Sponsored Links
Arubuce Ta Ke Hausa NovelHausa Novels

Arubuce Ta Ke 37

Sponsored Links

Page 37

Cak ta tsaya sanda suka isa bakin part din nata,ta juya tana fuskantar sa,fuskarta a narke,tana wasanda yatsunta,da alama magana takeson masa,amma ta kasa sai motsa yatsunta da takeyi,shi kuma ya kafeta da idanu,ganin ta kasa magana sai yayi gyaran murya,ta daga idanu ta dubeshi,kafin yace wani abu ta magantu

“Don Allah kada ka shigo” mamaki maganar tata ta bashi,sai ya kafeta da idanu yana neman ba’asi,bata gane ba,murya a narke tace

“Kaji?” Saiga qwalla ta biyo bayan maganar,bai shirya ba amma dole ta sanya qaramin murmushi ya qwace masa,sai ya kauda kansa gefe na sakanni yana danne murmushin kafin ya dawo da dubansa gareta,ya gama gano abinda take nufi,don haka yace

“Is okay” sai ya juya a hankali yabar wajen yana nufar sashen hafsat.

Ajiyar Zuciya ta sauke tana binsa da ido,sai taji dadi a ranta da ya tafin,don idan da ya tsaya ba shiga zatayi ba,da wanne ido zata kallesu?,me zatace musu?,ta samu relief don haka ta juya tana dosar qofar falon nata.

Kamar wata munafuka haka ta dinga rarraba ido tana rabewa a bango,jikin labulen bakin qofa ta tsaya tana leqen falon,inna laila ce saman dining ita da batulu,sai nujood zaune saman kujerar falon,Momma na zaune daga qasa,dukkansu kowa sanye da hijab,da alama tun tashin asuba ne basu koma ba.

Tana daga tsayen ta hangi anty deena ta fito dauke da wata jaka ta ajjiye saman kujera,ta kalli nujood tana cewa ta tashi su sake gyara falon,latifa ta riga ta gyaro ciki,saita matso ta wajen bakin qofa zata dauka mopper dake ajiye a wajen.

Motsin mutum ya sanyata waiwayawa ta dubi wajen,cikin mamaki take kallon widad

“Ke kuma me kike yi a nan a tsaye ke daya?” Rau rau tayi da idanu,a yadda anty deena ta kafeta da idanu saita fara hawaye kawai

“Meye haka widad?” Tambayar da ta sanya jikinta rawa,saboda tana ganin kamar anty deena din ta hangi abinda ya faru jiya,hankalin anty deena yadan dauko kadan,ta zaci ko wani abun ya gudana tsakaninsu,sai kuma taji hankalinta yadan kwanta kadan da taga yanayin tafiyarta bai canza ba,tana tausayinta,koda wani abun zai faru ma ta gwammace basa nan.

Sai data mata da gaske tabar kukan ta shigo,momma dake zaune ta bita da harara

“Ja’ira,zakiyi bayani ne” kasa hada idanu tayi da kowa,sai ta wuce ciki sum sum sum.

Dakinta ta murda ta fada tana sauke ajiyar zuciya mai qarfi,sai a sannan ta nutsu,ta soma bin dakin da kallo. Sosai ya qayatar da ita,an gama shirya mata komai sai qamshin sabinta yakeyi,ta waiwaya ta dubi bandaki inda anty deena tace akwai ruwan zafi,ta shiga tayi wanka,ta kuma zabi kaya masu kyau ta sanya,ta juya zata shige sai aka turo qofar,anty basma da anty ramziyya da anty marwa suka shigo,kowanne riqe da yaronsa,marwa dince kawai mai ciki bata samu rabo da wuri ba.

Nan bakin gadon suka zauna sunata tsokanar widad tare da da son jin me ya faru jiyan,kuka ta saki sosai

“Ni wallahi ku daina banaso,bayan ummu ta hana,babu kyau,wallahi ba ruwana” haka ta dinga fada tana sharar qwalla,su kuwa ganin abun suke kamar almara,wai yau widad din ummu ce aka aurar?,a wata uwa duniya?,ta tafi tabar ummu duk qaunar dake tsakaninsu?,Allah ne ya kawo anty madina ta korasu,sannan ta kada kan widad zuwa wanka,bayan ta fito kuma ta shiryata da kyau cikin wani lace da yayi masifar karbarta,ya fidda kyau da hasken fatarta,ita kanta ta dade tsaye gaban mdubi yana kallon kanta,tana ta zuba shirmenta na kyan da tayi,anty madina na binta da murmushi gami da goge qwalla a fakaice.

