Sponsored Links
Hausa NovelsHausa Novels and Love StoriesZafin Kai Hausa Novel

Zafin Kai 81

Sponsored Links

81
Washe gari dole aka fara Shirin fita da DD qasar waje cikin gaggawa babu Bata lokaci
Bena Kuma har lokacin Bata Isa sallama ba
Dan haka bada ita zaa ba zata samesu daga baya daga dd babba sai dad kaante da Zeenah wadda Bena tace taje kawai sbd tana bugatan
Wanda zata kira taji Yaya yake din kafin taji sauki itama.
Safnah Dayake tana gidansu ko ta kanta babu
Wanda yabi sukai Shirin tafiyarsu suka wuce cikin kwana biyu ba Bata lokaci.
****Babban Abinda ya bawa momy da Safnah mamaki shine zuwan Ababa har babban mahaukacin gidan Alh basheer bulama.
Da farko kasa yarda sukai da Abinda me gadi yazo ya sanar musu na cewan anyi bako yace a sanar dasu Ababa ne

Dukkaninsu suna Jin Hakan sukasan komai yazo musu a sauko kenan Dan haka aka ce ya shigo dashi palon baqi.
Ababa da aka shigo dashi karewa gidan Kallo yayi Yana tinanin wannan duk ya Dena Basa tsoro ko daga masa hankali tinda Suma masu kudin sun iya boyayyan mugunta,
Ba garamin ciwo da radadin Abinda dd babba ya shirya masa yaji ba,
Anne tayi masa Abinda ko kasheta yayi Bai cire bagin cikinta ba shiyasa idan tayi Hakan ne
Dan ‘yarta ta dauwama a Kaantes to shikenan kowa ya rasa.
Ko Daya zauna bai Kalli duk Abinda masu aiki suka zo aka Jere masa ba sbd shi abinda ya kawosa lissafi kawai.

Bai wani ima ba momy ta shigo palon Safnah na bayanta idanuwanta a abushe kaman yanda zuciyoyinsu suke,
Kallanta Ababa yayi Yana sake tabbatarda kafurcinta itama bane sauke bane,
Amma koma yayane shi yanzu baida bugatan ta idan har zata fanshi kanta da dukiyar
Bulama,
Baima da alaga a aynzu da ita bayan wadda zasu kulla yanzu ta kowa ya samu Saar Wani tasa ta fisshesa.
Zaman sukai babu Wanda ya gaida Wani a cikinsu sai Safnah data Bude baki zata gaishesa ya daga mata hannu Yana cewa
“Me kukeso Dani da kuka sameni da duka maganganun jiya??

Ajiyan zuciya suka sauke tare sbd yanzu ne
Akazo daidai inda sukeso.
Safnah ce ta mige ya koma ciki tareda fitowa da wata babbar jaka baqa ta ajiye gabansa momy tace
“Matsayinka na Wanda ya haifi Safnah nakeson siyewa har abada Kai ba ubanta
bane.
Wani shegen murmushi Ababa ya sake Yana kallansu sbd ko Basu siyaba har abada shi ba uban nata zai zama ba,to Amma idan zasu
Siya matsayinsa da Sunansa na ubanta da wanann jakar uban kudin to kenan Alh basheer bulama nawa zai Basa ya siyar masa da gaskiyar Safnah ba yarsa bace,RIBA BIYU ta farko kenan,
Take wannan lissafin Ababa a hau masa ya sake kallansu ya janyo jakar kudin gefensa yace

“Taje na barwa duniva ita har abada.”
Bayan shi sai me?
Zama Safnah tayi wanna Karan itace ta Bude baki sbd a yanzu ta Siya yancin ta daga
Ababan ta kallesa tace
“Zan baka duka kasona na duk abinda na mallaka ka raba auren Benazir da DD..
Wani murmushin takaicin Ababa ya saki sbd da alama dai ba lissafin komai akansu,
Koda su ko Bada su ba baida niyar barin Bena da Anne su samu zaman lafiya..
Katsesa momy tayi da cewa
“Nasan dama ba barinsu zakayi ba Amma hukuncin da mukeso ka dauka shine batar da Bena ta fita rayuwar kaantes gaba Daya har
Abada.”
Kai tsaye ya katseta Shima da cewa
“Bayason kaso kason dukiyar da ake cewa zaa
Basa rabawa biyu zasuyi daidai su Basa Rabi su dauka Rabi su biyu idan suka Basa yayi musu alkawarin Bena tabar rayuwar kaantes kenan har Abada barema asan asalin Safnah
Dan haka zata tabbata Safnah bulama har abada

