Sponsored Links
Hausa NovelsHausa Novels and Love StoriesKyalKyalin Kauna Hausa Novel

KyalKyalin Kauna 15

Sponsored Links

EPISODE 1️⃣5️⃣

For your original Egypt Abayas,home decor, Gold (new and used), shoes that are qualitative and unique at affordable price , siyen daya ko sari (wholesale and retail) contact +201123302418

Instagram @Shopper_topia
WhatsApp group *Maryam’s Egypt abaya *

Ahankali idanunta ke rawa rawa kafin gently tabude idanun nata dasukai wani kalan jaaaa suna kadawa suna juyawa tanabin kitson kalaban datagani nakan Nanah na lilo da kallo kafin tawani kalan lumshe idanu sannan tasake budesu tadaurasu kan fuskan Nanah dake kallonta tana wani kalan kuka bakinta abude majina har saman kan hancinta tana zaune akan kujera hannunta adaure kafafunta adaure, sosai take kallon Nanah da jajayen idanun nata dake juyawa tana ganin yanda take kuka amman batajin sound ko guda daya kunnenta yadaina aiki, lumshe idanunta tasakeyi tareda wani irin sauke ijiyan zuciya kaman daga sama taji. “Anty Yasmeen, Anty Yasmeen” wani kalan nesa nesa takejin sunanta ana kira hakan yasa tasake bude idanuwan nata kadan tai stretching idanun kaman wacce keson taga abu by fire by force, Farida tagani da Nanah ke tsakaninsu itama idanunta sunyi jajir ga hawaye shame shame asaman fuskanta azaune tana kallon Yasmeen din tace “Anty Yasmeen dan Allah kitashi kada ki kara kulle idanunki, Anty Yasmeen kalleni nine Farida ne, ga Nanah nan, an sacemu an daukemu anyi kidnapping namu bamusan ina ne nan ba, maza daban daban dasuka rufe fuskokinsu sai shigowa nan suke, Nanah tayi fitsari ajikinta, kitashi and do something, Anty Yasmeen!!!” Farida takirata dawani kalan karfi dayasa jikinta yawani kalan rawa, tasake lumshe idanunta kafin ahankali tabudesu babu abinda takeji banda karan kukan Nanah, Nanah nawani kalan kuka kaman ana yankata, sai alokacin abinda suka shakamata yasoma sakinta, tundaga kan hannuwanta dake jikin kujera a daure dawani belt dake attached to kujeran tabida kallo zuwa kan hannun Nanah dake kusada ita zuwa na Farida da duk suke kallonta Farida na kuka itama sosai tana kallon Yasmeen din dataga har yanzu bata dawo daidai ba kawai juya idanuwanta dake layi take, tabi kafafuwansu suma dake kulle da belt na kujeran tundaga kan na Farida har zuwa nata kafin ahankali ta daga kanta dake layi tabi saman dakin da kallo tana kallon fankan dake juyawa asama karan kukan Nanah na ratsa mata kai, tana mamakin inda take haka kafin kaman daga sama komi yasoma dawo mata ta tuna tana cikin Keke hanyar makaranta suka kusan samin hatsari sai wani yazo zai bata handky yasa a hancinta daganan bata sake sanin abinda ke faruwa ba, kaman wacce aka ciro daga rijiya wani kalan ijiyan zuciya tasauke mai kara tareda yunkurowa ta zauna da kyau takalli Nanah dake kuka dasauri, Farida dake kallonta sai alokacin tafashe dawani kalan kuka lafiyayye tace “Anty Yasmeen kin farfado”? Dasauri Yasmeen data rude cikin muryanta da baya fita da kyau takalli Nanah tace “Nana, Nana kalleni nan” cikin kuka Nanah takalleta tace “Anty Yasmeen ki kwance mini hannu da kafafu mutafi gidan mu ina ne nan” cikeda damuwa sosai, Yasmeen takalli Farida da itama ke kuka girgiza mata idanu tayi tareda nuna mata Nana da baki alamun tadaina kuka sabida Nanah tai shiru hakan yasa Farida tai shiru, Yasmeen takalli Nanah tace “daina kuka to zan kwance ki kinji, stop crying, zamu tafi gida wajen Ammi nan bada jimawa ba Auta” gyadamata kai Nanah tayi ahankali, dasauri Yasmeen taduka tadaura bakinta kan hannunta tana kokarin kwance belt din da bakinta da duka karfinta ganin haka yasa itama Farida tafara haka, bude kofan dakin akayi aka wani bugo kofan hakan yasa dukansu suka dago kansu Nanah takara fashewa da kuka sabida yanda bude kofan ya firgitata, Wike ne yashigo dawasu maza guda biyu da duk sun rufe fuskansu da hulan fuska ga ledoji a hannunsu dakuma bindiga, kallo daya Farida tamusu takulle idanunta tareda fashewa da kuka tashiga sambatu, jikinta narawa sosai, tasan Baba nada bindiga dan dansanda ne amman bata taba ganin bindigan shi ba sai yau take ganin manya manyan bindigogi haka ana yawo dasu agabanta, itama Yasmeen kallo daya tamusu tawani kalan runtse idanu tunda aka haifeta bata tabajin tsoron dataji tanaji yanzu ba, sace su akayi yanzu to mesukayi? Su waye mutanen nan? Mesuke nema awajen su? Hannunta tadaura akan hannun Nanah takama gam gam tarike tana karanto duk wani addu’a data iya azuciyanta.
