kwasa da gudu ya bar dakin. Safe kirjinta tayi, “Ni!” Sai kuma ta rufe dakin tana tana me fadawa gado. “Omo nice matar Elbashir?” Sai kuma ta fashe da dariya, tana me sake kallon Zeeno da tayi sororo.
“Me ya faru jiya da Mayor ya miki faɗa?”
Dariya tayi sosai, kafin ta ce mata.
“Jiya ne muka kusan cinye juna” ta faɗa tana kare fuskarta. “Meye?” Kunnen Zeenobia ta nufa ta ce mata. “Ya nima kuma na bashi ya tab’a shi ne zai wuce iyaka, Mijinki dake dan Aljanna ne ya zo ya nima mana me gaba-daya. ”
“Ke yanzu Hafsy sai ki bar shi ya!”
“Ai ni kaina ba a tukunya yake ba, yanzu yarinya zaki ga yadda ake bura uba, domin sai kun bar mana gidan nan, domin amarci zamu ci!” Buga kofar dakin yasa ta yin shiru, suka bude kofar. Wani katon kula Mamar Chu-chu ta bata, tana faɗin. “Tun daren jiya aka gaya mana, shi ne yau na kawo miki dahuwar kaza!”
“Taci a hankali dai, domin wallahi ba kome a cikin auren sai aiki daya.” Zeeno ta fada tana hararan Hafsy.
“Na shiga uku ba zan ci ba” ta ajiye kular.
“Ke ki rabu da Zeeno, da babu abin arziki shi wanann kunshin gaban rigarta ita ta kunsawa kanta?” “Ni ba haka nake ba!” “Ai dama na san ba haka kike ba, yasa na gaya miki oya maza wuce ki ci ki rabu da Zeeno kada ta yi spoiled din tunaninki.”
Tana fita Hafsy ta zauna ta cinye tas, ta ciro kayanta ta fara fito da wasu kayan matan, Indonesia ta fara sha tana duba expire date dinsu.
“Hafsy baki tsoro ne?”
“Ina tsoro mana, amma duk abin da zan ji dadin daren farkona wallahi zan sha. Babu wanda ya san me gobe zata haifar.”
“Amma Hafsy!”
“Kin ga ina sonshi, koda Malik bai hada mu ba, ban tab’a mafarkin samun wanda ya kai shi ba, bai tab’a mik maganar banza ba, jiya ma abin da ya faru kuskure ne, so don haka zan gyara jikina ni ba sakarya ba ce da zan bar mijina a banzace!”

“Hafsah magana kike gaya min?” Zeeno ta tambaye ta jikinta a mace, “A’a kawai na gaya miki abin da ba zan iya ba ne, duk abin da zai saka shi farin ciki ina maraba da shi”
“Yayi!” Ta faɗa tana me kwanciyarta, sannan ta ce mata. “Nima ba kin Malik nake ba, ba kuma sonshi ne bana yi ba kawai akwai abin nake dubawa ne, idan wani abu ya same shi, nice zan yi maraici har karshen rayuwata, idan wani abu ya samu cikin jikina, zan ta danasani har mutuwata. Idan nace bana sonshi ai nayi karya, sannan cikin jikina ma ya isa ya tabbatar da irin son da nake mishi!”
“Ai ba cewa nayi baki sonshi ba, wulakanta shi kike a gaban kowa!” “Karya kike Hafsy, baki kai, ki gaya min magana ba, baki isa ba. Har yaushe kika kai wacce zaki gaya min magana!”
“Ai matsalarki kenan, rashin fahimta. Wannan rashin fahimtar da nutsuwa a magana zai kai ki inda zaki yi kuka da kanki mtseew! Banza mahaukaciyar wofi! Wacce bata san darajar kanta ba, ana gaya miki abu kina wani kauce hanya!”
“Ni kike gayawa Magana?” Ran Zeeno yayi bala’in b’aci. “Anga miki, me zaki yi wacce bata san darajar aurenta ba! In sha Allah sai Allah ya kawo wacce zata rabaki da Malik, kin zata zan kyale ki ne don kawai mazajen mu abokan cinikayya ne? Idan kin so ki duba wannan sakon, na boye ne babzan gaya miki ba, gashi ki je ki ta tsanar mijin naki mahaukaciyan banza”
Yadda ta ajiye matar wayar ya saka jin kamar ta rufeta da duka.

*Ina son ki bawa Zeenobia wannan sakon, ta karanta domin na fahimci mahaukaciya ce ta gaske, mutumin da ya shiga rayuwarta da take dauke da cikin shi. Shi ne wanda ya kashe iyayenta. Don haka ya rage gare ta ta zauna da shi ko ta dauki mataki! Idan kina ganin karya ne ta tambaye shi.*
Wani irin rawa jikinta ya dauka, tare da jijjiga me bala’in tashin hankali. Bata iya fahimtar me kome, ta zube a wurin daidai lokacin da aka ɓalle dakin.
“Hafsah me ta miki da zafi kika mata sakayya haka? Me Zainaba ta miki da zaki bita da sharri haka.
—- kafin nan, bayan zuwan su gidan Malik yana hanyar zuwa office din yan sanda. Aka kira shi a waya. Daukar wayar yayi ya duba yana kallon Elbashir.
“Lalla Salmah ce!”
“Dauka mu ji me zata ce!”
“Dauka yayi ya saka a kunne!”
“Na turawa Matar Elbashir sakon da zai kara muku, kaunar juna kai da Zeeno dinka. Kayi fatan ta haifi cikin jikinta lafiya!”
Wani irin taka birki Elbashir yayi ya juyar da kan motar, saboda a handfree wayar take. Lokacin da suka isa ai sun same Safina Maman Chu-chu a tsaye ita da iyayen Hafsy. Dukar kofar Elbashir yayi, yaki budewa, cikin fushi Malik ya daki kofar dakin yayi da kafa, budewa yayi ya hangota kwance. Ita kanta Hafsy din a razane take. Bata san me ya shiga kanta ba, shiga dakin Elbashir yayi ya dauki wayarta ya shiga duba inbox dinta. Kudin da ya gani ya bashi tsoro.
“Kuɗi suka baki kika fada mata haka?” “Ina sonki da aure da kome, amma soyayyar da nakewa Malik!”
“A’a Bashir!”
“Wallahi ba zan zauna da ita ba, domin zata iya kashe mu. ”
Ya juya ya kalli Mahaifinta. “Bani da kowa sama da Malik! Dangina suna can wata duniya Malik shi ne dangina. Malam kayi hakuri ba zan iya zama da yarka Hafsah ba, ta zauna kafin na yanke hukunci.”

“Wayyo Allah na, don Allah ka rufa min asiri.” “Allah ya wadaran halinki, hankalinki ya kwanta sai ki cigaba da zama wallahi ba zaki tab’a jin dadinmu ba” asibiti suka tafi da Zeeno. Ba karamin wahala ta sha ba, domin cikin jikinta so yayi ya fito akai ta mata allurai dole ya tsaya. Domin wa’adinshi bai kai ya fito ba. Ya kira Ummi ya gaya mata, sannan ya kira Jalilah Zulfah da kanshi ya daukar mata excuse a wurin aiki.
Kwana uku tana barci domin jininta yayi mugun hawa, dukkansu suka iso. Suka saka ta a gaba, kamar zasu cinyeta. Sai ranar na hudu ta farka, Malik na gefenta. Kallonshi take da dukka zuciyarta, sonshi take kamar zata yi hauka, hawaye ke bin idanunta cikin tsananin kauna. Amma jinin iyayenta ba zai tafi haka kawai ba. A hankali ta janye hannunta daga na shi, ta juya mishi kai.
“Sannu Zainab” kallon Jalilah tayi, sannan ta juya ga Ammyn da Zulfah, haki ta fara tana miƙawa Zulfah hannu. Da sauri ta isa wurinta. Tana haki da kyar ta ce.
“Ki ɗauke ni daga wurinshi!” “Ki nutsu ayi fama da lafiyarki!” “Ya tafi bana son ganinshi!”
Ta faɗa da mugun ƙarfi, tana haki da tari. Fita yayi suka tawo da likita, allura aka kuma mata. “ku bar ta huta don Allah! Kunsan ba ita ɗaya ba ce sannan tana ganinku hankalinta zai tashi.”
Fita sukayi, sai dare ta kuma farkawa. Jalilah da Ammyn ne a wurin, da taimakon Allah da su, suka mata wanka, ko tsayuwa bata yi. “Ammyn!”
“Na’am!” “Ku mai dani wurin dangin Abban mu”
“Amma kya bari ki samu lafiya ko?”
“Ammyn idan na tafi can zan samu lafiya!”
Suna fama da ita, ya shigo tana had’a idanu da shi. Ta fara haki tana nuna shi da yatsa. Tana son magana haka ta kasa a hankali suka fahimci, bakinta yana shirin komawa gefe, “ka fita Malik!” Jalilah ta tura shi waje, tana kara cewa. “Ka kira mana likita!” Ko kafin su iso, yanayin da ba ason ta shiga dole ta fara shiga. “Me kuka mata?”
“Ni ta gani shine ta shiga wannan halin!”
“Don Allah ka daina zuwa! Zamu rike ta, idan cikin ya kai wata bakwai zamu cire shi. Saura wata guda ne, ka taimaka a cire cikin lafiya.”
“In sha Allah” ya fada yana me tafiya, idan hankalin Malik yayi dubu ya tashi, Elbashir hauka ne bai yi ba, amma har ga Allah yaso sake Hafsy. Malik ya hana shi ya ce ai itama ba laifinta bane, ba kowa bane yake da irin zuciyarshi, wani da kudi ƙalilan za a sayi tunaninshi. Malik yayi hakuri amma a wannan karon cewa Elbashir yayi dan barshi na kwana biyu, baya son hayaniya.
Tunda ya tattaro kome na shi ya dawo Waterfall ya zauna, kome da yake tafiya yana ji a bakin Jalilah. Ya tabbas sun yi nasarar wurga shi cikin kadaici. Bashi ga tsuntsu ba shiga tarko.
Yana zaune idanunshi akan wayarshi, hotonta ne da ya dauka, kafin ta zo Keivroto. Shatima ne ya kira shi. Ya dauka sannan ya ce mishi. “Ka tattara ka bar garin nan kawai, idan ba haka ba, shima cikin jikinta bai tsira ba. Sai nayi draging dinka to the hell.”
Dariya Malik yayi ya ce masa.
“Shi yasa ka nace sai ka ci dukiyar da baka san lokacin da aka tara ba ko? Ka saka a handfree domin Lalla Salmah ta ji, kin kyauta sosai. “Arwah da tana nan lafiya lau, kamar yadda kike boyewa duniya kunna tv kusha kallo lafiya, Shatima ai ka makaro, yanzu zaka ji bugun kofa. An kama yarka da hodar iblis.. ban san me yasa ka nace sai ka tab’a ni. Ita kan yarka bata cancanci samun uba irinka ba, yanzu zaka samu sallame manyan baki, zaka kamo inda ka fito a can zaka kare rayuwarka Idan na kyale ka kaci banza amma tabbas zaka rayu kana niman mafita kana jin labarina ina raye! Escape before su kama ka! Dama na kara baka domin rayuwa idan babu kai ba zan tab’a jin dadi ba. Ka sani zakai ta gudu ba dare ba rana, domin kare rayuwarka. Ni kuma na mamaye Keivroto daga cikinta har wajen ta. Shatima kenan ba fada da ni bane kwana mita, ba zan yi farautar rayuwarka ba, amma zan saka maka jin kamar ina bibiyarka. Zaka rayu kana kara jin ina bibiyarka.”
Ajiye wayar yayi yana murmushi, baya son hayaniya ko wani abu ya lalata tsakaninsu, amma dole ya hakura da Shatima.
Kuma yasan idan yadda ya tsara ne, ba su kama shi, zai ta jiranshi har ya kawo kanshi.
Lalla kan baya tunanin zata waiwaye shi.
****
Acan kuwa labaran da aka fara nunawa, yarta Arwa, da tayi fama da jinyarta laka aka nuna. Tare da cewa.
“Boyayyen sirrin Lalla Salmah”
Kafin aka fara magana kanta, bata iya sauraro ba, ta shiga hada kayanta. Zata bar gidan domin bata san yadda Shatima y kare da Malik ba, tana fitowa Yan sanda suka yi gaba da ita, tare da kin gaya mata inda zasu kaita. Domin rufe mata fuska suka yi, suka bar gidan da Ita.

Shatima kuwa gudu yayi ta yi, domin ceton rayuwarshi.
*Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/23, 1:53 PM] Yan Mata: 33- Yasan Shatima zai ta fatan ya kashe shi, zai yi fatan ya mutu ya huta shi kuma ba zai kashe shi ba, ba zai mishi kome ba, zai bar shi a raye domin fuskar ukubar rayuwa, zai kare rayuwarshi yana gudun da bai da karshe, Lalla Salmah ba zai kuma bin ta kanta, domin bai da lokaci na kulata.
Haka yasa shi zama strong da facing rayuwarshi da Zainaba. Baya wurin a zaune amma baki daya rayuwarshi yana tare da ita, bai san haka yake son lafiyarta ba sai da wannan abin ya faru kara jin lallai yana son ta haifi cikin jikinta lafiya lau. Don haka zai ta jiransu, har zuwa lokacin haihuwar abin cikin.
***
Wasa-wasa barci ya zama shine abinda yafi fa’ida a rayuwar Zeeno kodan cikin jikinta,da ake son rabata da shi few weeks.
Amma ana bukatar kafin ayi aikin ta farka, ta samu walwala yadda za a cire Babyn da koshin lafiya. Haka suke fata domin Zulfah har ta kira dangin Babansu ta gaya musu halin da ake ciki kuma Alhamdulillahi ya gaya mata ana kan shirin tarbansu, haka suna yawan kiranta su ji halin da Zeeno tace ciki. Haka ɓangaren dangin Mamansu na Maiduguri kuwa, ana saka ran za aturo kanwar Mamansu, daga can don har ana sa ran zata taso nan da sati daya ne.
Ba ciki daya suke ba, ƴaƴan mata ne, duk da Jalilah tana kokari. Amma suna bukatar wacce zata zauna da ita. Dake tana barci Malik yana yawan kiransu ya ji halin da take ciki, bayan nan babu wani abun da yake kuma kira yaji, amma ana kashe kudi, domin ko inda suke zaune dai an kashe kwantar da wani mara lafiya, ita ɗaya ce a ward din sannan an zuba jami’an tsaro, kamar ana faɗin shugaban ƙasa.

***
Sai da ya kwashe kwana biyar yana gudu, koda yake yana cikin Keivroto. Duk abin da yake tafiya duk yana sane, amma bai da ikon fita yayi yawo.
Katin bankin shi ma, wani ya bawa ya ciro mishi kudi me shegen yawa, yana huci ya ce. ” A ina kasan zaka samu min mahaya masu kashe mutum domin kudi?” Kallonshi yayi sannan ya ce masa.
“Kayi kokarin barin garin nan, zuwa wani wurin ba zaka rasa ba. Amma nan zai yi wuya ka samu domin suna yiwa Malik biyayya babu me maka wannan aikin!”
“Taya zan tafi bayan ina son ganin bayan Malik? Gaya min ina zan shiga bayan Malik ya mamaye min dukiya ta!”
“Kayi nisan kiwo, yadda babu me gane ka, ai ja da baya ga raggo ba faduwa ba ne, sabon shirin tunkarar makiya ne. Nasan zaka yi nisa kuma zaka dawo domin fansarka!”

D’ago kai yayi yana kallon mutumin kafin ya ce . “Zan tafi kuma zan dawo, amma dawowar ba zai zama me alkhairi ba, zan dawo na kashe kowa domin na rantse sai na saka kowa a cikin halin ni y’asu ” sannan ya kwashi abin da zai iya amfani da shi na kudin, sauran ya barwa mutumin yana tafiya yana surutun zai dawo, sai ya ga bayan Malik da yasa shi rayuwa a titi kamar ƙare, ko ta yarshi baya ji, don ma Malik yasa an sake yarinyar an mai da ita wurin familyns Uwarta, tare da kanwar Mamanta, domin ba yason ya gayawa Yarinyar abun da Ubanta yake aikatawa, ko wanda yayi mutuwar mahaifiyarta, baya ganin baya cikin tsarinshi ya lalata dangantaka tsakaninsu domin cimma manufar shi, shi ba ya tunanin haka, asalima da ya saka aka sake ta, kiranta yayi ya mata fada, da ta nutsu ban da rashin ji da rashin da’a. Yana son kafin wani lokaci ta fitar da miji ya mata aure ya gaji da ganinta, bata iya cewa kome ba, sai ya ƙara mata nasiha sannan ta ce mishi. “Wai da gaske Abbana ya cutar da kai?”
“Wannan tsakaninmu ne, idan har kika shiga tow kin yi shishigi” ya fada cikin rarrashinta. Bayan sun gana wayar ya ajiye, yana nazarin yadda zai bullowa matarshi domin bai san yadda zai yi da ita ba.
***
Lalla Salmah.
Bata taɓa zaton Malik zai iya zakulo abin da take boyewa ba, asalima gani take kamar ita ɗaya ta san sirrinta babu wanda ya isa ya san sirrinta. “Ku kira min Malik.” Ta faɗa da mugun ƙarfi, tana zare idanu domin inda aka kawo ta, bata tsammanin sun san Allah. “Nace ku kira min Malik!” Babu wanda ya kulata, ganin zata tara musu jama’a. Aka office din MD na hukumar kare hakkin dan Adam, “Sir Lalla Salmah ta ce a kira mata Malik” shiru yayi kafin ya ce. “Ok” kiran Elbashir yayi.
“Yallabai Elbashir, Lalla Salmah tana son magana da Malik!”
“Zan zo amma ba zata samu ganin shi ba, ku kyale ta.”
“Tow Yallabai!”
Ya lashe wayar yana kallon mutumin, “Malik ba zai zo ba, amma P.A dinshi zai zo, ka kyaleta abin da ta aikata shi take girba.”
Sai bayan one hour, ya iso office din. Ya sa aka fidda ta, ya zuba mata idanu yana kallon yadda tayi buzu buzu.
“Sati Daya kawai kika yi, kamar wacce ta shekara a daure?”
“Ka saka wancan dan iska ya sake ni!”
“Wa kike magana?” Ya tambaye ta a izgilance. “Wancan coward” murmushi yayi ya ce mata. “Ke kuma me zan kira ki? Monster Mother? Ni ina da ja akan Maidah anya ke kika haifeta? Ni ban san kome ba amma Malik yasan kome, ina saboda Sheikh ya musanta Maidah ba yarshi ba ce, kika rabu da shi kada ya gano yar shi ta asali!” Ba zata maganarshi ya zo mata, kamar ta fashe da kuka. “Kin san inda Shu’iba yake gaya mana!”
Dariya tayi sannan ta ce mishi. “Ba zan faɗa ba, ba zan gaya muku ba.”
“Kyale ta Bashir, an gaya min inda yake, ba sai ta faɗa ba.”
“Malik ka saka a sake ni?”
“Ki gaya min ina iyayen Maidah suke? Waɗanda kika raba su da yarsu?”
“Ban sani ba, ba zan tab’a gaya maka ba. Koda zaka kashe ni kana raya ni ba zan faɗa ba.”
“Ok! Kin ce kina son gani na?” Cikin takaici ta ce . “Ba zan amsa ba, sai kazo ba karenka zaka turo min ba!”. “Ok Bashir dismiss!” “Ok Malik!” Daga haka ya mike ya zuba mata idanu. “Idan ban da zuciyar Muslunci, da zuba miki harbi zan yi har sai kin mutu, amma na kyale ki. Kowani mutun yana farincikin rayuwarshi da aurenshi ni kin min sanadin da narasa wannan farin cikin. Shaidaniyar banza.”
Ya fice daga dakin, cikin d’aga murya ta ce mishi. “Baka tambaye ni yadda aka yi na samu, yarinyar zaka aura ba? Baka tambaye ni yadda aka yi na ja ra’ayinta ba? Shin baka son kasan yadda yar matsiyata ta sayar da yardanta da Amintarta? Idan har ina da hanyar da zan shiga jikin na kusa daku, gaya min ai kashe ku baa abu me wuya bane, saboda kowannenku nasan inda karfinshi yake, sannan bana jin zan iya kyale Malik ya saka idanu, tabbas sai ya amshi hukuncin da ya dace.”
“Ki godewa Allah, Malik ya hana ni aikata kome, da na miki abin da zaki bukaci gara ki bukaci mutuwa da rayuwa!”

Murmushi tayi ta ce mishi. “Ba zan kula dan kwaikwayo ba, zan kula zaki ne idan ya shirya zama dani!” “Baki yi wannan isar ba, baki kai wannan me isar ba, zaki kare rayuwarki a nan babu me cetonki!” Daga haka ya ficce daga cikin office ɗin, tana ganin ya fita ta fasa ihu, tana maganganun banza kamar mahaukaciya.

A hankali ta bude idanu tana kara
, har ta bude baki daya. Zulfah da Ammyn ta gani suna magana kasa-kasa, dafe goshinta tayi, tana faɗin. “Wash Allah na?”
“Zainab kin tashi ne?” Gyada kai tayi, fita Ammyn tayi ta kira nurse, ya duba ta. Sannan ta cire mata karin ruwan.
“Ko zaki cire mata, roban fitsari ne?”
“Ok” daukar hand glove tayi, ta cire mata, atana mata sannu,, ana cire mata ta ce. “Zan yi bayan gida!” “Tow muje!” Ta wuce da ita ban daki, sai da ta gama ta kuma tara mata ruwa tayi wanka, tana faɗin. “jikina ciwo!” “Sannu kinji!” Gyada kai tayi, Ammyn tana kallon yadda kafaffunta suka kumbura, tausayi ta bata baki daya ta fita ta hayacinta. Kamar ba ita ba, suna fitowa sallah ta gabatar sannan ta koma ta kwanta tana hutawa don ta gama gajiya, abincin Zulfah ta zuba mata, ta tashe ta. Tana ci tana mata hira. Har suka gangaro kan hiran iyayensu, kuka Zeeno ta fara tana faɗin. “Na zata idan yana kasuwancin shi da cinikayyar rayuwar mutane, ba zai tab’a saka iyayenmu a cikinsu ba, na tattara rayuwata na danka mishi ashe shi nashi rayuwar, ashe ba haka ba ne shi nashi rayuwar kawai ya kashe ya hana kowa magana.”
“Kin ga yanzu baki da lafiya, ko don abin cikinki, ki hakura ki samu lafiya sai mu san me zamu yi za a turo Aunty Yagana daga Nigeria tazo ta kula dake, amma nace musu subarta akwai Mommy Jalilah, ita zata kula dake, shi yasa basu zo ba, ana miki aikin sai mu tafi can ko!”
“Ba zan jira sai anyi min aiki ba, kawai ku mai dani wurin danginmu”
“Zainab kina da matsala, ki bari a fara ji da lafiyarki sai a san yadda za ayi kinji”
“Wallahi ba zan zauna a garin da Malik yake ba, kawai ki fita ki gaya musu a sallame ni!”
“Zeenobia ki yi hakuri mana, kafin a miki aikin!”
“Wallahi ba zan zauna a garin nan ba, kawai ku mai dani, wurin danginmu.” Yadda ta tire da bala’in rigima yasa suka nimo Malik akan lokaci, tunda ya shigo ta zuba mishi idanu, kafin ta janye nata daga gare shi. “ka sallame ni,”
“Ba zan iya sallamarki ba, ki nemi wata alfarman banda ita.”
“Ka sake ni domin ba zama zan yi da kai ba, rayuwata da abin.cikin jikina yana da muhimmanci a rayuwata da shi, bayan nan ban sanka ba, ban san waye kai ba. Na had’aka da Allah ka kyale mu daga ni har shi ba zamu kara waiwayarka ba don Allah!”
“Don Allah, kada ki min iyaka da abinda nake fadi tashi domin na rayu. Nasan illar kadaici, idan idan kika raba ni da shi zan shiga tasku!”
“Na maka adalci ne, na bukaci ka nisanta kanka da mu, idan kuma kana son a rasa mu gabakidaya zan hakura da nawa rayuwar mu tafi inda zamu huta, shawara ya rage gare ka ”
“Yanzu Zainab hukuncin da zaki yanke min kenan, na rabani da ke?”
“Shi yafi dacewa da zamanmu, a duk lokacin da na tuna kai ka kashe min iyayena. Zan ji kamar na kashe ka, amma idan na fahimci girman rabon da yaƙe tsakaninmu ya wuce na aikata abin da zai saka ni, kuka da abin cikina. Don Allah ka sahale min!”
Takawa yayi ya rungumeta, fashewa tayi da kuka, tana sonshi yanzu tun daga lokacin da Hafsy ta mata gorin taji ta shirya ta bashi kome, sai dai sakamon kashe mata iyaye da ta gani ba zata yafe mishi ba.
“Ba zan yafe maka ba. Ba zan tab’a yafe maka ba, koda zai rage daga ni sai kai a duniya ba zan yafe maka ba, na Barka da Allah na Barka da wanda ya halicce mu, rabuwa da kai ba wai bana sonka bane amma dole nayi nisa da kai, dole na nisance ka, da fatan zaka sahale min”
“Don’t let your heart led you to the mistake, ki fahimce ni na gaya miki gaskiya!”
Wani irin ihu da kuka ta saka tana rike cikinta. “Me kake nufi? Kana nufin zaka min dadin baki ne? Kana nufin zaka rufe gaksiya ce? Wato da kasan kai ka kashe min su, shi ne kazo ka yaudare ni, ka sani aurenka babu dalili? Me ysa ka min haka? Me yasa?” Ta fada tana kuka, a hankali ya ja kujeran gabanta yanzu yana kallonta.
“Kiyi hakuri! Wata rana zaki ji abin da ya faru, promise me, idan kika tafi ba zaki yi kukan bana tare dake, ki min alkawarin ba zaki yi kuka idan wani abu ya faru da ni ba, ki min alkawarin zaki bawa dan mu kulawa har girmanshi! Zainab ina sonki, ina kaunarki. Zan zauna jiranki da jiran kiranki. Kira daya kika min zan zo gare ki! Da kira daya kawai!”
Daga haka ya mike zai fita ta ce mishi.
“Don soyayyarka da Annabin Allah ka sahale min!…..
*Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/23, 1:53 PM] Yan Mata: 34- “Ka ji! Ka sahale min haka kawai zai saka na cika maka alƙawarinka” juyawa yayi ya zuba mata idanu, sannan ya taka har gabanta, ya rungume ta sosai. “naji zan sahale miki, zan baki iska, zan baki damar kiyi sabon rayuwa. Amma zan kare rayuwana ina jiran kiranki, zan jira kiranki har zuwa ranar mutuwata, zan jira ki zan jira zuwan kiranki, Zainaba zan yi kewarki zan yi kewarki zan yi kewarku da abin cikinki, ba zan daina kewarki ba” kuka take sosai tana kara tura kanta kirjinshi, tana jin wani irin kaunarshi, kamar ta janye bukatar ta na rabuwa da shi, amma ina idan ta tuna shi ne sanadin fadawarta dogon mantau sai ta ji dole ta rabu da shi.
“Idan har kana son na cika maka alƙawarinka, dole ka sahale min. Dole ka nisance mu, dole ka bamu damar mu rayu inda babu kazamar rayuwa, inda babu kazamar soyayya, inda babu haramtacciyar kasa, inda rayuwa da mutuwa ba a bakin kome ba ne, ka bamu damar tafiya can inda sai dai ka a ranka muna raye, amma ba zaka san me muke ba.”
“Zan baku kome zan baku damar kome, amma ki sani ba zan tab’a cire idanu akan ku ba, ko ƙarƙashin ƙasa kuke. Idanuna sa zuciyata tana tare da ku. Kune Duniya ta, kune rayuwata, farincikin da nake yana tare da ku ne, amma zan hakura da nawa farincikin na baku kuyi, na barku Ku rayu cikin aminci da salama, na san kinyi fushi ne idan kika yi sanyi zaki fahimce ni, Albashir zai kawo miki duk abin da kika bukata, duk abunda kike so akwai ki bukata kawai, sannan na amshi number Kawunki na can Maiduguri, zan saka a tura duk abinda zaki bukata na haihuwa. Zainaba don Allah, kada ki cusawa Yarona ko yarinya ta, kiyayyar da kike min. Don Allah na hadaki da shi.”
“Zan yi maka duk yadda kace, amma sai ka bani sarari.”
Idanun shi cike da kwalla, a hankali ya ce mata. “Daren yau zaku bar Keivroto, ki kula da kanki.”
Daga haka ya fice daga dakin, yana jin kamar ya fashe da kuka, zuciyarshi tayi nauyi, tunda ya saka kai ya fita ta rushe da kuka, kuka take yi na jin haushinsa da ita kanta. Me yasa ta dage sai sun rabu? Amma ai shi ya kashe mata iyaye. Shi ya kashe mata iyaye ba zata tab’a yafe mishi ba, gara da ta rabu da shi, domin ta haka ne kawai zata huce haushin da take ji, ta cusa mishi bakinciki da har ya mutu yana tunawa da ita,
Duk su Ammyn suna jinta, babu wanda ya iya kulata, asalima haushi ta basu suka zuba mata idanu. Har can yamma kafin Elbashir ya kawo mata wani karamin akwati, ya gaida su Ammyn sannan ya ajiye mata akan gadon.
“Ga wannan inji Malik ya ce na kawo miki, wannan kuma na baki!” Ya mika mata wata farar takarda, kasa amsa tayi ya ajiye yana nazarin yadda jikinta yake rawa.
“Ai ba zaki gane kuskure kika aikata ba, sai kin saka kafa kin bar garin nan zaki fahimci waye Malik menk Jordan, ba zaku tab’a danasanin rabuwa da shi ba, sai kin shiga kin ga yadda mata suke jiran samu karamin damar da kika wofatar.. wallahi da ina da ikon da ke, da tabbas ba zan tab’a barin ki rabu da malik ba. Domin duk inda ake bukata namiji ya kai, ko ni da nake tare dashi. Nasan illar kadaici da rayuwa da mutumin da kake so, Zainaba kina ganin zaki yi rayuwa cikin yanci da farincikin rayuwa ko? Tow wallahi ki ajiye zaki yi kuka ne, nan kaɗan da wani jimawa ba.
Zaki gane Allah da girma yake, idan kika ga Matan da suka fiki suna zaune aka wulakantasu, suna bibiyar namiji zaki fahimci yadda ake gudanar da rayuwa mara amfani. Kince Malik ya sake ki tow ki kwantar da hankalinki, zai sake ki. Ban da zuciya mara adalci taya mutumin da mata ke bin shi, ya aure su zai kare a tare dake? Kuma ki zauna kina gaya masa abin da ya miki, kuma ki zauna kina mishi danyen hali.
Allah yana gani idan Malik ya cutar dake sai ya saka miki idan kuma ke kika cutar da shi, ki san da cewa Allah ba azzalumin sarki ba ne, domin ba zai kyale ki ba, dole ya bi mishi hakkinsa. Sakarya wacce bata san kome ba sai rawan kai da yanke makauniyar hukuncin!”
Daga haka ya juya yayi tafiyarshi, a yau ya kara tabbatarwa kanshi Malik namiji ne na gaske, wanda babu me iya abinda yayi ya sadaukar da farincikinshi saboda yar karamar matsalar da zai magance da karfin tsiya. Ya dauke kai daga duk abinda yake ganin yafi karfinshi. A yau ya kara jin tsanar Hafcy ta kara fita kanshi.
Matukar Zeeno bata dawo rayuwar Malik ba, har abada ba zai taba yarda ta tare ba, Gara su kare rayuwarsu a haka. Koda yake bayan fitar Elbashir tayi kuka kamar ranta zai fita, har ta fara ganin duhu, a cikin asibitin kuwa, shige da ficce take. Ya kuma hana a mata magana yana son fahimtar zata iya tafiya ta bar shi ne? Ko zata iya zama ta ji me ya faru, har ga Allah. Dama daya tak yake nima ta ce zata ji daga gare shi. Shi kuma zai tsallake shingen rayuwa da mutuwa ya isa gare shi, idan bata nime shi ba, zai kare rayuwarshi yana jiranta.
Zai ta jiranta har ranar da zata kira shi, zai ta dakon da son ji daga gare ta, na don kome ba, sai don yasan bai da laifi. Yasan bai da hannu a kashe mahaifanta, ta yanke hukunci cikin sauri da fushi amma yasan daga ranar da gaskiya tayi halinta, daga ranar ne zata yi kuka, ina ma da yana tare da ita, ina ma da yana kusa da ita ya share mata hawaye, amma ina lokacin ya kure. Lokacin ya kure yadda ba zata daina kuka ba. Har karshen rayuwarta, baya fatan tayi kuka me yawa, hakan zai saka dansu ko yarsu suyi maraici.