Amincewa sukai babu ja,
Shima nasa sharadin ya bayar na duk abinda kaantes suke ciki gameda Abinda da babba zaiyi da duk Wani motsinta Safnah ta sanar dashi haka zalika a fili baida alaqar komai
dasu.
Wannan lamarin ya saka zuciyoyinsu duk gamsuwa da Abinda suke so shikuwa Ababa baqin cikinsa ne ya qare,
Dukiyar Daya rasa hannun kaantes ta dawo masa ta gidan bulama saidai Kuma tabbas
Rabin dukiyar bazata ishesa ba idan ya gama dasu Bena kodai su Basa sauran dukiyar ko
Alh basheer bulama ya Basa da Kansa idan yakai masa ziyara me kyau har porthacort.
Dag wanna driver akasa ya mayar da Ababan gida Wanda gabaki Daya yakejin duniyarsa ta fara dawowa daidai yanzu
****Bena kuwa Nafisat ce tazo jinyarta Dan haka tasaka akazo mata da Amnah Amma baa barta ba Abbakar ya mayar da ita gida.
Bayan tafiyar Amnah Bena wayarta ta dauko da aka kawo mata ta kunna sai alokacin sakon
Abbakar ya shigo na footage din da dd babba yace a tura mata ta duba.

Gabanta har faduwa yakeyi sbd Bata taba ganin matar D ba sai yau din Dan haka taji zuciyarta Bata cikin nutsuwa.
Bude video din tayi tafara dubawa na shigowan Safnah highbridge da fitarta.
Bata Wani ganeta ba sbd fuskarta ba sosai ya fito ba sai lokacinda Safnah din ta tsaya kofan shiga tana saka password din kofan shiga
Wanda daganan babu cameras a cikin Palo da dakunan gidan sbd privacy.
Dawo da footage din baya tayi ta sake kalla hannuwanta na rawa wayar na Neman kasa tsayuwa a hannunta.
Nafisat dake kallanta cikin mamaki da fargaban Abinda ya sameta ta kalla muryarta na sarkewa tace “Kinsan matar Daddyn Amnah?
Kin taba ganinta?
22 PA
Gyada Kai Nafisat tayi tana cewa “eh”
Da sauri Bena ta nuna mata wyaar tana cewa
“itace wannan??
Kallo Nafisat tayi tace “eh
Kasa yarda da Abinda take Gani tayi jikinta na rawa ta shiga Google tayi searching Safnah basheer bulama take hotinan Safnah suka bayyana har Dana aurenta da D.
Yawu Bena ke neman rasawa na hadiyewa ta dauko gadonta da sauri qafafunta na rawa ko taku biyu bataiba ta Yanke jiki ta Fadi gurin sbd ko mutuwa tayi ta dawo duniya tasan wannan Safnah dinsu ce.
81
A rikice Nafisat ta fito ta kirawo likita tana
Neman hawaye sbd batasan meya same Bena din ba.
Ciki gaggawa aka dauketa tareda mayar da ita gadonta aka Kwantar tareda dubata aka gano mummunan shock ne ya shiga.
Kusan awa Daya tayi kafin ta dawo daidai ta Bude idanuwanta dasukai mata Wani masifaffen nauyi hankalinta tashe ta janyo wayarta Kai tsaye Abbakar ta kira Bata tsava masa bavani ba tace ya tura mata numbern
Safnah matar DD.
Hannuwanta rawa duke kaman yanda zuciyarta ke rawa da matsuwa a turo numbern tafara Jin muryar wannan Safnah din ta sake tabbatarda Safnah dinsu ce,.

