Sponsored Links
Dabi'ar Zuciya Hausa NovelHausa Novels

Dabi’ar Zuciya 22

Sponsored Links

22

 

Wucewarsu bai sanya taron jama’ar da suka taru a wajen barin wajen ba,ciki kuwa harda wasila da labarin dukan yakai mata,ta kuma garzaya don ta ganewa idanuwanta,kowa gulma tana cinsa,yana son yaji ainihin abinda ya faru don su samu abun qadarwa,sai qananun maganganu sa qus qus ke tashi a tsakaninsu,gashi munzali ya wuce fuuu cikin fushi bare su nemi jin qarin bayani daga bakinsa.

Dai dai qofar shiga da fita daga gidan suka samu ummanmu a tsaye,ga duk mai hankali duba daya zai mata ya karanci tashin hankali saman fuskarta idanuwa harma da zuciyarta,macace mai tsananin biyayya wa aurenta,bata nemi izini ba,wannan ne babban dalilinta daya sanya ta kasa fita ceton diyarta,duk da yadda takejin gunjin kukanta cikin matuqar neman taimako,inna laure da zata mata kara kuwa birki taci ta koma ta zauna tana ‘yan maganganu ciki ciki,wanda ta tabbatar idan ta saurara da kyau,bana kome bane saina jin dadin irin jibgar da munzali yakewa kaltum din,ko a yanzun ma shewa take qasa qasa me cike da nishadi,saidai lauren ba itace a gaban ummanmu ba,hannun diyarta ta kamo ta taimaka mata zuwa cikin sashensu.

A hankali ta zaunar da ita,saita wuce kawa kanta tsaye zuwa rumfar da suka maida madafi tahau qoqarin kunna wuta,wannan yasa bilalu yabar abinda yake yazo ya karbi umman tasu,ya fara hada wutar da kanshi,qwalla na cika masa idanu,yau zaiwa yaya abinda itace kusan ba’a rufa sati sai tayi masa,bazai yafewa ya munzalin abinda ya yiwa yayar tasa ba,saboda baiga girman laifin data aikata wanda ya cancanci ayi mata wannan hukuncin ba,koda sata tayi bare ma ba ita tayi ba.

Umman bata iya dawowa ta zauna ba,sai taci gaba da tsaiwa a bayan bilal,ta rungume hannayenta a qirji,duk sanda tayi irin wannan tsaiwar ba shakka ranta a bace yake,koda ba zata furta kota nuna ba,har ruwa ya tafasa tana tsayen,ta juye a babban baho ta surka shi da zafinsa,tasa bilal ya kaimata gaban kaltum da har yanzu kuke take,jikinta ko ina yana mata ciwo,bilal tasa ya fita ya basu guri,sannan ta sanya kaltum din ta fitar da kayan jikinta tayi daurin qirji.

Sai data gasa mata duk inda tasan zai zame mata miki ko yayi mata zafi,kuka kam ta yishi matuqa kafin a gama gashin,sannan tasa tayi wanka da sauran.

Kafin tafito bilalu ya siyo mata man zafi kaman yadda yaga tana mulka masa,ummansu ta ajjiye mata abinci,tasa ta shafe dukka jikinta dashi sannan ta zauna ta sanyata a gaba taci abincin.

Duk wannan abun da ake batace da ita komai ba sai data gama cin abincin,muryarta cike da wani nauyi dake nuna ya taso ne tun daga qasan zuciyarta take tambayarta

“Me kika yiwa munxali,kaltume ban haneki shiga sabgarsa shida matarsa ba tun randa yaxo nemanki afujajan?”

Kuka ne ya qwacewa kaltum din,cikin muryar kuka ta amsa mata

“Wallahi ummanmu tun ranar ban qara ba,ban qara bi kota hanyar gidansa ba”

Kwashe yadda abun ya faru tayi ta gaya mata,shuru umman tayi,ranta yana suya,tanajin kamar haqurinta yana gab da gazawa,da wanne zataji?,duka tako ina wanne zata kare?,wanne hannuwanta zasu iya dauka,ida amadu yayi masu mijinta ne,mahaifinsu ne,idan inna tayi musu mahaifiyarta ce….jikokinta ne,to amma munzali fa?,saboda kawai yana a matsayin yayansu saiya kamata cikin bainar jama’a saboda tozarci da wulaqanci yayi mata irin wannan dukan?,kamar wanda ya kamata tana zina ko sata?.

Lokaci mai tsaho tana tausar kanta kafin ta samu zuciyarta ta fara sanyi,saidai bata gama direwa ba sababi masifa da tashin hankalin babansu ya biyo baya.

