Sponsored Links
Amatulmaleek Hausa NovelHausa Novels

Amatulmaleek 52

Sponsored Links

YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

 

52
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs๐Ÿ’ฏ๐Ÿ”ฅ๐Ÿ‘
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku๐Ÿ’ฏ๐Ÿ‘*

MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI’IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER

08142800199
07068558096

******************
Zaunawa Dr beeba tayi tana kallan Amatu cikin kulawa tace

“Yaya jikin naki?
Kin shiga ruwan zafi din Amma ba sosai ba Right??

Eh” Amatun ta Bude Baki ta furta kaman Wadda ke cikin sabuwan azabar ciwon.

Jin yayi Yana Neman shiga Wani tsaka me wuyar ganin yanda take magana kaman har lokacin tana cikin ciwo.

“Yanzu Yaya kikejin jikin harma da stitches din?
Kina Jin fever haryanxu?

Girgiza Kai tayi Kai tsaye.

“Are you sure?” Ya fada ahankali cikin nutsuwa Yana kallan cikin idanuwanta hannunsa har lokacin cikin nata.

Dauke idanuwanta tayi kansa tana gyada Kai kawai.

Numfashi Dr beeba ta sauke a boye Dan ita duk Neman rudewa takeyi daga duba Amatun Dan haka ta ce su shiga toilet zata Dan duba Amatun.

Dr beeba ce ta kamata da kanta suka nufi toilet din Yana bin bayan Amatun da Wani irin kallon yanda take tafiyar ahankali.

Basu Wani jimaba suka fito lokacin Dr beeba Kai tsaye Bata zaunaba ta sanar masa komai zai warke ahankali kulawa kawai take buqata.

Ficewa tayi sbd duk a rikice take da other side of ASH TALBA din da bata Saba gani ba ko tace jamaa Basu saniba.

Tana fita zaunar da ita yayi kan cinyarsa ahankali Yana matse tafin hannunsa da nata Yana kallanta yace

“Farha zata zauna anan ta kula Dake sosai is that ok with you??
Ko Zaki koma gidan Farha din kafin kiji sauki?
Wanne kikeso?

Ahankali ta Bude Baki tace

“Ta zauna anan din sbd maamah bazata bari naje koina ba harna kwana”

Wani irin murmushin da Bai san ya Akai ya sauka fuskansa bane ya dan sauko masa yana kallan bakinta Dake maganar.

Ajiyan zuciya ya sauke ahankali tareda kai bakinsa ahankali yayi kissing lips dinta yace

“Farha zata zauna anan din to Amma ki kula kema,zanyi kwana biyu kafin na dawo”

Sake kissing lips dinta yayi tareda tayar da ita ya tashi tsaye ya mayar da ita kan gadon zaune ya rufe mata Rabin jikinta yace

“Akwai sanyi ki Saka kaya me nauyi”

Kallansa kawai tayi batareda ta amsa da komaiba harya gama gyara mata rufan ya sunkuyo ya shafi wuyanta yai kissing idanuwanta ya mata sallama ya juya ya fice daga Dakin ta kasa bin ko bayansa da kallo sbd mutuwan da jikinta yayi gaba Daya idanuwanta na Neman cikowa da hawaye sedai ta danne ta hanasu cikowan.

Yana fitowa Kai tsaye baima lura dasu mum Aisha Dake palon ba ya fice zuwa hanyar palonsa.

Husnah kasa motsawa tayi Dan batama San ya fito ya wuce din ba Saida mum Aisha cikin muguwar gayya tace

“Ga ASH din na se yanzu ya fito daga dakin bayan Abeeda na can Rai hannun Allah tana jiransa Yana Nan gurin yar cikinsa ko me yake faruwa ne oho”

Anty Farha batama San me suke fada ba Dan waya takeyi tinda ta dawo daga raka Dr beeba.

Tashi tayi ta nufi bedroom din ta shige.

Mum Aisha kuwa ajiyar zuciya da numfashi ta ringa saukewa a Jere na rashin sanin meyake faruwa duk da zuciyarta na ingizata ga zargin abinda ya faru din na kodai ASH ya Maida Amatun mace ne to Amma Kuma bazai taba yiyuwaba take gani sbd yaushe har ya fara kallan Amatun da zai mayar da ita matarsa bayan Amatun ma ko kallansa bata iyayi har yanxu ko yaushe Kai a qasa tsohuwar munafuka data gada a gun uwarta.

