Sponsored Links
Arubuce Ta Ke Hausa NovelHausa Novels

Arubuce Ta Ke 59

Sponsored Links

Page 59

Ranar gaba daya wunin falo tayi,tayi kwance cikin kujera ta kasa hasala komai,,haka kawai take jinta wani sukuku,jikinta duka babu dadi,sai bayan sallar la’asar tana kwance kiran anty deena ya shigo

“Lafiya kike?” Ta tambayeta jin muryarta tayi qasa da yawa,sai ta kama mata hawaye kafin daga qarshe ta gaya mata ya tafi bauchi ya barta ne,abun ya baiwa anty deena dariya,wohoho…… widad har yanzu quruciyar dai tana nan,sai data bata baki sannan tayi mata zancan da yasa ta kirata

“Akwai watsapp groups da za’a saki,inason kowanne idan an sakaki ki tsaya kibi duk hirarrakinsu kinji ko?,akwai qaruwa sosai qanwata”

“To anty” ta fada tana gyada kai,sun jima da anty deena din suna hira,sai data debe mata kewa sosai sannan sukayi sallama.

Washegari haka ta tashi jikinta babu qwari har ta gama shirin makaranta,bayan kowanne minti daya saita kallin dukka wajen da yafi zama ko tsaiwa,sai taji hawaye sun cika mata idanu,tasa hannu ta share da sauri,sannan ta dauki school bag dinta zata fice a dakin,qarar wayarta ya dakatar da ita,ta waiwaya ga inda ta ajjiye wayar saman madubinta,ta koma ta zuba mata ido tana kallon number wayar,sai kuma ta miqa hannu ta dauka.

Lallausar muryarsa ta bayyana cikin wayar,gaba daya kamar wadda aka bigewa gwiwoyinta haka taji,ta koma da baya ta zauna tana qoqarin amsa sallamar tasa,yana jin sautin muryarta ya saki boyayyen murmushi

“Ina kwana?” Ta gaisheshi muryarta na rawa

“Kin tashi lafiya?”

“Lafiya qalau” shuru yadan ratsa sai yace

“Baki kirani kinji yadda na sauka ba,tsakani da Allah ba amana,ni ina nan ina tunaninki” wata irin kunya ce ta saukar mata,har taji kamar gata a gabansa,saita saki murmushi tana qunshe fuska

“Kayi haquri” ta samu kanta da fada,don ko kadan ta kirashin baizo kanta ba,hasalima ita batace ga number dinsa ba

“Yayi kyau,yanzu me kikeyi?”

“Makaranta” ta bashi amsa a taqaice,daga nan inda yake ya kalli agogon dake gefansa

“To a dawo lafiya”

“Allah yasa” ta fada cikin dan karsashin data samu

“Babu komai ko?” Shuru ta danyi,da kamar tace masa gidan babu dadi,kamar tace masa jiya da qyar tayi bacci,kamar tace masa ya dawo don Allah,amma kuma saita kasa ta amsa masa da babu,sukayi sallama ta kashe wayar ta barta saman gado sannan ta fito ta cimma driver suka bar gidan,tana jin ta samu wani karsashi Cikin jiki da zuciyarta.

Wayar yabi da kallo bayan sunyi sallama ya kashe wayar,hafsat data fito daga wanka tayi zaune gaban madubi tana shafa jambakin dole ta sake binsa da kallo ta cikin mudubin,tunda ya fara wayar gaba daya ta tattara hankalinsa a kansa,kusan wannan dabi’arta ce,tanaso ta cinye amma ta kasa,tadan gyara zamanta tana matso jambakin ba tare data shafa ba tace

“Dawa kake waya ne?” Kansa ya daga yana kallon fuskarta ta cikin mudubin,maimakon ya maida kai ga amsa tambayarta,sai duka tunaninsa suka koma daren jiya tsakanin shi da ita

“Hasbunallah” ya furta qasan ransa,bacin ranta ya motsa masa amma sai ya kori shaidan