Sai da aka hada su, da personal Dr da Nurse biyu, a daren ranar. Yana rike da jakarta, don ba zata iya dogon tafiya ba, dole a keken mara wheelchair aka turata, ya ɗan durkusa a gabanta. “Ba zaki ce min kome ba!” D’ago kai tayi tana kallonshi. Kafin ta ce mishi. “Me zance maka?” Murmushi yayi wanda kana gani kasan yake ne. “Ba kome!” Dauke kai tayi ta daina hango tashin hankalin yake cikin idanun shi. “Look at me?” “A’a ka kyale ni!” “Ba zan iya kyale ki ba!”
“Anya xan iya kyale ku kuwa?”
“Zaka iya mana, zaka iya mana, ko sai na gayawa duniya ka kashe min iyayena?” Yadda ta tsura mishi idanu yasa shi shiru.
“Ok haka ya miki?”
“Ko bai min ba, ka rabu da ni!”
“Zainab ina sonki yasa nake binki, ina girmanki saboda ina kaunarki. Zan kuma cigaba da ganin girmanki saboda dan da yake tsakanin mu.”
Hawaye ne sharr suka zubo mata, ta ce mishi. “Na tsane ka, bana son ganinka, da na dawo gare ka,gara kaji labarin mutuwata!” Yarrrrr yaji abu yana mishi yawo a tsakar kanshi. “Me nayi miki da zafi?”. “kai dodo ne, ka kashe min iyayena sai na.gaza jin zafin ka ? Ka raba da farincikina sai naji dadinka. Gara mutuwata zata zo maka lokacin da nace ba zan yafe maka ba, lokacin zaka gane cewa Allah yana tare da ni, idan har kai cikakken muslumi idan kana son Allah da Manzonsa, kada ka tako inda muke kamar yadda kace zaka jira sai na nime ka, zan nime ka. Lokacin da na sauke ajiyar da yake tare da ni, xan bukaci kazo kaga danka na hadaka da Allah, kada ka nime mu. Ka zauna a inda kake, idan ka sake ka bibiye mu. Daga ni har dan zamu mutu!”

Kallonta yake, yadda take maganar zaka fahimci, da gasken gaske gaskiya take gaya mishi. “Shi kenan! Allah ya tsare hanya, ki gaida gida ki ajiye a ranki ina sonku daga ke har abin cikinki.” Juyar da kai tayi tana me kifa kanta a kan cinyarta, kuka take, tana ganin bata mishi adalci ba. Ya dauki rabuwa da ita, gashi ta kuma raba shi da danshi ko yarshi. Da ita da shi waye azzalumi? Waye ya shiga tsakani? Ita kenan, itace azzalumar. Kuka take har cikin jirgin kuka take, gashi don gata privet jet dinshi ya basu, wanda xa a sauke ta a g1arin Jigawa, domin Dangin mahaifinsu sun bukaci haka. Kukan da take ya fara isar Zulfah ta ce. “Bana son iskanci, ke wata irin jaka ce? Kina sonshi kika watsar dashi. Ba ya sake ki ba?” Wani irin juyi cikinta yayi ya rike shi da sauri. “Kin bukaci ya sake ki ya sake ki uban me kuma ya rage? Shegiya me shegen kafiyar tsiya, wawuya idan kika mutu wutar su Fir’auna da Hammana zaki zauna jakar banza!”
Zaginta Zulfah take tana kara gaya mata magana marasa dad’i, har jikinsu ya tashi.
“Don Allah ki kyaleta!” Inji Ammyn, “Haba yarinya kamar aniyar, baki daya bata da mutuncin bata gaida mai mutunci ba, yar kika mara mutunci, wallahi ban da Malik ya roke ni nayi hakuri da naci ubanki haka mara hankali” kalmar jaka kuwa kamar a bakinta aka.fara kawo shi. Domin zagin tsamar miya takewa Zeenobia ita kuwa sai kuka take, tana jin kamar ta fita daga cikin jirgin ta fado ta mutu kowa ya huta, tunda ba a damu da ita.
“Madam ko zaki dan yi hakuri, domin condition dinta baya son tashin hankali.”
“Taya zan yi shiru yarinyar nan haushi take bani,kamar na rufeta da duka, don ubanta yar iska har akwai wanda zai min sanadin rabuwa da mijina ba a haifeta ba dan ubanta. Wallahi ko akan wata mace na ganshi ba zan hakura dashi ba. Balle don an gaya miki cewa mijinki ya kashe iyayenki, sau nawa ana haka? Sau nawa muna handling cases irin naki.”

Yadda take kuka ne, da haki yasa Dr ta mata allura, tare da saka mata ruwa barci ya ɗauke ta. “don Allah kuyi hakuri.” Nurse din ta faɗa, a takaice. Haka yayi ta barci.
★★
Shiru yayi yana kallon, sararin samaniya. Ba zai ce yaushe yayi danasanin fadawarshi duniyar fansa ba, amma a yau yana ji yana gani ya rasa wacce yake so, ya rasa matarshi da babynshi. Ta haramta mishi ganinsu, danne zuciyarshi yayi ya sake murmushi kamar babu abunda yake faruwa. “Hmm!” “Malik!”
“Elbashir me ba zaka Duba matarka ba?”
“Na hakura da ita dama ina son, idan kome ya lafa sai na sawwake mata.”
“A’a wallahi zata tare, ka je ka dawo da ita zan tafi China!”
“Malik!”
“Kayi abin da nace, bana son musu.” Ya faɗa yana kallon sama. “Malik kayi hakuri!” “Babu kome, ya wuce” Elbashir kamar zai yi kuka, ya ce. “Malik ka yafe mata, don Allah, wallahi ban san kome ba, kuma idan baka yafe mata ba zata iya zame min matsala.”
“Babu kome, jarabawa ce idan ban amshe shi ba ya kake tunanin al’amarin zai kasance? Ina ganin zuwa yanzu ya yaci ace ka gane cewa Zainaba ita ce tawa ƙaddaran, idan ban amshe ta ba zan iya butulcewa Ubangiji. Kayi hakuri ka amshi matarka hannu bibbiyu, don Allah ban da wulakanci. Don Allah kada ka mata kome wallahi Allah ya nufa haka zai faru ne.”
………
*Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/23, 1:53 PM] Yan Mata: 35- Elbashir ji yake kamar ya fashe da kuka, yana kallon yadda Malik ya shanye kome kamar bai faru ba, “Malik!” “Muje gida ai sun tafi!” Daga haka ya juya suka nufi wurin motar, bude mishi kofar yayi ya shiga ya zauna yana me kwantar da kanshi. Har suka bar airport ɗin. Koda suka shiga cikin gari kai tsaye gidan su Hafsy ya mishi magana su tafi, babu musu suka nufi gidan, suna zuwa da kanshi ya fita ba tare da ya bawa Elbashir damar fita ba, ya nufi cikin gidansu Hafsah. A mutunce suka gaida juna ya kalle su yana murmushi ya ce, “Nazo ne na tafi da Hafsah tunda daga ku har shi, zaku mai da ita wata iri!”
“A’a yallabai Malik ka saka shi don Allah ya sawwake mata!” “Ba zai yiwu ba, tazo mu tafi ai kowani mutum yana kuskure. Sannan dama can Allah ya ƙaddara haka zai faru, shi yasa ban wani ji ciwon abin ba, idan muka ce abin da muke so zamu yi ai ba zamu tab’a ganin daidai ba. Amma idan muka barwa Allah lamarin sai ya iya mana, bana tunanin haka zai saka na butulcewa Ubangiji, abu ne da dama na gaza tsayuwa na fahimtar da Zainab kuma da bata saurin fahimtar abu sai daga karshe.. wallahi babu kome ta fito mijinta yana jiranta!”

Kasa magana iyayen Hafsah sukayi, wani irin zuciya ce da Malik, a maka laifi kabi da alkhairi. Murmushi yayi ya ce musu. “Ku barta ta tafi da mijinta, nima tafiya xan yi.”
“Shi kenan, tunda kayi magana me yafi haka?” Murmushi yayi ya ce. “Babu!” Haka suka ya fita ya barsu, suka shiryata. Suka fita da ita, suna musu fatan zaman lafiya. Gaba ya bude mata suka saka ta. A hankali ya ce musu. “Mun gode!”
“Mune da godiya!” Daga haka suka bar kofar gidan, “Hafsah bani numberki idan wannan dan iskan ya miki, shiritita ki kira ni ki gaya min domin ba zai yiwu ya tab’a mana sahiba ba.”
Kuka take a hankali ta kasa magana, “Malik a bayan idanunka ba zan tsalleke maganarka ba, balle a kan idanunka. Malik duk abin da kace haka zan yi!”
“Tow ajiye a hotel din three stars!”
“Malik!”
“Haka na ce, ka sauke ni a three stars!” Ba mu ya nufi hotel din, ya sauke shi ya raka shi har cikin hotel ɗin, zuwa gobe ka kawo min kayana, suna shirye.”
“Me yasa Malik?”
“Ba xan iya jin kuna amarci, matata tana wata duniya ba.” Ya faɗa yana kallon Elbashir. “Don’t rejected your wife, she meant to you, and she need from you. Babu wanda baya kuskure.” Yana fadar haka ya juya ya nufi cikin luxury room din da ya kama, kusan penthouse ne a cikin hotel din, iya part din anyi shi ne domin mutane irinsa. Zuba gwiwanshi yayi ya fashe da kuka, yana cewa. “Malik ka bani daga abin da Allah ya baka, ka tsaya min domin Allah ya tsaya maka. Malik an maka laifi ta sanadina, Malik me yasa ka nisanta kanka damu? Ko kana ganin ta sanadina haka ya faru?” Juyawa yayi yana kallon Elbashir.
“Ka ji kunya, kato da kai kana kuka. Dariya ka bani. Ko daya kaje Allah ya baƙu zaman lafiya.!” Yaso Malik ya fahimce shi, amma yaki fir yana ganin kamar duk laifinshi ne da bai nime Hafsah ba a daren da haka bai faru ba, shi mutum ne da yasan waye Malik, kuma zai bugu kirji ya ce yasan waye Malik. Amma bai tab’a fahimtar Malik yana da karfin zuciyar ba zaka gane ba, ai irin wannan yanayin ba a faru. “Tashi ka je Allah ya baƙu zaman lafiya!”
“Malik me yasa?”
“Saboda haka zai saka ka samu nutsuwa, zaka sake da matarka kayi yadda kake so, sannan baka tunanin ina gidan, don Allah kada ka tab’a ran yar mutane.”
“Shi kenan!” Ya juya ya fita yana jin kamar ya dawo ya zauna da Malik. A haka ya bar hotel din, yana jin kamar yayi ta rugawa Hafsah zagi.

Bayan tafiyarshi, Malik yayi wanka. Babu kaya a dakin dole ya saka wanda ya zo da shi ya nufi Bouquet dake ƙasar hotel din ya dauki kayan, ya basu kati. Sannan ya dawo dakinshi ya zauna ya cire na jikinshi ya sauya, sannan ya zauna yana kallon tv. Lokaci zuwa lokaci hankalinshi yana kan wayarshi. Har dare yayi sosai, yana kallon wayar yana jiran kiranta.
***
Sai da safe suka isa Dutse, kafin nan ta farka sau biyu tana komawa, koda suka sauka a airport. Babban Asibitin dutse aka wuce da ita, kafin ta ji sauki a maida ita hadijia. Suma Nurse da Doctor sai da suka bada kome nata, suka huta sannan suka wuce airport. Dama abun da ya kawo su kenan, sun gama zasu koma inda suka fito. Yan uwa da abokan arziki, da suke hadeja da nan dutse suka yi ta zuwa ganinta, wasu su koma gefe su ce babu aure ta kwaso cikin shege. Wasu su ce da aure kafin wani lokaci kan mutane ya rabu da rumors na bala’in tashin hankali.
Duk yadda Zulfah taso kauda kanta, sai da ta kasa, domin abin da take yar iskar yarinyar nan amma taki. Haka suka yi ta fama da mutane babu wanda ya fahimce su. Kwananta uku dake ana zuba kudi dai gashi ranar na hudu ta farka, a gajiye. Bayan an gama dubata suka tabbatar lafiyarta lau. Sannan suka dan rike ta saboda case dinta.

A wasa a wasa, sai da ta kwashe sati biyu bata ganin kowa sai Zulfah da Ammyn. Sai Kanen Babansu mutum biyu. Baffa Barde, da Gwaggo Karime. Duk da bata cika son hayaniya ba, sai dai ta lura da mata yar tijara ce ta gaske. Ko waye ya vata labarin yadda ta tawo ba tare da son ran Malik ba, ai kuwa ranar har da gasa mata bakar magana. “Ce miki akayi zamu miki gatar da Yake miki ne? Ai bamu da wannan arzikin, Allah ya baƙi miji na rufin asirinki. Amma kika saka kafa kika mauje wannan gatar, sai kici uwar da zaki ci domin nan kan babu me karawa kanshi damuwa da matsalarki. Ai wallahi ko namar jikinki yake yaga yana ci kya hakura baki san yadda rayuwar take ba, shi yasa mara kunya da idanun a tsakar ka!”
Hawaye ne ya cika mata idanu, bayan ita ma sai da wata coursin din Babansu ya zo yayi ta mata rashin mutuncin daga yadda suke bala’i zaka fahimci akwai matsala a cikin zancensu.

Kwananta Biyu dangin Mamansu har da Jalilah suka zo, Wayyo Allah a nan tayi ta zuba shagwaba. Ana kara kambamata da riritatta. Ai kuwa yace ita a wuce da ita Maiduguri. Dake Familyn Mamanta suna da arziki sosai, shi yasa basu wani damu ba, aka dauke ta domin Aunty Yaganah sai wani mita take, akan an takurawa Zeenobia da maganar Malik, ai ya mata tsufa tunda babu aure a tana haihuwa kawai ta mika masa dansa ta yi fama da kanta. “A’a Aunty ba zan bashi Yarona ba, kawai ya san na haifa amma ba zan bashi Y’ata ba.”
“Allah sarki! Kada ki damu babu me rabaki da danki!”
Wasa wasa dai Washi gari aka wuce da Zeeno Maiduguri. A can aka shiga zancen haihuwarta tunda ance aiki ne, amma dake akwai yan uwan Mamanta da suke step Mother, suma suna aure manyan mutane nan bornon. Domin Alhaji shuwa ya rabu da uwargidansa, sai ya auri kakarsu Zeeno Hajja Abuh.
Dake matar kafin wannan abin ya faru, ta musu rikon tsakani da Allah sai gashi abin mamaki, suma suka lullube Zeeno da alkhairi. Kuma Mamansu Zeeno Batulah a wurinsu ta girma basu nuna mata yan ubanci ba. A gidan Babban wansu Mamanta aka sauke ta, a part dinta tare da saka.mata me aiki.
Akwai Mahaifiyarshi Kawunsu Zeeno, dake hutu da kulawa uasayba ka ganta kace tsohuwa ba, ita ke saka idanu akan Zeeno. Idan tayi wani abu zata fada, yace ba a haka ake ba. Suna kiranta Hajja Yayye. Tana da kirki da mutunci ga ilimin addini da ya samu mazauni a ranta, dake bayan rabuwa da kakansu Zeeno ta auri wani Kanuri ne suka tafi Madina a can ta kwashe shekaru sama da talatin da biyar. Koda ta dawo mijinta ya rasu. Suna da Yaran uku. A gidan kakansu Zeeno ta haifi maza uku mace daya, Alhaji Kazeem wanda suke gidanshi, sai Hajiya Kaltumah tana nan mai Borno, sai Alhaji Mustapha, yana Abuja yana aiki, sai Alhaji Awwal yana Rivas yana aikin banki,

. Fahdeelah tana auren W IIazirin Borno, Yaranta biyu Akram wazir (kun tuna shi🤗😂) sai Haris yana can owerria can matattan man fetur na kasa. Sai Umaimah Yaranta hudu ne, Babba namiji sai yan mata uku, biyu sun yi aure saura daya. Zata kai age mate Zeeno.
Sai Sumayyah wacce take aure a Kaduna, da Yaranta takwas, biyar maza. Uku mata matan ne manya ta aurar da daya saura biyu manyan.

Tun da suka ji labarin Zeeno dama suna shiri da Zulfah sosai. Sai ga Zeeno ai baki daya suka koma jikin Zeeno ana riritatta. Satinta daya da zuwa aka yi bikin murnan zuwanta. Sai dai a bari guda bata farincikin da haka, domin tunda sukayi idanu da Akram. Ya sakata a gaba da fitina. Tsoronta daya kada ya mata akuyancin da ya mata a Keivroto sai ta sha mamaki ko da wasa bai mata wannan kallon ba.
Haka ta cigaba da renon cikinta, har ya shiga wata bakwai, domin Malik ya roki Ammyn da ta zauna sai ta haihu, kuma ta amince. Sai da ta shanye wata na bakwai tass, sannan aka fara shirin mata aiki. Domin batun gaskiya bata iya barci cikin ya hanata sakat, bata da ikon cin abincin ta koshi sai ta kaza zama ta kasa tsaye.

Abin tausayi baki daya ya fita hayacinta, dake ana bata ruwan Addu’a sai take samun saukin abin, a satin da za a mata aiki. Ta je ganin likita kallon Ammyn tayi sannan ta ce mata. “Hajiya idan da hali kuyi hakuri da aikin nan, domin yarki bata da wani dogon matsalar .da za amata aiki. Sannan idan aka yi aikin Babyn sai ta dauki lokaci tana zaman kula da shi, shima aiki ne a wannan yanayin. Sam bana son ganin anyiwa mace aiki idan ba dole ba. Babyn bai gama kwari ba domin naga rahonta akwai zubda jini,idan aka duba da matsalar kin ga kwanakin ya koma baya, idan da hali a bar cikin ta cika wata tara mu gani zuwa sati 42 sai a cire domin zai fi kyau da koshin lafiya..amma idan ita tana so kuka zata iya jigilar jinya ba laifi sai a cire mata.”

Kallonta sukayi, baki daya idanunsu yana kanta. “à kin ji? Me kika ce?” “Ammyn a bar min shi kawai!” Ta faɗa tana cijewa. Idanunta yana cika da kwalla. Daren ranar da Washi gari abin ya faru, sai da ya gaya mata cewa. “No matter how much you want the baby out, a will sure that I’m there, for sake of you and my child!” Dakyar ta mike ta fito waje, tana son tayi kuka amma bata son tayi kukan for sake of Malik, bata son tayi kukan ta ji a ranta don shi ne. But she miss him badly. Bata taɓa sanin shi din wani gefe na rayuwarta ba ne dai da ta fahimci tana matukar bukatarshi, asalima ba shi yake hanata barci ba, bukatar Malik. Share hawayen tayi, tayi tana shashekar kuka. A hankali take tafiya a duk inda take ji take kamar ita ɗaya ce me matsala babu wani me shi, toh ya zata yi? Ya kashe mata iyaye ne fa, kamata yayi ya dauki wuka ta soke shi har lahira, amma ta zabi tafiya ta bar shi tafi mata kome sauki shi ne zuciyarta take cutar fa ita da kewarshi. Amma ai bata yi laifi ba, asalima gaskiya ce kawai ta tsaya akan ra’ayinta.
Gabanta ne ya fadi lokacin da ta tuna da takardar da ya bata har biyu. Bata yi aune ba, sai jin tayi ta tafi da baya zata zame…….OMG ME ZAI FARU🙄🤗🧐CIKIN ZAI RAYU KO ZAI SHEKA TARE DA UWAR…
*Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/23, 1:53 PM] Yan Mata: 35- Salatin da yazo bakinta tare da agajin wani mutum, da bata san waye ba ya dauke hankalin mutanen da suke wurin. Ita kanta idanunta a mugun rintse yake, numfashinta na hawa da sauka. Jira take kawai ta jita a kasa, amma wani hukuncin Allah taji ta rike a jikin mutumin. “Sannu ko?” Bude idanu tayi tana kallonshi, a hankali ta sauke ajiyar zuciya tana jin kamar zuciyarta zata buga. “Sannu!” Ya kuma faɗa a karo na babu adadi domin jera mata sannu yake yana karawa. A hankali ta mike tana jin bayanta ya amsa mata, “sannu, sannu Zainab!” Inji Ammyn. Kamar zata yi kuka ta ce. “Ammyn na auna arziki fa.” “Eh wallahi Allah ya kiyayye na gaba!” D’ago kai tayi tana kallon shi, ta ce mishi. “Na gode!” Murmushi yayi sannan ya ce mata. “Don worry yourself, tunda kin wuce baki fadi ba, ki gayawa Baban Baby. Ya kira ya min godiya, domin na cancanci yabawa!”
Gyada mishi kai tayi tana kallon shi, har ya gama maganarshi. Da zai tafi ya tsaya yana kallon yadda Ammyn take matsa mata hannun. “Sannu huta sai mu tafi ko!”
Murmushi yayi, sannan yq ce mata. “Babu abin da zai same ta, ai ta tsira. Suna na Tahir Sani Malami Jajja ni likita ne anan asibitin a bangaren Yara, da fatan zaki rike wanna card din nawa!?” Gyada kai tayi tana kallonshi. “Mun gode sosai!” Daga haka suka mike, yana d’aga mata hannu. “Zainab muje!” Mikewa tayi tana cizon bakinta, domin bayanta sai da ya amsa da ta kusan faduwa.
Suna fita suka samu drive yana jiransu, daga nan, suka wuce gida. Suna shiga ta zube a kujera tana faɗin. “Washi Allah na!”
“Sannu uwar uku, ai wannan cikin idan ba wani hukuncin Allah ba, uku ne ko biyar.”
“Hajja Yayye! Ki min fatar sauki wallahi bani haihuwar uku ko biyar.”
“Idan kika haifa me zaki bani?”
“Ni dai na gaya miki gaskiya bani haihuwar biyar, sai kace wata akuya.”
“A toh ko na akuya ba, wai zaki haifa mana, dama jibi zani umra sai na miki addu’a!” “Hajja Yayye, kin ga yau sauran na fadi a asibitin.” Ta fada tana tura baki. “Ke Yar nan, kin auna arziki fa.” Nan suka yi ta hira aka kawo mata abincin dan wake ne, sai kayan salat, tana ci tana lumshe idanunta. Shiru tayi lokacin da girkin Malik ya dawo mata, kamar ruwa ya cinyeta sai da idanunta suka tara kwalla. *Yanzu shi kenan sun rabu kenan?* A hankali ta ture abincin. Ta mike dakyar ta koma dakinta. Rufe dakin tayi ta fashe da kuka, bayan ta zauna a gadon. Tana kuka tana karawa, Allah ya gani tayi missed dinshi. Bukatar shi take, amma pride irin nata, yasa tana jin kamar tana nimanshi class ɗin ya zube.

Don haka ta cigaba da kukanta, domin shi yafi dacewa da ita, bayan ta gama kukanta, yayi sallah ta kwanta domin ba zata iya da ciwon kan da ya tasata a gaba ba.
★★★
Bayan sati
Elbashir kan, kasa sake jikin shi yayi domin gani yake kamar an sayeta baki daya zata iya kashe shi. Duk da yaga nadamar haka a tattare da ita, amma baki daya yaki yarda da ita. Sai da yayi sati biyu don kada Malik ya ce bai ji maganar shi ba, sannan ya fara fita ranar da su haɗu da Malik, ya sha tsokana. Kamar ba gobe kuma gefe guda babu abin ya bashi mamaki kamar yadda ya ga Malik din babu wata matsala a tattare da shi, haka ya bashi mamaki, har ya kasa hakuri ya tambayi Malik din.
“Malik ko kun shirya da Zainab ce?”
“Me ka gani?”
“Kawai naga kamar hankalinka kwance yake.”
“Tow so kake na.kashe kaina saboda mace? Yarinyar da koda na mutu babu ruwanta aure zata yi? ”
“Kai haba?”
“Wallahi kuwa, wacce take kaunarka ce zata kai shekara biyu bata yi aure ba. Wacce dama kuɗinka take so, babu ruwanta. Kana mutuwa zata buga aurenta, don haka babu ruwana da wata mace naci mana da da madara. Baka ga kibar da nayi ba, domin na samu sauki.”
“Dama baka da lafiya ne?” Ya tambaye,
“Hidimar mace ai lalura ce me cin gashin kansa, idan da na biyewa Zainab sai na lakad’a mata dukar tsiya, amma bana jin ta kai ni makurar da haka zai faru!”
“Allah ya kyauta, bana jin haka zai faru ai kasan me kake yi, kana da nutsuwa da aji.” Girgiza kai yayi yana dariya, ya ce.
“Aji sai kace mace, kawai abin da na sani mata irinsu Zainab ka barsu akan ra’ayinsu, ka sake suka rike maka wuya, sai kasan Allah daya ne, irin Zainab biyu wallahi sai ka kusan hauka. Bana jin masu mata biyu zuwa uku suna cikin salama.”
“Kai Malik kara bani tsoro, gaskiya ba zan iya rayuwarka ba, domin Zeenobia ta baka wahala.”
Dariya yayi ya ce masa. “Kuma sonta nake kamar na cinye ta danye.”
“Allah ya kawo maka ɗauki, domin ka zare!”
Tashi yayi ya zuba hannu a aljuhun wandon shi yana kallon waje. “Baka san wani abu ba ne, idan har zaka so mace kada ka sake ta ja ka a kasa, duk tsiya kada ka bari ta reneka. Da ace na sake Zainaba ta rena nani tow da na kad’e har buzuna, a haka ya aka kare hmmmm!” Murmushi yayi ya me sauti yana me shafa kanshi har zuwa wuyar shi.
“Malik me yasa ba zaka bincika ka ji halin da suke ciki ba, na ga kusan kwana uku kenan da tafiyarsu.”
“Tana lafiya, ita da abin cikin.”
“Masha Allah, ya batun aikin.”
“Ban san kome ba, ina jiran abin da zasu ce ne!”
“Allah ya raba lafiya!”
Gyada kai Elbashir yayi, yana mishi fatan alkhairi, d’aga wani riga Malik yayi ta cire wasu passport yayi ya wurgawa Elbashir ya ce masa. “Honeymoon!” Ya faɗa yana d’aga mishi gira. Kasa magana yayi yana kallon Malik. Daukar rigar shi yayi ya saka a arm dinshi, ya ce mishi. “Ka rufe baki Bashir, ina da wani Meeting a can Hall idan zaka zo muje, yana da kyau ka ji akan meye!”
“Zan je!”
Daga haka suka fita, suna hira har zuwa inda zasu yi Meeting. Sake baki yayi ya ga Lauyoyin Malik da lauyarshi. “Me zaku yi anan, Barista Hayatu!” Murmushi yayi, bayan Malik ya bashi kujera ya zauna. A hankali ya zauna yana kallon su. Ciro wasu takardun Lauyoyin Malik suke suna mika mishi yana cikewa, yana gama na farko sai ya tura su gefe sannan ya kuma. Sannan ya kalli Elbashir ya ce musu. “Wannan file din, na Elbashir ne baki daya da na amsa na Mr Jamal Arab, da aka kwace shekarun baya. Wancan da kuka saka hannu, shares na Zainab ce da abin cikinta.”

Hadiye yawun bakinshi yayi yana kallon Malik. Kamar yayi kuka ya gama aikinshi sannan ya ce. “Akwai masana’antar sarrafa man fetur, na shine na saya mishi shekarun baya, ga kuɗin shi. Mahir na gode!” Ya ajiyewa Elbashir ya ajiye mishi kome yana murmushi. “Na sallame ka, daga yau kada ka kuma makale min!” Ya fada yana dariya. Hawaye ne sharrr ya zubo mishi. Ya kasa magana, “kasan mata da buri ba zata ji dadi ta ga mijinta yana aiki ƙarƙashi mijin kawarta ba, ko ni ne ba zan yarda ba, salon muyi faɗa matata ta mata gori.”
“Har abada Zainab ba zata tab’a mata gori ba.”
Ya fada yana rungume Malik, cikin wani irin kaunar shi. Don abin da dan uwarshi na jini. Sai da aka gama suka fita. Su kansu Lauyoyin ba karamin alkhairi yayi musu ba. “Malik kamar zaka tafi wani wuri ne!” Tsayawa yayi yana kallon takalmin shi. Wani irin fisgar Elbashir yayi ya cillar da shi can, harbin ya wuce ta gefe can. Komawa bayan motar da suke wurin suka zauna. “Sannu babu abin da ya same ka ko?” Yana jin yadda ake harbe harbe, gashi mutane kowa ya gudu. Hannunshi ya kai kafarshi. Ciro wata karamar bindiga yayi ya saka hannu a cikin Aljahun wandonshi wani abu ya ciro. Ya saka a bakin bindigar.

Kafin kace wani abu ya gyara tare da cewa. “Ka zauna anan, kada ka sake ka matsa nan da can. Na hadaka da Allah.”
“Tow Malik”
A hankali, ya kalli jikin wata a’a BMW, baka wuluk. Yana kallon me harin, kafin ya juya da sauri ya shiga harbinsu. Kafin kace me ya harbe su. Sannan ya gama dasu, sannan ya mike yana gyara tsayuwar shi. Harbi aka kai mishi a hannun da yake rike da bindigar ya fadi can.
★★★
Rike take da bowl din fruit, wani irin faduwar da taji tare da juyin da cikinta yayi yasa ta sake bowl din, tana rike cikinta a mugun tsorace take kallon fruit ɗin, kallon Ammyn tayi tana son sanin da waye take waya, ganin yadda ya tsare ta da idanu yasa ta. Mikewa tana me dauke idanunta da yayi jajjur.
“Innalillahi wa inna illahirirajuun Ubangiji, ya tsare na gaba, wani hali yake ciki!”
“Eh tow, a halin da ake ciki sai du’a’i kawai amma al’amarin ana cikin wani hali da”
“Allah sarki Zainaba, Ubangiji ya kawo mata dauki daga ita har shi.”
“Wace ce Zainab kuke magana?” Sake wayar Ammyn tayi tana kallonta. “Wata Zainab ce yar uwar Abbanku!” Hawaye ne ya zubo mata, “shi kenan!” Daga haka ta wuce waje tana jin kuka ya kwace mata. “Hajja Zainaba, lafiya?”
“Hajja Yayye, kawai kukan ne ya zo min”
Duk da bata san me ke faruwa ba, amma jikinta ya bata babu lafiya, sai babu halin gaya mata. A hankali labarin ya bazu a cikin gidan, har da familyn Babanta kowa ya sani. Amma ita har lokacin babu wanda ya gaya mata, domin ana tsoron cikinta.

A daren ranar mugun zazzaɓi da nakuda ya hanata barci, dole aka tafi da ita asibiti, ganin halin da take ciki yasa ka shiga da ita aiki domin aka bari tayi nakuda za a rasata ko jinjirin cikinta. Haka aka shiga da ita aiki, basu fito ba sai karfe hudu na asuba, aka fito da yaran biyu maza, mace daya kamar yadda Inna da Hajja Yayye suka yi fatansu.