Sakon numbern ne ya shigo mata da sauri ta
Bude Kai tsaye ta saka Kiran numbern tahau ringing.
Ringing wayar takeyi har ta kusa tsinkewa
Safnah dake zaune tana cin abincin datai kwanaki Bata iya ci ba sbd tashin hankali sai yau datasan idan Ababa yaso Abu to tabbas yasan yanda zaiyi Koda masifa ya samo mafitarsa Dan haka su yanzu sun samu madafa.
“‘Hello” ta furta Kai tsaye tareda cewa
“Who’s speaking??”
Murya na yankewa Bena ta ambaci sunata Kai tsaye itama tana cewa

“Safnah,kece kuwa? Safnah kece matar DD???
Safnah dake cin abinci take ya dawo mata har ta hanci ta saki wavar tana Neman ruwa Tasha kada ta mutu Dan abincin yayi cikin kanta da hancinta.
Yanda take barin kayan abincin dake kan dining Jere gurin Neman ruwan Sha ya saka momy fitowa tana mamaki da cewa
“Ke lafiya Kuma?
Meya faru?
Ruwa Safnah ta samu ta Sha a gigice idanuwanta na ja ko daidai Bata gama dawowa ba tace
81
11⅝110
Q2 PA
“Bena ce,Bena ta Gane Miji Daya muke aure
Bena ta ganoni.. shikenan komai Zai lalace.
Momy cikin rikicewa tace
“Banganeba,garin Yaya?
Ya Akai ta Gane?
Meya faru wal.
Kasa amsawa Safnah tayi ta koma inda ta yar da wayarta da gudu ta dauko tana Neman numbern Ababa hankali tashe.
Ababa na gama Jin Abinda Safnah ta fada
Shima hankalinsa ya tashi sbd idan Bena ta
Fadawa Kaantes uwa Daya Uba Daya take da matar DD Daya Shima nasa wasan ya qare yanzu tin Bai fara ba sbd asirin su Safnah na tonuwa Shima tasa ta qare sbd dd babba
Daman hanyar garasa tarkesa yake,haka
Kuma shi hanyar samun kudi tazo masa Yana kwance saidai su sato su Basa bazai yarda komai ya samu wannan hanyar tasa ba,ko waye ya so kawo masa wasa wlh baddashi zaiyi bare su su Safnah dasuka Saba kisan.
A Asibiti kuwa Bena Neman zaucewa takeyi ta saka Kiran da babba wayarsa bata shiga sbd
Basu Isa sauka bama.
Rudewa tayi sai kawai ta tattara kayanta tacewa Nafisat su tafi gida bazata iya jiran ko driver yazo daukansu ba tana bugatan Isa gida asan babban masifan dasuke ciki na auren miji
Daya itada yar uwarta.

Babu likitan dayasan da ta fice daga Asibitin a Karo na farko data Tari abin hawan haya tin bayan shekarun baya.
Kai tsaye kaantes ta nufa suna Isa babban gate din farko aka ajesu ta zira kafarta Daya , zata fito napep din Datake ciki jikinta na tsananta rawa.
Wayarta ce tayi ringing Bata tsaya dubawa ba ta fito ta nufi gate aka Bude mata zata shige kenan Kiran ya sake shigowa ko dubawa bataiba ta daga.
“Idan kika gara taku daya daga inda kike bak
Zo yanzun Nan kin sameni ba kisani daga yau kinyi bankwana da Annenki har abada wih”
Cak ta tsaya idanuwanta na qafewa daga hawayen dasuka cikasu.

Kallanta securities sukai gain yanda ta tsaya kaman wadda komai na jikinta ya dauke wuta.
Nafisat ce ta dawo baya zatai mata magana
Bata ma tsaya Jin komaiba ta juya Kai tsaye ta fada napep din data fito securities Basu gama sallamansa ba tace ya juya da ita.
Lafiya suke kokarin tambaya Amma babu
Daman Hakan sbd jajir da idanuwanta sukai take.
Gudun gaske tasaka Akai da ita zuciyarta na
Neman Dena bugawa da tinanin idan Wani
Abu ya same Annenta
Koda suka iso ko Gani sosai batayi sbd nauyin zuciyarta cikin gidan kawai ta sauko ta shige.