“Wanka kikayi?” Ya mata tambayar data bata mamaki,a mamakance ta amsa masa

“Eh,baka gani ba?” Kai ya jinjina

“I see,but…..zo muje in nuna miki wani abu” ya fada yana yaye lallausan duvet dinsa sabo fil da dole ta sanyashi daukoshi,saboda yazo ya tarar da nashi anci ubansa,tun kafin yayi magana ma tace masa nawwara ce,haka ya tattarashi a daren ya bawa mai gadinsu yace ya yar,shi kuwa ya kaishi baya cikin murna ya jiqashi zai wanke,saidai shi dinma yana wankewar yana tsinewa qazantar hafsatun a ranshi,saboda wani irin gamayyar hadakar dauda ne a jiki harma da guntun kashi dana fitsari.

Kai tsaye ya shige bandakin,ta ajjiye jambakin ta bishi da kallo,itafa ba wannan takeso ba,bai amsa mata tambayar ta ba,abun yayi mata tsaye a rai tunda taji suna waya da yarinyar,abinda bata taba ji yayi da ita ba,to amma kuma dole ta lallaba a yanzun,bataso suyi tashin hankali,kada ta barar da umrarta,don tunda taji labarin tafiya umarar ranta ya raya mata harda ita a ciki,qilan bai fada mata bane,saboda ya saba,yana da wani irin miskilanci da shan qamshi ta wannan bangaren,ba kasafai idan zai maka abu yake gaya maka ba,har sai dab da faruwar abun,dole ta miqe ta bishi bandakin,zuciyarta nq raya mata dole ta kira yarinyar tabi ba’asi,ta kuma sake kada mata warning,dama ranta a bace yake tunda taga yazo babu ita,don ta hada himilin qazantarta,mai wankinsu ya gudu amma yace mata yana qauyensu,tana ta jira fa taji wayam,dole ta tattara duk wasu tarkacen kayayyakinta takaisu store din bayan gidan ta kulle saboda abbas din,ta tabbatar idan ya gani sai yayi fada,ita batasan uwar daya sanya yanzun sai yayi zuwa biyu baizo da ita ba,ko a yanzun wannan kusan zuwasa na biyun kenan,idan ta bigi cikinsa sai yace mata makarantar ya sanya haka.

Tana shiga bandakin yana tsaye da clipper a hannunsa yana daurata,ya daga tsimammun idanunsa dake motsa mata soyayyarsa koda bata shirya ba ya kalleta

“come closer” ya fada yana kallonta,kamar zata musa masa kota tambayeshi dalili sai kuma ta fasa,ta matso din kamar yadda ya buqata,bata kawo hakan a ranta ba kawai taji ya sanya hannu zai ware towel din jikinta,da mugun qarfi ta kama towel din ta riqe tana kallon idanunsa

“Me zaka yimin da safiyar nan kuma?” Ta tambayeshi ranta a bace,mamakinta ya sake cikashi,yana sane yace mata

“I want to be with you” ido ta zare ranta a bace

“Haba don Allah,duk abinda kayi jiyan bai isheka ba?, al’amuranka are getting worst gaskiya abban mimi, jiyan kamar zan mutu fa” bai amsa mata ba illa hannu daya daya saka ya fincikota,ya ware towel din,ya kunna clipper din ya daga hannunta ya fara kwashe mata gashin hammata,sai tayi shuru tana kallonsa,fuskarsa a hade,kunya ta kamata,ta rasa yadda zata nade masa tabarmar kunya da hauka,har ya gama sannan yace mata

“Kwanta na qarasa miki sauran,tunda bakisan yadda akeyi ba”yafadi ba tare daya kalleta ba yana goge gashin daya bata jikin clipper din, fuska ta bata

“Kawai da ranar Allah saina yaye maka jikina,kai ba zaka ji kunyar kalla ba?” A nutse ya daga kai yana kallonta,ko yaushe mamakinta kasheshi yakeyi,kamar wata jahila ko wadda batasan meye aure ba,ya zuba mata idanunsa da suka sanyata tadan daburce,sai tahau quna quni