Yaran farare tass kamar Uwarshi, dole aka saka su a incubator, domin kuwa babu me ɗaukarsu.
★★
Maganar gaskiya har zuwa liuokacin, babu labarin makomar Malik, domin kuwa anfi karkata da mutuwarshi, Elbashir shi ya dauki Malik, har zuwa asibitin. Jikinshi jinin Malik ne kamar an yi mishi wanka…
*Allah sarki Malik!*
*Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/27, 10:26 PM] Yan Mata: 35- Salatin da yazo bakinta tare da agajin wani mutum, da bata san waye ba ya dauke hankalin mutanen da suke wurin. Ita kanta idanunta a mugun rintse yake, numfashinta na hawa da sauka. Jira take kawai ta jita a kasa, amma wani hukuncin Allah taji ta rike a jikin mutumin. “Sannu ko?” Bude idanu tayi tana kallonshi, a hankali ta sauke ajiyar zuciya tana jin kamar zuciyarta zata buga. “Sannu!” Ya kuma faɗa a karo na babu adadi domin jera mata sannu yake yana karawa. A hankali ta mike tana jin bayanta ya amsa mata, “sannu, sannu Zainab!” Inji Ammyn. Kamar zata yi kuka ta ce. “Ammyn na auna arziki fa.” “Eh wallahi Allah ya kiyayye na gaba!” D’ago kai tayi tana kallon shi, ta ce mishi. “Na gode!” Murmushi yayi sannan ya ce mata. “Don worry yourself, tunda kin wuce baki fadi ba, ki gayawa Baban Baby. Ya kira ya min godiya, domin na cancanci yabawa!”
Gyada mishi kai tayi tana kallon shi, har ya gama maganarshi. Da zai tafi ya tsaya yana kallon yadda Ammyn take matsa mata hannun. “Sannu huta sai mu tafi ko!”
Murmushi yayi, sannan yq ce mata. “Babu abin da zai same ta, ai ta tsira. Suna na Tahir Sani Malami Jajja ni likita ne anan asibitin a bangaren Yara, da fatan zaki rike wanna card din nawa!?” Gyada kai tayi tana kallonshi. “Mun gode sosai!” Daga haka suka mike, yana d’aga mata hannu. “Zainab muje!” Mikewa tayi tana cizon bakinta, domin bayanta sai da ya amsa da ta kusan faduwa.
Suna fita suka samu drive yana jiransu, daga nan, suka wuce gida. Suna shiga ta zube a kujera tana faɗin. “Washi Allah na!”
“Sannu uwar uku, ai wannan cikin idan ba wani hukuncin Allah ba, uku ne ko biyar.”
“Hajja Yayye! Ki min fatar sauki wallahi bani haihuwar uku ko biyar.”
“Idan kika haifa me zaki bani?”
“Ni dai na gaya miki gaskiya bani haihuwar biyar, sai kace wata akuya.”
“A toh ko na akuya ba, wai zaki haifa mana, dama jibi zani umra sai na miki addu’a!” “Hajja Yayye, kin ga yau sauran na fadi a asibitin.” Ta fada tana tura baki. “Ke Yar nan, kin auna arziki fa.” Nan suka yi ta hira aka kawo mata abincin dan wake ne, sai kayan salat, tana ci tana lumshe idanunta. Shiru tayi lokacin da girkin Malik ya dawo mata, kamar ruwa ya cinyeta sai da idanunta suka tara kwalla. *Yanzu shi kenan sun rabu kenan?* A hankali ta ture abincin. Ta mike dakyar ta koma dakinta. Rufe dakin tayi ta fashe da kuka, bayan ta zauna a gadon. Tana kuka tana karawa, Allah ya gani tayi missed dinshi. Bukatar shi take, amma pride irin nata, yasa tana jin kamar tana nimanshi class ɗin ya zube.

Don haka ta cigaba da kukanta, domin shi yafi dacewa da ita, bayan ta gama kukanta, yayi sallah ta kwanta domin ba zata iya da ciwon kan da ya tasata a gaba ba.
★★★
Bayan sati
Elbashir kan, kasa sake jikin shi yayi domin gani yake kamar an sayeta baki daya zata iya kashe shi. Duk da yaga nadamar haka a tattare da ita, amma baki daya yaki yarda da ita. Sai da yayi sati biyu don kada Malik ya ce bai ji maganar shi ba, sannan ya fara fita ranar da su haɗu da Malik, ya sha tsokana. Kamar ba gobe kuma gefe guda babu abin ya bashi mamaki kamar yadda ya ga Malik din babu wata matsala a tattare da shi, haka ya bashi mamaki, har ya kasa hakuri ya tambayi Malik din.
“Malik ko kun shirya da Zainab ce?”
“Me ka gani?”
“Kawai naga kamar hankalinka kwance yake.”
“Tow so kake na.kashe kaina saboda mace? Yarinyar da koda na mutu babu ruwanta aure zata yi? ”
“Kai haba?”
“Wallahi kuwa, wacce take kaunarka ce zata kai shekara biyu bata yi aure ba. Wacce dama kuɗinka take so, babu ruwanta. Kana mutuwa zata buga aurenta, don haka babu ruwana da wata mace naci mana da da madara. Baka ga kibar da nayi ba, domin na samu sauki.”
“Dama baka da lafiya ne?” Ya tambaye,
“Hidimar mace ai lalura ce me cin gashin kansa, idan da na biyewa Zainab sai na lakad’a mata dukar tsiya, amma bana jin ta kai ni makurar da haka zai faru!”
“Allah ya kyauta, bana jin haka zai faru ai kasan me kake yi, kana da nutsuwa da aji.” Girgiza kai yayi yana dariya, ya ce.
“Aji sai kace mace, kawai abin da na sani mata irinsu Zainab ka barsu akan ra’ayinsu, ka sake suka rike maka wuya, sai kasan Allah daya ne, irin Zainab biyu wallahi sai ka kusan hauka. Bana jin masu mata biyu zuwa uku suna cikin salama.”
“Kai Malik kara bani tsoro, gaskiya ba zan iya rayuwarka ba, domin Zeenobia ta baka wahala.”
Dariya yayi ya ce masa. “Kuma sonta nake kamar na cinye ta danye.”
“Allah ya kawo maka ɗauki, domin ka zare!”
Tashi yayi ya zuba hannu a aljuhun wandon shi yana kallon waje. “Baka san wani abu ba ne, idan har zaka so mace kada ka sake ta ja ka a kasa, duk tsiya kada ka bari ta reneka. Da ace na sake Zainaba ta rena nani tow da na kad’e har buzuna, a haka ya aka kare hmmmm!” Murmushi yayi ya me sauti yana me shafa kanshi har zuwa wuyar shi.
“Malik me yasa ba zaka bincika ka ji halin da suke ciki ba, na ga kusan kwana uku kenan da tafiyarsu.”
“Tana lafiya, ita da abin cikin.”
“Masha Allah, ya batun aikin.”
“Ban san kome ba, ina jiran abin da zasu ce ne!”
“Allah ya raba lafiya!”
Gyada kai Elbashir yayi, yana mishi fatan alkhairi, d’aga wani riga Malik yayi ta cire wasu passport yayi ya wurgawa Elbashir ya ce masa. “Honeymoon!” Ya faɗa yana d’aga mishi gira. Kasa magana yayi yana kallon Malik. Daukar rigar shi yayi ya saka a arm dinshi, ya ce mishi. “Ka rufe baki Bashir, ina da wani Meeting a can Hall idan zaka zo muje, yana da kyau ka ji akan meye!”
“Zan je!”
Daga haka suka fita, suna hira har zuwa inda zasu yi Meeting. Sake baki yayi ya ga Lauyoyin Malik da lauyarshi. “Me zaku yi anan, Barista Hayatu!” Murmushi yayi, bayan Malik ya bashi kujera ya zauna. A hankali ya zauna yana kallon su. Ciro wasu takardun Lauyoyin Malik suke suna mika mishi yana cikewa, yana gama na farko sai ya tura su gefe sannan ya kuma. Sannan ya kalli Elbashir ya ce musu. “Wannan file din, na Elbashir ne baki daya da na amsa na Mr Jamal Arab, da aka kwace shekarun baya. Wancan da kuka saka hannu, shares na Zainab ce da abin cikinta.”

Hadiye yawun bakinshi yayi yana kallon Malik. Kamar yayi kuka ya gama aikinshi sannan ya ce. “Akwai masana’antar sarrafa man fetur, na shine na saya mishi shekarun baya, ga kuɗin shi. Mahir na gode!” Ya ajiyewa Elbashir ya ajiye mishi kome yana murmushi. “Na sallame ka, daga yau kada ka kuma makale min!” Ya fada yana dariya. Hawaye ne sharrr ya zubo mishi. Ya kasa magana, “kasan mata da buri ba zata ji dadi ta ga mijinta yana aiki ƙarƙashi mijin kawarta ba, ko ni ne ba zan yarda ba, salon muyi faɗa matata ta mata gori.”
“Har abada Zainab ba zata tab’a mata gori ba.”
Ya fada yana rungume Malik, cikin wani irin kaunar shi. Don abin da dan uwarshi na jini. Sai da aka gama suka fita. Su kansu Lauyoyin ba karamin alkhairi yayi musu ba. “Malik kamar zaka tafi wani wuri ne!” Tsayawa yayi yana kallon takalmin shi. Wani irin fisgar Elbashir yayi ya cillar da shi can, harbin ya wuce ta gefe can. Komawa bayan motar da suke wurin suka zauna. “Sannu babu abin da ya same ka ko?” Yana jin yadda ake harbe harbe, gashi mutane kowa ya gudu. Hannunshi ya kai kafarshi. Ciro wata karamar bindiga yayi ya saka hannu a cikin Aljahun wandonshi wani abu ya ciro. Ya saka a bakin bindigar.

Kafin kace wani abu ya gyara tare da cewa. “Ka zauna anan, kada ka sake ka matsa nan da can. Na hadaka da Allah.”
“Tow Malik”
A hankali, ya kalli jikin wata a’a BMW, baka wuluk. Yana kallon me harin, kafin ya juya da sauri ya shiga harbinsu. Kafin kace me ya harbe su. Sannan ya gama dasu, sannan ya mike yana gyara tsayuwar shi. Harbi aka kai mishi a hannun da yake rike da bindigar ya fadi can.
★★★
Rike take da bowl din fruit, wani irin faduwar da taji tare da juyin da cikinta yayi yasa ta sake bowl din, tana rike cikinta a mugun tsorace take kallon fruit ɗin, kallon Ammyn tayi tana son sanin da waye take waya, ganin yadda ya tsare ta da idanu yasa ta. Mikewa tana me dauke idanunta da yayi jajjur.
“Innalillahi wa inna illahirirajuun Ubangiji, ya tsare na gaba, wani hali yake ciki!”
“Eh tow, a halin da ake ciki sai du’a’i kawai amma al’amarin ana cikin wani hali da”
“Allah sarki Zainaba, Ubangiji ya kawo mata dauki daga ita har shi.”
“Wace ce Zainab kuke magana?” Sake wayar Ammyn tayi tana kallonta. “Wata Zainab ce yar uwar Abbanku!” Hawaye ne ya zubo mata, “shi kenan!” Daga haka ta wuce waje tana jin kuka ya kwace mata. “Hajja Zainaba, lafiya?”
“Hajja Yayye, kawai kukan ne ya zo min”
Duk da bata san me ke faruwa ba, amma jikinta ya bata babu lafiya, sai babu halin gaya mata. A hankali labarin ya bazu a cikin gidan, har da familyn Babanta kowa ya sani. Amma ita har lokacin babu wanda ya gaya mata, domin ana tsoron cikinta.

A daren ranar mugun zazzaɓi da nakuda ya hanata barci, dole aka tafi da ita asibiti, ganin halin da take ciki yasa ka shiga da ita aiki domin aka bari tayi nakuda za a rasata ko jinjirin cikinta. Haka aka shiga da ita aiki, basu fito ba sai karfe hudu na asuba, aka fito da yaran biyu maza, mace daya kamar yadda Inna da Hajja Yayye suka yi fatansu.

Yaran farare tass kamar Uwarshi, dole aka saka su a incubator, domin kuwa babu me ɗaukarsu.
★★
Maganar gaskiya har zuwa liuokacin, babu labarin makomar Malik, domin kuwa anfi karkata da mutuwarshi, Elbashir shi ya dauki Malik, har zuwa asibitin. Jikinshi jinin Malik ne kamar an yi mishi wanka…
*Allah sarki Malik!*
*Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/27, 10:26 PM] Yan Mata: 37- Elbashir da jikinshi yayi sanyi, ba zaka tab’a cewa shine ba. Domin baki daya baya ji baya gani. Lokacin da abin ya faru, yana kallon yadda Malik yake girgiza mishi kai, kada ya motsa ya tsaya, har zuwa lokacin da yan sanda suka iso wurin. Domin ba karamin shirin yaki aka yi ba. Yan sanda har ta sama suka sauka. Inda suka kashe maharar suka kama mutane biyu a cikinsu. Kafin lokacin Malik ya zubda jini sosai wanda ba a tsammanin zai rayu. Dafa kafadarshi Barista Hayatu yayi yana faɗin. “An kama su, sannan IG na kasa yana kan al’amarin shi yake binciken kuma muna, saka ran za a samu adalci babban burinmu da damuwarmu Malik ya rayu. Malik nagartaccen mutum ne, ga wanda ya san shi yasan adali ne, in sha Allah zai tashi.”
_A yau al’ummar garin Keivroto suka tashi da mummunar al’amarin, da ya firgita su. Sakamakon harin yan bindiga Dadi da suka kawai Mayor Malik Menk Jordan, a hotel din three stars, har yanzu babu labarin makomar Mayor din amma muna saka ran nan da wani lokaci, zamu samu labari daga hukumar gwamnati. A baya Malik yayi fama da tasku daga abokan gabanshi, wanda suka yi sanadiyar rabuwarshi da me dakinshi Zeenobia Nasr Hadejia, yayinda wasu suka ce. Mai dakinshi ta rabu da shine sakamakon kashe mata iyaye da yayi, babu wata majiya da zata saka a fahimci me yake faruwa da rayuwar Malik din, domin kome yake yi rayuwarshi a rurrife yake yinta,Allah ya kyauta_
Wannan shi ne abin da yan jarida suke yayyatawa, kowa so yake ya fadi akasain abin da yake faruwa, a bakin Asibitin kuwa gidajen jaridu ne, suka yi dafiffin son jin labarin halin da Malik yake ciki, yana raye ne ko yana mace. Kuma wani abu da basu gane ba,.ba za’a tab’a barin a sake labarin mutuwar Malik cikin sauki ba, balle kuma babu wani labari daga likitocin da suke kanshi. Sannan su kansu nurse da suke kanshi, anki bari su fito domin gudun abin da zai je ya dawo.

Daga fadar shugaban kasa, ya bawa IG umarnin a amshe duk wayar kowa, ajiye sai bayan kome ya lafa. A cikin asibitin har da Zulfah wacce ta amshe wayar kowa da Kwamishinan yan sanda, an yi cirko-cirko.
Har zuwa karfe biyar na asuba, kafin Likitocin suka fara fitowa, daya bayan daya. A mugun gajiye Doctor wardah tana fitowa, Abin da ta fara faɗa shi ne. “Alhamdulillahi!” Jin haka yasa Zulfah kiran IG ya gaya mishi. Shi kuma ya isar ga shugaban kasa. Sai dai a gefe guda Elbashir ya bukaci da kada a fitar da labarin, kuma daga IG har shugaban kasa sun yi na’am da wannan shawarar. Domin tsira da lafiyarshi, sannan itama Zulfah ta gayawa Ammyn. Kada ta gayawa Zeeno Malik yana raye. Ta wannan hanyar ce kawai zasu ci ubanta. Koda ta bata labarin an samu nasarar cire yara uku, amma yaran suna can wurin kula da su. Yasa ta jin kamar tayi kuka. Ta nufi Elbashir ta gaya masa. “anyi nasarar cire yara uku, biyu maza daya mace, daga su har uwarsu suna cikin koshin lafiya. ”
Hawaye ne ya zubo mishi, da sassarfa ya isa dakin ya samu Malik yana ta barci. Rike hannunshi yayi yana faɗin. “congratulations Aboki, Zainab ta haifa mata yara uku. Ka farka kaji labarinsu.”
Zama yayi ya fashe da kuka yana jin tausayin Malik kamar yayi yayya, baki daya sai yadda Ubangiji yayi da shi. Yana ji kamar ya cire ciwon daga jikin Malik ya mai da kanshi, domin Malik yayi mishi kome a rayuwa, babu abin da zai ce sai fatan Allah ya bashi lafiya, Allah ya bawa Malik lafiya, wanna shine fatan shi da burinshi.
Sai da gari ya waye, sannan aka samu labarin haihuwar Matar Malik, bayan an dauki hoton Yaran da video dinsu, an saka a gidajen jaridu da talabijin. Abin gwanin ban sha’awa, wannan aikin Akram wazir ne ya turowa Zulfah. Yara mazan biyu sanye da kaya skyblue, macen kuwa sanye da kaya pink. Sunyi kyau duk da basu cikin bad condition amma uwarsu, ana kanta domin har ta wuce lokacin da ya dace ta farka. Hankali ya kuma dugunzuma ya tashi a can Malik anan kuma Zainab.

Baki daya sun rasa hope ɗinsu, haka akayi ta samun tashin hankali a tsakanin mutane, a cikin gari an tashi hankula al’umma, domin gani ake kamar akwai wata makarkashiya, akan matsalar Malik, haka yasa aka karo doctors daga Gista suka tawo duba Malik din. A wannan karon da a iya cewa everything is fine. Domin har ya koma barci. Wani irin farincikin Elbashir ya tsinci kanshi a ciki..


Sai da aka taru akanta, kafin aka samu kanta, inda cikin ikon Allah. Ta farka baki daya. “Ina Babyna?” Ta faɗa tana kokarin shafa cikinta. Riko hannunta aka yi suna faɗa mata halin da yaran suke ciki.
Lumshe idanu tayi kafin ta ce musu. “ina Malik?” Yadda tayi tambayar yasa suka zuba mata idanu, kafin aka mata allura barci yayi gaba da ita, sai Washi gari ta farka, shima da sunan Malik ta farka.
“Ina mijina?”
Shiru suka mata aka rasa wanda zai bata amsa, Hajja Yayye ta fara da nasiha. “Zainaba, rayuwa da mutuwa na Allah ne, ki yarda Allah zai kara baki.”
“Yaron ne ya mutu!?” “Ko daya!” Shiru tayi tana kallonsu cikin wani mawuyacin hali ta ce. “Daadi ne ya rasu?” Juya baya Ammyn tayi tana jin kuka na taso mata, bata san hikimar Zulfah da Elbashir da suka ce a boye mata yana raye ba, amma kuma akwai cutarwa idan aka cigaba da ajiye maganar a sirrace.
“Hajja Yayye! Shine ya rasu?” Jinjina kai tayi tana matse kwalla. Domin ko ita ba a gaya Mata ba, gudun kada ta ce musu babu kyau, amma nufin Elbashir ya san ya Zeeno zata amshi labarin mutuwar Malik?
*Kiyi hakuri! Wata rana zaki ji abin da ya faru, promise me, idan kika tafi ba zaki yi kukan bana tare dake, ki min alkawarin ba zaki yi kuka idan wani abu ya faru da ni ba, ki min alkawarin zaki bawa dan mu kulawa har girmanshi! Zainab ina sonki, ina kaunarki. Zan zauna jiranki da jiran kiranki. Kira daya kika min zan zo gare ki! Da kira daya kawai!* Wani irin ƙara kanta yake mata a cikin, ta lumshe idanunta tana jin yana juya mata, “Na kashe shi ko? Eh nice na kashe shi,” sai kuma ta fashe da kuka, kafin ta fara haki, kiran nurse suka yi. Aka fara kokarin hanata shiga attack. Amma ina tayi nisan kiwo. Sai da suka shafe awa biyu akanta, kafin ta farfaɗo. Amma barci yayi gaba da ita.

Haka alamarin ya kasance, a can bangarenshi. Ya farfaɗo kuma Elbashir ya gaya mishi gaskiyar abin da suka yanke. Ai kuwa sun sha faɗa, kamar ya dake su amma kuma daga baya sai ya ga kamar sun mishi kome, ta haka zai saka tasan amfaninshi. Sai dai kuma wani abun mamaki shi ne. Tun daga ranar Malik yake fuskantar hatsari mafi muni. Domin kuwa hari ake kawo mishi ta ko ina, har zai aka yi isolate din shi a barikin sojan kasar, daga nan yake samun duk wani kulawa.

Gidanshi kuwa sojoji ne ba na wasa ba, a hankali gwamantin kasar ta fahimci yadda ake tunkarar Malik da fitina, tow su abin zata shafa, domin ko daukar ma’aikata da yayi ai ba na wasa ba ne. A kamfanonin shi, wanda taɓa shi ya janyo zanga-zanga a kasar baki daya, suna sa state goma sha huɗu, sannan a cikin states din nan, yana da kamfanonin shi na kansa, bayan nan kuma gwamnatin kasar baki daya, tana samun kudin shigarta ne ta hanyar ma’aikatan shi da suke bin manyan Bus da taxi zuwa wurin aiki.

Taya ma zasu so a kawo karshen Malik, dama a duk lokacin da aka samu wanda ua ragewa gwamanti aiki, ba karamin nasara ake samu ba. Don haka aka kara ninka tsaro sama da baya a barikin da yake, sannan aka shiga bashi duk wani kulawar da ya dace, a wani majiya mai tushe, ta tabbatar da cewa. Ai kusan duk wani shugaba ko primeminista, tow Malik shi yake tsayawa a samo adali.

Haka yasa bayan party ɗinshi na siyasa, babu abin da ya dame shi, shi yana gefe guda yana nad’a wanda ya so ne, ya kuma sauke wanda yaso, ko primeministan da aka kashe, ai Malik ya saka aka daura shi, tare da alqawarin zai rike ƙasar da Al’ummarta, sai daga baya abubuwa marasa dad’i sukayi ta fitowa, sannan ko Khuldu Jahid Khan, yasan baya cikin jarin makiyanshi. Haushin shi sa Khuldu yake ji don ua kashe mishi ba bane, da bai kashe mishi uba ba, tow Banu abin da ya dame shi.
Sannan wani abun da yake damun Malik a wannan harin waye ne? Waye yake niman rayuwarshi? Yasan Ba Shatima bane tow waye ne?
Waye ne yake bibiyar rayuwarshi haka? Yasan Amjad yana hannunsu, sai Shu’iba yana sane da shi na zai iya ba, duk wanda yake bibiyar rayuwar Malik yasan shi, ya kuma san waye shi, ya shiga jikin Malik. Wannan yanayin yana mishi kama da wanda ya san waye shi, zaune yake a dakin da ke cikin gida na musamman. Ya zubawa Elbashir idanu da yake ta aiki da computer. “Bashir ko kai kake bibiyar rayuwata?”. D’ago kai Elbashir yayi yana kallon Malik. “Idan da ina son kashe ka, tuntuni zan yi haka. Sannan ba zan tsaya a gefe ina sararka ina boyewa ba. Malik idan ka kuma.kiran suna na Alqur’an sai na shigar da kai karar cin zarafi da sharri.”
“Allah ya baka hakuri kaji”
“Ban yi hakuri ba! Nace ban yi hakurin ba!”
“A’a al’amarin ya kai har haka? Tow kayi hakuri!”
“Malik sai nake ganin, kamar wanda ya san mu yake kawo mana irin wannan harin. Domin haka kawai ba za a samu me zuciyar kawo maka hari ba!”
“A wannan ranar da abin ya faru, akwai wani abu da na gani a tare da wanda ya harbe ni. Kasan me?” Girgiza kai Bashir yayi yana gyara zama. “Na ga wani abin hannu, wanda Lauyar Baba yake sakawa!”
“Ikon Allah, kace fansa ce kawai ake biyar ka da shi!”
“Yes Fansa ce! Na gamsu babu abin da tafi fansa kawazuci! A nimo iyalan shi, domin ta haka ne zan san ta iya nayi kuskuren.”
“Ta hanyar kashe mishi mahaifi! Ka kashe mishi mahaifi shima yazo daukar fansa kana tsammanin zai kyale ka ne? Don haka dole musan waye shi sai mu shiga bibiyarshi!”
“Ya Allah! Me yasa ban san cewa wani xai biyo bayana daukar fansa ba? Me yasa ban gane cewa daukar fansa yana iya zama alakakai, gashi nayi nawa . Wani yazo yana nashi. Ga na Zainab a ajiye a gefe wallahi na rasa yadda zan yi da rayuwa, Zainab ta rufe Ni” “kada ka damu zamu yi iya kokarin mu, mu nimo bayanin Lauyan babanka, domin ta haka zamu gano bakin zaren”

Dafe goshinsa yayi, kanshi kamar zata yi bindiga. Ya zubawa Elbashir idanu kafin ya ce mishi. “Ma rasa mene min dadi baki daya na cilla rayuwata cikin matsala!”
“Banu wata matsala kome zai zama da sauki in sha Allah ”
“Anya kuwa?”
“Da gaske!”
“Jeka wurin matarka mana”
“Tow xan tafi Malik, amma ka daina zargina domin raina yana ɓaci “….
*WAYE NE WANNAN ME ZUCIYAR KAIWA MALIK DIN MU HARI?*
*Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/27, 10:26 PM] Yan Mata: 38-Shiru Malik yayi amma yana ji a ranshi, tabbas akwai matsala wanda yake bibiyar rayuwarshi ba karamin Sani yake da shi akan shi ba. Lumshe idanun shi yayi kafin ya buɗe. “Kasan me Elbashir?” Juyawa yayi yana kallon Malik. “Da fatan ba sharri zaka min ba?”. “kai dai baka da hakuri! Wanda yake bibiyata. Izuwa yanzu yasan ina barikin sojojii me yasa bai kawo min hari ba?” Kallon Malik yayi kafin ta ce mishi. “Me yiwa yana tsoron farmakin sojojin Keivroto ne? Me yiwa kuma yana son sai ka fita zai dauki matakin da ya dace!” Kawai bai san me yasa zuciyarshi taki yarda da Elbashir ba, gani yake kamar akwai hannunshi a cikin abin da yake faruwa, don haka ya mike tare da ɗaukar kayanshi yana faɗin. “Bari na fita cikin town na ga me zai faru?” Rike shi Elbashir yayi yana zaro idanu. “Baka da lafiya ne?” “Ras nake da lafiyar kawai jikina ne, yake bani fitatta shi ne karshen rikicin da yake faruwa!” “A’a Malik ba mafita ba ne, don Allah kayi hakuri ka bar fitar nan, kai Uba ne yanzu, ko dan Yaranka ka tuna da halin da Zainab take ciki ya zata ji idan ta kuma jin labarin wani abu ya same ka?”
“Zata ya min, amma bari na tafi dai!”
“Don Allah kada ka je, yau nake son fara amarcina don Allah kada ka bata min daren yau da tashin hankali.” Ware idanu Malik yayi yana kawai Elbashir duka. “Kai dan iska dama ajiyeta kayi kamar hoto?” “Hmmm kawai ban yarda da ita bane, amma yanzu naga duk abin da yake faruwa bata sani ba, shi ne nake son mu!”
“Ai kuwa kasan ba zan zauna a cikin gidan nan ba, Gara na fita.”
“Haba Malik”
Elbashir ya rike kafarshi, yana dariya.”wallahi baka barin gidan nan, haka kawai ka ja min masifa a wurin matarka da take can bata waye a kanta ba.”
“Tow uwar me zan maka?” “Ka zauna dai mu ta ganinka wannan ma arziki ne!”
“Kai bani zama a cikin gidan sabin aure, ku lalata min tsufa na.” Ya faɗa yana dariya, kusan don dole Malik ya hakura da fita. Amma a ranshi yana shirye da ya fitan, don haka ba tare da Elbashir ya sani ba, ya shirya wani fita na musamman, Cikin dare inda tare da wasu zakwakuran sojaji.

Abin da suka fara shi ne, bibiyar shiga da ficcen mutanen da suka ziyarci 3stars a cikin kasa da wata shida, a watanni shidar an raba shi gida uku, wata biyun farko. Sai wata biyun tsakiya, sai wata biyun ƙarshe. Sannan baki ɗaya, an ga mutanen da suka shige da ficce a unguwar kasancewar sojojin akwai masu kaifin basira, suka tattara kome, suka bar wurin da Malik. Wani abin mamaki sunyi bincike a daren har zuwa gari ya waye.. sannan suka mikawa Malik sakamakon da basu samu wani gansashen bincike ba. A lokacin ya kira Yasir Aswad da Zulfah ya basu aikin domin ya gama shirin fuskantar makiyin shi.
Su suka cigaba da binciken daki-daki da har inda aka yi abin, wanda akala xai dauki wani lokaci. A gefe guda kuwa Elbashir murza amarci yake babu ruwanshi, sanin haka yasa Malik yaki zaman gidan domin kada ya ga abin da zai dame shi. Kuma ko ba kome ya basu damar su sarara da junansu. Binciken da suke yi ne yafi daukar hankalin shi. Domin kuwa a cikin kwanakin da ake binciken nan. Da dare aka buga gidan Zulfah Allah yasa akwai yan sanda a kofar gidan, aka ajiye mata wani kwali a kofar. Ba ita ɗaya ba hatta yan sanda sun sha mamakin yadda aka kawo kwalin aka ajiye.

Hoton Zeeno da Yaranta aka saka alamar (×) da jar pen. Shiru tayi a lokacin ta kira Malik da Yasir ta gaya musu, kai tsaya headquarter yan sanda suka nufa, duk da dare yayi. Malik bai hana shi zuwa ba. Yaranshi guda Uku. Da matar shi da yake so kamar me? Hmmmm. Ya faɗa yakai sau ba adadi, yana kallon al’amarin kamar wasa, sai zaga cikin office din yake yana kara kallon hoton Yaran.
“Ku yi min hanyar magana da shugaban yan sandar Nigeria, ina son magana da shi.” “Yallabai zata yiwu barazana ce!”
“Barazana da rayuwar iyalina? Barazana da rayuwar Yarana? So kake na koma gefe nayi ta kallon abubuwan da suke faruwa kamar wasa? A hada min waya da shugaban yan sanda Nigeria, su rubayya tsaronsu kan iyalina idan ba haka ba.” Ya juya ya bar office din yan sanda.

Tabbas abun yana son shan kanshi, jifa daga kanshi zata fada kan Yaranshi. Kafin gari ya waye Yasir Aswad yayi magana an kara tsaurarra tsaro a asibitin domin halin da ake ciki. Lokacin da gari ya waye Malik ya fito da shirin zai fita Elbashir ya kalle shi. “Jiya da kafita baka dawo da wuri ba!”
“Matata da Yarana suna cikin hatsari!”
“Innalillahi wa inna illahirirajuun, kuma dai?” “Tow me zan ce maka? Matata da Yarana suna cikin hatsari ina fatan ka fahimta. Koma waye yake bibiyata idan na yi idanu biyu da shi, sai na aika shi lahira. Domin haukar shi da shirmenshi ya tsaya a kaina kawai!”
“Malik ka nutsu!”
“Taya zan nutsu! Me bibiyar rayuwata, yana can ya raba mana aiki. taya zan yi barci matata da Yarana suna cikin masifa! I will turn myself, shi kenan Yarana da Matata su samu yanci!”
“But why Malik!”
“Na hakura da kome, amma matata da Yarana bana son su fuskanci ƙaddarar da ma fuskanta, Ina son suyi rayuwar yanci da Mahaifiyarsu.”
“Tow Malik ya zayi kenan?”
Zama yayi ya lumshe idanunshi kafin yaƙ ce .
“Ban san me zanyi ba, kawai ina kan nazarin abin da zai yiwu ne ” “mu barwa Allah kome, mu ga abin da zai faru.” “Allah ya kawo min dauki” “Amin Ya Allah!” A cikin kwanakin nan, idan ka ga Malik sai ya baka tausayi, domin ya masifar laushi da shiga tashin hankali. Sannan damuwar tayi mishi yawa. Wanda yaja shi faduwa bai shirya ba, domin har kullum barazanar da ake mishi kara yawaita yake sosai, domin har an kai, an turo mishi da cewa.
*Likitocin da suke asibitin babu wanda ba zai min aiki domin kudi ba*
Lumshe idanunshi yayi, kafin ya mike tare da ɗaukar top dinshi ya fita, bai tsaya ko ina ba, sai tsohon gidan lauyan Babanshi. Gidan ya koma kango, babu kome a cikin gidan sai ciyawa, shiga yayi yana nufar cikin gidan. A bakin kofar tsakar gidan ya tsaya. Sakamakon hango mutum zaune da bakaken kaya, an juya mishi baya.
“Gani nan, free my family!”
★★★
Tun da ta farka, kusan bata da abokan hira sai Yaranta, idanunta yana kansu. Daukar wanda ya dan fi sauran girma tayi, tana kallonshi yadda yake kama da Malik. “Kuyi hakuri! Ni ce na raba ku da shi, na kuma kashe muku shi. Kada ku tsane ni don Allah.”
“Madam idan kin gama basu nonon, zamu mai dasu cikin wurin kwanciyarsu.”
“Tow!” Ta ajiye shi, tana me gyara mishi kwanciyarshi. Sannan ta dauki dayan ta rungume shi, tana shashekar kuka. Sannan ta ajiye shi ta dauki macen tana shafa fuskarta. Wani irin kaunar Yaran take ji. Haka ta fito a hankali ta nufi dakinta. Dake babu nisa da ward ɗinsu. A hanyar ta na komawa dakinta ne. Wata mata ta bangajeta. Har ta kusan faduwa. “Ke tinkiya baki gani ne?”
juyowa matar tayi, hannunta dauke da karamar wuka. Gyara tsayuwa tayi tana kallon matan, yadda ta nufota a shirye. Yasata kura mata idanu. Tana isowa, ta kai mata wukar da sauri ta goce matar ta fadi. Sake juyowa tayi a fusace ta kuma kauce mata, a karo na uku ne, ta koma asalin yar kunamarta, wato Xnoo, tana kawo mata wukar zata yanketa. Tayi maza ta rike hannun tare da murgud’a mata shi, sai da ya karye. “Da alamu turo ki,aka yi idan har nice ki gaya musu su shirya irinki, goma.” Ta karya hannun, sannan ta take kama kafa sai da ta targad’a yatsun.

