Sponsored Links
Hausa NovelsHausa Novels and Love StoriesZafin Kai Hausa Novel

Zafin Kai 5

Sponsored Links

5
Haka suka sake kwana da Anne a hakan babu sauki ko kadan saima galabaituwar datayi ga daurin da sukayi mata yana cin hannuwanta da qafafunta dole suna kallo sbd ba yanda suka iya,

Sumayyah ce ta fara fahimtar Yanda duk suka bar Annen da safnah a daki sai jikin Annen ya tsananta musamman fizge fizgenta gashi duk ta goge gefen fuskarta har jini yakeyi sbd yanda take goga fuskar daga kwancen datake tana buga kanta.

Cikin mamaki da kasa gasgatawa suka tambayeta meyake faruwa duk suka bar anne tareda ita
Bata boye ba ta sanar musu ta fadawa Anne ne zata tafiyarta kaman samirah.

Cikin firgita sumayyah tafara hawaye tana riqo safnah din tace “ me kika yiwa Mahaifiyar data haifeki?
Kinason kasheta ne?
Kinada tinani kuwa?
Wane irin burin guduwa ne ze saika ki ringa cinnawa mahaifiyarki hauka dan kawai ki gudu.

Benazir fararen idanuwanta dasukai laushi da galabaita ta zubawa Anne dake sake goge fuskarta da qasa batareda da jin zafin ciwon data yiwa fuskartata ba,
Sarewa qafafuwanta sukayi tanajin kaman zata gaza,
Itama taya qwaqwalwar jin tayi kaman zata buga dan lamarinsu na gab da qarasa tabarbarewa idan suka fara samun son kai da rashin tausayin juna a tsakaninsu.

Safnah da zuciyarta tafara bushewa ta kallesu tasake tabbatar musu da guduwa zatayi ta zabi bin duniya akan zama karkashin Ababa.

Sumayyah kuka kawai takeyi tana kokarin dawo da tinanin safnah din a hanya amma sam safnah taki sauraranta sai hayaniya taso barkewa tsakaninsu
Benazir data rasa abin fada ko yi sai kawai ta qarasa gurin Anne ta dagota zaune ta kwantar da kanta a jikinta tana goge mata jinin fuskarya da hannun zumbuleliyar doguwar rigar gwanjon dake jikinta sbd sune suturarsu.

Sumayyah da duk ta firgice da tashin hankali da tsoron jin kudirin Safnah din kallon Benazir tayi cikin tsoron abinda zai iya biyowa baya tace

“Benazir kiyi mata magana dan Allah kada ta aikata hakan”

Rintse idanuwa Benazir tayi tareda yiwa safnah din kallo daya wadda ke kallonta itama kaman suna yiwa juna kallon dayake faduwar da gabansu su duka biyun saidai kowannensu ya kasa furta kalma ko daya.
Daga hakan dakin ya dauki shiru sai hawayen sumayyah dake zuba tana fidda karamin sautin kuka.

Da daddare duk fada da yada maganganun Hande akan rashin fitowar Anne basu ce komaiba sbd kada ta tsananta tace sai Annen ta fito.

Safnah bata saduda ba cikin kwana biyu ta tabbatarda ta zaburar da ciwon Anne gabaki daya ta hanyar dawo mata da yanda Samirah ta rasu da yanda itama zata tafi ta barta,
Babu mai imanin da zai kalli Annen bai zubar mata da hawaye ba hakama su benazir sun shiga mawuyaci matsanancin hali na yanayin mahaifiyarsu haka Safnah kusan takoma tamkar maqiyarsu sbd yanda ta fidda asalin son kanta da tsame kanta daga halinda Annensu take ciki gashi basuda ikon hayaniyar da zata ankarar dasu Hande halinda suke ciki dan haka suka zabi tattarawa su koma bangaren dabbobi sbd tsanani da lamarin ya qara.

A ranar da sukai kwana biyar a wannan halin da rana tsaka Suna can suna aikin wankin kayan Ababa dana Hande ga aikin wankin fatar da aka kawo kusan mota biyu sunata yi cikin gajiya da yunwa.

Safnah silalewa tayi ta koma dakin dasuka rufe Annen ta tsaya a kanta tana kallonta tsawon mintina kafin ta sauke numfashi mai zafi ta durkusa ta warware mata daurin da sukai mata na hannuwa dana kafa.