Miqewa tayi ta nufi hanyar sauka Dan maamah na buqatan farkawa daga baccin kwadayi da burin da takeyi akan ASH.

Kai tsaye bedroom dinsa ya nufa cikin qanqanin lokaci yayi wanka ya fito sanyeda qananun kayan Balenciaga da fcap hannunsa wayoyinsa ne kawai Se luggage dinsa me tsadan gaske.

Husnah data kasa zuwa ganinsa hawayene masu zafin gaske take dannewa suna komawa cikin idanuwanta suna soya zuciyarta.

Qin tasowa tayi duk da Kiran da yayi mata a waya tana kallo taqi dauka sbd kanta Dake juyawa har Kiran ya yanke.

Sake kiranta yayi Bata daukaba Daman a kaidansa Baya wuce kira Daya sai iyalinsa kawai yakewa biyu Dan haka Bai sake kira ba sai maamah Daya kira a wayar y sanar da ita ya wuce ta kula da Gidan,su kudi Daman ba matsala bane a gidan idan Jameel Baya Nan akwai me kawo kudi ko duk abinda ake buqata a gidan ASH TALBA din.

Kai tsaye su Mr Jameel Dake jiransa kaman masu naqudar tsaye tsoron su rasa flight dinsu ga Kuma ba Daman kiransa Dan haka suna ganinsa suka taso gaba dayansu da sauri.

Mr Jameel yayi saurin karban luggage dinsa Yana Bude masa mota driver ya Bude bayan motar ya Saka kayan ya dawo ya fada motar da sauri ya tayar aka wangale musu gate suka fice da sauri.

Suna fita text ya rubuta mata akan Shan magani da kulawa sosai ya tura ya kashe wayar gaba Daya Yana miqawa mr Jameel daya karba yana Satan kallan time ahankali.

*******Bayan ficewansa daga gidan Husnah kasa riquwa kukanta yayi sbd zuciyarta zata iya bugawa Dan haka ta fasa Wani irin kuka Mai ciwo da zafin zuciya batareda ta motsa daga inda take ba.

Mum Aisha da maamah Dake palon qasa mum Aisha na fadawa maamah maganganun da suke Neman buga zuciyarta sbd damuwa da tashin hankali suka ji fasa kukan Husnah wadda yau ne ranar farko dataji tana Dana sani da baqin cikin takurawa dad dinta ya dawo da maamah kota halin Yaya.

Saman suka hawo suna kallan Husnah din maamah cikin damuwa
Mum Aisha Kuma cikin takaici.

Jajir idanuwanta sukai ta dago tana kallan maamah din cikin kukan da batasan mema zata ce ba bayan kalman “Maamah mum dina ta tashi bayan shekaru Amma Dad haryana da lokacin batawa a gida sbd ciwon Amatun data kasa fadan gaskiyar me yake damunta”

Anty Farha data fito daki taji abinda Husnah ke fada ta katseta da cewa

“Meye ruwan maamah to a zancen tinda itama yanda kikaga yanada lokacin batawar itama haka take Gani,
Da nice ke Kai tsaye zanje na tambayesa tinda kaf gidan keda Matar gidan ne kuka Fi kusanci dashi akan kowa”””

Mum Aisha bakin Farha take kalla kaman zata fasa mata shi da kwalba Amma ASH ya daure mata itama tinda yar amanar Amatu ce.

Maamah data kasa cewa komai tanajin kukan Husnah da maganganunta har cikin ranta suna yankar zuciyarta Amma ta hadiye sbd Husnah kaman yanda Abeeda bazatai fushi da itaba haka itama bazatai fushi da Husnah ba tinda kaman Amatun take a ranta.

Mum Aisha Dake jin kaman ta tarwatsa gidan da bomb barin gurin tayi ta sauka ta wuce dakinta tana tsinewa masifar data shigo gidan.

Anty Farha ma barin gurin tayi ta sauka Dan kawowa Amatun abinda zataci da daddaren.

Maamah ma jiki ba qwari ta ringa rarrashin Husnah data ringa rokon maamah din ta Saka Amatu barin gidan gaba Daya ma kafin mum dinta ta dawo taji maganar auren ta sake komawa coma.

Wannan maganar ce tafi daga hankalin maamah Dan haka ta qudurtawa ranta ko Abeeda ta dawo bazata taba barin ta tarar da wannan auren ba.