Ko sallama bai samu zarafin yi musu ba sai qwala kiran sunan kaltume!….kaltume!!!!..

Tana daga zaune ta amsa masa don ba zata iya miqewa cikin hanzari ba,kafin wasu sakanni ya bayyana cikin gidan

“Ni na banu na lalace,wannan wacce irin diyar jaraba Allah ya jarabceni da ita?,don ubanki munzali sa’an wasanki ne?,ba sbine madadina ba randa bani?,kin dauki baqar hudubar uwarki kin fara muna musu ‘yan ubanci ko?,wallahi wallahi kaltume ki fita daga idanuna,kiyi qoqarin da hannuna bazai kai jikinki ba,kinsan Allah?,duk sanda kika bari hannuna yakai jikinki saina qarar miki da numfashi”.

Sosai furucin ya sauka zuciyar ummanmu,a wannan karon ta gaza shuru

“Malam….ka daina fadar haka,idan ka fada da bakin mala’iku fa?”

“Da zan fada da bakin nasu ai da nafi kowa murna,me za’ayi da yarinya irinta?,to na soma gajiya,kuma wallahi aka kaini bango ran kowa saiya baci a gidan nan,kowa bazaiji da dadi ba,kin taramin jama’a qofar gida saboda dai ni a tozartani?,kamar ni kadai ne me ‘ya’ya a duk garin nan?,to idan xaku shiga hankalinku ku shiga,in ba haka ba zanbi takan kowa a cikinku,ai ba gagarata kukayi ba” daga haka yayi gaba kamar zaiyi ball da qafar umma dake miqe.

Shuru ne ya ratsa wajen na wasu sakanni ‘yan kadan,kafin kaltum takasa jure abinda take ji ta saki kuka me sauti,sai umman ta kasa hanata,ta miqe tayi daki,tabar bilalu da rarrashi.

********Washegari wani abun mamaki sai ‘yan dubiya suka dinga shigowa gida nasu,wannan na fita wannan na shiga,kowa ya shigo abinda zaice shine

“Allah ya kiyaye gaba,ya sawwaqe”.

Da amin umma ke amsawa,tun tana irga wadanda suka shigo har ta daina,saidai tana jiyo inna laure daga can babbar farfajiyar gidan tana ‘yan waqe waqenta cikin madaukakin sauti,da alama ma abun shinfida ta zauna kamar me karbar gaisuwa,duk kuma wanda ya fita daga wajen ummanmu sai yaja birki wajen inna laure,mafi qaranci mutum ya kwashe minti talatin kafin suji fitarsa yana yiwa inna laure sallama,ranar haka suka wuni har dare,abun ya yita basu mamaki,saida cikinsu babu wanda yayi maganar da dan uwansa.

*********A wata washegarin misalin qarfe shida na safe tana kwance kan shimfidarta tana jiyo motsin umma a tsakar gidan nasu,duk kuwa da yadda iska ke kadawa.

Lokaci lokaci takanyi juyi a hankali saboda yadda har a sannan wasu sassa na jikinta ke ciwo,musamman qugunta daya bugu,a duniya ya washi ta tashi cikin lalurar da zata hanata taimakawa ummanta,kota kama mata wasu ayyuka,a rayuwarta tana bala’in tausayin uammansu,tunda ta taso ta sameta ne cikin haquri da rayuwa,haquri da halin duniya,haquri da mutanen da take mu’amala dasu,mutanen da take jin dadinsu dai dai kune,wata irin bahaguwar rayuwa mara dadi,wadda babu wata walwala ko nishadi a cikinta ko kadan.

Sama sama take jiyo sallama daga tsakar gidan nasu,tana jin ummansu dake duqe can bakin magangara tana wanke kwanukan abinci tana amsa gaisuwar da akeyi mata,saidai kaltum din bata dauki muryar ko wacece ba,sai taja tsaki,ta gayara kwanciyarta,tana fatan ba ‘yan dubiya bane.

Ita ko daya dubiyar da aka dinga zuwa din nafa burgeta ba,saboda magi akasarin mutanen da suka shigo din babu wani abu dake hadasu da ita,wasu ko gaisuwa bata shiga tsakaninsu,wasunsu ma bata gama wayewa da fuskarsu ba,saboda tun asali ita din bame shige shige bace,koda yaushe tana maqale jikin ummanta,tana da ƙawa zuci da kuma ƙulafucin uwa,kuma kusan duka haka yaran umman tasu take,saboda itadin macace mai tausasawa ga yaranta,ta iya bi da damuwar kowannensu.