Wani irin tsoro ne ya kama matar, “ki gaya musu. Ni ba kanwar lasa bace, ban yi wannan lalacewar ba” ta kai mata naushi a fuskarta, matar ta sume a wurin sai lokacin yan sanda suka karaso, a hankali ta jingina da bango. “Da fatan kina lafiya, ku kama matar ku tafi!”
“Lafiya lau,ita ce zaku duba domin ta suma. Kuyi magana da shugaban asibitin nan, a mai da min Yarana dakina.”
“Tow!”
Daga haka ta wuce dakinta, tana haki domin baki daya ta gaji, rabonta da ta motsa jini ta jima. Tun kafin Malik ya aureta. Yau kuwa tayi da hujja. Kafin ta gama hutawa, An dawo mata da Yaranta, tunda gansu, barci me nauyi ya dauke ta.

Washi gari yan sanda, suka zo tambayarta, ta fadi abin da ya faru. “Ban san me yasa ta farmake ni ba, amma kuma nasan ba mamaki daga Keivroto zata zo domin daga can ne, kawai abin da na sani haka kawai ba zata kawo min farmaki ba, sai da dalili meye dalilinta?”
Shiru suka yi, kafin suka ce mata. “Mun tambaye ta, amma har yau bata bamu amsa ba” shiru tayi kafin hawaye ya zubo mata, wato tun daga ranar da ta rabu da Malik bata cikin nutsuwa, yau gashi nan an fara bibiyarta.
“Ba mamaki suna haka ne, saboda abinda ya faru da mijina, ko nace don mijina suke bibiyar rayuwata. Amma bayan nan nasan bani da wata mummunan alaka da wani, sai ta alkhairi. ”
“Tow tace an turo su ne, domin an biya su iya adadin da zasu kashe ke ko Yaranki, sannan wannan abin da muka fahimta tana aiki ne anan don haka zamu mai da ki gida, ki cigaba da jinya a can saboda rayuwarku tana da muhimmanci!” Hawaye ya zubo mata, ta saka bayan hannu ta goge, tana faɗin. “Shi ma ba laifinshi bane, wasu suka daura shi a haka, da zasu fahimci yadda rayuwar shi take baza su tsane shi ba, babu ruwanshi kawai ƙaddara ce, don Allah su bar mishi Yaranshi, idan ta kama ni ce, su hukunta ni da abin da ya aikata na amince na yarda. Amma Yaranmu babu ruwansu.”
“A’a Madam, zamu duba al’amarin nan, ba zamu bar su, su bata mana gari ba domin yin haka kamar tozarta hukumar tsaro ne, don haka zamu mai da ki gida, ki cigaba da jinya”

Fita suka yi, bayan Ammyn sun hada mata kayanta, suka fita suna jimami. Ita kuwa kuka take, tana karawa kaunar yaran kamar me ya cika mata rai. Yanzu kalaman Malik ya dawo mata, dama yasan haka zai faru ne yasa shi cewa.
*Zan baku kome zan baku damar kome, amma ki sani ba zan tab’a cire idanu akan ku ba, ko ƙarƙashin ƙasa kuke. Idanuna sa zuciyata tana tare da ku. Kune Duniya ta, kune rayuwata, farincikin da nake yana tare da ku ne, amma zan hakura da nawa farincikin na baku kuyi, na barku Ku rayu cikin aminci da salama, na san kinyi fushi ne idan kika yi sanyi zaki fahimce ni, Albashir zai kawo miki duk abin da kika bukata, duk abunda kike so akwai ki bukata kawai, sannan na amshi number Kawunki na can Maiduguri, zan saka a tura duk abinda zaki bukata na haihuwa. Zainaba don Allah, kada ki cusawa Yarona ko yarinya ta, kiyayyar da kike min. Don Allah na hadaki da shi.”*
Wani irin kuka ne ya kamata tana yi tana karawa.

★★★
“Gani nan nazo ka kashe ni, ka bar min zuri’a ta, sun zauna lafiya bayan nan shi kenan! Ina magana ne kaki kula ni waye kai? Nace waye kai?”
Ya kai hannun kenan zai tab’a, aka juyo gare shi, with all surprise ya ce.
“Ke ce??……..
Happy weekend 🤗🤣🙄
*Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/27, 10:26 PM] Yan Mata: 39- “Nice Daadi Malik!” Wani irin takaici ne ya kama shi, ya kura mata idanu. “Me yasa Nadrah?” Hawaye ne ya zubo mata. “Saboda Abbana!” Kura mata idanu yayi, yana sauke wata numfashi “Ok muje naji domin Abbanki kika yi, babu me miki kome muje!” Ciro wuka tayi zata yanke shi. “Me yasa..” wani irin ƙara yaji a tsakiyar kanshi. Wanda ya tilasta mishi faduwa babi shi. Domin baki daya ya dauke wuta, wasu matasa ne a tsaye. “Daure min shi, na tsani mutumin nan, ke kuma kin yi abin da ya dace zaki iya tafiya.” “Shi kenan da fatan babu wani matsala ko? Domin ina tsoron kada a kama ni na rasa inda zan saka kai na, ga Abbana ban san inda yake ba!”t faɗa kamar zata yi kuka, tsayawa mutanen suka yi, sannan daya daga cikinsu ya ce mata. “Kije abinki, shi wannan karen zamu kashe shi, ai kin gama mana aiki.”
“Da fatan suna na, ba zai fito ba bana son a kamani!” Kar’ar motar yan sanda ne, ya cika unguwar, babu shi matasan suka tsalleke Malik suka gudu, sai Nadrah da take tsaye ta kasa gudu, a wannan takin ina zata? Gara kawai a kamata abin da take gudu kenan. Kuma gashi ta faɗa hannunsu. Da gudu suka shigo gidan, ganinta tsaye da wuka tana nuna Malik yasa suka dan dakata. “Kin ga ki ajiye, wukar.” Wuyarta ta kai wukar. “Ku kyale ni, ko na yanke wuyata.” Tashi dakyar Malik yayi yana rike kanshi. “me kike so nayi?” “Abbana nake so, ka nimo min!” Kallonta yayi tare da mika mata hannu. “Ba ni zan nima miki, shi i swear!” “Kace kada su kama ni.” “Shima na rantse miki babu me kama ki.” Hawaye ne ya zubo mata ta ce mishi. “Me yasa ka fasa aurena?” Ta saka wukar sosai, a wuyarta. “Daadi Malik me yasa kace ba zaka aure ni ba? Ka je ka auri street girl! Bani da quality na matar da kake so ne? Ko ban isa na aure ka ba ne?”
“Nadrah! Ki bari muje gida!” Wani uban ihu tayi tare da buga kafarta a kasa, tana faɗin. “Me yasa ba zaka bani amsata ba? Ita wancan yarinyar da me ta fini?” “Bani sai na gaya miki abin da baki sani ba!” Kallon cikin idanunta yayi, na wani lokaci kafin ya sunkuyar da kai ya ce mata. “Are taking drug’s?”
“Me yasa ba zan dauka ba? Kaina ya gaza daukar kome, da kai nake kwana da kai nake tashi, me yasa ba zaka gane ina sonka ba.” “Ok na yarda kina so, shi kenan ajiye wukar kada ki cutar da kanki, domin bana son ganin tab’o ko karami ne a jikin matar da zan aura, so nake jikinta ya zama kamar na maciji.” Sake wukar tayi, a hankali ya taka gabanta, zubewa zata yi ya tare ta. Ta kwanta a jikinshi. Tana kuka tare da dukar kirjinshi. Cak yayi sama da ita, suka fita a gidan. Kallonshi Zulfah tayi na wani lokaci, kafin ta kauda kai. Tana taya yar Uwarta kishi. “Ina ga zamu kaita asibiti sai mu saka jami’an tsaro su kula da ita.”
“A’a zan wuce da ita, gida kawai likita zaku turo min, sauran bayanan zuwa jibi sai mu bincike ta.”
“Shi kenan!” Ta fada tana barin wurin. Haushi ne cike a ranta, sai kumbure kumbure take, sai da suka wuce kafin ta tuna ta tura mishi. *AN KAIWA ZEENO HARI AMMA Allah ya tsare babu abin da ya faru ita da yaran suna gida!* Yana tuki ya gani. _Allah ya tsare_ yasan duk rikicin Zeeno akan idanunshi da gabanshi take, yayi imani da Allah, mutuwa ce zata shiga tsakaninsu da Yaranta. Da tana da hali ba zata bari wani abu ya cutar mata da Yara ba, ua yarda da matar da ya aura.” Ya kuma yarda da wacece ita, don haka ya wuce abinshi, har cikin barikin ya shiga da ita, a falon gidan shi ya kwantar da ita. Elbashir ya fito rike da cup. “wace ce?” “Kai makaho ne?” “Ba mamaki!” “Hmmm!” Leka fuskar yayi, sannan ya ce masa. “Yar shatima ce?” “A’a Shatima ne!” “Dadina da kai bakar magana, tow me ya faru?” “Ita ke turo min sakon barazana!”
“Hmmm! Kuma shi ne kake jin haushina? Tare da min sharrin ni nake bibiyarka.”
“Ai inda matsalar take, ba ita ke bibiyar ba, wani ne na daban, wanda ya san ni kwarai da gaske!”
“Tow Allah ya tsayar haka, kada a kuma min sharri domin wallahi ba zan yarda ba.” Ya faɗa in serious tone, tabe baki Malik yayi, kiran wayar Zulfah tare da gaya musu gasu tare da likita, yasa dole suka yi shiru. Har cikin gidan sojoji suka rakota, tare da wasu likitoci sojoji, suka zo ana duba abubuwan da za a mata amfanin dasu kama daga allura drip, da kome sannan suka dibi jininta.

Yadda zaka san, ana girmama Malik, a tare aka tafi da shi lab na sojajin aka gwada, na tsawon awa hudu, kafin aka dawo da shi. Amsa Dr Abdulwahab yayi yana dubawa, soja ne. “Taya yarinyar nan ta samu, sinadarin Cocaine a cikin jininta? Wanda karfinshi ya kai ya kashe mutum.” Duba hannunta suka yi, suka ja rigarta saman hannu. Fatar wuyar hannunta, ta sama har wani irin ja da kore yayi. “Me ta faru ne?” “Babu wanda ya san asalin abin da ya faru, sai dai ta ce min mahaifinta take nima! Duk wanda ya santa, tow yayi amfani da kalmar mahaifinta ko abin da yake tsakanin mu ya yaudareta ne, amma na yarda da nagarta Yarinyar.”

“Gaskiya tana da nagarta shi yasa, ni har kwnaan gobe ka ke min fatar na zama Ni ke cin amanarka!” Inji Elbashir da yaji haushi. “Bashir wannan ba abin wasa ba ne!” “Abin wasa ka dauki magana ta? Ko ka ga na maka kama da me wasa? Kasan yadda nake ji kuwa idan kace bakan yarda da ni ba? Is killing me insane. Karfin hali nake domin wata rana zaka gane, haka ka daina zargina. Bana kaunar ko ciwon kai ya same ka. Amma kai dake dan ku…”
“Jama’a kun ga zagina Elbashir yake, har na kai ka zage ni?” “Eh na zage ka, wallahi ka kuma zargina tafiya zan yi ba Barka, sannan ka mikawa hukuma yarinyar nan, domin bata da wani amfani a wurinka. Idan na kuma ganinta sai na kira Zeenobia na gaya mata ka fara kwashe-kwashen mata.”
Abin dariya ya bawa su Zulfah, saboda rigimar kamar ta yara, “Yanzu Zulfah me ake ciki!”
“Hey! A fitar min da yarinyar nan, a gida domin bata kuma zama ayi maza waje da ita.”
“Heey hey!! Babu inda zata, na gaya maka zama zatayi domin aurenta zan yi?”
“Kutumar uba?” Elbashir ya fada. “Billahi Azim baka isa ba, aurenka da Zainab mutu karaba, duk shegen da ya gaya maka zaka kuma aure ya gaya maka karya ne, don ubanshi, kuma na gaya maka Zainab ta cinye kome naka, yara uku ai baka da kome a cikin dukiyarka ita da Yaranta suke da iko da shi.”
“Tow kuyi fatan na mutu mana, sai ku raba dukiyar da hujja!” Ai kuwa rigimar gaske , aka yi kafin kuma aka ajiye Maganar a gefe. “Elbashir zaka tafi Nigeria, kai da matarka. Kayiwa Yaran huduba, macen ka saka mata sunan Maidah, mazan ka saka sunan mahaifina da na Zainab!”
“Na me zaa saka sunan Maidah, kana nufin.” “Kayi yadda nace, ina sane nace haka!” “Shi kenan Malik!”
“Ita wannan yar kwayar fa?”
“Aurenta zan yi!” Malik ya fada babu wasa a kalamanshi. “Me yasa to?” “Saboda idan na barta tana watangaririya a gari, wani zai kuma amfani da ita, idan na aureta babu me sauya mata tunani!”
“Amma Yallabai Zainab ba zata ji dadin haka, zata ga kamar mun boye mata ne. Gaskiya ba zan iya daukar wannan rigimar ba.”
“Hmmm! Nima haka nake ji, haka nake ji amma for sake of my family, har da ita Zeeno saboda ita, da Yaranta. Ba don rayiwata ba. Idan na bar Nadrah ta fita a hannuna ban san waye zai kuma sakata a cikin yanayin fansa ba. Kin san kaifin Fansa kuwa? Yafi wuka kaifi don Allah ku fahimce ni.”. “Idan matarka kake bukata, ba sai mu tafi Nijeriyar da kai ba!” Murmushi yayi yana kallonshi. “a duk inda haka ya taso, dole cikin biyu ayi daya. Imma ka hakura da kome ka rungume ƙaddara imma ka amshi kome a zauna lafiya, a halin da muke ciki da Zeeno bata gaya min matsayina na mijinta tana son zama da ni bata son zama da ni. Zainab ta ajiye ni ne, domin na jira kiranta. A wannan lokacin matukar ba ita ba ce, ta nemi ni ba zan tab’a kai kaina gare ba, kun san yadda zaman jira yaƙe? Koda kuka gaya mata na mutu, ya kamata ace ta kira layina taji da gaske ina raye? Amma dake mace ce, ba zata kira ni ba. Sai lokacin da wani abu me karfi ya tab’a ta, a nan ne zata nime ni, a lokacin ni ma zan tafi da kwarin gwiwata.

Amma a halin yanzu ba zan tab’a kai kaina gare ta ba, domin ina iya zuwa ta min wulakanci, na san wace ce ita a banza zata min wulakanci a gaban uban kowa. Tow ban da mace wacece zata maka haka? Musamman aka yi katari kana sonta kamar yadda kake son kanka, ai magana ya kare. Sai ayi ta juya ka kamar dan duros.”
Me zasu yi ban da dariya, domin maganar Malik akwai abin tausayi, amma kuma abin dubawa ne, tunda ya tona damuwar da take ranshi, haka yana nufin yana matukar azabtuwa da matsalar shi da Zeeno, sannnan gefe guda yana jiran ta kira shi, kiranta kawai yake jira, da kira daya zata gyara wasu abubuwan. Amma har yau bata kira ba, shi kuma bai ji a ranshi ya nime ta, tunda yana jin labarin halin da take ciki.

Da wannan bayanin aka rufe kome, sai dai akwai binciken da za ayi wa Nadrah, wanda dole yana bukatar sai ta nutsu, idan bata nutsu ba, dole haka zata kaita ofishin yanda, su kuma su turata ga kotu . Yarda da tayi da Malik yasa baki daya, take jin zai aureta, kuma zai kare ta daga duk wani abu. A bangaren Malik kuwa, shirya Elbashir da Matarshi yayi suka tafi zuwa ganin Zainab, wani abin mamaki kuwa yadda yayi ta sayayyar da za a kai musu, kome ya saya sai ya raba biyu. Ya ajiye rabi, “su kuma rabin na meye?” Elbashir ya tambaye shi, yana kallon. “Na matarka!”
“Ce maka nayi tana da ciki?” Lumshe idanunshi yayi ya mai da shi kan Elbashir ya ce masa. “Ni dai naga al’amarin nan gaba, sai na ci dan banza duka a hannu ka.” Dauke kai Elbashir yayi yana faɗin. ” Ka ga ni bana son sharri, babu dukan da zan maka, kawai dai nasan bata da wani ciki. Idan kuma akwai tow daren jiya aka same shi!”
“Koma meye na dai saya, idan bai maka ba. Sai ka watsar da shi.” Ya faɗa tare da ɗaukar wani takalmin Yara, musamman na jarirai. Ya jida kaya kamar bai san ciwon kudi ba, sannan suka je aka biya kuɗin suka nufi gida. Lokacin da suka isa sun samu Nadrah a wurin wanka, dauke kai suka yi, domin baki daya yarinyar tana masifar attempting ɗinsu. Musamman yadda take sexy dress. Jiya sai da aka kai ruwa rana da Hafcy da Elbashir, wasu irin karuwan kaya ta saka sannan ta zo ta tsaya mishi a kai.
Wai ya duba mata, meye ya samu wayarshi. Dauke wuta yayi, suna tsaye sai ga Hafcy tana ganinta shine na mata ya motsa, ta ture ta waje, tana faɗin. “kin kasa auruwa ne kika zo zaki lalata min mijina, mayya mara kunya kada na kusa da miji.”.
“Hafsat me haka?”
“Meye kuwa bayan abinda idanunka ya gani, kai kuma ka tsaya kana kallonta, tsirara ne bana yawo a cikin gidan nan, tun dare kafara surta har tsakiyar dare, ba barina kake ba, shine har akwai wata karuwar da zata burge ka wallahi sai na kashe ta….!”.
*Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/27, 10:26 PM] Yan Mata: 40- Rungumeta yayi yana me sumbatar wuyarta. Zata kuma magana ya ce mata. “shiiiii! Ya isa haka, a yanzu babu ra’ayin aure amma idan aka cigaba da da barin waɗannan yan matan suna irin wannan shigar, tow zan haukace na karo aure, babu shiri.” Sake Rungumeta yayi yana dariya, yadda take kuka cike da sakalci da shagwaba. Duk hayaniyar da ake Malik yana jin su, ina zai iya da damuwarsu.
Nadrah da taga Malik bai wani dauki mataki ba, sai ta kyale su, ta kuma tsoro yawon dare. Kafin Elbashir su bar Keivroto Malik shima ya shirya visar kai ta wurin dangin Mahaifinta, tare da nuna mata shi maganar aurensu ne a gabanshi ,a tunaninta haka ne, har su Elbashir suka bar kasar, sannan shima ya sakata a gaba suka nufi kasar iyayen Shatima Dan kasar Gabon, domin su fulanin can ne, koda suka isa wani abun mamaki sun samu kyakkyawar tarb’a daga wurin dangin mahaifinta.

Duk da sai yamma suka sauka, basu samu zama ba. Sai Washi gari da safe bayan sun karya. Ana ya tara su baki daya. Ya saka Nadrah a tsakiyarsu, sannan yayi shiru ya ce musu. “Kune yan uwan Khamis, Ni bani da matsala da kowa amma a gefe guda, Khamis yana takun saka da ni da nayi kokarin magance matsalar amma ya kuma sako yarshi, idan ma ba shi bane. Hmmm ku mata fada, domin ni uba ne a gare ta kada ta kuma yunkurin shiga rigimar mu;”
“Dama an gaya min, ka kware a cikin amana da yaudara, me yasa ba zaka fadi exactly abin da yake ranka ba, sai ka buge da min alqawarin ka aure ni?”
“Ko da can baya ban yi miki alkawarin zan aure ba, ki gane ina da matar da nake so. Ina son Zainab sosai, koda zan aure ki ba zan iya nutsuwa naci ko na sha daga gare ki ba, saboda kin sha yunkurin kashe ni, daga ranar da na kai ki inda nake, sau nawa kika zuba min magani a cikin abin sha? Kin san me? Koda na ke zaune da Khamis ban tab’a yunkarin kashe shi ba, amma burinshi ya ga baya, ban san me yasa ba.”
“Ina sonka”
“Baki sona,wani abu kike nima daga kin samu zaki rabu da ni” daga haka ya kalli dangin mahaifinta ya ce musu. “Gata nan, ba zata gaya min wanda yake sakata tana wasu abubuwan ba, amma nayi imani da Allah, daga ranar da gaskiya tafito, zan hukunta har ita ba zan bari ba wallahi!” Ya mike yana kallon agogon hannun shi, ya ajiye mug din hannunshi yana faɗin. “ban yarda da cin kome a hannun kowa ba, ga tea dinku. ” Ya ajiye ya kalleta tana kallonshi. “Tow cikinka na jikina ya zanyi da shi?!”
Idan bata yi haka ba, ai ba jinin Khamis ba ce. “Ki zubda ko ko barshi ya rayu, matsalarki ce!”
“Dole ka aure ni, domin na riga da na turawa Yar gwal dinka. Matar da ta ƙasa yarda da kai, a karon farko kayi nazarin taya zata yarda da kai a karo na biyu. Ba zaka aure ba, haka kuma nayi alqawarin ba zata zauna da kai ba.”
“Kin kyauta, na san hanyar da zan ganar da ita.” Yana gama fadar haka, ta juya ya fita yana jin kamar yayi ya tarwatse ya huta, yarinyar ta shayar da shi mamaki. Haka ya bar gabon babu wani ci-gaba domin dai yasan akwai wanda yake behind din ta.
Idan da yasan tarkon Nadrah da ya faɗa, toh kuwa da ba zai tab’a barin garin ba, sai ya tisata a gaba har Maiduguri.
Amma ina baki daya, kome ya wuce tunaninshi, bai tab’a sanin haka zai faru ba, kuma koda ta gaya mishi abin da tayi bai yarda zata yi ba, domin dauka yayi tana mishi barazana ne, bai san zata aikata ba.
★★★
Maiduguri.
Kusan kwana biyu kenan da Zulfah ta gaya mata, gasu nan zuwa da Elbashir. Ita tasan iya shi da Zulfah zasu zo. Bata kawo a ranta zasu zo da Hafcy ba. Sai da suka iso.

Aka je aka dauko su, tana zaune a falo, suka shigo a tare da Zulfah, Hafcy tana bayansu. Mikewa tayi tana kallonta kafin ta ce.”Ki fita a gidan nan, kafin na baki mamaki.”
“Zeeno ki saurare ni don Allah!”
“Wallahi ba zan saurare ki ba, yanzu ma ban san da me kika zo ba, ki cutar min da Yarana. Ina tsoron Allah ina tsoron mutumin da na mishi rana, ya bini da masifa oya fita.”
“Zainaba! Malik yana raye.” inji Zulfah Dafe kirjinta tayi tana zare idanu, “Yana raye?”
“Eh yana raye, ki bar maganar Hafsah sai na kira shi kuyi magana ma ” ta cigaba da da gaya mata abubuwan da bata sani ba, a haka ya mantar da ita zancen Hafsah an aka shiga hira da Elbashir yaushe gamo.
Ba karamin hira suka yi ba, sannan aka basu yaran, ita kan sai da Hajja Yayye ta fito tayi ta mata fada, baki sun zo ba a basu abinci ba. Daga nan aka shiga jera musu abincin. Yara kuwa ana kawowa Elbashir yayi musu huduba. Sannan ya ce mata. “Wannan da yake babban su, sunan sa Muhammad Menk! Wannan kuma Muhammad Nasr, wannan kuma ya ce a saka mata sunan Maidah!” Kallonshi tayi tana me dauke kanshi. “Me ya samu maidah da aka sakawa Yarinyata?” “Allah ya mata rasu ne!” “Allah ya mata rahama!”

So take ta tambaye shi, amma baki daya bata san yadda zasu dauki Abinba, don haka ta mike tare da nufar saman gidan, ta zauna tare da fashewa da kuka. Wani irin kuka take me matukar cin rai, haka ta share awa guda tana kuka, Zulfah da Hafcy sun biyo bayanta, su kawo mata Yaran amma ganin halin da ke ciki yasa dole suka kyaleta. Kafin zuwansu tun da ta dawo gida, take fama da damuwa da yanayin gajiya. Ga Yaran Masha Allah, bata cika magana da kowa ba, sai Yaran shi yasa baki daya bata son shiga cikin mutanen, bayan dinbun damuwar da yake ranta. Haka bai hana ka ganta cikin yanayin sanyin halin da tsokanar Hajja Yayye ba..
Idan ta samu farinciki wuni guda, mantawa take da kome, har da wayarta yadda Malik ya turo musu kaya, yasa ta fita tana kallon kayan, ana saukewa.
“Ina zamu kai kayan nan?”.
“Ai na Yaranshi ne, don haka a kula mishi da Yaranshi da kyau!”
“Hmmm! Da ya damu da yaji halin da Yaran suke ciki da ya kira mu!”
“Amma ai ke kika ce ya jira kiranki sai ya zama laifi?”
“Ni nace ya kira ni tow!” Ta faɗa tana turawa Zulfah baki, ita bata son haka. Harara Zulfah ta watsa mata, suka komawa cikin gidan. Anan suka zube aka wuce aka yi sallah, bayan an idar aka shiga hiran abun da ya faru, watanin baya duk da bata fito ta nuna farincikinta ba, amma daga yanayin yadda ta zuba nutsuwa akan labarin da Elbashir yake bata,zaka gane she missing Malik lots.

Amma shegen halinta da zurfin ciki, yasa taki nunawa ta damu, akan kome har dare ya fara ja, can part din da aka warwa baki, suka nufa dama tun wurin magariba, Zulfah ta gaya musu part din, a can suka sauka. Ita kuma kasa barci tayi ita da Zulfah, tana bata labarin Malik. Har barci ya dauki Zulfah. A hankali tayi ta kuka mara sauti. Sai da kanta ya dame ta da ciwo, ya sha magani ya kwanta. Sai wurin karfe biyar na asuba ta farka, ta shiga ban daki tayi wanka da alola, tazo ta gabatar da sallah, har gari ya sha, sannan ta haura gadon ta kwanta tana jin wani irin gajiya na rashin barci. Tunda ya kwanta bata kuma sanin waye akanta ba, har aka gyara yaran aka kwantar da su. Don ma ana hada musu da Madara da nono, idan sun sha madara kafin suka samu awa guda sai su sha Nono.

Sai karfe daya na rana ta farka, sannan ta kuma wanka ta gyara jikinta, ta sauko kasa, ana ta hira yan’uwan Babansu fa basu samu zuwa ba ne, suka zo. Suka ga yaran. Kallon yadda ta sake kamar ba ita ba. “Zainab iyayen rikici!” Murmushi tayi, tana me zama ta gaishe su, tana kallon Hafcy da take ta kallon Maidah. “Yaya me yasa kika bata Yarinya?” “Wannan matsalarku ne, Ammyn sun futa da mijinta shi yasa take rike da Yaran gwal. ” Amsar yaranta tayi ta kwantar da su, tana me cigaba da hira duk yadda Hafcy taso danne zuciyarta amma ta kasa, sai da ta fashe da kuka. “Kiyi hakuri don Allah!”
“Ni kada ki tara min mutane, da kin san yadda rabuwa da miji yake, ba zaki gaya min magana akan Malik ba, kika gaya min tare da nuna min yadda zan tsane shi, ban tab’a mafarkin na cutar Dake ba amma ke me yasa kika yi mafarkin cutar da Ni? Ban da mugun nufi akan ki me yasa ke kika gaza gane haka? Ba ke ba wani wanda ya min halacci ya min haka, ba zan yafe mishi ba, ki kyale ni kiyi rayuwarki nayi nawa. Kada ki kuma kusantar inda nake na gaya miki!”
Baki daya kansu ya daure ban da Zulfah. “Dalla ya isa haka, san baki kirki, mai sonka shi yake bibiyarka, tayi kuskure kuma ta gane laifinta da ace ba a yafe mata ba? Ko kema ai kinyi wasu kuma haka zasu yafe miki. ….
*Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/27, 10:26 PM] Yan Mata: 41- Hawayen da suke makale a cikin idanunta suka sauko, “Kiyi hakuri Zeeno!” Bata rai tai, ita don dole zata kula Hafcy, amma ba wai don ta cancanci haka ba, asalima haushin Hafcy din take ji, dangin Babansu, kwanansu uku, dake ba ayi suna ba, sai bayan zuwan su Elbashir aka yi taron sunan, sai a daren ranar ta tuna sa wayarta. Kwanansu Elbashir uku da zuwa kenan, da dare ta nimo wayar da ta faɗa can ƙasar gado, har mantawa take da shi. A hankali ta saka a charge, tana faɗin. “wai sako kenan!” Ta zauna tana buɗe Wayar, Allah yasa Yaran ana can ana musu wanka saboda jigilar da suka sha na taron suna.
Inbox ta shiga na text messages, ta fara karo da wani sako. _Wawuya jaka, dama haka mijinki yake sarrafa mace kika bar shi a hannuna?_ hadiye yawu tayi ta kuma ganin wani sako. Ta ce mata.. _Jakar ashe baki Whatsp! Ki duba Email ɗinki, mahaukaciya ashe haka yake binki da masifar kauna shi yasa mana ya kasa hakuri da kanshi yake bin yar abokin shi_
Da sauri ta duba Email dinta, bayan ta kunna data. Jikinta yana rawa kamar an jona mata electric, hotuna ne da video Malik ne Nadrah, na farko inda ya dauko ta, na biyu a dakinshi, yana kwance ita tana kanshi, sai aikin arziki suke. Na uku ya fito yana dariya daga shi sai towel a daure tana mishi video yana dariya, duk videon nan babu murya.

Wani irin kuka take tare da buga wayar da kasa,ta dauki kasko turaren wuta tayi ta bugawa a samar wayar, da bai mata ba ta dauko kwalbar turare tana bugawa har sai da ta fasa wayar, daidai shigowa Ammyn ta ganta a durkushe. “Ammyn! Don Allah ki ce Malik kada ya kuma takowa inda nake idan ba haka ba, zan kwashe Yaran mu gudu.”
Cikin gajiya da halin Zainab ɗin ta ce. “Ni ba yarki ba ce, baki san number Malik din ba ne? Mtsew mahaukaciya wacce bata san ciwon kanta ba, zan bi su Elbashir na tafi, idan kin gadama ki tuna rayuwarki da ta Yaranki idan baki so ba, ki lalata gobenki da dangatakar Yaranki da mahaifinsu. Na gaji da abun da kike, ki godewa Allah da ya baƙi miji nagari da har kike hauka ya miki laifi, sannu waliyiya mara laifi!” Tass Ammyn ta mata, dake iya su biyu suka san abun, bata kuma bin ta kan Zeenobia ba, saboda abin nata har da iskanci, ai zuwanta ta ga yadda wasu mazan suke kula da matansu, wasu ma kamar su ke da hakkin aure a kansu, amma ita ta samu dattijo mutumin kirki, duk da tasan yana da baya mara kyau, amma haka baya nufin ta wulakantashi ba, shima rayuwa yake bukata ne kyau, ta zauna tana shirme.