Daga bakin gadonta take zaune riqe da waya a hannunta,lokaci lokaci tana saka hannu ta share hawayen fuskarta,duk furuci daya da zatayi da anty ummee tana jin kamar zuciyarta zata tsinke saboda baqinciki bacin rai da zallar kishi kai daci

“Har kusan qonewa nayi garin saurin na hada masa tea nakai masa,amma wallahi acan na sameta,namiji dan babansa……alamun dana gani ma sunsha dambene,saboda ko dankwalin kanta gashi nan watse a qasa,don Allah anty ummee mai zaiyi da wannan mitsitsiyar yarinyar,banda tsabar cin fuska?” Tayi maganar tana jin kamar zuciyarta zata fito ta bakinta.

“Kinga ki ajjiye wannan a gefe,matuqar zakici gaba daga inda kika tsaya,zaki nuna komai ba komai bane…..hatta kusantar tata ma saikin hanashi gaba daya,meye a cikin ido ne banda ruwa?,ai nasara tana tare da jajircewa”

“Wannan nasarar anya kuwa tana tare dani?”

“Kin saare a dare daya kenan?” Anty ummeen ta tambayeta tana jinjina zallar gajen haquri irin na hafsa din

“Shin ba’a gabanki komai ya dinga gudana tsakanina da amaryar abban sayyid ba?,yanzu tana ina?”

“Banqi ta taki ba…..amma akwai nisan tazarar banbanci mai yawa tsakanin abbas dashi…..abbas anty…..yana da ra’ayin riqau kafiya da kuma magana daya,yana da wuyar sha’ani,yana da wuyar canza ra’ayi,idan yace eh…..tofa a haka zata yita tabbata”

“Uhmmm,mace fa tafi gaban tunanin dukkan wani mai tunani,saidai idan ba zaki iya ba”

“Zan iya” ta fada tana son sake bawa kanta qarfin gwiwa,ji take kamar ta rufe idanu ta kuma bude taga komai ya tarwatse,komai yazo qarshe,ta rufe idanunta kana ta budesu duk kusan lokaci daya sannan tace

“Na rasa ta yadda abbas yaga yarinyar nan anty ummee……abbas fa?,mara damuwa da abubuwa masu yawa,wanda wani abun ma sai kinta cewa kalli….ko ka gani” ta jefawa anty ummeen tambayar da taketa damunta tare da yi mata yawo a kai,har yanxu kums bata samu amsarta ba

“Namiji yafi gaban haka,kedai ki maida kai ga mission dinki…..”

“Ina zuwa” ta fada da sauri tana sauke wayar daga kunnenta sanda fa jiyo alamun taku ana nufowa dakin,ta kuma san babu wanda zai shigo din sai shi.

Da hanzari ta ajiye wayar,sannan ta fada bandaki ta maida qofar,da tattausar muryarsa yayi sallama ya tura qofar ya shigo,sai ya tsaya daga bakin qofa yana qarewa hargitsatsen dakin kallo,komai baya kan tsarinsa,baisan kuma sai yaushe zata gyara ba.

Ajiyar zuciya ta sauke,ta matsa gaban babban madubin dake bandakin wanda ya cika da jirwayen ruwan wankan da ba’a wankewa,ta debi ruwa ta wanke fuskarta,saboda batason ya gane ruwan hawaye ya fita a idanunta,taja zaninta da tayi daurin qirji dashi saman t.shirt dinta ta gyara daurin,sannan ta goge fuskarta da towel ta fito.

Suna hada idanu ta cika fuskarta da fara’a,sai ya dan lumshe idanunsa ya kuma budesu lokaci daya yana kallonta,qasan zuciyarsa kuma yana masa sanyi na yanayin da ya ganta a ciki,ba wata damuwa

“Yanzu nake shirin fita mu gaisa da baqi,gashi ka tarar dani” ta sake fada tana murmushin da ita kadai tasan ciwon da yake mata.

Agogo ya kalla kafin ya amsa mata

“Kaman yayi wuri,gwara ki kwanta ki sake hutawaYou are very tired, you need a rest maman nawwara” ya fada yana sauke mata murmushi.