Tsaiwa taji anyi daga bakin qofar dakin ana cire takalmi kafin daha bisani ayi sallama a shigo ciki,sai a sannan ta daga kanta tana duban me shigowar,lantana ce,mamaki yadan kama kaltum,saboda lantanar bata tana shigowa gidansu a irin wannan lokaci ba,dole ta miqe daga lullubar da tayi da wani tsohon xaninta data maida abun rufa tana amsa sallamar lantana.

Gefan kaltum din ta qaraso,tana zama tana furta kalmar
“Sannu kattume” dan murmusawa tayi cikin qarfin hali,saboda sam batajin murmushin a zuciyarta

“Yauwa lantana”

“Yaya jikin naki?” Lantana ta tambayeta

“Alhamdulillahi,da sauqi”

“To Allah ya rufa asiri”

“Amin lantana,na gode” kaltum ta amsa mata.

Shuru ne ya biyo baya,cikinsu babu wanda yace wani abu,daga bisani lantanar ta sauke ajiyar zuciya

“Waime ya hadaki da munzali yayi miki irin wannan dukan kaltume?” Lantana ta fada fuskarta qunshe da alhini da damuwa.

Ajiyar zuciya kaltum ta saki,tana jin zafin irin yadda ya munzalin yayi mata bainar jama’a,inda cikin gidansu ne gaban mahaifiyarta ya daketa irin hakan da da sauqi,bata boyewa lantana komai ba ta labarta mata,sai taga lantanar tayi qasa da kai bayan ya dafe kuncinta da hannu daya.

Zuciyar kaltum cike da tamabaya take dubanta,bakinta ya gaza shuru

“Lafiya lantana?” A hankali ta dago ta dubi kaltum

“Don Allah wai me kika yiwa wasila ne a rayuwa me zafi haka data zabi ta saka miki ta wannan hanyar?” Kasa gane kan maganar tayi,saita zabi taci gaba da kallon lantana ko zatayi mata bayani,ganin hakan ya sanya ta gyara zamanta,ta dora dukka idanunta da hakalinta kan kaltum

“A iya sanina a abinda ya faru….na riga wasila zuwa wajen ma,saidai babu yadda zanyi na qwaceki daga hannun munzali,saboda idanunsa sun rufe,kuma wadanda suka fini shekaru ma sunyi sunyi ya bari yaqi…..amma kuma bayan komai ya lafa muna shirin barin wajen……kawai sai wasila ta fara wasu maganganu da suka jawo hankalin mutane kanta,wai ai dama ta gaya miki,ki daina duka abubuwan da kike,saboda ta sani cewa idan wasu sunyi sunci riba,ke din duka zakici hannun ‘yan gidanku,yanzu wa gari ya waya?’ “kowa dai bai gane abinda take magana a kansa ba,don haka wasu suka takura da tambayarta meke faruwa?,ta fara cewa ita ba za’aji mutuwar sarki a bakinta ba,wasu suka tafi,wasu suka matsantsa saboda sunsan baki da makusanciyar qawa irinta,budar bakin wasila……” Sai kalaman lantana suka tsaya a wajen,tana jin nauyin qarasa gayawa kaltumen abinda ya faru,tana jin nauyi,don ita kanta ba qaramin razana tayi ba dajin labarin da wasilar ta qirqiro cikin qaramin lokaci ba,don har ga Alla sam bata yarda ba,hankalinta bai dauka cewa hakan zata faru ba

“Me tace lantana?” Kaltum ta tambayeta a sanyaye,haka nan tun kafin taji komai taji gabanta yana faduwa.

Daga ido lantana tayi ta dubi kaltum
“Kiyi haquri,ya zama dole ne na gaya miki,tun jiya naso zuwa,amma naga gidan nan ya cika da ‘yan gulma,masu zuwa dubiyar qarya……wai cewa tayi cikin shege kikayi,labari yakai kunnen ya munzali,ita kika fara gayawa tace ba ruwanta….babban abun baqincikin shine,duk wanda yazo dubiyar ya biya ta wajen inna laure don tabbatar da gaskiyar lamarin saita bashi tabbaci,ta kuma dora da nata bayanin qanzon kuregen”.

Wani irin abu taji yana yamutsawa saman kanta,wani sanyi ya saukar mata tun daga saman kanta har qafafunta,tana daga zaune amma ji take kamar ana dawafi da ita,saita lumshe idanuwanta tana kiran ya Allahu,ya Allahu,tausayinta ya kama lantana,cikin salo na rarrashi tace

“Kada ki damu katume da abinda kikasan baki aikata ba,baki isa ki iyawa mutum ko ki burgeshi ba” sannu a hankali ta bude idanuwanta tana duban lantana

“Tabbas haka yake,na gode lantana da qaunar da kike min saboda Allah,su kuma…..amma babu komai,akwai Allah…..ya ubangiji kana kallo…..Allah kaine shaida” daga haka bata sake cewa komai ba.