Husnah Bata samu sassaucin abinda take ji ba Saida maamah ta tabbatar mata da Babu abinda zaisa ma Abeeda ta tarar da auren bare saninsa tukuna ta samu Kanta ta silala ta shige daki kanta na juyawa kaman zata zauce takeji depression dinta na Neman tashi.

Maamah kuwa daurewa tayi ta shiga dakin Amatun dubata tana kasa kallan Amatun
Itama Amatun kallo daya tayiwa maamah jikinta yayi tsananin sanyi sbd karanto damuwa me girman gaske a tareda ita.

Zaman shirun sukai a dakin sai sama sama maamah din ke Dan magana
Ganin Farha da Kuma yanayin jikinta ya Sanyata barin maganarta kafin Amatun ta samu sauki Kuma farha ta tafi tukuna.

Har qarfe goma maamah na tareda Amatun da Farha Kuma ko da wasa Babu abinda sukai Daya Saka maamah zargin ciwon Amatun.

Ko da zata tafi dakinta Farha ce ta rakota Amatun Bata tashi daga inda take ba sai bayan ficewan Maamah din anty Farha ta kamata ta sake Dan shiga ruwa tayi wanka tai Shirin bacci ta kwanta cikin kayan bacci masu kauri.

Washe gari ko data tashi jikinta ya Dan sake samun karfi da sauki Dan haka ta daure tana nuna samun saukinta ahankali ahankali sbd kada maamah Taga abin yayi yawa.

Anty Farha ce ta tsaya take kulawa da ita sosai hakama suna iya kokarin Hana maamah fahimtar komai musamman yanzu da mum Aisha da Husnah suka qarasa gurbata tinaninta gaba Daya akan auren tsana take masa me nauyi Dan har cikin ranta tafison ‘yarta ta koma bazawara da Abeeda ta dawo ta tarar da wannan auren.

Husnah kwana biyu da tafiyar Dad din nata tabi jirgi ta tafiyarta porthcrt Dan ganin Amatu a yanzu Kawai suqar da ita takeyi Dan kuwa kishinta takeyi ta ko wanne bangaren,
Bangaren Taya mum dinta kishin Dad dinta me zafi,dakuma kishi da baqin cikin haryanxu Faisal Bai cire Amatun daga Rai ba Wanda ke Sakata shiga wasi wasin kada Amatun ta fito hannun Dad dinta Wani bangaren sbd tana fitowa Allah ne kawai ze Hana Faisal aurenta ga Haydar ta riga ta haramta garesa tinda ta auri Dad din bare ta fito a aura masa ita maimakon Faisal.

Bayan tafiyar Husnah damuwa me tsanani maamah ta sake shiga sbd qarara a Fili sbd Amatu Husnah tabar gidan ta bangaren Daya Kuma sunyi magana da ASH dai Abeeda ta farfado Daram Amma Bata iya ko magana kusan komai nata Baya aiki yi mata komai akeyi.

Anty Farha ce kawai hankalinta kwance cikin rashin damuwa take kulawa sosai da Amatu wadda itama kusan cikin damuwar take sosai na yanda maamah ta sauya mata gaba Daya da Kuma yanda komai yake Neman juyewa a rayuwarta,

Taji sauki sosai ta warke Amma Bata cikin kuzarinta sbd damuwa duk da ta rasa Menene ma abinda yake Sakata damuwan bayan sauyin data samu daga mahaifiyarta,
Koyaushe ya kirata a waya Bata iya dauka Dan ta rasa tayaya zata iya magana dashi a lokacinda yake can din,
Rashin daukan wayarsa ya Sanya sedai yayi mata text kullum da dare.

Mum Aisha zaune take gaban Naufal Daya shiga shock na Jin tashin Madame abeeda ya Kalli mum dinsa da jajayen idanuwansa zuciyarsa na radadi yace

“ASH zai dawo da ita ne?

Kallansa mum Aisha tayi tana cewa

“Ta farfado me zata zauna acan tayi mijinta na Nan Yana rayuwarsa da sa’ar ‘yarsa”

Fadan kalman yarsa da tai ya Saka Naufal Jin zafin zuciyarsa ya qaru yace

“Yar Dan uwansa dai Dan da ‘yarsa daya Haifa da cikinsa ce bazata kirani ta turani zuwa ga matarsa ba gashinan Ashe tarko ta nada min Dan su……

Kallan da mum Aisha take masa ne ruwan datake sha suna kokarin biyowa ta hancinta ya sanyashi yin shiru kada ta mutu ya shige uku baida me tsaya masa.
##MAMUH#

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at๐Ÿ‘‡
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button