Sponsored Links
Arubuce Ta Ke Hausa NovelHausa Novels

Arubuce Ta Ke 80

Sponsored Links

Page 80

Tsaye yake gaban mirror yana taje kansa,shirye yake cikin mulberry silk da ya kwanta sosai a jikinsa,ya kuma fidda kyan fatarsa data wadata da tsafta da kuma hutu,jikinsa na fidda sassanyan qamshin turarensa.

A nutse take takowa zuwa qofar dakin nasa,tura qofar a hankali saita tsaya tana kallonsa ta cikin madubin ba tare data saki hannun qofar ba,hakanan bata koma ba bata kuma shigo dakin ba.

Idanu ta zuba masa sosai tana kallonsa,yayi bala’in yi mata wani sassanyan kyau,a yau din quruciya kyansa da haduwarsa sun sake fito mata muraran fiye da ko yaushe, shigar ta karbeshi,duk da dama zaiyi wuya ya saka kaya a jikinsa basu karbeshin ba,ta’ammali da uniform saboda yanayin aikinsa ya sanya yafi mu’amala da manyan kaya akan qanana,saita saki qofar a hankali ta goye hannunta a qirji taci gaba da kallonsa.

A nutse ya sauke idanunsa a kanta,shi dinma shigarta ta yau ta fusgi hankalinsa sosai,abaya ce a jikinta ruby color,saita dora dan qaramin Vail a kayanta dusty rose,dan siririn pink lips dinta na fidda qyallin lipstick data shafa musu, fuskar ta ta kwanta da color din powder din data shafa

“Ma sha Allah” ya fada ta hanyar motsa labbansa,ya ajjiye comb din hannunsa a hankali,yana so yau ne ya kamata real tana satar kallonsa,abinda ya lura fa koya kenan cikin satin nan,idan kuma ya fada saita waske harda qananun hawayen ita ba kallonsa take ba.

Batayi zato ba taga ya waiwayo gaba dayansa,idanunsu suka sarqe cikin na juna,kunya ta kamata,tayi taku biyu baya zata koma ya dakatar da ita

“Don’t move baby” yayi maganar muryarsa nadan sarqewa,ganin da yayi mata a yanzu da idanu sai yake ganin kamar madubin ashe ya rage kyan da tayi,turarenta da ko yaushe yake tsaye masa a rai ya iska na kadoshi kadan kadan yana cakuda da nasa yana bayar da wani kalar qamshi na musamman,sai ya cira qafarsa ya soma takawa a hankali zuwa inda take, qafafunsa na nutsewa cikin lallausan carfet din daya malale dakin dashi,bazai iya kauda kai ba a yanzun,yana qishirwa wadan nan labban nata,yanason yaji duminta sosai…….wanda rabonsa da hakan tun randa ya maidata tasa halak malak,duk kuwa da cewa gado daya suke kwana,amma bai sake neman komai daga gareta ba, saboda yana son fidda duk wani sauran tsoro nasa dake ranta.

Qugunta ya kamo da dukka hannayensa biyu ya matso da ita jikinsa sosai har jikin nasa yana gogar nata,gabanta ya fadi sosai ta lumshe ido tana son hadiye tsoronta

“Bude idon na gani….. please my baby” ji tayi ba zata iya tsallake umarninsa ba,sautin muryarsa gaba daya ta kashe mata jiki,ta bude manyan idanuntan fes a kansa,sai yaja numfashi da kyau,yasa yatsunsa biyu ya kama kumatunta yadan ja kadan

“Inason wadan nan idanun,inajin kamar na hadiyesu” ido ta fidda fuskarta na washewa

“Ana cinye idon mutum uncle?” Ta fada a sakarce,sai ya saki murmushi kawai yana tunanin yaushe widad din tashi zata gama girma ne,ya girgiza kansa a hankali,yana jin komai na jikinsa yana amsawa

“Ba’a cinye ido,amma ana iya lasheshi,ana lashe kunne,ana lashe baki ana lashe harsh……..”