Har ana gobe zasu koma, sai da Ammyn ta mata tass, domin kuwa da safe ta yanki jiki ta suma, saboda damuwa. Aka kaita asibiti suka ce jininta ne yayi sama, don haka Ammyn take gaya mata. “Namiji halittar shi ce son mata, sannan kuma idan akan mace kike suma da faduwa me yasa baki zauna a wurinshi ba? Dole yayi yadda yake so, naji labarin aure zai kara. Sai ki shirya da kyau” duk da bata yi haka don ta cutar da ita ba, tayi haka ne domin ta zaburarr da ita, amma yarinyar nan me shegen taurin kan tsiya, da suka dawo samun Elbashir tayi ta ce mishi. “Ka gaya mishi, ya sake ni don Allah! Duk cikin sakonnin da ya bani babu saki na duba, yayi hakuri ya sake ni. Ina son kwanciyar hankali. Don Allah ya bar ni haka don Allah ” ta faɗa tana kuka me tsananin gaske.
“Malik yana sonki sosai, amma tunda baki ga wannan soyayyar ba, Zainab zai gaya miishi ya sake ki. Amma ki sani kafin ki samu namiji irin Malik wallahi sai kin sha wuya, domin shi daya ne a cikin dubu. Shi kenan ai”

Daga haka suka bar Nigeria, cike da takaicin Zeeno. Har ga Allah haushinta yake ji. A jirgin suka tattauna akan matsalar Zeeno da Malik, nan Ammyn ta ce kowa ya fita harkanta, ganin ana bibiyarta da zancen Malik ne yasa take yiwa kowa abin da taso shi yasa take wasa da rayuwar aurenta.

Koda suka isa abin da Elbashir da Zulfah suka gaya mishi haka ya dauka karshe, ma booking apartment yayi ya koma Saudiya da zama, tare da mai da hankalin shi akan Ibadarshi, Allah ya mishi arziki da zai iya zama na tsawon wani lokaci. Don haka kamar yadda ta mishi iyaka da Yaranshi. Haka yayiwa kanshi alqawarin ba zai taba zuwa inda take ba, sai ta nime shi. Karshe ma da ibada da tuba yasa kanshi mantawa yayi da ya tab’a rayuwa da wata mace. Yana jin shi a wannan lokacin kamar yana tare da Ubangiji ne, a can kuwa an ta niman shi babu labarin shi, Elbashir yana Demark, domin can ya koma aikin kamfaninsu na can, anan kuwa gwamnati take ruined din kamfanonin Malik din. Haka ya tsara kuma yake tafiya dai-dai.

★★★
Kwanaki suna rikidewa zuwa satittika. Satittika na juyewa watanin a haka har su Zeeno sun Shure wata bakwai, yayinda yaranta suka yi nisa a zama da rarrafe. Tunda suka shiga wata bakwai, suka koma Hadeja. Ashe Maiduguri tana cikin kwanciyar hankali da jin dadi. A hankali ta fahimci dangin Babansu, suna da mugun son kai, da son abin duniya kuma kowa nashi ya sani. Don ma Allah ya taimaka sun karshen wata, zata ga kudi ne in dollas ya shigo a account dinta, wanda tasan aikin Malik ne, sai gashi basu nime kome sun rasa ba, sannan a bangaren Alhaji Kazeem da Alhaji Mustapha, suma ba a barsu a baya ba, domin sosai suke mata aike shi yasa da farkon dawowanta Hadeja, ta fuskanci halinnsu. So daga baya sai ta koyi zama da su, and wani abun da ya kara d’aga mata hankali yadda kowa yake jiran ta mishi ko ya daka mata warwaso akan dan abin Yaranta.

Da farko idan tayi wankin kayan Yaran, ta shanye. Zata samu an dauke Kayan. Bata kuma gani sai dai idan wani harkan biki da suna ya haɗa sai ta ga a jikin Yaran matan Cousins dinta, da farko bata yi magana ba, sai da aka yi na biyu a na uku. A gaban jama’a ta cirewa Yarinyar kayan Maidah ta saka a jakarta ta kalli Uwar Yar.
“Kika kuma ɗaukar min kayan Yara ba ke ba, wata ma sai na karya hannunki!” Tayi maganar a asalinta wato yar kunama.

Sai gashi maganar har wurin, stepbrother din Babansu, shine kakan Yarinyar da ta cire mata kayan. Bayan sun dawo yazo ya ci mata mutunci, har da kiran Yaran shegu marasa asali. Tunda a bariki inda aka kashe ubansu anan ta dauko musu Yaran, shi ba kome bane yasa shi yin haka, sai masifar hassada da tsana da yakewa Mahaifinsu, saboda family babu me rufin asirinsu, da mahaifinsu zance na gaskiya ana ma zargin shi yayi sanadin barin Alhaji Nasr din gida.

Kallonshi tayi ido ciki ido ta ce mishi. “Yarana ba shegu bane, idan da naso nayi alfahari da samun uba irinsu, da da shi zaj zo yayita bina kamar bindi. Da ban gadama ba nazo abina, sannan da kake cewa bariki eh bariki ne, ka gayawa Matar danka idan na kuma ganin ta ɗaukar min kayan Yara sai na karya hannu!”
“Ke shegiya karuwa!” Inji dan Baffanta, a wani fusace, ta kai mishi wawan naushi, a fuskar sai da hancinshi da bakinshi ya fashe. Ta yarfe hannunta. “Kul ka kuma kirana da sunan banza nan, idan ba haka ba sai na gigita maka lafiyarka da dukar. Kai kuma Baffa ka fita idanuna. Maganar mata ne idan ka kuma shiga sai na karya kafarka na saya maka keken guragu!”
Daga haka ta samu sauki, kowa shakkar ta yake, kuma aka daina tab’a mata kayanta, sannan kiri-kiri aka ce ta bar part din da take, ta koma na babanta, wanda sun san wurin ba a gyare yake ba, don haka ta kira kanin babansu da yake Dutse aka turo mata wasu ma’aikata na gini na musamman.

Haka ta bar garin ta koma dutse, ta saka suka rushe part din aka shiga mata, wani irin part me bala’in Kyau. Domin ta ajiye a ranta, koda Malik ya zo ya ce zai zo anan zai sauka, haka idan Zulfah tayi aure ta zo da mijinta ba sai sun tafi hotel ba. Anyi mata ginin kamar a kasar Turai, to meye banbancin Keivroto da Turai din. Sati uku aka gama ginin, Baba Umaru yana ganin ginin kamar zai mutu, baya fatan yaga cigaba Yaran Nasiru. Kwafa yayi yana kara jin tsanar Zeeno.
Ana gama aikin ta dawo, ita da Muttallab dan kanin Babanta, shi ya je har kano ya saya mata katon Injin da kayan electronics, ya kawo mata bata jin ta rabu da mamaki amma zata maida kanta ga gyara gobenta.
Don haka ta cigaba da gyara gidan, har ta dauki hoton gidan ta turawa Zulfah. Taji dadi sosai, tunda suka gama gyara ta ja ruwa da wuta, albarkacin zumunci da bawa cikin gidan, amma dan ta mutanen gidan ne ba zata basu ba. Sannan wannan aikin da tayi ya saka dayawan yan gidan dawowa jikinta, domin sun ji a bakin mutane ita din mijinta mahaukacin arziki yake da shi, wanda bata san iyakar shi ba,.sannan ba rabuwa suka yi ba, idan Zainab ɗin ce ta bukaci ya rabu da ita. Amma yana sonta haka yasa baki daya suka goge zarginsu da karya da Baba Umaru ya shirga musu.

Watansu sha daya, Zulfah ta zo mata da wasu takardun da Malik ya bata kafin ya bar kasar, wurin shakatawarsu ce da Mutane biyu suka bude, jininsu ya zuba akanta. A ranar tayi kuka da take ganin kome like a dream. “Har yau babu labarin Malik?”
“Gaskiya babu!” Kallon yaranta tayi, tana faɗin. “Zulfah nice nace kada yazo, na samu kome, kowa tsorona yake kuma ana min kome domin ina da shi, Zulfah ban san me yasa nayi abandoned ɗinshi ba, Kin ga Khalifan da Afif, ban san yadda aka yi suka iya kiran Daadi ba, duk da nayi kokarin ganin ban koya musu ba.”

“Kina son ganin mijinki ne Yanzu?”
“No kawai ina jin babu dad’i ne, ki sau daya ya bukaci ya ga halin da Yaranshi suka ciki, domin dayawa basu yarda ta aure na same su ba”
“,Allah ya kyauta, idan kina son ganshi. Sai ki nime shi!”
“A’a ba zan nime shi ba,nasan zai zo.”
Shareta Zulfah tai, haka suka tattara suka tafi Umrah dake bara tana bayan sallah ta haifi yaran, bana ita dasu da Yar Gwaggonsu suka tafi Umrah. Domin yarinyar ta dawo gaban Zeeno, tana mata reno da hidimar yara. Ita kuma Zeeno ta biya mata school of nursing, idan suka yi hutu, yarinyar take zuwa mata.
Basu tsinke da kirkin Zeeno ba, sai da kafin su tafi Umrah ta sayi kome na azumi ta raba musu, sannan ta haɗa har da kayan sallah, ta bar ƙasar. Dake a can zasu yi sallah. Hatta abin da zasu bukata duk ta ajiye musu, ( malam arziki yayi ne, babu egen da zai rainaka idan kana da shi 🤔🙄)
Haka abin ya kasance, suka yi hidimar azumi da sallah, suka dawo lokacin Yasir ya turo magabatan shi, aka yi maganar aure. Dage ba yarinya ba ce kawai aka saka bikin wata bakwai masu zuwa, a lokacin ne aka fara takura mata da maganar idan babu aure a kanta, tow ta fara shirin aure don yaranta sun shekara guda.
Ganinta a haka yana damunsu, ita ba matar aure ba, ita ba sakakkiya ba. Haka suka uzura mata har bikin yazo, a lokacin Dr Tahir Sani Malami Jajja, shima ya sako kai, ga Akram wazir da ya sako kai. Ana cikin wannan Yanayin Dr Tahir ya bata hakuri an mishi mata a gida(Guess? Waye wannan! Ku ajiye a ranku! Akwai labarin Dr Tahir Sani Malami Jajja)
Akram kuwa bata sonshi, kuma taya ma zata gaya musu ita tana son mijinta domin bai sake ba, ana saura kwana biyu bikin ta kira Wahida ta tura mata number Daadi, tunda da ta tura mata, ta kasa zaune ta kaza tsaye. A hankali ta zubawa number idanu. Kafin tayi gundunbalar kiran shi. Ringing daya yayi ya kashe, ya biyo kiranta.
“Zainab……… *Shin kira daya zai sauya ƙaddara ko zai kuma haifar da wata ƙaddarar…. Kira daya!
*Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/27, 10:26 PM] Yan Mata: 42-“ZAINAB!” Ya kuma kiranta in hucky voice, wani irin kuka take. “Talk to me! Baby Girl!” Kara sake mishi wani sakaltacen kuka tayi. “Oum Hassan!” Ya kuma kiranta. Jin wani abu tayi a tsakiyar kanta yana wani azabar yawo. “Abu Hussain!” “Wa Maidah!” Ya karasa mata, bata san lokacin da ta kuma sake mishi wani munafikin kuka me, cuccure da shashekar kuka ba, “Ya isa haka, gaya min me ya saki kuka? Kina niman wani abu ne?”
“Abu Hussain aure zasu min!” “Tow Queen Zeeh Allah ya bada zaman lafiya!” Bata san lokacin da ta wartsake daga kukan ba ta ce mishi. “Ka sake ni ne?” “Hmmmm! Me zance ai kin ce baki sona, so na baki damar kiyi kome.” “Amma auren da zasu min akan aure!”
“Tow ni yanzu zan tafi masallaci.”
“Ban gane ba?”
“Ki musu biyayya kawai.” A wani mugun rud’e ta ce mishi. “Mali….Abu Hussain!”
“Sai kiyi hakuri.” Ya kashe wayar, ta kira shi ya fi sau goma bai sauka ba, daga karshe ta mishi text. Amma mutumin nan bai dauka ba, asalima share ta yayi, kamar tayi hauka. A ranar tasan babu kome a cikin taurin kai da kafiya. Baki ɗaya kamar ta mutu ta huta, bata san me zata yiwa Malik ba, amma ta roke shi da Allah amma yaki sauraronta.

Ta kira Elbashir a ranar yakai sau goma, shima amsa daya ya bata, tayiwa iyayenta biyayya. Bata kuma sanin ta kashe kanta ba, sai da ta kira Sayyada Quddisiya ya roketa akan tayiwa Malik magana, ta ce ai yanzu shima maganar aurenshi ake don haka tayi hakuri ta zauna da wanda iyayenta zasu bata, a cikin kwana ɗaya, sai da tayi wani irin ramewa. Yaran ma baki daya kasa gane kanta suka yi, karewa wurin Zulfah suke, wacce ake ta hidimar baki, amma idan kaga yadda ta rungume Yaran ita da Ummi yar Gwaggonsu. Domin uwarsu bata da lokacinsu.

Kiran Alhaji Mustapha tayi, ta gaya mishi abin da yake faruwa. Shiru yayi kafin ya ce mata. “Yanzu zai abin da zaa yi shi ne, ki kwantar da hankalinki zan kira Malik din naji matsayinki.”
“Don Allah ka taimaka min Kawu!” “In sha Allah!” Daga haka ya kashe wayar,. Sannan ya kira Malik, yadda Malik ya mishi bayani shima ya gamsu, don haka bayan sun gama waya, ya kirata ya gaya mata.
“Kin ga koyi hakuri, tun farko ya dace ki san cewa ba kome kake samu ba, sannan ba kowa yake iya hakuri ya saukar da kai a zauna lafiya ba, lokacin da kuke samun matsala ya baƙi hakuri ki fahimce shi, amma kika ki. Shima wannan shi ne damar shi, domin ya samu wacce take girmama shi, kuma zata rike shi a duk yadda yake mata. Zainab iyayen mutanen kirki ne, amma ke kin samu Malik kika yi ta janshi a kasa kina mishi abin da ranki yake so, Zainab Malik ya so ki tsaki da Allah, amma ke sai da kika cusa mishi kiyayyarki.

Ba kowacce mace bace take samun namiji irin Malik ta sake shi ba, amma kin same shi, kin watsar da shi ai ko bai haife ki ba, ya ci darajar igiyar aurenshi da yake kanki. Ya turo min da sakon rabuwaku,tun tuni ya jima da rubutawa ya ajiye miki jiran wannan ranar, Yaran kuma yace yana jiran su cika shekara biyu zai zo ta dauke su. Amma ni nace mishi ya kyauta, kuma mun gode. Mutumin da bayan rasuwar Iyayenku shi ya kawo Zulfah har nan, sannan ya nimo dangin Mahaifinku ya hada ta dasu.

Mutumin da har kwanan gobe, bai yi barci ba, Yana can yana niman Fahad wanda shi ne ya kashe iyayenku, Maahifin Amjad Fahad, amma dake ke jahilace, kin zauna kina wulakanta shi, Yan waye gari ya waya? Waye ya rasa damar shi? Ke ce don haka kiyi hakuri ki rungume ƙaddarar ki, Allah ya baku zaman lafiya ”
Zuwa yanzu ta kasa kuka, sai ajiyar zuciya take bata san cewa tana masifar kaunarshi ba, sai yanzu da take ganin kamar ta rasa shi, a hankali ta fashe da wani irin kuka, sannan ta kira Malik din.
“Don Allah ka mai da ni dakina! Kayi hakuri zan girmama ka, zan maka duk abin da kake, wallahi ba zan tsallake duk abin da kace ba.”
“Zainab ba sona kike ba, kina bukatar na kasance dake ne, idan na biya miki bukatarki zaki mai dani abin tozartawa. Don Allah ki kyalr Ni”
“Me yasa ka ce zaka jira kirana daya tak? Me yasa ka sanya min yakinin cewa idan na kiraka kaddarata zata sauya? Me yasa ka saka min yarda cewa kai kawai zaka kawo min dauki a duk lokacin da bukaci agajinka.”
“Saboda ko lokacin da kike tsammanin kece kika kashe Ayuba da Wasim ba ke bace. Tabbas kin dake su amma ni ma saka aka karasu, duk wanda kika tsammanin kin kashe shi, nake bace. Ni na aikata haka. Saboda sun lalata min suna kuma sun tab’a min matata da idanuna suke kanta, Ki tambaye Ammynku ba haka kawai, Alhaji mahaifin Abbas yayi adopt dinki a gidanshi ba, ni na bashi Amanarki.

Zainab ni ne inuwarki, ina bibiyar rayuwarki da duk motsinki da kike a cikin tsohon garin Keivroto, domin na san wata rana zaki zo gareni. Amjada basu suka nime ki ba, ni na saka kuka nime. Saboda ta haka kawai zan mallake ki, ko da na bukaci muyi cantract marriage, idan nazo miki da kafa, ba zaki aure ni ba. Amma idan nazo miki as mara lafiya tausayin mutane a jininki yaƙe.

Zainab kece mace na farko da koda baki sona. Baki yi kokarin cutar da ni ko lafiyata ba, ke dai kaiwa na addabi rayuwarki ne, shi yasa kika yi ta min rashin hankali, da cin fuska haka bai tab’a damuna ba, amma nasan wata rana zaki bukaci nazo kina son na mai da ki, dakinki. Zainab ban san yadda zan gaya miki ba. Amma kin bani abin da ban isa na wulakantaki va, sai dai maganar komme kiyi hakuri. Kiyi hakuri Allah ya baƙi hakuri.”
Wani irin kara tasata tare da yankar jiki ta fadi, sumammiya.
—– Bayan awa hudu, farkawa tayi ya ganta a dakinta, Zulfah tana bawa Maidah abinci, dake yaran suna da hakuri da kuma kuzari basu jiran na shanu uwarsu, shima wani lokaci mita take tana cewa ita kan Nononta zai zube, don Allah su bar mata na kwalliya.
A hankali ta zuba musu idanu, kafin ta dafe goshinta. “Kin tashi?” “Malik ya kira ya tambaye ni ya jikin naki. Nace mishi da sauki! Shi ne ya ce na baki hakur.” Bata bari Zulfah ta karasa ba, tacce mata. “Ya isa haka.” Sannan ta mike tare da nufar ban daki, wanka da Alola tayi, sannan ta fito dakin tayi sallah, tana zaune Aunty Yaganah ta kawo mata wani katon kwanon sha, ta ce mata. “Maza ki shanye sannan ki hada da farfesun nan plat din!”
Dake ta saka damuwa a ranta, ko gyaran taki sake jiki a mata, tana idar da sallah, ta ci abincinta tasha ruwan da farfsun tana kuka, wanda ta jima bata yi ba, ganin wayarta a bakin gadon ta dauka, sannan ta kira shi. Bai daukar ba ya kashe ya kirata.
“Sannu ya jikin naki!” “Mutuwa zan yi idan baka zo ba, kazi nace ko na rataye kaina.”
“Kin ga matsalarki ko? Ba zan zo kin jima baki rataye kanki ba”
“Nadrah zaka aura ka manta da UWAR Yaranka.”
“Bani da lokacinki, aure ne nace bana yi.” Kuka da masifa, basu gyara kome ba, karshe ya kashe wayar. Ta daina samun shi. Tunda ta zauna a daki tana jin ana ta hira da hidima amma bata leka waje ba.

Haka zaman dakin ya aureta, washi gari ta tashi da mugun ciwon kai, a haka tayi wanka. Ta shirya sannan ta fito tayi mugun rama, kamar ba ita ba. Tana fitowa bakin Demark suka iso. Wahida da Wahiba, Sayyada Quddisiya da Jalilah, Adnan da iyalin shi. Shatima da Hafcy, haka akayi ya ta shige da ficce, bayan saukowa daga sallah juma’a aka daura auren Zulfah da Yasir Aswad Al Yemini, dake ba iya auren Zulfah ba akwai wani daurin auren aka yi har uku. Lokacin da labari ya zo cikin gidan, ba karamin farinciki aka yi ba, bayan daurin auren. Aka shiga shirin kai Amaren gidansu, ita Zulfah za a wuce da ita Yemen ne, yayinda Zeeno aka wuce da ita Borno. Yaranta sna wurin yan uwansu, shi da ta fahimta Yaran sun yaye kansu, domin baki daya sun ki nono, ga zazzabin kumburin da nonon suka yi, haka ta shiga mota aka wuce da ita Maiduguri, su sayadda suna biye da ita

Sai la’asar lis suka isa, sannan aka shiga wani gagarumin walima da ba a tab’a yi ba, sosai.aka yiwa walimar tanadi ba musamman, ba a gama walimar ba sai dare, sannan aka tafi aka yi sallah. Tana daki Wahiba ta shigo cikin girmamawa ta ce .. “Mommy kizo Aunty Jalilah tana son ganinki;”
“Tow!” Ta faɗa kamar zata yi kuka, a hankali ta mike, tana shiga dakin ta kalle ta, sannan ta ce mata. “Kwabe ki shiga wanka mijinki yana jiranki yau zaku wuce!”
“Ummi Yarana fa?”
“Sun yaye kansu, basu da matsalar suna da sabo da mutane. Cire maza ki shiga wanka.”
Haka ta wuce ban dakin tayi wanka, sannan ta fito ta tsuguna a gaba wani runshi da towel, shafe mata jiki Jalilah tayi da wasu kayan gyaran jiki, sannan ta jibga mata bargo, sai da ta bushe ta d’aga. Ta murje mata jikinta, kafin ta kawo wani oil ta goge jikin dashi, sannan ta kuma hada mata ruwan wankan. Tana fitowa, ta kuma saka mata wasu mayukan turare, ta shiga tayi wanka. Sai gashi tana fitowa ta ce mata. “Yanzu an gama, mijinki yana son kamshi, wannan shi ne damar da zaki yi amfani da shi. Domin kama zuciyarshi. Sai biyayya shi ba Malik bane, da zai na biye miki. Kike sake ya gano kina da taurin kai zai sake ki, sai a fara kirga miki aure.”
Gyada kai tayi, tana mata nasiha har da mata misali da kanta, har ta shiryata tsaf, sannan ta fito da ita, ta nufi cikin gida wurin Hajja Yayye ta mata addu’a, ta kaita wurin Alhaji Kazeem ya mata nasiha, Alhaji Mustapha ma haka, duk sai taji meye ribar taurin kai? Yau da ace Malik ne da babu abin da zai faru, haka hawaye yayi ta zuba mata, har ta iso wurin motar, ta shiga tana kuka. Haka suka tafi da ita bata san wani unguwa ba ce, amma tabbas. Sun yi tafi me dan nisa.

Haka aka kaita wani gida, ita ɗaya ta shiga cikin gidan babu kowa, dakin da ta gani a bude ta tabbatar nata ta shiga, sannan ta rufe kofar ta kwanta, har dare ya raba babu labarin miji, sai da bayan tayi barci. Aka shiga dakin aka kashe wutar dakin. Sannan aka ja mata kofar aka fita.

Washi gari bayan sallah asuba, aka bga mata kofar, ta shirya karfe tara zasu tafi Kano. Kafin karfe tara ta gama shirinta tsaf, sannan aka zo aka ɗauki kayan aka fita da shi. Koda ya shiga cikin motar tayi notice Imperial majesty da yake tashi, amma baki daya kwakwalwarta bai bata lissafi ba. Don haka ta cigaba da kunshe kanta tana kuka, har suka isa airport. Aka gama kome, ta shiga jirgin . Suka wuce kano,. Tunda suka iso jikinta yayi sanyi.
…….Tana saukowa wasu matasa biyu, da mace babba suka suka amshi jakarta, suka nuna mata mota, babu musu ta bisu. A hankali suke tafiya matar tana jan ta da hira. Har suka isa unguwar, rimin kebe. Babban gida me tarihin malamta da kasuwanci. Nan aka kaita, amma an zamantar da gidan. Nan ta samu anata harkan biki da jama’a, wani irin gud’a ake ana watsa mata kudi, ko ba a gaya mata ba Familyn mijinta suna da rufin asirinsu, yadda kake rawan jiki akanta ya kara mata sanyin jiki. “Ina Yaranmu, kai ba dai ita ɗaya kuma dauko Babu Yaran ba?”
“Suna tare da Hajja ai, zasu zo wata sati. Shi Abdul ai zai wuce da ita yau ne.”
*Waye Abdul? Lallai ma Abdul fa, wannan wacce irin ƙaddara ce* abin da zuciyarta yake raya mata kenan.
*Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/27, 10:26 PM] Yan Mata: 43- *Haka zan kare rayuwata ban ji dadin shi ba kenan? Waye shi kuma?”
Hawaye ya zubo mata, dake ta sunkuyar da kanta, bata san har sun isa dakin ba. Haka aka ajiye ta, gyara jikinta tayi ta ci abinci. Zazzaɓi ne a jikinta rau-rau. Zuwa yamma tana kwance domin sai da aka kira likita ba familyn ya duba ta, sannan ya bata magani, tayi Barci. A hankali ta mike ta wuce ban daki tayi wanka. Da Alala tazo tayi sallah.
Tana idarwa wasu yan mata biyu suka iso, dakin. Suna masu gaishe ta. “Inji Uncle Abdul ya ce kizo yana sama ” gyada kai tayi. “ya jikin Oum Hassan!” Murmushi tayi ta ce mata. “Da sauki sosai, amma a ina kika ji sunan!”
“A wurin Uncle ya ce kin haifa mana, Triple don Allah next time ki haifi hudu;” ware idanu tayi, ta ce mata. “kiyi shiru!” Ta saka hannu a baki. “Babu kyau ko?” Gyada mata kai tayi, sannan suka fita, ita kuma ta shirya ya fito, suka nuna mata hanyar. A hankali take tafiya a hanyarta ta komawa suka hadu da wata babbar mace, cikin girmamawa ta gaishe ta. Bata rai matar tayi ta ce mata. “Kada ki ga kin samu wuri, Abdul bazai zauna da mace daya ba, sannan naji haihuwar ki na farko uku kika yi, tow ki kwantar da hankalinki Y’ata Rahma tana zuwa ba gudu ba ja da baya;”
Sunkuyar da kai tai, toaw meye ya haɗa yaranta da mutumin da bata sanin waye shi ba. Haka ta mai da kwallarta, ta haura saman. Dariyar mace ta ji, tana faɗin. “Kai Bro kace kawai, honeymoon zaka tafi da guzumar matarka, amma haihuwa daya sai kace akuya yara uku!” A hankali ta juya zata bar wurin yarinyar ta ce. “La Yar kunama!” Wani irin kunya ce ta kamata, ta juya tana kallon fuskarta. “But na tab’a ganin fuskar kira vogue!” “Ita ce!” Ya faɗa kasa kasa, “karaso ashe mai kyau ce dole Bro ka kasa hakuri da ita, but am jealous!”
Ta faɗa tana dariya, karasawa tayi ya juya mata baya, yana kallon fili ne, dake akwai glass, na waje ba zai ganka ba, amma kai zaka ganshi. “ok Bro bari na baku wuri, Zeeno nice kishiyarki bani da zafin kishi, amma kuma duk abin da nake so, ina mallakar shi ne da karfin tsiya.”
A hankali ta fice, tana wani kareraya kamar maciji.
A hankali ya ce mata. ” Ya bayan rabuwa?” Da sauri ta isa gabanshi. Hannunshi daya riƙe da mug, daya yana cikin aljuhun wandon shi, Malik dinta ne a gabanta. Juyawa tayi zata fita. “ki rufe kofar da key! Idan kuma kika fita ita wannan Yarinyar da ta fita zata rufe abubuwan da kike gab da rasawa!” Cak ya tsaya hawaye na zuba mata. A fusace ta rufe kofar, ta juyo tana kallonshi. “Ki bar kallona, domin haka ba sai sauya kome ba!”
“Me yasa haka?”
“Saboda na baki dama na biyu, ko zaki iya kare kanki ta hanyar yi min biyayya.” Wani irin kuka take, da ta durkusa a ƙasa tana jin zuciyarta yana wani irin bugawa.
“Me na maka da zafi haka?”
“Ni baki min kome ba! Daraja ta ce idan ba zaki gani ba, gari da yawa. Maye baya cin kanshi.”
Zama tayi a wurin tana kuka, ya zauna shima yana kallon ta. “Amma kasan yadda naji da kace ba zaka dawo dani dakina ba?” “Amma kin san yadda naji lokacin da kika ce na sahale miki? Ji nayi kamar na tara Al’ummar Keivroto nayi ta sakawa ana musu yankar rago, domin wadanda suka bata miki rai daga cikinsu suke. Ni kuma nayi yayya?” Tausayi da kaunarta yake kara ji, da take kukan nan sai yaji zai zauna da ita, no matter how she a. Matsawa yayi jikinta, ya janyo ta jikinshi. “Wash!” Ta sake yar karamar kara, tana ture shi. “Mene ne?” Kuka take tana kara jin kamar, ya tab’a mata da gayya ne. “Naji an ce baki da lafiya, tun a can Maiduguri meke damunki!”
Cikin kuka ta ce mishi. “Yau kanana uku da suka bar nonon. Ciwo yake min.”
Shiru yayi a hankali ya kai hannunshi, samansu, ya tab’a su kaɗan, tayi maza ta ture hannunshi. D’aga rigar yayi sama, sannan ya janyo ta jikinshi. Ya kai bakinshi kan Rufaida yorgot din. (🙊🙈) A hankali yake zukarsu, sai da ya tabbatar da ya zuke ruwar daya tass sanan ya koma kan daya, yana sha yana lumshe idanun. Rike kanshi tayi kamar zata yi hauka. Haka ya rungume ta, yana sauke ajiyar zuciya. Kuka take mishi cikin shagwaba. Rungumeta yayi yana faɗin. “Kada ki dauki haka, a matsayin wani abu can, taimakawa nayi domin aiki na ne wannan!” Daga haka ya gyara mata rigarta. Sannan ya wuce zai fita, da sauri ta mike tare da cimma shi, ta rungume shi. “Ka yafe min!” Tab’e baki yayi ya ce mata. “Kin ga kin da na bata kayana, kada a na fita amaryata ta ji haushina.” Sake shi tayi, ya fita a kan idanunta. Itama a sace ta koma dakinta, ya shiga wanka. Tana jin tausayin kanta, Malik yayi mata nisa kenan. Ita da wata zasu na raba Malik.
Bata yarda ta kuma fitowa ba, har dare lokacin da zasu bar garin kano. A lokacin nonon ya kuma cika, sai zogi yake mata, yana bukatar a zuke shi. Haka suka nufi Malam Aminu Kano airport. Rahma tana makale mishi, kamar zata shiga jikinshi.
“Bro kada ka manta dani!”
“Akan me zan manta dake!” Kallon Zeenobia tayi a ranta ya ce . *Saboda wannan aljanar matar taka* a zahiri sai tayi murmushi ta ce mishi. “Saboda Oum Hassan!”
Dariya yayi ya ce mata. “Ba xan mata da kanwta ba” haka suka yi ta sallama me cike da kulawa da tararaye, tana lura da yadda yarinyar take kokarin bawa Malik dariya koda abun bai kai na dariya ba, tana son ta san me haka yake nufi sai da suka tashi zasu tafi, yarinyar ta rungume shi ya gefe. “Bro ina jiran ka!” “Soon dear!” Haka suka raba jikinsu, ta juya tana kallon Zeeno. “Please Madam a kula min da Bro na, kada a bar shi babu kulawa.” Kallon yadda yarinyar take zakewa take. Murmushi tayi ta kalli Malik ta ce mata. “Allah yasa idan ya dawo ya tuna da ke.”
“Waw me zaki yi?”
“Wife’s duties!” Daga haka ta bi bayan Malik, tana wani taku ikon.