Binsu gabaki daya Wike da shi kadaine baisa face mask ba da kallo kwashewa da dariya sosai yayi ganin duk yanda suke a tsorace sunyi zuru zuru kaman sunga mala’ikan mutuwa, kafin yakalli Nanah dayaga tana kara sakin wani fitsarin ganinsu cikeda mugun hali yace “ke nan gidan ubanki ne dakike mini fitsari” “Ammmiiii!” Nanah tawani kalan kwala ihuuu dayasa Yasmeen tafashe da kuka tabude idanunta takalli Wike tace “dan Allah kayakuri bazata kara fitsarin ba I promise she’s really scared please” wani mugun kallo yama Yasmeen kawai yaja tsaki yakalli yaran yace “drop ledojin” karasowa cikin dakin sukayi suka ijiye ledojin, suka juya zasu tafi hakan yasa cikin wata kalan murya batare da Farida tabude idanunta ba tace “Anty Yasmeen inajin kashi” dasauri Nanah tace “Anty Yasmeen nima” wani kalan ijiyan zuciya Yasmeen tasauke, kirjinta na bugawa kaman guduma takalli Wike daya juya zai fita tace “z…..mu…..yi..” wani kalan kallo Wike yajuyo yamata yace “Oga bai bada izini akwance ku ba” yana maganan yabi bayan Boys dinshi shima yafita suka kara bugo kofan, cikin kuka sosai Nanah tace “Anty Yasmeen Baba, ki kiramini Baba yazo ya kwance mu, wayyooo Anty Yasmeen kashin zai fito yafara” wani kalan kuka Yasmeen taji yazo mata juyarda kanta gefe tayi hawaye suka gangaro mata takasa cewa uppan, kusan 5min da fitansu aka kara bude kofa Wike ne yashigo yace “you girls are lucky Oga yace na kwance ku da nine da wlh bazan budeku ba harsai Ubanku yasaki kayanmu da direbobin mu” yay maganan yana fara kwance kafafuwan Farida data kasa kallonshi yace “and idan any of u try nonsense saina harbe ku wlh” kwance musu hannuwa yayi sannan yamusu pointing wani daki yana komawa baya tareda tashe hanci yanama Nanah wani kalan kallon kyama jin tai kashi juyawa yayi yafita dasauri tareda rufo kofa, chak Yasmeen tadauki Nanah tareda kama hannun Farida tayi hanyar bayin dasu, bude kofan bayin tayi bayi ne Mai kyau babu wani datti aciki, kayan makarantan tashiga cirema Nanah itakuma Farida ta tsugunna awajen tafashe da kuka kawai bata taba ganin tashin hankali irin wannan ba, saida tacire mata kayan sannan ta wanke mata jiki tareda daurata kan masai takarashe kashin ta wanke kayan makarantan da ruwa dan bataga sabulu abayin ba ta shanya daidai nan Nanah data daina kuka tace “nagama Anty Yasmeen” wanke mata tayi tai flushing sannan takama hannun Nana takaraso inda Farida ke tsugunne tana kuka mara sauti ahankali takai hannunta tareda jawo Faridan wani kalan kankameta Farida tayi tana kuka itama Nanah saita fashe da kuka dukansu suka rungume Yayarsu Yasmeen, sotake itama tayi kuka kaman su but itace hope nasu, she have to be strong, Farida tace “Ya Yasmeen kidnapping namu akayi ko su waye”? Murya chan kasa Yasmeen tace “nima bansani ba” Ahankali Farida tace “kashemu zasuyi Anty Yasmeen”? Wani abu Yasmeen taji yadaki zuciyanta dasauri tadago fuskan Farida, wani kalan murmushi takakalo tamusu takai hannunta tashare fuskan Farida sannan tashare Nana, cikin charming voice nata tace “babu wanda ya isa yatabaku inada rai, bazaku mutu ba, I will do koma menene to protect my sisters, sannan karki kara irin magana haka agaban Nanah” gyadama Yasmeen kai tayi, ahankali Yasmeen tace “kinsa singlet”? Gyadamata kai Farida tayi dasauri Yasmeen tace “cire kibani nasaka M