“Stop uncle,wallahi kunya nakeji” ta fada a narke kamar zata sanya kuka,yadda fuskarta tayi ta sake tafiya da imaninsa,mitsitsin bakinta data turo gaba ya kalla,zuwa yanzun gaba daya burinsa ya tattara a kai,a tausashe yace

“Bari na nuna miki ki gani” bai qara ko second biyu ba ya hade bakinsu waje daya,cikin wani irin lallausan salo da kuma qwarewa yake aike ma qwaqwalwarta saqo ta hanyar bata zazzafan french kiss daya birkita tunaninta gaba daya,ya kuma zare mata kowanne kuzari da qarfin hali da take jin tana dashi.

Ba inda bai aika da harshensa cikin bakinta ba,ya lasheshi tsaf ciki da waje sannan ya saketa yana jan numfashi.

Taga taga tayi zata fadi saboda yadda jikinta yayi laushi gaba daya,yayi hanzari da sauran nasa kuzarin ya tarota yana kallon qwayar idanunta,sai ya jinginata da jikinsa,hakan kuwa ya mata,don boye fuskarta tayi a qirjinsa,wata kunya tana dawainiya da ita.

Qaramar dariya mai hade da ajiyar zuciya ya sake

“Good baby…..da alama kin fara daukan haske ko?” Ya fada yana leqa fuskarta,saita kebe masa baki ta soma ‘yar sheshsheqar kuka,har cikin jininsa ta aike masa da wani saqo daya huda zuciyarsa,sai ya dinga jij sheshsheqar tata kamar da manufa,yadan janye jikinsa kadan don bayason abun yaci gaba da tafiya,amma saita riqe hannunsa tana sake neman wajen buya a jikinsa,don gaba daya ya gama aza mata nauyinsa,amma ta lura shi ko a jikinsa,abinda yayi mata a yanzun tana jin kamar ba zata iya sake kallonsa ba har abada

“Ohhh…..kina buqatar qari kenan?” Kai ta girgiza da sauri,saita sakeshi taja da baya tan lalubar qofa ta fice da sauri.

Da kallo ya bita kamar wani sakarai harta fita din,ya koma da baya ya zube gefan gado,wannan din wani dadadden mafarkinsa ne da a yau ya cika,he loves kisses sosai,yana bala’in so body contact da iyalinsa qwarai,amma hakan bata samuwa sam sam a gareshi,saidai yayita fama da hakan a tarin mafarkansa,yayi loosing abubuwa masu yawa da yasha tsarawa kansa a tsarin rayuwar gidansa,saidai da daya da daya komai yake rugujewa ya rushe,tsarinsa da ra’ayinsa yayi nisa qwarai dana hafsat,wasu abubuwan ma tana kallonsu as bata lokaci,ko kaiwa maqura,yana jin kamar a yanzun zai gina dukka mafarkansa ya kuma rayasu in reality.

Gaba daya ta saka jikinsa yayi laushi,bayajin zai iya driving dinsu daga kaduna zuwa bauchin,bashi da wannan qarfin kwata kwata,don haka ya ciro wayarsa ya kira samuel yace yazo zasu wuce bauchi yanzu yanzu.

Minti goma kacal samuel ya kirashi kan ya iso,already motar dama a wanke take,hakanan dukka kayansu suna ciki,sai ya miqe yana gyara rigarsa,ya dauki agogo da hularsa duka ya sanya,ya sake fesa turarensa,sannan ya kwashi wasu documents dake cikin wata folder ya fito.

A gaban fridge ya sameta tsaye tana shan ruwa,ya taka a hankali ya tsaya a bayan nata yana dora hannunsa saman nata hannun da ta riqe ruwan dashi tana sha,hannun ya qawatu sosai cikin wasu siraram banguls kusan guda goma ruby color da duka haska farar fatarta datayi wani fresh.