“Lallai ma” Rahmah ta faɗa, lokacin da suka shiga jirgi, sai ya zama shiru babu ha’incin a cire son kai, yana son Zeeno amma mace irin Rahmah duniya ce, kamar ta san me yake tunawa, kawai ta shiga bashi labarin fadar Hassan da Maidah, har da videonsu, yana kallon yana murmushi. “Ina Hussain!” “Zaka ganshi a gaba ai, ai shi ina ganin Malik ne a wurin, halinshi kamar naka!” Ai kuwa sai ga a cikin videon ya daura daya akan ɗaya, yana wasan shi da takardar kuɗi. “Na shiga uku! Shi kudi ya saka a gaba.”
“Shi ma second daadi kenan!”
“Ya kika yi da renonsu?” Ya tambaye ta, yana kallon yadda take murmushi. “Kamar yadda kace nayi renonsu da soyayya. Amma kuma sun fi sabawa da Ummi domin ita ce kome nasu.”
“Ta kyauta min!”
“Ban yi, tsammanin zaka dawo gare ni ba. Sai gashi na ka dawo.”
“Ba dawowa nayi, domin ki wulakanta ni ba, na dawo ne domin Yarana.”
Maganar ya bata mata rai amma bata san yadda ta iya Malik. Ta lura kamar jiranta yake da magana ya cab’a mata bakar magana. Sai tayi ƙoƙarin kwantar da murya a zauna lafiya, barcin da bata yi ba me kyau kwana biyu ta fara yi a jikinshi. Gyara mata kwanciyarta a kafadarshi.

A hankali yake shafa hannunta, zai iya cewa yayi tafiyar ƙaddara kafin ya cimma soyayyar gaskiya, sai da ya fidda rai da samun damar barin Saudi, sannan yasan ba wayon shi ba ne, jin kai ne da rahamar Allah, yasa zasu kuma zama a karo na biyu.
Koda suka isa Dubai, rikota yayi suka shiga takawa, tana jin kamar ta cire kanta ta huta, saboda ciwon kai. A hotel din da zai huta. Ya kaita sannan ya nimo likita aka kara mata ruwa, da allura tayi barci.
A hankali take shafa kanta, ban daki ta wuce yayi wanka, ya sauya kaya ya gabatar da sallah. Dole suka soke tashin wannan jirgin. Haka yayi ta kula da ita, har garin yayi duhu. Lokacin da ta farka. Shi ya hada mata ruwan zafi, ya dauke ta, da kanshi. Babu karfi a jikinta amma don karfin hali cewa take. “Kaje zan yi da kaina.”
Cire kayanta yayi ya cire nashi, covering fuskarta tayi a kirjinshi. Sumbatar kanta yayi yana jin wani sabon nutsuwa a ranshi, lokacin da ya kamo Rufaida yorgot din ta, yana wasa dasu, sake narkewa tayi a jikinshi. Malik daban ne, Malik shi din ba musanman ne, bata san lokacin da ta biye shi ba, suka yi ta kashe junansu a cikin ruwan zafin nan, dakyar ta lallabashi suka yi wanka, ta fito daga ruwan suka kara tsarkake jikinsu tayi alola, sannan suna fito sallah.

Ba karamin kokari yayi ba, domin dai ya kai matakin da baya gane kanshi. Odar abinci yayi musu, aka kawo kaɗan taci, ta sha magani. Ta koma gado ta zauna. Cire towel din kanta tayi jikaken kitson kanta ya sauka har gadon bayanta. Juyawa yayi yaga tana shafa man turare a wuyarta daga ita towel domin ya bata baya. Mikewa yayi. Ya nufi bayanta, tare da sumbatar bayan, yana lasar dokin wuyarta. Hannunshi ya kai ya rungume, kirjinta yana lasar wuyarta. Cikin wani irin bala’in kauna yana yi yana matsa na fulaninta da yake zubda ruwa, kamar a na tatsarsu. Juyar da ita yayi ya kai bakinshi yana shanyewa.

Tabbas ta yarda yaye biyu zata yi, bayan ta yaye Yaran Malik, tana bukatar lokaci domin Yaye Malik din ma, domin kuwa shima Baby ya koma. Yana ganawa ya koma jikin bedwall din, yana kallonta irin dirty look ɗin nan, kallonshi tayi a kasalance. Sauka tayi a gadon, ta nufi wurin kayansu.

Bude akwatinta tayi ta cire wasu dankwalayen abaya, tazo ta daure hannuwanshi, sannan ta nufe shi tana kallon fuskarshi, wato bai gama tantance abin da zata aikata ba, sai jin yarinyar nan yayi a wata duniyar, da sai da ya sake ihu. D’ago kai tayi tana murmushi. “Kana mamaki ba? Sai na fanshe kukan da ka sani babu iyaka!”
Sannan yar albarka, ta shiga cinye tsohon yan uku. Ai dauke wuta yayi yana faɗin. “Kyale ni haka, bar ni Zainab. Bar ni haka yar kunama.” (🙊🙈🤔🤣🤭) Yar kunama ta cinye dattijo dai, sannan ta koma ta zauna ta shiga aikin arziki.
“Da dai nasan baki jin magana amma rashin jinki na yanzu kan rashin jinki ya wuce tunanin tsohon mutum irina, kyale ni da tsufana yarinya!”
Hannunta ta kai ta kunce daurin hannunshi, ya matseta da hannu daya, sanan ta kunce dayar, ya wani juyar da ita. Ya shiga gaya mata labarinshi sala-sala. Sinki-sinki.
Daki-daki, daya bayan daya. Cikin nutsuwa da kulawa yake gaya mata waye shi waye ya bashi damar tsayawa a yau, gaskiya ta gurzu a hannunshi, shima tsinannen zazzabin guduwa yayi ya barta da Malik dinta. Amma ina sai da Malik ta ga tayi wani irin laushi, sannan ya kyaleta.
Ajiyar zuciya take tana jin kamar an gama, mata dukar tsiya a jikinta. Kallonta yake kamar zai cinyeta.”Sannun jinki!” Lumshe idanunshi yayi yana faɗin. “Sannun Baby girl…….
Wadannan ma’aurata zasu lalata min guntun tarbiyyar da Mamana ta min. Barka da Maulidi yan uwa da abokan arziki, tow ni dai zan tafi kallon Maulidi 😂🙊🙈 Mu hadu gobe ko!🤗❤️🤩🥰 Team one love, Rahmah tana jiran Malik a can fa. Ya labarin Shatima da Lalla Salmah, ina Nadrah 🙄🤔k
*Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/28, 10:26 AM] Yan Mata: 44-Tayi laushi sosai, don haka komawa jikinshi tayi tana wasa da gashin kirjinshi. Da suke kwance luf-luf. Janyota yayi kirjinshi ya kwantar da ita, yana wasa da gashinta. “Kin ga Kanwata Rahmah?” Gabanta ne ya fadi, ta d’ago kai tana kokarin kallon fuskar shi. “An bani aurenta, tun zuwan da nayi bayan rasuwar Iyayenku. Amma ban amsa ba, saboda bana tunanin haka ta sauki.” Gyaran murya yayi, sannan ya cigaba da cewa.
“Mahaifinta tun kafin na tafi ya bani auren yarshi, amma ban amsa ba domin ina tunanin gobenta. Ashe yarinyar ta saka haka a ranta, taki kula kowa sai ni. Don haka koda nazo akan su tafi min bikonki. Suka taso da maganar Rahmah. Ba xan iya kin musu ba, shi yasa na amince da zancenta. Saboda naga kamar baki da ra’ayina.” Tashi tayi zaune, ya kalle ta ganin take ƙoƙarin danne kukanta yasa shi juyawa, zai sauka a gadon. “Kuma aurenta zaka yi?” Murmushi yayi a ranshi ya ce. “Eh ai da mahaifiyarta da Mahaifina abokan wasa ne, Sayyada Quddisiya ta auri Wan Babanta, kin ga kenan duk lamarin daya ne, Babanta kakansu daya da Abbana.”
Ya faɗa yana me daukar towel ya daura akan idanunta. Kallonshi take daga sama har kasa, wani irin kuka ne ya kwace mata.
“Tow meye na kuka?” Ya tambayeta, bayan ya wuce banɗaki, yana wanka ta shigo itama. Tana kuka tana wanka, tana gamawa ta fito ta nufi wurin kayanta. Ta wanda zata kwanta, wani abin mamaki shi ne barci ua kaurace mata baki daya, babu al’amarin barci a idanunta. Shima aikin shi yake a laptop yana lura da juyinta, har ya gama bata rintsa ba, yana gamawa ya haura gadon. Ya janyota jikinshi yayi mata wani irin runguma da dole ta kwanta a jikinshi. Domin tana rigimar ba zata kwanta ba ne a jikinshi. A hankali ya take sauke ajiyar zuciya. A haka barci yayi gaba da ita. Wurin asuba, tunda ya sakata a gaba da fitina sai da taji a ranta kamar ba zata iya ba, domin al’amarin babba ne a gare ta, sai da tayi kuka kafin ya kyaleta, yana kyaleta ana fitowa sallah asuba. Ban daki ya shiga ya tara mata ruwan wanka, ya zo ya dauke ta cak, ya je ya sakata, sannan ya shiga suka yi tare, suna fitowa Abin sallah ya shimfida musu, sannan ya jasu sallah. Barci sosai tayi bayan sun idar. Wurin karfe daya tana barci tayi ta jin maganarshi sama-sama, saka kunne tayi ta ji yana dariya sosai. Dakyar ta shiga ban daki ta gasa jikinta, riga da skirt ta saka tare da hula ta fito falon, fuskarta iya kwalli ta zizara, sai man baki amma babu laifi ta zuba turare a jikinta.

Takowa yayi har bayanshi, Video call suke da rahama, tana nuna mishi Yaranshi da draman da suke, shine yake dariya, itama rahamar ta dage sai biye musu take. Mace kenan ya faɗa a ranshi, domin ta fahimci yadda yake son walwala. Sumbatar kumatun Malik Zeeno tayi tana faɗin. “Kanwata ya kike?” Ta faɗa tana dariya itama, bata rai Rahmah tayi. “Hi Babys ya kuke?” Yuuu suka yi kan wayar suka fara mata gwaranci. Sannan ta biye musu. A hankali ta kwace wayar bayanta dawo kan cibiyar shi ta zauna, a hankali ya rungumeta, yana shafa bayanta. Kashe wayar tayi, ta ajiye a kan center table ta ce mishi. “Yunwa nake ji!” Sumbatar kanta yayi yana jin kamshinta yana fisgar shi.
“Nima yunwa nake ji.” Ya faɗa yana ciwon kunnenta. “Ai kaci rabonka, ni gaskiya ina jin yunwa.” Landline phone service na dakin ya dauka da yake gefensu, yayi odar kome, sannan ya ajiye yana mata wani shu’umin kallo. “Ni yanzu yunwa nake ji, don Allah a bar ni na karya.”

Murmushi yayi ya cigaba da jagwalgwalata, har aka kawo abincin ya amso, dakyar ya barta ta ci abincinta. Tana gamawa ya ce mata. “Nawa ne kudin kwalliyar nan? Zan saya ne.” Ikon Allah, anya Malik yana da lafiya kuwa? Ta tambayi kanta. Murmushi yayi yana me janyota yana shafa fuskarta. “Na sayi kwalliyar.” Tun a nan wurin ya fara tura rundunan yakin shi, kamar zata yi kuka domin baki daya so yake ya saka kanta yayi Bindiga, salon alamarin shi, babba ne don haka tana ji tana gani a falon sai da ya surfeta, tass sannan ya kyaleta. Shima don yaga kamar zata shid’e ne yasa shi kyaleta.
Tunda tayi wanka, ta shiga bargo bata kuma yarda wani abu, ya haɗa su ba. Dama tayi sallah tuntuni. Izuwa yanzu zata iya cewa amarcin dasu yi ba suke yi. Domin wallahi sai da taji baki daya garin Dubai ya dame ta, kwanansu uku ya fita da ita shan iska, da shopping ba laifi ya kashe mata kudi kamar hauka, domin bai ki ta kuma ɗaukar min wani cikin ba, an ce hali a jikin rai yake, babu me iya sauyawa. A dan tsakanin nan, ba karamin sauyi ya gani a wurinta ba.
Asalima babu zafin nan, ita take binshi a wannan kadamin. A bangaren da ya fahimci gazawarta wurin mu’amalar aure, shi kanshi har tausayinta yake ji, domin baki daya tayi laushi, sannan a bangare guda. Tunda yace zai kara aure ta saukar da duk wani abinda take yi, ta zubawa Sarautar Allah ido.

Duk da shima a na shi, bangaren yana lura da ita, ta saka shi hira. Duk wani abinda tasan zai faranta mishi yi take. Kwanansu biyar suka wuce China. Basu tsaya a ko ina ba, sai a garin Beijing.
Anan suka sauka, sannan ya tafi maganar kasuwancinshi. Baya dawowa gida sai dare, a wannan kwanakin ta fara period dinta, wanda ya shiga tsakaninsu. Dake baya dawowa da wuri, sai a asuba yake d’aga mata hankali da fitina. Don ma ba dogon kwanaki take ba, kwana hudu zuwa biyar ne. Tun a ranar na hudu yake rokonta don Allah idan ya dauke ta gaya miishi, yayi missing dinta. Dariya ya bata domin ta huta a kwanakin, ranar da ta gama ai kuwa bawan Allah nan, kiri-kiri yayi ta murna, har da ɗaukarta sama a kunne ya gaya mata cewa.
“In sha Allah, wannan karar idan na buga wasan yadda ya dace. Sai a amai da toshe hanci”
Murmushi tayi, wato tun da suka yi sallah isha, ta ci abinci Malik yake abu ɗaya. Tun tana daurewa har abin ya wuce tunaninta, sai da ya ga da gaske bata motsin arziki, ya kyale ta.
Ba karamin wahala take sha a hannunshi ba, baki daya ta zabge. Haka suka yi ta fama har suka bar kasar, suka yi ta yawo, watansu biyar, suka dawo kano. Har lokacin babu al’amarin zata kuma.wani cikin shima ya daurawa ranshi masifar son haihuwa. Haka yasa yake yawaita magana har ta fara jin babu dad’i.

Tana barci, ta ji hayaniyar yan mata a gidan, farkawa tayi ta fito falo. Malik ne da yan matan Cousins dinsu. Suna zaune sai hira ake. Murmushi tayi tana faɗin. “Sannunku da zuwa!” Kallonta suka yi, kafin suka ce mata. “Yawwa!” Daga haka suka cigaba da hiransu, tashi yayi ya nufe ta yana faɗin. “Muje kici abinci.” Wannan halin Malik ne, a gaban uban kowa yana nuna darajarta. A madadin wasu mazan da suna ganin danginsu zasu fara maka iskanci da renin hankalin. Yana musu girki yana bata labari, tana dariya. Har suka gama ya fita falon. Kus-kus suke suna zuwa suka yi shiru, anan yake janta da hira har ta sake aka yi ta hira da ita.

“Wai ba zaku bamu abinci ba ne?” Murmushi yayi, ya ce mata. “Ba zaki basu abinci ba ne?” “Zan basu mana, sai dai muje muyi abincin tare da kai!” A hankali suka nufi kitchen a tare, suna hira. Shinkafa da miya suka daura, yana kallonta yadda take ciro kayan, yana gaya mata abin da zata saka, tana gama cirowa ya nuna mata yadda zata gyara, shi kuma ya ciro kaza ya zuba musu ruwa, suna sakewa ya fara yankawa, yana gaya mata yadda zata yi, abin gwanin ban sha’awa, tana gama markade kayan miyar, wanke kasar ya zuba a tukunya ya shiga gaya mata. “Kina gama wanke namar, sai a zuba a tukunya, spicy da sauran kayan kamshi da dandano, zaki zuba.
Sai ki zuba, ba zaba daure a wuta ba, sai an soya wannan albasar da mai, sai mu cigaba da suya shi. ” Haka suka cigaba da hira, a waje kuwa kiran Rahmah yan matan nan suka yi, albasar nayi golden, ya juye mata kazar, ya haɗa kome ya rufe yana sumbatar wuyarta. “Kin yi kokari!” Juyawa tayi, tana sumbatar kirjinshi.
(Tsakani da Allah 😂😭💃🤔 saboda kishiya Zeeno ta sauko daga bishiyar kace)
Aikuwa duk abin da suke akan idanun Rahmah, ganin yadda suke cinye juna. Jikinta yayi sanyi, dake transparent glass door ne, su na ciki basu lura da ita ba, amma ita ta lura da su. Juyawa tayi jikinta a mace. Idan ta shiga tsakaninsu ita ce zata wahala, ita tana son mijin da zata gina mishi soyayyarta a zuciyarshi. Amma wannan maganar gaskiya Malik da Zeeno. Sun gama gina soyayyar junansu, zai yi wuya wani abu ya raba su. Don hakan tana ganinsu, tunaninta da lissafinta suka bata ta hakura da Malik d shi, har abada domin Malik na Zeeno ne shi daya.

Suna can suna girki, ita tana zaune a Falo, ana ta hira da ita suka gama abincin suna fara fito da shi suna shiryawa a tsakiyar falorn, suna gamawa suka nufi dakin Malik, suka yi wanka dake akwai kayanta a dakin ta saka, suna hira.
Abin burgewa suka shirya a tare suka fito, tana gudu yana Binta da gudu. “Sannunku da zama.” Idanun Malik sauka yayi akan Rahmah, tana murmushi. Bayan sunci abinci, ta kalli Zeeno ta ce mata. “Oum Hassan, bani aron Mijinki!” “Gaki gashi.” Ta faɗa muryanta a sake.
“Muje ko yallabai!” “Wai kin yarda na je?”
“Me zai hana!” Fita suka yi, bayan sun tsaya a jikin motar shi, Rahmah ta fi Zeeno a shekaru, amma bata da ra’ayi akan abubuwa dayawa, kallon shi tayi tana murmushi ta ce mishi.
“Kana son matarka sosai, me yasa ba zaka gayawa kowa ba? And ni a nawa ra’ayin aurenka babu wani cigaba da mace zata samu? Kasan dalilin haka. Kai da matarka kuna haukar son juna, idan har nace xan shiga, karshe zamu bawa juna wahala ne, Ni ban same ka yadda nake so ba, ita kuma ban barta ta same ka kamar yadda kake mata ba, kai kuma baka samun kwanciyar hankalin da ya dace ba, tsakani da Allah waye azzalumi? And shawara daya xan baka, shi ne ka dauki matarka, ka koma dasu inda ya dace. Ana maganar mutane ba zai taba barinku, ku zauna lafiya ba me saka muku idanu, anan kuwa awa society zasu iya haifar maka Matsala tare da gurbata maka tunani, ina gaya maka ne bisa ga zaman da nayi cikin al’ummar mu, please ka tafi da ita. Yarinya ce sosai. Sannan tana bukatarka ainun.”
Rungume ta yayi yana buga bayanta. “Thank you ” ya fada yana sake ta. Dariya tayi tana faɗin. “Idan ka sake wani ya ga wannan abin sai ya maka kallon dan bariki!” Tsayawa yayi ya saka hannu a habbar shi, sannan ya ce mata. “Kuma haka ne fa, bari na fara barikin akan matata.” “Allah ya kintsa tsohon nan” ta juya wurin motarta, ta wuce abinta.

Wato da ana samun mata irin Rahmah da an zauna lafiya, domin cikin ruwan sanyi ta magance rikicin da zai iya kunno kai. Amma wasu matan da bala’i sai sun auri namiji. Kamar yaki idan suka ga namiji sai sun mallake shi, sai aka yi dace ita bata cikin irin wadannan matan, domin she only need love. Shi yasa ba zata tura kanta cikin yanayin da ba zata iya fita ba. Tasan me take yi ta san me take ji, tana son kanta da kuma yadda zata rayu cikin aminci da salama, bata son a rabata da mijinta, gara itama kada tayiwa wani balle a ce za amata….
*Maganar gaskiya akwai matan da sun san namiji baya sonsu, kuma baya kaunarsu, amma don bala’in sai sun aure shi, koda kuwa ajalinsu ne shi. Sannan sun san da haka kuma su hana shi auren wacce yake so, karshe su yi abandoned ɗinshi a duniyarsu! Let met in Nazneen*
*Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/28, 8:16 PM] Yan Mata: 45- Dariya yayi yana faɗin, “Allah ya baƙi wanda zai saka ki farincikin!” “Amin Ya Allah!” Ta faɗa tana d’aga hannunta sama, ta fita ta bar gidan, sauran yan matan da Zeeno wacce hankalinta yake can waje, suka zubawa kofar da zata shigo da shi cikin falon idanu, hadiye abincin bakinta tayi, tana kallonshi. Yana isowa wurinta sumbatar wuyarta yayi a gaban jama’a, kunya ya kamata, shi ko a jikinshi. “Kin san me? Ni babu abinda ya dame ni, kulawa nake bukata!” Ya faɗa mata kasa-kasa, kafin su ankara ai baki daya yan uwanshi sun watse, mikewa yayi ya dauki sauran kayan abincin ya shiga da su kitchen, yana shiga ya fito yana me sumbatar goshinta. “Kin kore mana baki!”
“Ni ban kore su ba, kai ne ka kore su.”
Zama yayi ya saka hannu ya fara cin abincin. Suna hira har ya gama. “Ban ga su Hassan ba?” “Sun bi matarsu sun gudu, me zasu miki?”
“Kawai na tambaya ne!” “Gulma ko? Gaya min gaskiya ko kina son su zo ne, ke da kike ce a cire cikinsu.” Tura baki tayi tana faɗin. “abin har da yar sharri ne? A dai ji tsoron Allah.”
Bakinshi ya kai kan nata, yana tsotsa. “Tsoron Allah ne yasa na fadi Gaskiya, da ba zan fara faɗa ba. Gaya min me kika min da na ka sa boye wacece ke a gare ni?”. Rufe idanunta tayi, tana dariya ta kai bakinta kunnenshi ta ce mishi. “Abin da kake bani kullum a cikin daki a rufe ” “sure?” “Yeap!” “Lallai ma, kin kore min Rahmah kin bar ni a matsayin Yayan gwauro!” Wayar shi ce tayi kara, ya zaro yana dubawa, kashe kiran yayi yana tsaki ya ce. “Elbashir lafiya kuwa?” Bin kiran yayi, ya saka a kunnenshi. “Ya dai Bashir?”
“Malik Hafsah ta sauka, an samu Y’a mace!”
“Kai Masha Allah, Ubangiji ya raya tafarkin addinin Muslunci, cikin satin nan muna hanya. A gaisheta.”
“Allah ya nufa ”
Kashe wayar yayi, yana faɗin. “Kin ji jaruman mata suna ta abin arziki, ke kuma sai sharewa kike?” “Ban san meye matsalarka da karin haihuwa ba, amma ni Alhamdulillahi, uku ma Allah ya musu albarka, a ka’idar likita sai na shekara uku na kuma haihuwa zaka addabi rayuwata da maganar karin haihuwa, sai kace kai zaka dauke min.nauyin cikin.”
“Tow Allah ya baƙi hakuri!” Ya fada yana dariya, itama dariyar tayi. A cikin satin suka bar Kano, zuwa Demark..kafin nan sai da suka tafi Hadejia da Maiduguri, Ummi, sai da ta roke shi ya saka baki a dawo da ita wurin Aunty Zeeno, kuma wani ikon Allah, Ubanta ya yarda aka batawa Zeeno ita, bayan Malik ya saka wani ya nima mata transfer. Zuwa Keivroto.

Abin gwanin dad’i, haka suka tafi cike da kewar juna. A lokacin da suka isa Demark domin har da ita Ummin, suna isa sai da ta ga kanta kamar bakauyiyya, ranar da suka isa tare da Malik suka tafi gidan Hafsy, ba laifi yarinyar tana da kyau domin ta dauko hasken fatar ubanta, basu wani jima ba suka bar gidan, har lokacin babu wani ƙawancen da suke da Hafsah, kowa harkan gabanshi yake, ranar suna kuwa don Elbashir tazo tare Ummi da Wahida, domin Wahiba bata cika shiga mutane ba.

Haka suka je awan su biyu suka bar gidan sunan, Elbashir da Malik sun so lallai su daidaita matansu, amma Zeeno ta hau muƙamin naki, haka yasa dole Malik ya kyaleta. Haka kwanakin suka tafi, watansu guda suka bar Demark suka wuce Keivroto.
Sun iso lafiya, har da ita maijegon da Wahida da Wahiba, haka suka iso. Motar da tazo daukarsu ta kamfanin Malik ne, tun kafin su iso an sanar Malik zai dawo. Don hakan garin ya tashi da wani sabon biki, ga tashin ganguna da yake karade garin. Lokacin da suka isa whiter town, da aka gyara shi a nan Zeeno ta ga Ammyn, cikin farin ciki, ta isa wurinta. “Da alamu yarinyar Ammyn ta girma, ko kefe? Dubi yadda kika koma don Allah?” Dariya tayi aka shiga kawo abinci. Kafin wani lokaci sun huta, Elbashir ya dauke matarshi da Yarshi suka bar gidan, Ammyn ta dauke yan uku, da su Wahiba suka bar gidan suka wuce can bangarensu. A matukar gajiye ta nufi Malik tana faɗin. “Daadi na gaji jikina ciwo yake min!”
Cak ya dauke ta, yana faɗin. “Muje nayi miki wanka da tausa!” Kwantar da kai tayi tana sauke ajiyar zuciya.

Murmushi yayi yana faɗin. “Me yasa kika matso mu dawo, gashi kin kore min yan hira na” “dama ai ba zaman nan zasu ba, wurin Ammyn zasu koma ni nan da mijina ne, idan da mutane ba zan sake nayi abinda nake so ba, a bar ni da tsohona lafiya.”
“Allah ya taro min ke!” Ya fada bayan ya kwantar da ita a gado, ya nufi ban daki ya haɗa ruwan zafi, ya dawo ya dauketa. “Ban cire kayan ba!”
“Zaki cire ai idan kika ji ki a ruwa!”
“A’a Abu Hussain, don Allah taimaka na cire kaya.” Murmushi yayi, sai da ya kaita ban dakin ra cire kaya, suka shiga wankar. Basu fito ba, sai dab magariba, sallah suka yi, suka koma cin abincin. Suka kara fitowa falo.
Bayan sallah isha, dakyar Zeeno ta kai tara. Barci da gajiya yayi gaba da ita. Sai wurin Asuba, ta farka ta ga babu Malik. Ban daki ta shiga ta same shi, a cikin ruwa yana wanka, shiga ruwan tayi, tana me daura kanta a kirjinshi, bata damu da jikar da tayi ba, ta ce mishi. “Shi ne zaka bar ni daki ni ɗaya!”
“Saboda kin san zan iya damunki, shi yasa na dawo cikin ruwan zafi na rage zafi.”
“Ba gani ba, kawai kayi kome da kake so.”
“Ji kamar da gaske dake kin ga asuba tai ba.”
Dariya tayi tana kwanciya a jikinshi. Haka suka gama wankar suka fito, kafin wani lokaci. Sun shiga ya tafi masallaci. Ita kuma tayi sallah, tana idarwa ta zauna azkar har ya shigo. Kur ya mata da idanun tasan halin abinda, sallamewa tayi ta mike, tana cire hijab a hankali. “Don Allah a daina ja min class!” Ya faɗa yana amsar hijab din.

Dariya ta mishi, sai da ta bari ya gama ninkewa ta zille ta fara bashi, wahala dafe goshi yayi ya ce mata. “idan na kama ki zaki sha wahala ne kawai.”
“Oho dai!” Ta faɗa yana juya mishi kugu. “Zainaba idan na kamaki zaki yi kuka kina rokon don Allah a kyale ki,amma ina ce no one more second round!”
“Dake ni tuwo ce ba” ta fada tana juya bom-bom.
“Hmmm Baby girl kada na kama ki fa!”
“Oya kamani mana”
Ai kuwa kafin ta san me tuni yayi sama da ita. “Ayya Daadi kayi hakuri ba zan kuma ba.” Ta faɗa da karfi tana dariya, ai bai bata amsa ba, ya shiga da ita Chinese royal bed dinsu, wanda yake zuwa da labilaye da net. Bawan Allah nan, ya rutsata sai da ta gane Allah da girma yake,domin ya nuna mata no mercy.

Sosai ya gurjeta kamar zai yagata, sannan ya kyaleta suka kama barci, me nauyi. Basu farka ba sai karfe daya, tow an jima ana cin uwar Sabada ina dalili. Sai da suka yi wanka suka huta, kafin ta fita ta dauko musu abinci, ta kawo dakin. Suka zauna suna ci, kallonta yayi ya ce mata.
“Mun dawo Keivroto! Ina son ki koyo dauke kai, wasu abubuwan zaki ji ko zaki gani don Allah ki xama adila a kaina. Ina ruwa ne akan makiya, idan na samu kwarin gwiwa a gare ki, ba zan tab’a nadama da jin tsoro ba, Zainab kece kwarin gwiwata. Don Allah ko text ko kira, kada wani ya turo ya baƙi mamaki, idan kika yi haka kin gama min kome. Wancan abin da ya faru don Allah kada ya kuma faruwa.

Ki tuna akwai Hassan da Hussaini da Maidah. Don Allah kada wani ya gaya miki abu, kiyi fushi fuuu ki same ni muyi magana . Zan saurare miki, Zainab ba sai na gaya miki waye ni, ke kanki kin san waye ni. Ki ɗauke kai daga kan duk wani a abinda zai bata miki rai please.”

Yadda yake bata hakuri da son ta fahimce shi, ya kara mata wani mahaukacin sonshi. Matsawa tayi ta sumbace shi. Sannan ta ce mishi. “Kome xaka yi ina tare da kai.” Rike wuyarta yayi ya shiga lallubar soft and smooth lip’s dinta, ya shiga grabbing ɗinshi crazy.

★★
Shatima.
Idanunshi yana kan Tv yadda aka nuno saukar su Malik da Matarshi da Beautiful kids ɗinshi. “Nadrah kina gani ko? Kice kada na kashe wancan tsinannen, sai na ga bayan shi, saboda shi aka yanke min kafa saboda shi na shiga gararin rayuwa. Dukiyata ta kare, kome nawa ya kare kije ki gayawa media press ki ce musu cikin da Malik ya miki sai ya amsa.”
“A’a wannan ba mafita ba ne, mu fara zuwa ga mahaukaciyar matarshi mu haukata yardan da yake tsakaninsu. Ina son gidanshi ya kama da wuta, kafin na kara bakanta mishi rai da batun aurena.”
Murmushi yayi yana faɗin.
“Yanzu na haifi yar halak!”
Nan suka yi ta shirya sharrinsu.

Bayan tafiyar da Shatima yayi nason ganin Bayan Malik, ya hadu da masifa da bala’in da sai da aka yake mishi kafa, a sannan ka kwashe kudin shi na cikin account dinshi, zuwa yanzu bai da kwanda na shi dai na hannun Nadrah. Ba karamin wahala ya sha, shi yasa ya kuma kullatar Malik a ranshi.
Sai da yayi jinya a gadon asibiti, sannan ya warke. Yanzu haka babu kafarshi na dama an yanke mishi ita. Sakamakon tetanus da suka shiga kafar har ya fara rubewa. Dakyar aka nimo Nadrah ta fara mishi magani, yanzu haka bai daina maganar Malik ba, shi bai gane Hassada ce ta kawo mishi haka….
*Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/29, 8:01 PM] Yan Mata: 45- Kwana uku kenan da dawowarsu. Da yamma ta shirya ta nufi ɓangaren Ammyn duk da a cikin gidan suke amma ko wani gida da tazara a tsakanin juna. A dawowarsu da Malik, ita kanta tasan zuwa yanzu tayi jiki. Domin tana tafiya tana jin kamar jikinta ya mata nauyi. Kiba tayi shi tun wata biyu da suka wuce, izuwa yanzu kuwa kowa ya ganta yasan tayi kiba ba laifi, sai dai a yadda take jin nauyin jikinta. Cinyoyinta sun fi kome d’aga mata hankali. Lokacin da ta isa falorn Ammyn, zubewa tayi a kujera, tana haki. Kallon Mamaki suka bita da shi. “Mommy baki da lafiya ne?” Lumshe idanunta tayi, tana me girgiza musu kai, alamar A’a, dan tafiyar nan da tayi ya saukar mata kasala da gajiya me tarin yawan gaske. Don haka ta bige da barci. Ita da dazo hira dole aka kyaleta.