Cikin hikima lantana take bata baki har na wasu lokuta kafin tayi mata sallama,bayan ta bata shawarar duk wanda yazo dubiya kada ta sake fita,su qaraci gulmarsu su koma.

Ita kadai cikin dakin,tana jinta kamar wadda aka haqa rami aka zurata iya wuya,labarin da lantana tazo mata dashi ke yawo a kanta,sai data fada din sannan ta tuna irin yadda duk wanda ya shigo yake mata wani kallo da bata fahimci dalilin yinsa ba sai yanzu,qwalla ce ta silalo mata duk da yadda take qoqarin riqeta,ta kuma sanya hannunta da sauri tana ta qoqarin shareta sanda taji ummansu na shigowa dakin tana tambayarta bata tashi bane?

“Na tashi ummanmu” dai dai sanda ya daga labulen,dan tsaiwa tayi na sakanni tana kallonta,sai kuma tace

“Ki tashi ki saka ruwan zafi a jikinki,kizo ki sanyawa cikinki wani abun”

“To ummanmu” ta amsa tana qas da kanta tare da yunqurin miqewa.

Rana batayi nisa ba ‘yan dubiya suka fara shigowa,a hankali cikin hikima da nutsuwa take karantar duk matar data shigo,saita fara tabbatara da zancan lantana,duk da cewa tayi yunqurin yin zamanta cikin daki taqi fitowa koda anzo,sai kuma wata zuciyar ta gaya mata,yin hakan tamkar tana tabbatar da zargin dake cikin zukatan mutanen,don idan wani ya fahimta…..wani cewa zaiyi da gaske cikin shegen tayi take buya bata son a ganta.

Yadda jama’a ke kallonta yayi bala’in kadata,bata taba tsammanin akwai wani qunci a duniya sama da wanda suka ciki ba sai a wannan karon,dama aminta da qawance yana juyewa ya zama sharri mai girma da nauyi haka?,dama qauna da soyayya tana jirkita ta koma mummunar sakayya irin wannan?,babu wata daqiqa da zata kubce mata ba tare da abun yana mata yawo cikin qwaqwalwarta ba,wai wasilanta?,wasilan da suke kuka tare suyi dariya tare,wasilan da take gayawa sirrinta,wasilan da suke shawara tare,su kashe su kuma bunne tare,to wai shin meta aikata mata data cancanci sakayya mafi muni irin wanna?,tambayar data dinga yiwa kanta da kanta kenan,saidai ta gaza gano amsar tambayar tata.

Sati gida cur tayi tana jinyar jikinta kafin ta warware,a tsahon satin bata ga koda gilmawar mai kama da wasila cikin gidan ba bare ita,sai tarin qawayenta da kullum ke kaw mata zancan abinda wasila keta yamadidi dashi.

Dakatar dasu tayi,ta kuma shaida musu batason ji,saboda jin bashi da wani amfani,hakanan babu wani magani da zaiyi mata,face baqin wasila da zata dinga gani.

Randa ta cika satin misalin sha daya na rana,tana tsakar gida tana tsince musu busashshen zogale da suke shirin yin miyar zogale ayau din,cikin shinkafar da yakumbo indo ta ajjiyr musu,har zuwa yau kuma suke amfanarta.

Alamun sauti kamar na kuka datake jiyowa kamar daga nesa kadan da inda take yasa tayi sak,ta kuma dakata da abinda takeyi,tana jiran taji daga ina kukan ke tahowa.

A hankali taji alamun sashensu yake yowa,kuma kamar muryar habibanta,abunda yasa babu shiri ta dangware farantin dake kan cinyarta ta miqe tsaye,gabanta da wani irin mugun faduwa,ta zubawa qofar shigowa sashen nasu idanu,tana jira tagani shin ita dince?,idan itace da wacce tazo?,me kuma ya faru,bugun zuciyarta na daduwa har batasan ummansu ta fito tana tsaye daga bayanta ba itama tana jiran shigowar habiba,dukkaninsu kowa ya kasa motsawa daga inda yake tsaye bare yaje ya tarota.

 

 

D/Z
23

*_Littafin kudi ne,ki guji shiga haqqin wasu ta hanyar yadawa,ki tuntubi wadan nan numbers din don biyan naki ki karanta cikin aminci_*

08184017082
Ko kuma
09134848107

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button