Sanin da rana Ababa baya gida Hande ce take tsaronsu ko ina bata zuwa sbd su din haka koma ta fita tabar musu gidan a bude Annensu bazata taba iya guduwa tabar gidanba sbd aikin da Ababan yayi mata daga ranar daya aureta duk tsanani da azaba bazata iya tafiyaba har sai ranar daya gaji yace ta tafi da kansa.

Janyo Annen tayi ta nuna mata dakin Hande tace mata taje can samirah na ciki Hande ta boye.

Jin hakan yasa Anne da qafafuwanta duk sukai sanyin dauri amma bata damuba sbd ciwo ta nufi dakin Hande da gudu ta fada tana zubar da kaya tana neman samirah idanuwanta a waje bata ji bata gani.

Cikin bacci hande taji kaya tako ina a kanta a firgice ta tashi tana neman dauki sbd komai janyowa Annen keyi ta yadda ta fasa tana neman ‘yarta.

A rikice zani na neman sauka Hande ta fito tana ihu tana neman agaji saidai su benazir na can gangaren dabboni basa ji sosai
Safnah dake boye tana jiran hande ta bude gida ta sake leqowa zuciyarta na wani irin tsalle da azababben tsoron yaya tata qaddarar guduwar zaya qare.

Kan Hande dake daura zani Anne tayi tana kokarin duba ‘yarta cikin zanin
Tini hande tayi hanyar kofar gida tana fizgo dankwalin kanta sa mukullan gidan ke ciki daure ta bude gidan da sauri hannuwanta na rawa dan a duniya tana tsoron mahaukata tunda sukai sanadiyar rasa hakorinta biyu a wani kauye dataje biki.

Tana bude gidan ta fice da sauri tayi bayan gidan tana kwada kiransu Benazir dake ta cikin gidan hankali tashe dan bazata shigoba sai sun kama uwarsu sun daure.

Safnah dataji wani nannauyan abu ya fada daga kan kirjinta bayan ficewar hande fitowa tayi daga mabiyarta ta mufi kofar gidan batareda ko so daya ta waiwaya ta kalli inda mahaifiyarta ta fadi qasaba tana buga kanta sa qasa ta fice daga gidan ta bi ta bayan da Baa nan Hande takeba ta lullube kanta ruf da qaton mayafin Hande data dauka a igiyar shanya ta dosa daji kai tsaye sbd idan ta nufi cikin gari zata dade bata bar garin ba.

Su Benazir dake galabaice suna aiki ba wani qwari ko cikakken kuzari a jikinsu sukaji ihun kiran da Hande ke musu ta katangar bayan gidan da sauri suka taso hankalinsu tashe.

Benazir ce tayi kan Anne da gudu tana riqeta daga ciwon datake jiwa kanta,

Sumayyah kuwa tsaban rikicewa da firgici ‘dakin handen ta nufa tafara tattarawa babu inda baya rawa a jikinta cikin mintina kadan ta gyare dakin ta maida komai inda yake ta fito har lokacin a rikice take dan tasan yau suda mahaifiyarsu sai Allah.

Benazir kuwa cikin matsanancin tashin hankali take jan Annen takaita daki ta fashe da kuka mai qarfinda bata taba sakiba a rayuwarta.

Kukan Benazir yasa Anne tsayawa cak daga mutsu mutsun datakeyi ta zubawa Benazir din ido kaman me nazari.

Kuka sosai Benazir keyi tana sarewa daga komai na rayuwa,
Sumayyah na shigowa a firgice sunan safnah tafara kira tana cewa,

“Ina safnah?
Ina tayi?
Bangantaba?
Bata koina…

Dakin tabi da kallo bataga safnah din ba qarin sautin kukan Benazir ya tabbatar mata da safnah ta tafiyarta kuma tabbas itace ta warware Anne ta sakota,
Kenan da mahaifiyarsu tayi amfani dan cimma burinta a mafi wulaqancin hanya tayi amfani da uwar data haifeta.

Silalewa itama tayi qasa ta fasa kuka mara sauti dan batada karfin yin me sautin ma koda taso.

Wani irin kuka sukeyi wanda radadinsa ke fitowa daga qarqashin qasan rai mai ciwo da qunci da baqin ciki tareda qaqa nikayi.

Kaman an yayyafawa wuta ruwa ta mutu haka Kukansu ya yayyafawa yanayin Annensu sanyi gabaki daya ta rakube guri daya tayi shiru tana kallonsu da idanuwanta dasu kansu ciwo sukeyi na rashin bacci da zarewa.