Kuma maganar gaskiya, Malik fitinanen mutum ne, duk yadda ta kai ga hakuri da shi, sai ya kureta. Idan yayi farkon dare zuwa tsakiyar dare sai ya kuma yi. Kafin asuba sai ya sake yi bayan asuba ma zai ce Bismillah. Shi da kanshi yau da safe yake gaya mata cewa. “Baby Girl, kina shan wani abu ne?” Girgiza kai tayi tana kwance. “Gaskiya akwai wani abu, domin naji new change’s!” Lumshe idanunta tayi, tana faɗin. “Babu kome kawai dai bana jin dadin jikina ne!”

Haka ya tafi yana zolayanta da cewa, ta gaya mishi yaushe zata dauki babynshi, murmushi tayi kawai, ta cigaba da barcinta. Haka tayi barci har aka kira sallah magariba, kafin ya shigo domin ya shiga gida ya samu tana barci. Ammyn kan hana kowa taba tayi, domin daga kallonta ta gano ciki ne danyen a jikinta. Shi yasa take yanayin gajiya da barci.

“Sannu Ammyn, ya Yaran ina mutumina?” “Ya fita gidansu Hibba!”
“Allah ya dawo da shi lafiya.” Ya faɗa yana kallon Zeeno. “Tayi sallah ma kuwa?” “A’a kasan a wannan tak’in ana dan musu uzuri ne, domin yanayin ba yadda take da ba ne, abinda zan faɗa shine kada a matsa mata, kasan har yanzu bata san ciwon kanta ba, yanzu take ashirin da biyu. Idan Allah ya bude idanu lafiya sai a koma kamar da!” Murmushi yayi yana faɗin. “Ita dai mai albarka, Allah ya sauketa lafiya!”
A hankali ya dauke ta, yana faɗin. “A gaida min su baki ɗaya.” Yadda ya ɗauke yana kallon fuskarta, sai yanzu ya lura da yanayinta da ya sauya. Da barci da take yawan yi idan sun gama kula da junansu.

Ayya ashe cikinshi ne, ko da safe sai da ya mata fadar rashin cin abinci. Ta ce miishi. “Baki na ne ba dad’i, da naci.” Shiru yayi yana faɗin . “Ke albarka ce a gare ni, ke Allah ya albarkace ki, !” Tun kafin ya isa kofar entery din main falorn dinsu, aka bude mishi kofar shi,. Yana shiga suka rufe kofar, yana murmushi har ya wuce da ita dakinnsu. Tunda ya shiga ya kwantar da ita, ya zauna, yana shafa kanta. Tun tana jin abin daga sama, har ta bude idanunta. Riko hannunshi tayi tana faɗin. “Barci bai ishe ni ba.”
“Lokacin sallah ya wuce!” Dakyar ta yunkurin tashi, ta koma tana sauke wani irin wahalallen numfashi. “Ko na d’aga ki ne?” “Hmm!” Ta mike dakyar, kallon yadda take kara barcine. “Ya hakuri ki tashi muje.” Murmushi tayi tana faɗin. “kai na kamar zai fashe. Na gaji wallahi!”
“Sannu kin ji” daga haka ta mike zuwa bandaki yana kallon bom-bom dinta, da suka kara cika bayan. “mazaunan ko?” Share shi tayi tayo alolanta, tana faɗin. “Don Allah Daadi taimaka min da abinci!”
“Ok Madam!” Daga haka ya wuce yana faɗin a ranshi. “Duk wanda ya ce ba zai zama bawan mace ba, yayi karya. Keivroto baki daya tsoron malik Menk Jordan ake, amma yarinyar nan saka ni aiki take.” Ya fada yana shiga kitchen yana murmushi. Hada ya hado abincin ya nufi dakin, ya same ta . Bata idar ba sai ya ajiye ya koma gefe yana jiranta ta gama.

A lokacin da ta idar da sallah, ta koma tana addu’a, shima kuma shafawa yayi yana kallonta. Da sauri ta nufi abincin kamar ta shekara bata ci ba, tana hadiye na bakinta, tana tura wani. Tausayi ta bashi, domin a yadda take ci kamar vata tab’a cin wani abu ba, dole ta karya maka zuciya. Wato haka uwa take fama da ciki, cikinsu Yan uku, ashe jinya ya boye laulayin.
Kafin ya dawo daga duniyar tunani, ta tashi da flat din. Kallonta yayi ya ce mata. “Are you okay?” Gyada kai tayi zufa na karyo mata. Mika mata ruwa yayi ta buɗe, ta sha sosai, sannan tayi gyatsa.
“Bari na kwanta kafin ayi isha!” Riko hannunta yayi yana faɗin. “A’a ki zauna, dai sai ya faɗa mikiko.” Gyada kai tayi ta zauna tare da ku jingina da jikin gadon, kamar jira take ta jingina sai jin ajiyar zuciya take saukewa, barci me nauyi yayi gaba da ita. Zuba mata idanu yayi yana jin wani abu yana ratsa ranshi, tare da jin kamar ya cire zuciyarshi ya bata, wani dadi yake ji, yana kara jin kaunarta yana cike wani kebataccen wurin da ya jima da wawakewa, shafa sajenshi yayi yana kallon agogon hannunshi, saura minti biyar a kira isha, don haka ya kyaleta.

Sai da aka kira sallah, sannan ya tashe ta, shi kuma ya tafi masallaci. Kafin ya dawo ta idar, a daddafe tayi sallah. Ta koma gadon ta kwanta.
Lokacin da ya dawo masallaci, ya samu tayi barci. Wanka ya shiga yayi sannan ya fito ya saka gajeren wando da singlet ya shiga bargon ya kwanta a bayanta.
*Asuba ta gari, Zeemalik*
*** A hankali laulayin cikin ya tasota a gaba, duk da bata amai amma kuma tana ji a jikinta. Domin bata cin abincin sai kwadayin masifa,

Shi kanshi Malik, tausaya mata yake duk da craving din bai bar shi ba, domin kome dare idan ta ji kwadayin ya taso mata, toh ba zaman lafiya sai ya nimo. Karewa da fitina ya kai fitina. Ranar cewa tayi ita lallai ya nimo mata farfesun ganda. A daren ya kira Ammyn ta tambaye ta a ina zai samu farfesun ganda? Shiru tayi kafin ta kira Hafsy, aikuwa aka samu a gidan, ta kuma kiran Malik ta gaya mishi gidan Elbashir zai tafi ya amso, ba tare da bata lokaci ba, yaje ya amso mata. Yana bata ta shaki kamshin ta ce mishi. “Gidan Hafcy ka amso min?” Ta ajiye kwanon. Bata kuma waiwaya ba, ta koma barcinta sai da safe, ya kira Wahida ta amsa musu.

Satinsu uku da dawowa, Nadrah ta kirata a waya, ta mata zagin tsamar miya. Allah yasa Malik din yana nan, kwace wayar yayi domin itama Zeeno ba tayar baya bace kuma ta ce idanunta idanun. Nadrah ta fara gudunta.
Kiran Elbashir yayi ta sa a mishi trace number, kafin wani lokaci an turo a inda suke, daukar motar shi yayi bai dauki kowa ba, ya tafi har gidan Shatima. Ba tare da an bashi izini ba, yar aiki na bude mishi kofar ya shiga, inda Shatima yake zaune sai zare idanu yaƙe. Zama yayi yana faɗin. “dama baka da lafiya ne?”
Shiru ya ratsa falon, kafin ya cigaba da cewa. “ka kira min Nadrah!”
“Ba zan kira maka ita ba, sai me?”
“Ba kome, amma kuma bana son daukar doka a hannu, tsakanina da kai babu kome sai alkhairi, sannan kana cin darajar Mariyah yasa nake dauke kai, daga abinda kuke min, idan da wani ne da tuni ya shafe tarihinku.

Ban san me yasa nake jin a raina na maka uzuri ba, amma nasan har ga Allah kuna cutar dani. Rigimar ta tsaya iya kanmu me yasa sai mun gayyato Yaranmu? Na Kyale ka ne yasa kake wannan tunanin da ba cigaba da farautar rayuwarka, ba mamaki dole ka kyale ni nazo da kafana, kada ka sake na fusata. Domin ba zan maka da kyau. Idan kuma muka sake haduwa. Abinda zai faru ba zai mana kyau ba. Khamis! Kada yarka ta kuma kiran matata, nasan halaccin da kai min, ba zan tab’a mantawa da kai ba, ba zan tab’a yada kai ba, domin ka min adalci da halacci, haka ba yana nufin idan kuka min abu na kyale ku ba. Don haka idan kuma haka ya sake faruwa, sai na baka mamaki!” Yana kai karshen maganar, Nadrah tana fitowa daga dakinta. Razana tayi ta sake wayarta. Takawa yayi har gabanta ya daka mata tsawar da sai da ta kusan faduwa, domin fitsari ta sake a jikinta. “Kada na sake jin ko text messages ki turawa Matata, kada na kuma ganin ko ji wani ya gankin kina me niman tab’a min matata, bari na gaya miki idan layin sadarwan suka ga sakonki. Abin da zai aikata babu me ji ko gani.”

Daga haka ya juya ya fice, kallon yarshi yayi da take kuka. “Ki hada mana kayanmu,mu bar garin nan.”

“Ni ba xan tafi ko ina ba, zan zauna sai naga bayan matarshi.”
“Ki shirya mu tafi, zai kashe ki ne! Tunda ya iya zuwa nan ba tare da yasa an wulakata mu ba, Malik ya shirya yakar mu har sai mun dawo muna rokon shi ya kashe mu. Tunda ya zo da kafarshi yana niman zaman lafiya ne, na bi Malik da sharri babu iyaka, gashi nan Allah ya mai damun abina, don haka kiyi hakuri mu bar garin nan ba zamu kuma dawowa ba. Yayi magana akan halaccin da na mishi wanda kafin nayi mishi, shine ya min har kwanan gobe ina cin halaccinshi. Ba zan iya juyawa alfarman da yayi min ba, gara nayi nesa da shi da haka zan kara samun nutsuwa, da tsira da rayuwata da mutuncina. Na hakura na nisancin rayuwar Malik.”
‘Jin haka yasa baki daya, tsoro ya kamata. A ranta kuwa baza ta tab’a barin garin nan ba, sai ta haɗawa Malik bala’i. Har zai wuce ya ce mata. “kada ki sake tunanin hanyar da zaki cutar da shi. Ke daya kika rage min, idan na sake na rasa ki ba zan yafewa kaina ba, domin ni na kai ki na baro”
Yadda yake mata magana yasa ta hakura da abinda take da niyya, domin kuwa bata taɓa kawowa mahaifinta zai risina ba. Don Malik yazo masa na, sai dai yayi yadda yake so.
—- A bangaren Malik kuwa, da yake gayawa Elbashir tsaki yayi ya ce masa. “Me yasa baka gaya min, na ci uban yarinyar ba. Sam daga Shatima har Lalla Salmah, basu san darajar haihuwa ba, shi yasa suke ganin yaran sun zame musu karfen kafa da zasu na cusa su cikin kowacce badakala.
Allah na tuba ko ina wasa da rayuwata, ba xan yarda Yarana cikin cinikin rai ba, domin ba zan iya kukan da bai da karshe, rayuwa irinsu masifa ce, domin ko sun rasa Yaran basu da kaico. Amma Allah ya kyauta.”
“Yawwa dan gari ka kyauta, ba gashi nan ka bi da Allah ya kyauta ba, ai babu wanda baya kuskure, na dai gaya masa ya jawa yar shi kunne, domin ba zan zuba mishi idanu yarshi tana jangwalo min liki a gidana ba.”
A haka ya kashe wannan rigimar,. Domin kuwa yasan Matarshi a wannan halin da take ciki na laulayi, baya fatan wani abu ya same shi.
Lokacin da ya koma cikin gidan, suke hira yaƙe tambayarta. “Idan kin haihuwa waye kike son a daukota?”
“Ummi Jalilah!” Ta faɗa tana kallonshi. “Hmmm! Ba wata ba?” “Ita dai, nake son zuwanta.”
“Zata mai dake karuwa ne ki fi karfin zariyar wandona.”
Kur ta mishi kafin ta ce mishi. “ba dan tab’a fin karfin zariyar wandonka ba, don haka Boy ka gane ita nake son ta min wanka, domin akwai gyara na musamman da take son ta min tun haihuwar su Hussaini.”
“Hmmm! Tow dai kada a yi abinda zai tsinke min shi, na shiga uku don ba yarda zan yi ba.”
“Sai na ajiye shi, a friji ina kallonshi lokaci zuwa lokaci tunda haka kake son jin magana.”
“Ko daya ba son jin magana nake ba, tausayin tabaryata nake ji, kada ta tsinke wurin cin dad’i.”
“Lallai kuwa, ni kuma turmin nawa ahaka zai zauna ba zai ji wahala ba.” Rike baki yayi yana faɗin. “na shiga 9, haka kike ashe kema?”
*Arewabooks iya book 2 da three*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/29, 10:36 PM] Yan Mata: 47- A hankali cikin yake kara girma, lokaci yana ja. A wannan lokacin babu wani tashin hankali, sai ma ajiye aiki da yayi, musamman na mayor yace baya bukata, matarshi da Yaranshi suna buƙatarshi a tare da su.
A bangaren Shatima sun koma ƙasarsu da Yarshi, don suna komawa ko wata uku batayi ba, ta auri wani dan majalisar kasar, ya cigaba da rayuwarta, Lalla Salmah kuwa itama yarta da take fama da lalura ta rungumeta, suka Zauna a oman.

A lokacin da Malik zai ajiye aiki sai da ya tuntubi Elbashir ko yana son zama mayor, cikin tsoro ya ce masa. “Chab Allah ya min tsari da wannan abin. Kawai ka rike kayanka. Kaine zaka iya da mutanen nan.”
“Allah ya shirya ka.”
“Amin Ya Allah! Tab kai kenan, baka sha dadi ba, sai ni ina zaman lafiyata zaka hada ni da masifa da bala’i. Abin da kowa ji yake kamar ya kashe ka a kai, balle kuma ka bani a shiga yawo damu duniya Malik ya sauka ya bawa hannun damansa, dama abun ana mishi kallon gado ne, ko kaima nasan ba dadin shi kake ji ba, tunda babu me saka ka, babu me hana ka.”
“Duk me yayi zafi ne haka Elbashir?”. “Abin da yayo zafi kenan, zaka hada dani masifar duniya, ana zaman lafiya.”
“Allah ya baka hakuri!”
Ya faɗa yana nazarin yadda Keivroto zata koma hannun wanda basu sani ba. “Kasan meye tunani na?” “Ina zan sani ” ya faɗa yana hada kayan office din Malik ɗin. “Makomar Keivroto nake tunawa.”
“Hamm! Sannu ko? Allah ya taimakawa Dan Madam teresa uwar marayu, Malik kana da kome na rayuwa, don Allah ka kyale jama’a nan haka.”
“Ban san hannun da zasu faɗa ba ne, gani nake kamar za a zalince su?”
“Tow yayan Malik da Zeeno ko?” Fita yayi yana faɗin. “Ba zaka gane ba ne.”
“Da haka gara ka cigaba da rike su, kawai.”
“A’a bana ra’ayi, kawai barsu su gwada wani.” Ya faɗa yana barin bakin kofar, har ga Allah bai san wani hannu garin zata fada ba, sai dai a wannan lokacin zai dauka bai san waye mahaifinsu Wahida ba, haka ya fi kome yi miishi ciwo. Domin baya tunanin zasu samu wanda ba harin albarkatun garin yake ba.
**
Tun baya fitarshi, ta wuce bangaren Ammy. “Assalamu alaikum!” Sallamarta ne ya makale sakamakon hango Hafsy. “Wa’alaikumun Salam! Mamman Maidah kece?” Inji Hafsy tana mikewa da Yarta, Nimrah. Dauke kai tayi tana faɗin. “hmmm!” Ta faɗa can ƙasar makoshinta.
Zama tayi daidai fitowa Hassan yana kiran sunanta. “Moooo!” Haka suke kiranta, basu iya cewa Mommy ba. “Na’am Baby love!” Tabdauke shi tana lila shi. “Ummi!” Ta kwalawa yarinyar kira. “Na’am, Mommy!” Itama tabi bakin sauran. “Duba min Ammyn ta gama dan waken ne?”
“Tow!” Tana shiga ta samu ta gama kuwa, amso mata tayi, ta fito tana ajiye mata, ta saka tare da barbad’ad’a yaji.

“Zeeno kiyi hakuri mana, sai kace ba musulma ba. Ina ta binki ina baƙi hakuri amma sai wani share ni kike!”
Bata ce mata cikanki ba, haka ta zauna tare da saka hannu a cikin abincin, har lokacin bata d’ago kai ba, shigowarsu Malik yasa, Zeeno ta d’ago tana sakar mishi murmushi, tana mika mishi hannu. A hankali Hafsy ta cire hannunta, Malik ya zauna a gefen Zeeno. “Sannun da dawowa, ba zan iya tashi ba ne, karshe abincin ya fitar min a kai!”
Zama yayi ta kalli Elbashir ta ce mishi..”Uncle Elbashir!” “Madam Zainab, a waje Malik zaki ne a wurinki kuwa, abin wasan yara yafi shi, sauƙin ɗauka.”
“Daadi ka ji shi ko?”
“Hmmm! Ina da ja a cikin maganar nan”
“Allah kuwa, gashi nan ko.mace ce tayi mishi magana cewa yake ai sai ya kira Madam”
“Elbashir dauke matarka, ku bar gidan nan, kafin ka tado min rigimar da ba zan iya kwatar kaina ba!”
“Hmm! Dama yan mata kake kulawa, a waje.”
“Karya yake miki, Elbashir ka ji tsoron Allah. Yaushe kaga wata mace na kula wallahi Allah sai. Kama ka, mara mutunci. Abar kauna, kin san ba zanci amanarki ba, da gaske bana kula kowacce mace.”
Murmushi tayi ganin Elbashir, ya fita yana dariya. Sai da ta cinye dan waken sannan suka yiwa Ammyn sallama, yana rike da hannunta. Har cikin gidansu.

Bayan ta taimaka mishi, yayi wanka. Abinci ta zuba mishi. Tuwo ne tare da Ummi suka yi, ya ci sosai. Ya ce mata.
“Idan kika haihu a kawo za a yi sunan, sannan zamu zauna.na tsawon shekara daya domin hannunki ya faɗa da girki.”
“Duk yadda ka ce Mayor;” ta fada tana kwantar da kai a kafadarshi. “Kashe wutar ki zo nan!” Tashi tayi, ta kashe wutar falon ta zo.ta zauna a gefenshi. Janyota yayi ta zauna a cinyarsa. Hannunshi ya kai ya rungume ta, yana faɗin. “Nayi kewarki!”
“Na gode!”
Ya fada yana goga hancinsa a bayanta, gashin da suke fuskarshi yana tsikarar bayanta. Sauka zata yi ya rikota. Tunda cikin nan ya bayyana shi kenan ya zama marayan dole. Sai yadda aka yi da shi, yana fara tab’ata ta ga zai wuce iyaka, sai kawai ta fara gudu. “Zainaba ina kewarki!”
Kwantar da kai tayi a kirjinshi, tana rike hannunshi. “Mayor na gaji ne, jikina kamar ana duka na.”
“Ina jin ƙishirwa ki taimaka na kashe kishina!”
Juyawa tayi tana kallon shi, sumbatar bakinta yayi.
Ta kai hannunta wuyarshi, tana sauke wani irin ajiyar zuciya. A hankali ya shiga grabbing boons dinshi, sama yayi da rigarta. Idanunshi ya sauka a na fulaninta. Yana me sumbatarsu, kafin ya shiga binsu cikin wani fitar hayyaci da kewarta. Itama kamar zata susuce mishi domin ta kwana biyu ba ayi ban ruwa ba, yau kuwa kasa boye halin da take ciki tai, ta mika mishi baki daya abinda yake bukata. Kamar zai hadiyeta, karshe da labarin yayi labari. Cak yayi daki da ita, anan ya surfeta kamar zai kaita makera.

Sosai, ya murzata son ran shi, sannan ya koma gefe yana ajiyar zuciya bayan ya janyota jikinshi, yana shafa bayanta. “Na gode sosai, ban san me zance miki ba, amma ina da yakinin kin fahimci yarena.”
Baki daya ta saka hannu ta rungume shi, tana me barcinta.
***
Fitowa tayi daga wanka, tana kallon Elbashir da yake rungume da yarsu. Yana waya kasa-kasa. Ganin ta fito ya kashe wayar yana murmushi. “Kin fito!”
“Hmmm!” Ta ce kafin ta koma ta fara gyara jikinta, sannan ta koma tana kallon wayarshi da take haske. Ya share kamar bai san me ke faruwa ba.”
“Dadyn Nimrah ana kiranka”
“Hmm! Na gani amma kawai”
Bata ce kome ba, ta kashe wutar dakin ta kwanta, kwantar da yarinyar yayi.yana me kashe wayar. Sai lokacin ta dauke ajiyar zuciya, amma kuma zuciyarta bata yarda ba.

****
Wurin karfe biyu, ta farka ta ga bayana nan. Tashi yayi zata shiga ban daki, ta ji muryan shi a Falo, ban dakin ta shiga tayi abin da zata yi ta fito ta leka falon. Yana tsaye yana waya, da alamu yana jin dadin wayar.
“Na gaya miki, zan sauke ki a school kada ki damu.” Juyawa tayi ta koma dakinta ta kwanta tana jin zafi a ranta. Haka yazo ya kwanta sannan ta sauke ajiyar zuciya, rungumeta yayi, suka cigaba da barci.

An ce yau da gobe bai bar kome ba, domin tun Elbashir yana waya a sace, har ya fara yin wayar a fili. Haka yasa Hafsy fuskarta wani yanayi da ta rasa wanda zata gayawa, sai ta fara ramewa wanda hakan ya sa lallai shiga damuwa. Idan suka dawo da Malik zai fita idan ya fita ba zai kuma dawowa ba, sai dare ya raba.

Wanna abin ysa ta nufi wurin Malik, da sassafe, sakamakon fadar da suka yi. Har Elbashir ya mare ta. Domin rashin kunya tayi mishi. Ya mare ta, lokacin da tazo da assussubar fari, ko masallaci bai je ba. Yadda take kuka zata baka tausayi. Zeeno da itama taji abin wani irin yasa sai da ta damu.
“Shi kuwa sai ya dake ta, yar shi ce? Nace yar shi ce Malik? Gaskiya wallahi ba zai yiwu ba. Kuma itama shegiyar ya mari Kawata akanta, sai naci ubanta dole ma na nimo ta” yadda take masifar karamin haushi taji ba. Daga masallaci, gidan Malik suka nufa.
Sai da suka shiga falon Malik ya ce masa. “Zauna na kira ta” ya faɗa yana nufar cikin dakin Zeeno ganinsu kamar zasu shige jikin juna ya ce mata. “Hafsy zo nan!”
Mikewa Zeeno tai, ya mata wani irin kallon gargadi, fuskarshi babu fara’a.

Yasata komawa ta zauna, tana bata rai. Ita bata so haka ba. Taso lallai sai ta yiwa Elbashir rashin mutuncin. Lokacin da suka fita, suka shiga tattaunawa. Ita kan Hafsy ta kasa magana sai kuka take, ganin yadda take kuka Malik ya kalle shi yana faɗin. “Bashir meye tayi maka da zafi kake mata hakan? Idan laifi tayi sai ka gaya min na mata fada kawai dai ka dakar musu Y’a xaka ji dadi idan mijin Wahida ya dake ta ”
” Malik, maganar gaskiya yarinyar bata da kirki. Jin ina waya da wata mace, sai ta buge min wayata. Abokiyar aiki na ce fa?”
Wani kuri Malik ya mishi yana son lallai yasan, wacece abokiyar aikinshi.
“Hmmm! Wacece ita?”
“Tana nan dai tare muke aiki da ita.”
“Hafsah wai ashe abokiyar aikinshi ce.”
Cikin kuka ta ce mishi. “Baban Hussaini! Musanya kalaman batsa suke, ban hana shi aure ba, amma kuma kalaman da basu da ce ba, maganar gaskiya zuwa yanzu na fahimci bani yake bukata ba, wani abu be can don Allah ka saka shi ya sake ni.”
“Kiyi hakuri dun abin bai kai haka ba.”
Dakyar ya lallabata ta koma cikin gidan, “wace ce ita? A ina kuka hadu?”
“Malik Ummi ce!” “Ummi kuma wace ce ita!”

Sai da ya sauke ajiyar zuciya, sannan ya fada mishi. “Kanwar Zainab ”
“Karya kake Bashir na zaka lalata zumuncin da muke da matarka ba, gobe gobe sai na maida ita wurin danginta kuma.na hana a baka auren…
Mai_Dambu
*Arewabooks iya book 2*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/30, 10:31 AM] Yan Mata: 48- “Kada na kuma ganinka da kanwar Matata, idan ba haka ba sai na bala’in sab’a maka.” “Amma Malik muna son juna, ban ga dalilin da zai saka ka dauki zafi haka ba, Hafsah ko ban auri Ummi ba, dole wata rana zan ga wata ina so gara ta bani hadinka mu zauna lafiya, domin aure kan zanyi shi.” Ya faɗa yana kallon Malik. “Ba zaka saka Hafsah ta tsane mu ba, ta ga mun mata rashin adalci ba, na haɗaka da Allah ka tashi ka tafi, ita Ummin zan mai da ita garinsu.”

Sosai Malik ya dauki zafi ainun, domin yafi Hafsah daukar zafi, koda ya shiga ya kira Zeeno ya ce mata. “Hafsah ta fito su tafi.” Ba musu ta fito suka tafi, ya koma dakin ya zauna yana kallon madubi. Zama tayi kusa da shi, tana faɗin. “lafiya ka zauna haka?” “Lafiya lau, auren Hafsah yana da matsala idan na cire matsalar rabi mune muka haifar mata da shi.”
“Ban gane ba? Kamar ya?” Gyara zama yayi yana kallonta, sannan ya ce mata. “Misali a saka ki a matsayin Hafsah. Ita Hafsah a matsayinki, sai ta kawo yar Uwarta gidan nan ta ganni tana so, ya zaki ji bayan kin kama ni, ina waya da kanwar Hafsah.
Ya zaki ji idan har na kasance kamar Elbashir, domin ina son Kanwar Hafsah, nasan ba kowa zai gane yanayin ba. Amma ke zaki fi gane yanayin. ” Kana nufin Elbashir yana soyayya da Ummi kenan?”
Gyara zama yayi ya riko hannunta, yana murzawa, “adalci daya da zamu yi mata, yana hannunki, duk yadda kika ce zan tsaya kuma zan saurare ki.”
Kura mishi idanu tayi, sannan ta ce mishi.
“Ban san yaushe suka fara soyayya ba, sannan ban san yaushe har wannan al’amarin ba, idan na bari aka cigaba da haka gidan Hafsah ya kama da wuta, wanda nice Sanadi. Don haka nice zan dauki duk wani matakin da ya da ce, idan na jira sai ta zo ban kyautawa kaina ba, domin zai iya kiranta ya gaya mata, gara na je na kirata da kaina.”
“Ki bari tazo da kanta, ba zai gaya mata ba.”
Idan ranta ya kai dubu ya b’aci, asalima kamar zata fashe dama ga ciki shi niman rigima yake balle kuma, an samu. Haka tayi hakuri ko dan matsawa da suke yi na safe Malik, bai samu ba domin baki daya bata da walwala. Shima kuma tunda yaga haka ya bai ja da nisa ba, ya kyaleta.

Wurin karfe bakwai saura Ummin ta shigo, bayan ta ajiye abincin karyawansu. “Mommy Ina kwana?” Ta gaida Zeeno wacce ta fito sanye da doguwar riga.
“Lafiya lau, bani wayarki zan dauki wani number ne!” Mika mata tayi, domin ta shirya zata tafi school ne. “Meye code din wayar?”
“Sunana!”
Sakawa Zenobia tayi ta shiga, wayar ta fara dube dube, kafin ta gama abin da zata dauka. Ta kalli Ummin da take can gefe.
“Ina ga zan gayawa Daadi kawai ya mai daki, Nigeria ki koma can kiyi karatu zai fi zaman lafiya sama da zamanki anan!”
Zubewa tayi akan gwiwarta, ta rarrafo gaban Zeeno. “Don Allah ki rufa min asiri, wallahi shi yake ya bina, amma na rantse da Allah bana sonshi, domin na ji labarin kawarki ce tun na yarinta, wallahi na daina kula shi, shi ne yaƙe ta kirana kome dare. Na rantse da Allah Aunty Zeeno ban ce ina sonshi ba.”
“Me yasa baki gaya min tun farko ba? Me yasa kika ja bakinki shiru?” Yadda Zeeno ta balbaleta da faɗa, ta ji kamar ta rufe ta da duka, ko Malik da yake cikin dakinshi, sai da ya fito ya same su. Riko hannun Zeeno yayi ya tura ta dakinsu, sannan ya fito ya same ta, yana kallon yadda take kuka. “Muje na kai ki makaranta” ba musu ta mike tana kuka, tare da kallon kofar dakin Zeeno. Haka ya kaita makarantar bayan ya gaya musu dalilin da yasa ta makara, sannan ya juya ya koma. Zama yayi yana kallon yadda take mita. “Kiyi hakuri, ta gaya miki gaskiya ai!”
“Gani zata yi kamar cin amanarta nake son yi, shi yasa nake ganin kanwata.” Rike hannunta yayi yana faɗin. “Duk wanda ya ce haka, bai miki adalci ba. Domin nasan wacece ke!”
“Idan kai kasan haka, ita ba zata san haka ba.” Murmushi yayi yana faɗin zata fahimce ki. ” D’aga rigar jikinta, ya sumbaci cikinta. Ture kanshi tayi tana faɗin, ” ina zaka kai da ka daina aiki?” “Dole na fita tunda ina bawan mace, zan tafi kwadago.”
“Ikon Allah, kamfanonin fa?” “Dole na duba su, ko zan barsu a hannun wasu ne? Ina son Yarana su huta, su mori wahalar kakaninsu ” ya fada yana tsare ta da idanu.
“Ai shikenan!”
Sumbatar goshinta yayi yana faɗin. “Bari na karya, sai na tafi wurin aikin!”
“Ok” ta fada tana nufar waje, yana murmushi yadda take tafiya. Rungume ta yayi suka tsaya. “Please tsaya haka, bani ba a dawo Lafiya!”
“Aikin ?”
“Idan na koshi zan yi, yanzu kuwa taimaka min, domin tsufa zai kama ni.”
“Wannan abin na fara gajiya fa!” Kamar va zata barshi ba, kafin kuma ta shiga sumbatar bakinshi. A hankali ya zuge zip din rigar ya fadi kasa. Yana kallon yadda take kara tsawo, dan sunkuyar da kai yayi yana sumbatarta.
Bakinshi ya kai kunnenta, yana faɗin. “Come and ride me!” Ware idanu tayi, zata girgiza kai, kamar ba zata iya ba, domin bata taɓa yi ba, domin bata gane kan ta hau kanshi ba. Ai kuwa wannan karon ba karamin yanayi ya shiga ba, domin kuwa abin da take kafin ta isa abinda yake bukata, sai da ya kusan sumewa. Wato lokacin da ta hau dokin kuwa, yadda take abin ba karamin gigita mishi lissafi tayi ba,

Hannunshi baki daya riƙe da kugunta, yana sake wani nishi yana lumshe idanunshi, domin shi yasan adali yadda yake ji, yadda take sauri-sauri yasa shi juyarda ita, ya sakar mata da wani irin karfi, zare idanu tayi domin har mararta sai da ya amsa, kamar zata yi kuka take rike shi. Bai san yadda take ji ba, domin shi dadi yake kwasa, sai da yayi yayi kamar zai dawwama akanta. Zufa take yi tana jin mararta kamar zai fashe da zafi. “Malik! Sauka marana da cikina da ciwo.” Bai saurare ta, domin kuwa baya jin ta sai da ya samu nutsuwa sosai. Kafin ya janye a jikinta. Janyota yayi yana shafa bayanta. Yana janyewa daga jikinta, ta nime ciwon ta rasa.
Sai barcin da yayi gaba da ita, haka ta shirya ya barta ya tafi aikinshi. Ance baya bata kaɗan. Yana barin gidan ko awa guda ba ayi ba, taji kamar ta jike jabga, ga ciwon mara bude idanu tayi tana kallon agogon dakin. Da mamaki take jin yadda jikinta. A hankali. Ta janye grey duvet cover ɗin da ya rufa mata, jin ruwa me dumi a jikinta yana fita, yasa ta wurgi da duvet din. Jini ta gani. Ta koma ta kwanta tana jin wani irin bala’in ciwon kai. Wayarta da yake side bed, ta janyo ta lallubi number shi. Kamar zata yi kuka, ta ce miishi. “kazo ka kai ni asibiti ina ganin bari zanyi!” Ta faɗa tana jin kamar zata sake kuka me karfi, “gani naj zuwa!” Ko minti biyar ba ayi ba, Ammyn ta shigo, ita da Wahiba da bata da class. Suka shiga, domin suna gama wayar ya kira Ammyn ya gaya mata, da taimakon Allah suka taimaka mata, ta shirya amma kafin su gama shirin ta suma sai biyu, domin jini ne yake zuba,

Kafin wani lokaci sun rud’e, haka yazo ya samesu. Suka nufi asibitin shi, anan akan kwantar da ita, ana ƙoƙarin tsayar da jinin. Sai dai kuma cikin ya zuba, tun jin ciwon zasu iya hikimar tsayar da shi. Domin itama mahaifarta bai da kwari. Fitowa Dr Wardah tayi tana faɗin. “Sir! Ana bukatar jini.”
“Ok muje diba.”
Asalin office dinshi, na cikin asibitin ya je aka zo dibi jinin ya kwanta. Ya huta, a nan dakin ya cigaba da hutawa har Elbashir ya zo. Ya kalle shi, “Malik taya haka ya faru?”
“Wallahi naji tana ce min, ciwo ciki da mararta, ban san yadda zan kare kaina ba domin wallahi kuwa zata iya daukar hakan a matsayin rashin adalci.”
“In sha Allah, babu abin da zai faru.” Sau dare suka bar dakin ya tafi dakin da take. Ya samu bata farka ba. Haka ya gama ya dawo gida, yau a wurin shi Yaran suka kwana, domin Ammyn tana asibitin.
Washi gari ta farka da safe, tana kallon dakin abin da ya faru ya dawo mata.