ma Nanah saina bata hijabina” tashi Farida tayi ta kwabe rigan makarantan ta tabama Yasmeen ta karba tarike sannan tacire farin singlet na jikinta yarage saura bra kadai Yasmeen ta amsa sannan tabata school shirt din tasaka da small hijabin school din tai maza tasaka ma Nana shimin yamata yawa sosai but at least yarufe mata bombom dababu pant ajiki, hijabinta tacire tabama Farida tace “saka wannan kibani naki” saka na Yasmeen tayi, Yasmeen ta karbi na School din tasaka ma Nanah shima ya mata yawa amman yasauka, Farida tace “kefa”? Dan kwalin kanta ta zare tace “dawani abu yasameku gwara ni, farin rigan school naki is transparent gashi ba singlet gwara kisa hijabi ba,” warware dankwalin atampanta tayi ta lullube kanta zuwa kirjinta dashi dan anan ya tsaya takama hannun Nana tace “kiyi poop bari mufita” dawani kalan sauri Farida tarike hannunta tace “dan Allah karku fita ku barni am scared kijirani” Gyadamata kai kawai Yasmeen tayi sannan suka juyamata baya poop Farida tayi tagama tai flushing daidai an bubbuga musu kofan bayin wani kalan firgita dukansu ukun sukayi duk suka kankame Yasmeen, ahankali tamika hannunta dake rawa tabude kofan bayin Wike ne dawasu maza 2 dasuka rufe fuskansu cikin ihu yace “are you trying to escape”? Fashewa da kuka daga Farida har Nanah sukayi duk suka boye abayan Yasmeen, ahankali Yasmeen tace “a’a” dariya Wike yayi yana kallon yanda su Farida ke kuka sun tsure yace “kumayi nasan karnukan mu saisufi kowa murna kwana biyu basuci naman mutum ba dama, ku wuce” dawani kalan sauri Yasmeen tawuce tana kankame da Farida da Nanah dake bayanta zuwa kan yar katifan da Wike ke nuna musu zama sukayi dukansu suka cure gu guda kaman zasu shige jikin Yasmeen, binsu da kallo Wike yayi sannan yajuya zai fita dakewa Yasmeen tayi tace “dan Allah kusaki kannina niku kamani dan darajan Allah, Nanah bata da Lafiya measles take and she’s just a kid she’s only 4, Dan Allah, Dan Allah let them go hold me instead pl…..plz….” Takarashe maganan da kuka daya kufce mata kanta akasa, kwashewa dawani kalan mahaukacin dariya Wike da boys nashi yayi yace “da Babanki yasan yanada kananun yara irinku da baiyi abinda yayi ba, inda yasan waye Oga na, yasan halin Pablo Escobar da baiyi abinda yayi ba so kukanku duk abanza ne pretty girls” yasake fashewa da dariya ya kawo ledan dasukazo dashi ya jefar gabansu sannan suka wuce suka fita, bin ledojin tayi da kallo kafin ahankali tasa hannu tajawo tabude slice bread ne da fanta kananu guda uku, dago Farida tayi daga jikinta tace “zokuci abinci” tai maganan tana ciro Nanah itama, ledan bread din tabude taciro slice guda bibbiyu tabasu sannan tabude fanta tabasu dasauri suka shiga ci barinma Nana, Farida itama yunwa takeji dan bataci abincin safe ba, yanda sukecin abincin dasauri taji wani kuka yazo mata ta juyarda kanta gefe, shanye fantan ta Nanah tayi tace “Anty Yasmeen akaramini” daukan dayarage Yasmeen tayi nata tabude tabata suka cigaba daci, saida slice bread din yarage saura 2 Farida ta tsaya daci takalli fuskan Yasmeen dake kallonsu idanunta yay jajir tace “bakici ba ke” dan murmushi ta kakalo tace “banajin yunwa ni kuci” kaman jira Nanah take karasa daukan sauran biyun tayi dan dama ita kuran buredi ce tashigaci duk sai sukahau kallonta tass tacinye sannan takalli Yasmeen tace “nakoshi Anty Yasmeen mutafi gidan mu wajen Ammi na” dan murmushi Yasmeen tamata tace “anjima kadan zamu tafi ko Farida” dasauri Farida ta Gyadamata kai tace “eh” cikeda son mantar da Nanah tace “kinsan takalmin da Baba yasayo mini yafi naki kyau” zaro idanu Nanah tayi tace “wai haka Ya Farida? Ai Ammi tace nawa duk yafi naku kyau dan kuji, kuma tamiki kayan salla kala saba’i” zaro idanu Farida tayi tace “zuki ta mallo” ahaka suka dinga mata hira kasa kasa duk da zuciyansu na cike da tsoro har wajajen 9 nadare bacci yay awon gaba da Nanah ajikin Yasmeen itama Farida bata jimaba bacci yay awon gaba da ita ta kankame hannun Yasmeen gam kaman zaa saceta.

Binsu da kallo Yasmeen tayi sai alokacin wani kalan barawon bacci ya saceta.

✨KK✨

✍🏻M SHAKUR

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button