Qwarewa tayi, saboda gaba daya bata ji takunsa ba,ya sanyata a kafadarsa yana dan dukan bayanta harta daina tarin sannan ya janye jikinsa kadan

“Ki dauko komai?,samuel yazo xamu wuce” kai ta jinjina masa alamar eh,sai ya miqa mata document din hannunsa,ya ja mayafin dake kanta ya soma nada mata shi.

Baya ya danja ya kalleta,she looks very gorgeous,sai yaji kishinta yayi bala’in kamashi,har yaji kamar dama bai kira samuel ba.

Hannunta ya kama ya isa da ita gaban wani dan fashion mirror dake maqale cikin falon, murmushi ya subuce mata,ya akayi ya iya rolling haka?,ta cikin idanunta ya karanci tambayar dake cikin zuciyarta,sai ya saki murmushi

“Mimi da nawwara” a taqaice ya amsa mata amma ta gane,saita kauce gefe daya saboda kallon da yake jifanta dashi ta madubin yana mata nauyi da yawa.

Kafin su fita ya kira samuel ya masa aiken dole,wai fita dan kantin dake kusa da gidan ya karbo kasa biro,kafin ya dawo suna cikin motar,yana isowa yace ya aje masa wajensa zai karba,don kada ma.ya juyo har ya ganta,ya amsa masa a ladabce ya kunna motar suka fice daga gidan.

Tun basuyi nisa ba bacci ya soma fusgarta,sai yayi mata majingina da kafadarsa sosai,ya lalubo hannunsa ya sanya a tafin hannunsa ya hadesu waje daya.

Kusan awa biyu ta kwashe tana bacci,sanda ta farka saita janye jikinta daga nasa cikin jin nauyi,ya murmusa kadan yana dubanta

“Kin more min kafada,sai naci tararki” kafada ta noqe tana dariya cikin jin kunya.

Awa biyu da rabin suka shiga garin bauchi,sai tadan dubeshi har yanzu hannunsa yana cikin nata

“Gidan hajiya zaka saukeni” ta fada qasa qasa,don sam sai taji bata qaunar zuwa gidan.

Waiwayowa yayi ya zube mata manyan fararen idanunsa yana kallonta qasa qasa,cikin zuciyarsa yake son qiyasta yadda hakan zata faru,sai kuma ya girgiza kansa a hankali kafin ya dauke idamunsa a kanta

“Ba yau ba” ya fadi kansa tsaye,don baya jin zai iys nesa da ita

“Don Allah uncle” ta fada a mugun shagwabe kamar zata saki kuka

“No,Baby” komawa tayi ta lafe jikinta a sanyaye tayi shuru,tafison gidan hajiyan,tafi qaunar zama a can,saita fara sharar hawaye kafin ta sake masa siririn kukanta.

Idonsa ya lumshe yana jin wani abu mara dadi yana taba zuciyarsa,irin abinda bai tana jin kamarsa ba,duk da dama shi din kusan weak point dinsa kenan

“Is okay” ya fada yana sanya hannunsa cikin nata,sannan ya bawa samuel umarnin canza titi zuwa titin da zai kaisu unguwar gida dubu.

Ajiyar zuciya ta sauke,ta sake lafewa tana dan sakin murmushi

“Na gode” waiwaya yayi a hankali ya kalleta,sai ya sanya hannu yaja hancinta

“Karkiyi saurin godemin,don idan munje ba lallai bane na barki ki kwana ba” baki ta tura gaba,sai ta kwantar da kanta ba tare da tace masa komai ba,ya sake sakin qaramin murmushi yana kallon hanya hadi da matse hannunta sosai kuma a tausashe cikin tafin hannunsa,can qasan zuciyarsa yana jin wani abu mai qarfi a kanta yana sake ginuwa.

Ita ta fara shigewa gidan hajiyan cike da karsashi, zuciyarta fal farinciki,don kusan wata guda kenan bata zo ba,zuwanta na qarshe har suka koma batazo gidan ba.