“Sannun Baby Girl!” Ya fada yana d’agota. “Ban daki zan shiga!” “Tow bari ba kira miki nurse!” Fita yayi can sai gashi da nurse aka cire mata karin ruwan sannan, ta shiga ban daki da taimakon shi. “Ammyn ci abincinki, bari na karasa aikin.” Haka ya taimaka mata har a ban dakin tayi wanka, da ruwan dumi. Sannan ya fito ya dauki mata pant da pad, ya kai mata ta saka sannan ya koma ta daukota. Ya ajiye ta a bakin gadon. “Sannu kinji!” Ya faɗa yana kallon yadda take yatsina fuska. “ciwon ciki ko?” Ammyn ta tambaye ta. “Eh Ammy amma da sauki.” Ta faɗa tana murmushi. Abincin me zafi ya zuba mata yana faɗin. “kici sosai, kuma dumin domin ya gasa miki gurbin da ya zauna.”
Ture shi tayi, ammyn tayi kamae bata gansu ba.
Murmushi yayi yana faɗin. “sannu!” Haka ta ci abincin sosai. Kafin yamma su Ummi da Wahida sunzo, sai dare suka koma da Yara don sun zo da yaran.
Washi gari Hafsah a asibitin ta wuni, sai dare Elbashir ya mai da ita, kwananta uku aka sallameta. Jikinta yayi kyau. Sun dawo da daddare Zulfah ta iso. Tayi kyau ga wani kibar da ta ajiye.

Haka suka wuni, sai dare ta koma gida. Kwananta biyu Jalilah tazo, da kayan gyaran jiki, su da suna tab’a bariki ai sun san kan kowani namiji, don haka ya shiga gyara yarta, ciki da waje, taba kara gurje fatarta tana mara mata huduba. A gidan Ammyn ake gyaran kafin kice me jikin Zeeno yayi kyau, ya kara laushi da taushi.

Sai da ta samu wata guda, domin cewa tayi bata daina ganin jini ba, jin haka shima Malik ya shiga busy domin tafiye-tafiye yake yi, baya nan baya can. Abin ya mata dad’i, kwananta arba’in da biyar, ya dawo daga wata tafiyar da yayi,. Domin lokacin za ayi bikin Ababas da hidima dama karanta ake son ta kammala. Tunda Malik ya ga Zeeno hankalinshi yayi mugun tashi, gashi duk inda ta wuce sai ya bita da idanu. Kafin kace me tuni ya kasa ya tsare, sai da ya wuce da ita dakinshi, Yaren daya ne, amma na yau sai da ya wuce tunaninshi.

Dayawa wasu mazan suna son mace me budadden idanu, haka yasa baki daya Malik yake son Jalilah tana jan Zeeno a jikinta, domin ta haka ne kawai zai more, kuma a kwanakin da ya dawo har ga Allah Zeeno ta zama karuwar da yake bukata, ai kuwa idanunta tar. Sai ma wani iyayi da rawan kai take mishi. Haka ba karamin dadi yake mishi ba.
*Arewabooks iya book 2*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[9/30, 9:16 PM] Yan Mata: 49- kallonta yayi cikin linjeria night gown. Babu abinda yake kara driving ɗinshi crazy, kamar ya ga dark nipples dinta, wani irin rsumma jikinshi yake, yana ganin yadda take wani iyayi da juya jiki, rigarshi ya riko ya kama bakinshi yana mata wani dirty look. Pop candy ya janyo tare da b’are ledar ta wurga bakinta, tana juya shi a saman harshenta. Kura mata idanu yayi yana takawa da sassarfa.
“Me yasa kike min haka!” Tura baki tayi, tana mishi wani irin duba, durkusawa yayi a gabanta yana sauke ajiyar zuciya. Ya sumbaci kafarta. Sannan ya sake bude baki zai magana, ta daura mishi pop din a bakinshi ala dole yayi shiru ba wai don yana da ra’ayin haka ba, haka ma shin pop din, bayi da niyyar sha. Amma ganin yadda ta daura mishi yasa shi kama tsutsa tana wani kallonshi, fuskarshi ya kai bakinta tana lasarshi. Ƙasa jure abin da take mishi yayi, ya maza ya juya bakinshi, tureshi tayi tana dariya ta ce mishi. “Kai matsalarka kenan! Yau babu sai ka saya.” Komawa yayi ya zauna akan gwiwarshi. “Duk abinda kika ce, zan amince ranki shi dade.” Hannunta daya ya kai baya, tare da rike tsinken pop din, ta wani zauna tana kallonshi. Sannan ta ciro pop din ta kira shi da shi. Tasowa yayi yana faɗin. “Ranki shi dade, duk abin da kika ce ni me biyayya ne!” Murmushi tayi tana kallonshi. Dauke wuta yayi yana gyada mata kai da abinda take nufi, cikin girmama shu’umancinta, Hadiye yawu yayi, tare da janyo stool ya zauna bayan ya (🙊🙈🤭🥱 a toh me zan faɗa.) Kwabewa yayi, ta shiga mishi hudubar Umminta Jalilah, tun Malik yana gane a raye yake, har ya tafi duniyar da iya shi da ita, suka fahimci kome da kowa. Daga ita har shi, wannan daren jin shi, suke kamar daren farkonsu. Iya murza juna suke, kamar zasu cinye juna. Sai da suka hada minti arba’in da biyar, kafin suka zube a gadon suna dauke ajiyar zuciya, wasa yake da gashinta. “Baby Girl! Na gode.”
“Khmmmmm!” Riko fuskarta yayi yana yana faɗin. “Mene ne?” “Ban koshi da kai ba ne!” Ware idanu yayi yana faɗin. “anya gaba ba zan gudu da kafana ba? Baki koshi ba!” Dariya tayi tana faɗin. “Eh ɗin!” Tsarki suka yi, sannan suka daura daga inda suka tsaya, wato sai da suka yi laushi sosai. Kafin suka zube a gadon a karo na biyu. “muje muyi wanka, dole ma ba shirya mana tafiya, zuwa Fisto muje muci amarcin mu!”
“Duk yadda kace!” Ta fada, haka suka shiga wanka, suna fitowa yake kara mata maganar Bikin Abbas, wanda a cikin satin za a yi shi. Haka kuwa aka yi tunda aka fara hidimar bata zauna ba, har sai da aka daura aure aka yi dinner da daddare, aka kai amarya bangarenta.

Malik yayi matukar kokari, duk wanda yake da muhimmanci a rayuwar Zeeno sai da ya dawo dashi jikinshi. Sannan hankalinshi ya kwanta. Bayan bikin suka tafi yawon hutawarsu wanda asalima. Kasuwanci ya kawo shi, saboda akwai wasu yan Film da zasu zo shirin Film, kuma zasu dauki hayar hotel din ne baki daya. Haka yasa dole yazo ya basu damar suyi Film a wurin, a cikin hotel din, akwai inda aka warewa asalin masu hotel ɗin.

Anan suka yi sati Uku, sunyi yawo sosai. Har tsawon gidansu ya kaita inda su Zulfah suka yi kwanankin amarcinsu. Ba karamin dadi taji ba, suka koma gida.

Bayan wata guda.
Da yamma suna bangarenta, domin hira suke yi kamar me, sai ga sako ya shigo mata inda aka turo mata.
*Da alamu kin manta waye kike aure ko? Tow ko binciki mijinki Yan matan da yake rike dasu, Yayanshi ne ko kuma farkokinshi ne?*
Dauke kai tayi tare da share sakon, can kuwa aka kuma turo mata da cewa. *Da alamu fa so ya rufe miki idan ba karuwanshi ba ne, tow meye yasa bai nemi ubanshi ba! Think wise*
_Bana bukatar shawara, koma ya mijina yake ina sonshi haka. Sannan ko karuwan Gista baki daya yake ci ina sonshi haka, domin ƙaddarar shi ce, don ƙaddarar shi ba zan fasa zama da shi ba, kai ne ko kece wahalalle ko wahalallun da ba zasu kashe wutar gabansu ba._

Tun daga lokacin ba a kuma turo mata wani tashin hankali ba, sai bayan sati biyu. Gidan tv da Radio suka shiga yayyata. Karya akan shi, na cewa shi ne mahaifinsu Wahida, kuma an ga yana yawan fita da Kanwar matarshi. Lokacin da labarin nan ya fita yana yawo, kamar zai magana Zeeno ta hana shi. Ta ce mishi. “Alokacin da nake daba, idan irin wannan yanayin ya taso, dauko GD dinsu nake na saka a cassa min shi, sai yayi magana.”
Kallonta yayi ya girgiza kai. “Wannan ba shawara ba ce!” Ya share ta, amma kuma a kasan ranshi yaji yayi na’am da abinda ta ce, duk haka daga shi sai sojoji da yan sanda, suka tafi gidan GD. Ganin Malik a gidanshi yasa shi, sake abubuwan da suka faru. Ba tare da ya fahimci kome ba.

Kafin wani lokaci, wasu abubuwan da yake boye suka yi ta fitowa ya ce masa. “PM na yanzu Mr Haris Jabir dayawa basu san cewa kai ne ka kaishi wannan matsayin ba, amma duk wani munakisar da ake yi da sunanka, shi ne yake aikatawa kome domin shi yasa bawa shatima duk wani abinda yake bukata a kanka, ban gaya maka hakan domin na kare kaina ba, hatta Yaran da ake maganarsu. Shi ne mahaifinsu. Room mate dinka ne a gidan yari!”
Shiru yayi sannan ya cigaba da warware mishi duk wani kulli. “Hatta harin da aka kai maka 3star shi ne ya samu taimakon Nadrah da Shatima. Malik hatta kashe Iyayen matarka Mr Haris Jabir ne, domin daga shi har shatima suna Amfani da sunanka, mutanen da suka kashe da sunanka babu iyaka, har yau da ya bamu aikin nan. Kaf duniya tana maka kallon dan taa’ada ne, amma shine yake ta’ddncin. Kashe Primeministan da aka yi, shine yayi hanyar kashe shi. Ta hannun KJK tare da Shatima da Lalla Salmah. Idan na gaya maka abin da yaƙe faruwa ba zaka iya tsayuwa ba, yanzu harinshi na gaba matarka ce, domin ko yayya ta bar gidanka da yake Whiter town. Sannan lokacin da ake yayyata kana luwadi, shi da Shatima suke haƙa, kuma suke fadar kai ne, Ban san iya sharrin da suke binka da shi ba, amma nasan gara ka fuskanci waye a tare da kai, su waye kake taimakawa suke sararka.”

Zama Elbashir yayi yana jin kamar zai suma, domin ba shi aka yiwa irin wannan cin amanar ba, amma ji yake kamar zai mutu da tashin hankali. Murmushi Malik yayi yana faɗin. “Allah yana sona da rahama, shine ya bani wannan a gefena, ba shi aka yiwa ba, ji yadda yake gumi. Tow yanzu ina dan iskan yake?”
“Yana gidanshi na bayan gari.”

Juyawa yayi y bar gidan, bayan ya saka Elbashir da bai da karfi a jikinshi suka bar gidan. Karewa Malik ne ya cigaba da tukin. Yana tuna zamansu na gidan yari, a lokacin da kowa ya guje su, shida Shatima a lokacin shi ya zauna da su, duk da kusan shekarunsu daya, haka suka cigaba da zama. Har zuwa lokacin da suka fita, shi ya koma kasar waje da zama, a can yayi samu damar karatu da kome, kafin ya dawo ya tsunduma harkan siyasa.

Da taimakon Allah da Malik ya isa inda yake bukata, amma yau bai da makiyi sama da Malik. Murmushi yayi yana kallon hanya, har suka isa gidan. Ganin Malik ne yasa suka har shi ya shiga cikin gidan. Har falon da yake ya same shi, domin bai shiga shi daya ba, sai da Elbashir. Lokacin da ya shiga yana kallon Malik sai da ya sha jinin jikinshi.
Murmushi suka yiwa juna, kafin Malik ya ce masa. “Kada kirki kazo ka makale ka ki nima na, ya dace ace ka nimo dan uwanka tunda duniya tasan dai kai daya kake raye!” Murmushi yayi yana faɗin. “Nace bari na huta sai na nime ka. Wai meke faruwa ne, naji labarin marasa tushe.”
“Ina zan sani, abin wasan chess din nan!” Kallon Malik yayi har cikin ranshi ya ji shakkar chess game ɗin, matukar Malik ya nime ko ubanka shaidan ne, sai ya kai kasa. “Me zaka yi?”
“Babu kome, sai wasa.”
Tashi yayi, wani yaro saurayi ya fito daga shi sai rigar barci na mata, a jikinshi yasha kwalliya kamar Bobrisky. Kana ganinshi kaga dan duniya gaba da baya, “sugar kaga yadda n.” Malik bai yi mamaki ba, domin yasan zasu aikata domin sau biyu yana.kama shi da Shatima da wasu ma a wurin wanka. Yayi.musu fatan shiriya Allah ne bai.nufa ba, amma yasan zuwa Yanzu Shatima ya daina.
Ajiye musu abin yayi da abin wasan. “Har yau baka daina buga sunuka ba?”shafa kai yayi yana faɗin. “Zan daina ai!” Yana ganin yadda ya fito da bindigar shi ya ajiye. “Ya da ciro abokiyar tafiya.”
“Saboda tsari domin masoyi yana, iya komawa makiyi.”
Gyada kai, hankali ya ce gaskiya kan. A hankali aka fara buga gamen, kai tsaye ya ce masa. “idan ka fadi fa?” “Ban yarda da faduwa ba, nafi hangen nasara a cikin lamarina, shi yasa na yarda da Allah. Da yake bani nasara akan makiya na!” “Malik ka yarda da kanka, alfahari ya maka yawa. Bari muga inda ba kasa.”
“Ana ake gardamar kokuwa!” Suka ci gaba da game ɗin, yayinda Haris ya dauki bangarenshi, shi kuma Malik yan kare sarauniya.
“Idan na cinye sarauniya tabbas, zan samu Keivroto.”
“Idan na kare Keivroto hatta sarauniyar zan kare, sannan na ƙareta tare da kashe duk wanda ya kutsa sansanin mu…
*Arewabooks iya book 2*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*
[10/1, 10:06 AM] Yan Mata: 50- “Idan baka yi nasara ba, zan kashe ku tare da binne tarihinku anan!” “Ina da tarihi akan chess don haka mu buga a ga waye gwanin.”
Basu kuma magana ba, sai da Malik ya fadi, Haris ya ce masa. “Da alamu tun zagayen farko zan tashi kanka da harsashina. ” Malik bai ce mishi cikanka ba, suka tafi zagaye na biyu. Nan ma Malik ya kuma faduwa. D’ago kai yayi ya kalli haris ya ce masa. “Kuskuren da ka aikata bai ishe ka ba, sai ka shiga rayuwata meye na maka da na cancanci kyautarka haka?”
“Ko wannan don bai da ra’ayine amma waye zai zauna da kai ka mai dashi bawanka? Shima don bai da zuciya ne, taya zan zauna da kai kullum ina ganin yadda kake cigaba. Kai bako ne, kazo kasar mu ka cigaba mu kuma muna binka kamar bingo!”

“Amma kasan dukiyar nan ba nawa bane, na dangina ne da aka rike me yasa kuka min haka!?” Ya faɗa bayan ya bude dogarin da yake tsaye ya saka farin sarki, a gaban bakin Sarki. Kallon juna suka yi. A fusace Haris ya ce. “Kowa a garin nan Malik yake ambaton ka tab’a tunanin yadda nake mutuwa da jin an kira sunanka?” A lokacin Malik Allah ya bashi nasara ya turo bakin Sarki ya kai sarauniyar farin doki sansanin Haris. “Ban sani ba, amma me yasa ka zabi cutar dani sama da kome bayan na maka adalci.” Ya fadi haka , bayan ya ture dakarun bakin Sarki ya kafa bakin Sarki da sarauniyar shi, alamar ta cinye wasar.
Saukar bindigar Haris yayi ta cire bullet din, ta kalle shi. Sannan ya ce masa. “Ga Camera can na kallon, ba zan iya share hujja ba. Amma zan ajiye hujja idan ka gama bayani bullet uku ne, na farko ni na biyu Elbashir, na uku ka ajiye shi domin gobe zaka ji sabon labari, ai na gaya maka ni me nad’a sarki ne! Sannn sai batu na gaba, ka goge abin da ake yayyatawa domin ta haka ne kawai zaka min adalci s tsawon rayuwar da na muku adalci.”
Daga haka ya ajiye shi, suka bar gidan. Zuwa yayi gaban camera footage ya tsaya.
Karfe bakwai na safe, sabon labari ta watsu a social media da gidajen jaridu, inda Haris yake tabbatar da cewa shi ne ya sake cin mutuncin Malik maganganu masu yawan gaske, sannan ana kallonshi ya kashe kanshi, ba tare da wani ya saka shi ba.
Bayan awa daya da mutuwarshi, Malik da damuwa ta hana shi barci, domin raba daki yayi musu, ita kanta Zainaba ganin halin da yake ciki yasa ta nutsuwa, bata je mishi ba. Yana barci aka kira shi a wayarshi. Dakyar ya ɗauka ya saka a kunnen. “Malik!” “Meye?” “Haris ya mutu! Kuma kasan dan jam’iyyar adawa ce.”
“Elbashir Jamal Arab, tare da Khuldu Jahid Khan, sune zasu zama shuwagabannin kasar.”
“Allah ya taimaki Malik, an taya su murna. Amma Khuldu Jahid Khan kuma?” “A rayuwa ana bukatar abokin ciniki koda kuwa makiyi ne, a ya zama Mataimakin Elbashir din!”
Haka kuwa aka yi, Khuldu Jahid Khan, yana kallon labarai aka ambaci sunanshi a matsayin mataimakin Shugaban kasa, sai da yaji kamar ya gudu ya bar kasar, domin abin yazo mishi a bazata, Elbashir kuwa kofar part din Malik ya nufa, ya durkusa yana faɗin. “Na haɗaka da Allah, ka raba ni da mukamin nan, na amince zan amshi Mayor shugabancin kasar nan na jarumi ne irinka, ba irina ba.”
Yana faɗa yana karawa, Banza Malik yayi da shi, bai ko yarda ya bude kofar shiga part din ba. Shiga dakinshi Zeenobia tayi tana kallon shi, yana tsaye a jikin Window zuwa tayi ta rungume Bayanshi tana dariya. “Me yasa ka bashi bayan kasan baya so.”
“Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama, ya ce hana Abuzarin gaffari, matsayi a cikin Muslunci ne don yasan yana da rauni, tunda ya tambaya, shi kuma gudun matsayin yake yasa ba bashi wannan zai kamanta adalci.”
Kwantar da kanta tayi a bayanshi ta ce mishi. “Ina tare da duk hukuncin da zaka yanke domin nasan mai kyau ne.” Goyan bayan da yake samu daga Zainaba yafi mishi kome dad’i. Haka yanayin ya kasance ana ta kiranshi aka taya Elbashir murna.

Garin Keivroto kuwa, bai tashi yin kome a kai ba, sai da za a rantsar da shugaban kasa, sannan ya ayyana Jalilah shuwa a matsayin Mayor, ya haɗa mutanenshi a duk inda Idanunshi yake kai.

Abu daya ya lura da shi, shine idanun matarshi akansu Wahida, don haka tare suka tafi asibiti aka mishi gwajin jini dasu. Aka tabbatar babu alaƙar jini da ya hadasu. Anan ma sai da ta nuna damuwarta amma bata gaya miishi ba.
Tunda suka dawo, ta bude mishi damar cin uwar sabada, gefe guda tattara tsufar mijinta, tana ririta shi.
Haka aka yi bikin rantsar da su, Elbashir aka tashi lafiya lau, Hafsah kanta rawa yake sama da kullum domin yanzu ta zama First lady, duk da haka tana matukar ganin girman Zeeno.

***
Bayan shekara daya, sunan Matar Abbas ake inda ta haifi ya mace aka saka mata sunan Ammyn, an sha suna domin bajintar da suka yi ba na wasa ba ne. Bayan sunan Ummi ta tafi hutu Nigeria, dake har zuwa lokacin Elbashir bai hakura ba, bai boyewa Hafsah ba, itama dake yanzu tana mugun sonshi, bata son ya dauko mata wata mace a waje ta amince ya auri Ummin domin da kanta ta samu Malik ya kore ta. Da cewa Elbashir ne ya turo ta, sai da ta sako iyayenta a gaba suka roki Malik din ya saka baki aka tafi har Nigeria aka nimo mishi auren Ummi, wanda Malik ta ce musu. Shi ya dauki nauyin kome da kome mata kawai zasu basu.
A lokacin bikin ne Akram ya roka a bashi Auren Wahiba, yayinda Sultan kanin Rahmah ya ce yana son auren Wahida, ganin hakan yasa aka haɗa kome aka yi, Malik ya musu kome musamman Yaran da basu da kowa sai shi, shi kuma Malik din ta dauke su a matsayin mahaifinsu baki ɗaya.
Sai da aka yi gaggarumin bikin da ba a tab’a yi ba, domin a Kano aka daura auren, duk da ana bikin nan, Zeeno karfin hali take, domin Malik ya mata shuka, wanda yasa baki daya bata da wani kuzari sai yadda yayi da ita, abin dariya abin tausayi domin a gajiye take wannan karon cikin ya shiga jikinta, domin hutun da tayi ya ratsata.

Haka aka gama bikin, ana laulayi aka turowa Elbashir matarshi, aka tafi da ita. Ita da Malik suka zauna hutawa, domin ta masifar laushi, shi kansa wannan karon lallabata yake yaki zakewa akanta. Haka suka kwashe wata biyu, tana laulayi. Yana mata sauki suka wuce gida, a ranar da suka isa Zulfah ta haihu da dare, kusan wani hidimar ya karu mata, ita da Jalilah. Wacce take Matsayin Mayor.
Sati daya suka yi ta zirga-zirga, tsakanin gidanta da na Zulfah, har aka fita suna. Sannan ya dawo ta nutsu. Abin gwanin ban tausayi. Domin tana samun hutu. Jikinta ya dawo sabo sai da asibiti suka rike ta.
Tsawon sati Uku, kafin suka sallame ta. Alhamdulillahi cikin yana nan lafiya. Domin tana shiga wata hudu, ta samu lafiya babu wani laulayi ko rashin cin abinci. Ranka shi dade kuwa yace ya dawo kan duties.
***
Goge gashin kanta take, yana kwance yana kallonta, “Baby girl! Kin ga wannan karon cikinki ya fito sosai.” Bude towel din tayi tana murmushi. “Ajiyarka sai kara girma yake ba!”
“Da alamu wannan karon babban mutum zan kuma samu, babban mutum an ga gender ɗinshi kuwa?”
“Ai kuwa ban tambaya ba.” Ta faɗa tana daka riga. Ta sanshi da son sanin meyye zata haifa, taki yarda a gaya mata. Wannan karon tana jin nauyin cikin har cikin jikinta.
Hafsah da Ummi, zaman lafiya sosai suke da junansu, ga girmama juna haka yasakawa mijinsu mugun kaunarsu. A hankali zaman ya kara samun fahimtar juna musamman da ya kasance yana boye son da yakewa Ummi domin har ga Allah yana sonta, sama da Hafsy da kawai Malik ne ya zaba miishi ita.
Haka suka zauna cikin Amincin Allah.
★★★
Kwanaki dari biyu da yan kai yake daukar mace,renon cikinta da haihuwa, idan aka hada jimilar kwanankin zai bada sati arba’in da daya ko da biyu. Wanda shine kawai lissafin da azayi kafin a kai da wata tara, ranar haihuwar kuwa daga ita har Malik sai da suka san haihuwa tayi, domin an ci wahala, sannan aka haifi Yaranta mace da namiji. Ɗaukarsu yayi ya musu huduba, namijin shine karami ya saka mishi. Muhammad Elbashir, macen kuwa Sunan Mahaifiyar ya saka, tare da jin kaunar Yaran ita kanta tana son yaran,

Lokacin da Elbashir yana jin labarin, yana da Meeting da manyan mutane, haka ya ajiye ya tawo Keivroto. Sai da Malik ya kore shi. Ranar suna kuwa ba karamin walima aka yi, kyautar da Elbashir ya mata, da yaran, sai da Malik ya tsare shi da tambaya.
“Da fatan ba dukiyar Al’umma ka dauka ba? Ina cewa ba kuɗin mutane ba ne?” Girgiza mishi kai yayi yana faɗin. “Wato Malik baka yarda da nagarttta ba ne? Malik ba zan iya cin hakin kowa ba, ina da shi ina da abin da ko bana raye matana zasu kula da kansu, wallahi daga aljuhuna na cire wannan na basu.”
“Alhamdulillahi, ina tsoron kada Allah ya kama mu da hakkin al’umma ne, shi yasa na ji tsoron kada hakkin Al’umma ce ”
“Rayuwar da babu aboki irinka bata da ma’ana Nagode Malik”

Bayan suna suka cigaba da wankarsu, har zuwa bayan arba’in, inda suka zo Nigeria ta’azxiyar rasuwa Baffa Umaru, wanda yayi fama da dogon jinya, a bakin Gwaggonsu take jin labarin abin da ya faru, tun kafin bikin Ummi yayi hatsari. Shi kenan ya kwanta jinya, satinsu biyu ta wuce Maiduguri, kowa sai son Barka, Inda ta samu Wahiba, tana jan cikinta itama.
A dakin Hajja Yayye ta zauna suna hira ta ce mata. “Hajja Yayye, kin san lokacin bikin Abbanmu da Ummin mu a ina suka hadu?”
“Maganar gaskiya ina Saudiya lokacin, amma labarin da naji ance yazo karatu ne nan, makarantar nan Maiduguri, suka hadu a jami’a, kuma a lokacin har an mata miji amma tace sai shi, ba a ja da ikon Allah ba. Domin mahaifinta mutane da Allah ya mishi baiwar ilimi da yarda da ƙaddara shi yasa ya bata wanda take so.”

“Tow ya aka yi suka yi aka bar Ummi Jalilah Demark?” “Wannan kuma hatsari ne ko nace fashi da makami, ita Mamarku bata bisu ba, don tana makaranta, aka samu labarin abin da ya faru, Allah masani!”
Kawai abin da ta yarda da shi, ƙaddara da rabo. Haka ta gama kwananki ta koma,

Bayan wata biyar, suka zo sunan Wahiba, wacce dama.sai da tayi tunanin haka, domin ta riga Wahida samun ciki.
Bayan sun da sati Uku, Wahida ta haihu itama suka sha hidima sosai. Dukkansu abin mamaki sunan Malik suka saka mata.
Tana nan aka kira Ummi tana asibitin. Dole suka koma kafin su isa aka kira su aka gaya mata ta sauka lafiya, koda suka isa. Bata bai gista ba, sai da aka yi suna da sati biyu. Sannan ta bar garin, ta dawo gidan mijinta.
★★★
Bayan shekara hudu.
Tun safe da Paul yazo gidan, bata san me ya kawo shi, sai bayan tafiyarshi Malik yake bata labarin ashe son Auren Jalilah yake, dake shi yake kare lafiyarta. Shi ne ya gaji yazo rokon Malik ya aure mishi ita, domin zai iya kome domin mallakarta da karfi da yaji. Shi ya shirya musulunta.
Shi kuma Malik ya kira su Alhaji Mustapha ya gaya musu.

“Yanzu dai kinji abin da ake ciki” daukar Adnan tayi dan wurin Abbas tana dariya.
“Allah ya bada zaman lafiya!”
Jan hancinta yayi yana dariya, haka aka.daura auren Bayan Paul ya musulunta.
Walima aka yi, kawai. Jalilah kamar zata yi hauka. Amma wani abin dariya, tunda ya nuna mata shi ba lusari ba ne, tuni tayi watsi da cewa bata son Yaro domin ta bashi kusan shekaru goma sha huɗu.
Yana da talatin tana da arba’in da hudu, sannan abin ya matukar bada kyakkyawan Chemistry.
Duk wasu mutanen da suke jikin Zeeno, Suna cikin amincin Allah da cigaba, musamman wadanda suka yi daba tare, kai ko iyayen Hibba sun ci albarkacin auren Abbas da Hibba tayi, Al’umma Charity House, yana can da su Maman Chu-chu Malik ya dauke musu kome.

Lalla Salmah tazo sau biyu niman, yafiyar Malik da Zeeno ta ce ta yafe, Shatima kan yana can yana girban rayuwa, itama yarshi tana can sai godiyar Allah.
****
Tun da ya shigo ya samu tana tsakiyar Yaransu. Muhammad Nasr, Hussaini, Muhammad Menk Hassan, Maidah, Muhammad Elbashir, sai Sassabilah Mami suke kiranta. Zama yayi ya ce mata. ” Da ace ke wata ce sai ko karo.mana Ammyn da Alhaji Ahmed” mahaifin Abbas da Ammyn. Dariya tayi ta nufi kitchen, tana aiki. Biyota yayi ya rungume ta. “Da gaske ki kara mana biyu ko!”
“Wanda yake ajiye a kasar marana cikin wata hudu fa.” Juyata yayi da sauri ya shiga sumbatar bakinta. “Happy birthday Daadi!” Breaking kiss din yayi yana kallonsu da dukkan mamakin shi. “Gashi nan, Uncle Elbashir ya ce a maka surprised!”
Sumbatar goshin Hassan yayi ya bi sauran ma haka. Tana murmushi, sannan ya sumbaci cikinta da yake cikin riga.
*ALHAMDULILLAHI, NA KAMMALA A PAGS SABA’IN DA DAYA IDAN MUKA HADA DA BOOK 1&2 NA GODE SOSAI MUSAMMAN MUTANEN DA SUKA NUNA MIN KARA NA GODE SOSAI FA KADA KU MANTA NI TAKUCE HAR KULLUM*
*Arewabooks iya book 2*
*Assalamu alaikum……! Guys wannan littafin na kudi ne! 500₦ normal 1k VIP. 0472282105 ramlat Abdulrahman Manga GTBank. Ko katin Mtn, a tura shaidan biya ta wannan number +2347035133148 yan Nijar zasu tuntubi Nana A’ishah. +227 84 50 64 76 500*

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button