“Zanji kunya mana,wannan uwar gayyar da kika tarawa wajen ai dole aji kunyar kallansa” batasan abinda zai maida mata dashi ba kenan,sai zancan nasa yayi mata ciwo

“Me kake nufi?,daga fadin gaskiya zaka mayar min da baqar magana?” Baice mata komai ba,ya qarasa gefanta inda take tsaye ya ajjiye clipper din ransa ya suya,kome zaka.mata a duniya baka iya ba,bakuma zaka fita ba

“Kada ki fito baki kwashemin wannan go slow din da kika tarawa wajen ba” ya fada adan zafafe ya qarasa sink ya wanke hannunsa da detergent ya fita yabar mata toilet din.

Binsa tayi da kallo idanunta na hada qwalla,to wai ina ruwansa da sumar wajen?,badai ta bashi abinda yake nema ba?,why not zai dameta harda baqar magana?,banda tasan halinsa sarai tana kuma tsoron hukuncinsa da ba zata aske ba,tasanshi hukuncinsa bashi da dadi idan ka kaishi bango.

Ko kafin ta fito ma shi tuni ya gama gyaran sassan nasa,suna falo suna breakfast shi da yaransa,wucesu tayi tana shan qamshi,ita ala dole ya bata mata rai,can qasan ranta kuma kunya ce fal bayan ta gama askewar taga uban tulin gashin data tara,taji kuma iska tana ratsata, baibi ta kanta ba shima,don idan da sabo ya saba da irin wadan nan dabu’un nata.

Wankansa yayi ya shirya ya kuma shirya yaran,ya aikasu ta saka musu kaya,taja tsaki

“Wato baima san tanayi ba,ficewarsa zaiyi kenan,me yasa ne duk fushin da zatayi baya iya lallashinta?” Ta tambayi kanta zuciyarta na quna,haka ya figi yaran ta watsa musu wata shadda ta kadasu daga dakin.

Sanda suka shigo sai daya dakata daga taje sumarsa da yakeyi,ya juyo yana kallon kayan jikin nasu sosai,gezner ce mai mugun tsada daya siya musu kwanan nan da aka qara masa girma su da mamarsu,ya kuma biya kudi mai yawa aka muau dinki mai tsada,ita mamartasu tun randa suka fita a hannunsa bai taba ganinta a jikinsa ba,su kuma bai tashi ganinta a nasu jikin ba sai da wannan muguwar kamar,gaba daya ta fita hayyacinta,kamar ma ta soma dafewa,ga wata muguwat squeezing da sukayi

“Allah ya kyauta”kawai ta fadi bayan ya taba shaddar ya tabbatar itace

“Daddy mu tafi,daddy tare zamuje ko?” Mimi ta fada,saiya gyada mata kai,tausayinta na cikashi,sam bata damu da yanayin da kayan jikin nata suke ba

“Muje na canza muku kaya tukunna” ya fada yana hada kansu suka wuce sashen hafsa din.

Gaba daya dakin a qazance yake sannan a hautsine,dama kusan kaso casa’in na gyaran dakin shike musu,idan ya gama nasa gyaran saiya hada da nasu,yana saka ran kuwa ba’a sake bi ta kansa sai idan ya sake zuwa wani weekend din,baya qaunar yadda taje barin rayuwar yaransa cikin qazanta,yara mata ne,wataran dole gidan wani zasu,uwa uba ma lafiyarsu,yana tsoron wata cutar a tattare dasu,haka ya dinga hadiyar bacin ran bayan ya bude cupboard dinsu,duka kayan ma baya ganesu,baya gane masu wanki da wadanda babu wanki,ga kaya cike da cupboard din amma babu na zabe,ya zubo dasu duka,ransa a mugun bace,wai me yake damun hafsat ne?,kayan yaranki kamar na mahaukata?,banbancinsu kadanne?.

Wayarsa ya zaro yayi kiranta,don bayason su hada fuska ma ta qara tunzurashi,tana ganin kiran taqi dagawa,har ya gaji ya tura mimi tayi kiranta.