Su biyu ne falon,ita da gwaggwo fanteka suna taba hira,sun gama cin abinci kenan tayi sallama,sosai farincikin dake fuskar hajiyan ya bayyana,ta amsa sallamar tana cewa

“A’ah,mutan kaduna…..irin wannan ba zata haka?”

“Aiko dai,haka amaryar abas din ta fara canzawa,ah lallai yarinya taji kiwo” gwaggwo fanteka data kama haba cike da jin wani abu a ranta me kama da qyashi qyashi ta fada,maganar da ta yiwa widad din nauyi,karon farko da kunyar hajiya ta kamata,musamman da ta tuna abinda ya wanzu tsakaninta da abbas din,sai take ganin kamar ma kowa yana iya karantar hakan,don haka tun daga dan nesa dasu ta zube tana gaidasu.

Cikin kulawa hajiyan ta amsa, gwaggwo fanteka kuwa ta zuba mata ido tana kallonta,sosai widad din ta canza,ta fara cika ta kuma yi kyau abinta,ta amsa tata gaisuwar tana sauke numfashi hadi da gyara zamanta

“Kundai tafi kunbar uwar gida da jiran gida ko?” Ta jeho widad da batasan ma kan asalin abinda kae faruwa ba tambaya

“Uhmmm,ina ruwan widad,ita da batasan komai ba akai” hajiya tayi saurin karbar zancan

“To ai shikenan,Allah ya kyauta” ta sake fada tana gyara zamanta,dai dai sanda abbas yayi sallama ya shigo parlor din,qaninsa muneer yana biye dashi da babban ledar da muddin da ransa da lafiyarsa baya gaza shigowa da hajiyan tashi ita.

Washe baki gwaggwo fanteka tahau yi tana sake gyara zama,lallai yau din ta shigo a sa’a,tasan cewa shar da ita zata fita,harda ita wajen marabtar abbas din,ya duqa ya gaidasu cikin girmamawa sannan ya koma ya zauna sosai daura da hajiyan tasa.

Miqewa gwaggwo fanteka tayi tana cewa

“Ni bari na wuce gida,naga la’asariya ta kusa”

“Ki tsaya mana ki karbi tsarabar taki?”

“A’ah haba,kya dai aiko muneera ko muniru ya kawomin,yallabai Allah ya huta gajiya” hannu abbas ya sanya a aljihunsa ya fidda sabbin ‘yan dubu dubu ya miqa mata,tasa hannu kuwa ta amshe babu tayi tana zuba godiya.

Nan falon hajiyan yayi zamansa suna hirar yaushe gamo,duk danda widad dake kitchen tare da muneera ta gifta sai taji ranta ya mata sanyi,ta kuma sake godewa Allah,kallo daya ta yiwa abbas din harma da widad din ta karanci akwai wani gagarumin sabon canji cikin rayuwarsu,walwalar abbas din ta qaru,idan ma ba idonta bane ke mata gizo har ‘yar qiba taga yadan qara,abinda bata taba gani a tare dashi ba,sannan duk sanda widad din zata gifta idanuwansa suna biye da ita,kamar yadda itama duk sanda ta ratso ta falon saita saci kallonsa.

Ana idar da sallar la’asar yayi shirin wucewa gida,yace ta fito su wuce,amma saita sakar masa darunta tana maqale wuya,idan zata shekara tana masa wannan shagwabar yanason gani,ba kuma zai gaji ba,tilas ya haqura ya barta bayan hajiya ta sanya baki,ya wuce gidan shi kadai,amma cikin jikinta da zuciyarsa duka sai yakejin wani iri babu dadi,kamar ya baro wani b’ari ne na zuciyarsa a wani waje.
[3/18, 3:06 PM] +234 903 685 1413: *H U G U M A*

*_A RUBUCE TAKE_*
(K’addarata)
*Arewabooks:Huguma*

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button