A tsakar gidan ta tadda Annenta yashe a qasa gabaki Daya kamanninta sun sauya tana rakube ko hankalinta bata ciko.
Da gudu benazir tayi kanta ta rungumeta tareda Sako wasu irin hawaye masu tsananin zafin gaske.
Bata gama sauko da hawayenta ba taji muryar
Ababa a kanta yace
“Zan baki mahaifiyarki a yau ki tafi da ita har abada na sauwake mata tareda karya kafi na akanta Amma kema Kuma Zaki bace daga rayuwar kaantes gabaki Daya ku tafi inda babu
Wanda ya sanku idan ba haka ba wlh daga yau bazaki sake ganinta ba kema har Abada

Cikin Wani mummunan yanayi na firgici da tsoro tareda mummunan bugawan zuciya ta juyo ta kallesa ko bakinta ta kasa lya motsawa bare magana.
81
ll Bis
Q Ад
Safnah da momy ne suka shigo gidan Kai tsaye kowannensu hankalinsa tashe Dan Basu dauka Bena ta iso gidanba.
Tana ganinsu ta miqe tsaye jikinta de mutuwa
Yana garasa sakewa gaba Daya zata nuna
Safnah da yatsa tayi magana Safnah din ta juya baya ahankali sbd bazata iya kallansu ko hada idanuwanta dasu ba ita da Anne.
Ababa ne ya katse mata Dan sauran hanklin
Daya rage jikinta na fahimta da cewa
“Idan kin amince ga mahaifiyarki Nan ki dauka

ki tafi na sallameta.
Benazir kasa daukan zancen kunnenta yayi ta zube qasa gurin tana Neman sumewa Safnah tayi saurin tarota jikinta tana jujigawa tace
“Karkiyi gardama Bena sbd Anne Zaki yarda da Hakan ku tafi kuyi rayuwa cikin sauki da kwanciyar hankali”
Tashin hankali da firgicin kalmomin Safnah suka saka Bena kasa sumewa ta zubawa
Safnah din Ido kenan da alama sunsan miji
Daya suke aure.
Muryarta na rawa tace
“Safnah kinsan miji Daya muke aure??
Sakinta Safnah tayi tareda miqewa tana cewa
“Nasani shivasa nace akace ki dauki Anne Ku taflyarku Dan Allah,
Kece kawai Zaki kula da Anne yanda ya kamata Dan Allah ki dauketa ku tafi”
Wasu hawaye da Bena Bata taba fidda masu zafinsu ba tinda take a rayuwarta suka zubo mata tana Jin kanta na juyawa.
Anne da batasan me ake fada ba Jin a raffafo ta kama Bena tareda riqe hannuwanta gar tan kallanta alaman karta barta.
Wace nannauyar qaddarar ce wanna ta afko mata?
Bata tashi sanin miji Daya suke aure ba da
‘yar uwarta Sai bayan da sukai kwanciyar aure bayan shekaru da aurensu.
Ta bangare Daya Kuma batajin a yau din zata bar mahaifiyarta a Nan din Koda Hakan na nufin zatai nesa da DD kaman yanda suka bugata.

Miqewa tsaye kawai tayi da Annenta a hannunta Bata iya furta kalma ko Daya ba ta wuce tana daga qafafunta da qyar.
Ababa Data kusa ficewa tabbaci ya Bata akan duk ranarda ta dawo ko Neman Daya daga cikin yan kaantes to tabbas ba fashi aikin dake kan Annenta daga ranar zai karye Kuma karyewansa na nufin rasa rayuwarta.
Bata iya waiwayowa ba ta garasa ficewa
Annenta na gangameta cikin tsananin tsoro.
Fitarsu gidan Anne ta sake wani ajiyan zuciyan da batasan ma da a sauke ba ko waiwayo babu Wanda yayi acikinsu suka nufi babban titin bayan garin Kai tsaye.
Tafiya sukeyi babu Wanda yake hayyacinsa a cikinsu har sukai Nisan Daya kusa fiddasu gari gaba Daya.

Wata Black beymach ce tayi parking gabansu tareda Bude musu motar aka ambaci sunata
Ta dakata daga ita har Anne suna juyowa a tare
Itace tafara ganin Wanda yake cikin motar ko bugawa zuciyarta Bata samu Daman Vi ba ta
Yanke jiki ta Fadi gurin a some.
fitowa yayi daga motar ahankali tareda zagayowa ya dauketa ya saka motar ya kama hannun Anne itama ya saka motar ya rufe yaja da mugun speed duka kama hanyar barin garin gabaki Daya.
#MAMUH#
#DBENA
#BILAL KAANTE
#newlife

*_Arewabooks@Mamuhgee_*

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button