Sai data mula sannan ta taso,ta tura qofar suka hada ido,saita kauda kanta saboda yadda taga bacin rai baro baro saman fuskarsa,tayi gefe da kanta tana jiran jin tashin boma boman fada,saboda ta hangi himilin kayan yaran daya watso qasa

“Meye matsalar me muku wanki?,bai iya bane?” Ya tambayeta calmly yana qoqarin dannar kansa,duk da can qasan ransa wani irin bacib raine kecin zuciyarsa

“Kawai yaron bashi da mutunci ne,ba kasafai nake bashi wanki ba” ya jinjina kai kawai,saboda yasan ta fada ne kawai don ta kare kanta

“Shi kuma engine wankin gidan fa?”

“Ya lalace wata hudu kenan” wani abu mai tauri ya hadiye,ransa na baci, engine ma ya lalace amma ta buda baki ta gaya masa ba zata iya ba?

“Yayi” kawai yace da ita,saita saki handle din qofar ta juya ta fice abinta

“Ka qaraci jarabarka kai kadai” tafada can qasan ranta tana buga tsaki.

Wayarsa kawai ya zaro ya kira hajiya

“Ka iso ne?”

“Ina dai hanya,muneera zaki turomin gida yanzu”

“To gata nan” ta fadi ba tare data tambayi ba’asi ba,amma cikin ranta tana addu’ar Allah yasa lafiya.

Babu dadewa kuwa sai gata,ya sakata ta zauna ta ware sababbin da rashin tsafta da kulawa yasa suka lalace,sauran kuwa yace dukka ta samu manyan buhu ta duresu ta fita dasu,hakan kuwa tayi,yasa takai waje ta baiwa mai gadi,sauran masu kyan ta saka masa a booth din motarsa ya sakasu a gaba suka fito a dakin.

Jin motsi ya qaru a gidan da surutun yaran yasa ta kasa zaman dakin,tayita kai kawo tsakanin dakinta da kitchen tana kallon qofar dakin nasu tanaso taga waye yazo,dai dai sanda ta fito daga kitchen din muneera ta fitowa da jakar kayan dasu mimi, cikin girmamawa ta rusuna tana gaidata.

Fuskarta kadaran kadaham ta amsa mata tana kallon jakar kayan a hannunta,shikam tuni yayi gaba,sai itama muneera tayi mata sallana tabi bayan uncle din nata.

Baqinciki kamar tayi me,tabi yarinyar da kallo,tabbas shike sake wulaqantata tare da basu damar da zasu gaya mata magana su kirata da qazama,ya kira yarinya har cikin gidanta cikin dakin yaranta ta kwashi kaya an fita dasu,tome za’a je ayi mata da kayan yara?,da wannan bacin ran ta dinga mita da.surutu ita kadai a cikin gidan,banda tana shakkarsa saita tsaidasu tabi ba’asi,kai da babu ma mai daukar mata kaya ya fita mata dasu a cikin gida,saidai ta sani,bacin ransa bashi da dadi,dole tana jiyo qarar motarsa ya tasheta suka fita a gidan.

KI KULANI miss xoxo

DAUDAR GORA Billynabdul

RUMBUN K’AYA hafsat rano

IDON NERA Mamuhghee

A RUBUCE TAKE huguma

_sinkin labaran dake dauke da dukkan wasu nau’ikan salo da kuke so_

_masoya ku biya kudinku ta wannan hanyoyin_

0022419171
Maryam sani
Access bank

Saiku tura shaidar biya ga
+234 903 318 1070

*Masu katin waya ko VTU zaku tura ta nan*
09166221261

*Al’ummar nijerπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺ zaku tuntubi wannan number*
+227 96 09 67 63

*Thanks for choosing us*πŸ”₯πŸ”₯πŸ”₯πŸ”₯πŸ”₯πŸ”₯
[3/12, 9:02 PM] +234 813 343 4840: *H U G U M A*

*_A RUBUCE TAKE_*
(K’addarata)
*Arewabooks:Huguma*

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button