Duk da cewa bata kalleshi ba amma tana jin saukar murmushin nasa har tsakiyar zuciyarta,murmushi ne da ita kadai tasan tsadarsa

“To ya za’a yi,kamawa takeyi ai,gashi na kasa hada musu breakfast” ta sakeyin maganar tana zaqulo hijabinta cikin hargitsatsun kayan wardrobe dinta wadanda yana daga tsaye yake tayata kallon yadda suke a hautsine,haka suke koda yaushe,idan kayi magana tace su nawwara ne tana bacci suka aikata,ko kuma suna neman teddy dinsu ne

“Ba matsala,kinyi qoqari sosai,zan saka a kawo musu breakfast”

“Da dai yafi,na gaji da jegon jaka” ta fada qasan ranta tana zura hijabin a jikinta,sannan ta matso tana cewa

“Bari naje mu gaisa kada suga rashin kyautawa ta,mun tashi gida daya ban leqasu ba” da kallo ya bita,duk da qoqarin sakewarta amma yana hangen wani.abu can qasan qwayar idanunta,zuciyarsa na alaqanta hakan da kishin da takeji a kansa.

Hannayensa ya bude mata,cikin taushin nan nasa

“Zaki wuce bamu gaisa ba madam” kallonsa tayi saita kauda kai tana qoqarin kawo murmushi kan fuskarta,tabbas idan tace zata shiga jikinsa a wannan yanayin kuka zata barke dashi,kukan kuma zai zame mata tonon silili ne.

“Ina kwana oga?” Ta fada tana ci gaba da tafiya,sai ya maida hannayensa yayi folding nasu a qirjinsa yana kallonta,qaramin murmushi na sauka saman labbansa,irin gaisuwar da yafi qauna daga wajenta kenan,amma dama yasan zaiyi wahala ya samu yadda yakeso din

“Alhmdlh madam,a dawo min da yarana mana?”

“Zasu dawo dole yau” ta bashi amsa ba tare data juyo ba

“Alright” ya amsa mata yana kallota ta cikin madubinta

“Bari naje na dawo” ta fada tana jan masa qofar,tana so taje ta saje tantance widad din,yadda ta ganta a jiyan haka take ko idanuwanta ne da kuma sharrin dare?.

Idanuwanta nakan dukka wani kayan qawa na falon,da qyar ta iya riqe kanta saboda yadda zuciyarta ke wani irin tsalle,ko ba’a gaya mata ba auren ‘yar gata ne daga dukkan alamu,saboda yadda aka shirya gami da qawata sassan nata gaba daya,babu ce kadai babu,jere mai aji da nutsuwa.

Ta basu fuska sosai ta gaidasu inna laila dasu momma,har tadan zauna suna dan taba hira,tana ta baza ido taga ta inda widad din zata fito,saiga nujood,kamar inna laila tasan buqatar ta tace da ita

“Kira widad,kice tazo ta gaida yayarta”

“To” ta amsa tana okomawa ciki da mopper din hannunta data goge inda ruwa ya zuba.

“Yaaa latifa” widad din ta fito tana fada,hannunta riqe da dankwalin lace din nata da yaqi dauruwa,anty deena dake wanka kuma tace lallai saita daura.

Hankalin hafsa ya fara kaiwa wajen,tana tafe da dankwalin fuskarta a kwabe tamkar shagwababbun ‘ya’yan fari,gashinta dake wani irin sheqi da walqiya a daure cikin ribbon jelarsa na reto a bayanta, yanayin qirar jikinta kadai abar kallo ce,sai kace wata babbar budurwa,tun a yanzun coca-cola shape dinta ya fita sosai,kallo dayan data mata ya kusa tafiya da numfashin ta,ta dinga qoqarin riqe kanta da kyau,kada ballinta ya watse a wajen.

*Arewabooks:Huguma*

KI KULANI miss xoxo

DAUDAR GORA Billynabdul

RUMBUN K’AYA hafsat rano

IDON NERA Mamuhghee

A RUBUCE TAKE huguma

_sinkin labaran dake dauke da dukkan wasu nau’ikan salo da kuke so_

_masoya ku biya kudinku ta wannan hanyoyin_

0022419171
Maryam sani
Access bank

Saiku tura shaidar biya ga
+234 903 318 1070

*Masu katin waya ko VTU zaku tura ta nan*
09166221261

*Al’ummar nijerπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺ zaku tuntubi wannan number*
+227 96 09 67 63

*Thanks for choosing us*πŸ”₯πŸ”₯πŸ”₯πŸ”₯πŸ”₯πŸ”₯
[3/2, 5:28 PM] +234 704 440 6400: *H U G U M A*

*_A RUBUCE TAKE_*
(K’addarata)

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button