Lokaci mai tsayi suka dauka a hakan kafin suka fito sukai Alwalan sallar magriba suka dawo sukayi kafin suka kama Annen suka fito da ita zuwa can bayin baya da akai musu a cikin dabbobi sukai zaunar da ita kan kujerar karfe sukai mata wanka fes sbd tunda tafara ciwon bata samu wanka ba.

Kaman yarinya qarama haka suka kamota suka dawo da ita abincin da Hande ta basu cin mutum daya shi suka barwa Annen tacinye rabi rabin duk ya zube.

Shiru sukayi a daki babu me iya magana sbd rashin sanin makomarsu data Annensu suna jiran dawowar Ababa.

Addua sukaita tofawa Annensu suna rokon Allah sauki da mafita sai gashi cikin yardar Allah bacci ya dauketa a inda take zaune dan haka suka gyara mata kwanciya tareda rufeta da wani barkakken zani.

Guraren karfe tara sukaji bude kofar gidan a tare dukkaninsu suka miqe daga kwancen da suke jikin sumayyah na wani irin kerma da fizga ta kalli benazir wadda su kadai suka ragewa juna gashi benazir nada juriya da jarumta amma sam ita Allah bai bata ko daya ba sbd kusan rauninta yafi na kowannensu.

Ahanakali Benazir ta tashi tsaye tareda kama sumayyah din da bazata iya miqewa ba sbd tsananin kerma da tsallen da zuciyarta keyi kaman zata buga.

Kafafuwansu na rawa suka fito tsakar gidan da tini Hande tafara zayyane masa abinda ya faru.

Tsayawa sukayi daga inda sukasan yana basu umarnin nesancinsa dasu.

Wani wulaqantaccen kallo yake musu kowaccensu kanta na qasa suna kokawa da tarin tsoron dake zuciyoyinsu.

Ganin su biyu kawai yasashi juyowa da kyau yana kallonsu babu alamar rahamar kauna ko tausayi na digo daya a fuskarsa da Amon muryarsa me gigita duk wani ruwa da abinda yake aiki a jikinsu kai tsaye yace,

“Ina Safnah?”

Wani qarar kuka mai qarfin gaske ne ya fito daga cikin Sumayyah datake gab da shidewa sbd tashin hankali.

Idan yana tsaye sumayyah bata taba iya magana sbd firgita dan haka Benazir da itama take cikin mawuyacin halin tashin hankali dole tayi qarfin halin bude baki muryarta na wata irin rawa tace,

“Bata nan ta tafi……..Wani jahilin marin bayan hannu ya saukar mata ba zata a fuska wanda yasata kifewa a gurin bakinta na fashewa.

Tasowa tayi batareda ta dora hannu a gurin ba still kanta na soke a qasa dan basa dagowa a gabansa.

Shaqota yayi idanuwansa waje take wani kumfa na tsananin masifa ya cika bakinsa yana fesowa ya sake sauke mata wasu marikan guda uku a jere yace,

“Bata nan ina taje??

Duk wuya baya tambaya aqi amsawa dan haka cikin azaba tace,

“Ta gudu”
Wurgi yayi da ita dukkanin jikinsa na rawar masifa da tsananin bacin rai na wutar masifa dake babbaka jininsa ya shaqo sumayyah wadda takusa sumewa dan numfashinta iya wuyanta yake tsayawa baya kaiwa cikinta sbd ganin tashin masifarsa.

Mari daya yayi mata ta zube a qasa tana jan numfashi da qyar bakinta na jini dukkanin jikinta na kerma.

Take qafafunta yayi ya janyo Benazir da hannuwansa yana cewa,

“Tayaya zata gudu?
Ni zaku boyewa uwarku na hauka acikin gidana?
Duka guduwa kuke da niyar yi ku barni da asara batareda na fanshe kudina ba da asarata?
Wallahi akan ku biyun nan saina fansa daga kan sisi har Dubunnan dana kashe akanku da uwarku,
Kune zaku biya duk wata asarata ficika woh bazan yarda na rasa ba.

Shaqe Benazir sa bakinta itama yake jini yayi ya damqo sumayyah dake yashe qasa ya ringa jansu kaman ba mutane ba yakaisu dakin da uwarsu take ciki tana bacci ya hadasu su duka ukun yayi musu shegen dukan dayasa babu mai iya tashi zaune daidai acikinsu.
#MAMUH#
#KANTEES#
#BENAZIR
#LOVE
#ROMANCE
#DEEP
#SISTERS

ZAFAFA BIYAR🔥

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-FURAR DANKO
Billyn Abdul

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at
09033181070
09032345899

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button