Sponsored Links
Amatulmaleek Hausa NovelHausa Novels

Amatulmaleek 46

Sponsored Links

YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

 

46
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs๐Ÿ’ฏ๐Ÿ”ฅ๐Ÿ‘
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku๐Ÿ’ฏ๐Ÿ‘*

MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI’IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER

08142800199
07068558096

**************
Dayake da wuri tayi bacci Bata tsaya duba massage dinsa ba sai washe gari,

Shirin tafiya makaranta tayi ta fice sbd bikin anty Farha tanason baro school da wuri Dan ta samu attending.

Su Maamah dai ta waya tayiwa anty Farha din Allah ya Sanya alkhairi
Husnah Kuma daga adduar har zuwan Babu Wanda takeda niyar yi bare mum Aisha da ko sunan Farha baa fada a gabanta bare shiga shaaninta.

Karfe uku ta baro school ta dawo gida.

Kadan ta huta tayi wanka tai Shirin tafiya bikin ta fice
Da kanta taja motan zuwa gurin waliman.

Ko data Isa anty Farha zuba mata idanuwa Tayi tana Jinjina kyanta da komai nata dayake da kyau da tsari musamman gyaran da Akai mata jiyan ya Sakata komawa kaman wata sabuwar ‘danyar amarya.

Fara waliman Akai cikin farin ciki da burgewa,
Manyan Yan mata da Yan matan Dake auren manyan qasa irinsu ash din kusan duk mutanen anty Farha ne sun halarto sosai anyi komai a tsari Se magrib aka watse.

Anty Farha riqeta tayi ta hanata komawa Saida suka gama komai taja motar Amatun sbd bazat iya barinta tayi driving da kanta ba magrib tayi.

Suna isowa aka bude musu gate din Mansion din suka shigo.

Anty Farha ce tana parking tace

“ASH TALBA ya dawo qasar kenan shine kika bari na riqeki har wannan time din Amah?”

Se a lokacin Amatu ta dago idanuwanta ta Kalli inda motocin ASH din suke suna kallan gate a maimakon yanda suke a Baya sun bawa gate din Baya ne alama ce ta ya dawo din anfita dasu anje an daukosa Kokuma ana jiran isowansa aje a daukosa.

Sanyi taji jikinta n Neman yi ta daure ta fito motan a natse tayi sallama da anty Farha wadda ta fito motar itama driver ze kaita gida da motan Amatun ya dawo.

Cikin gida Tayo ta kofan kitchen ma tabi sbd sanin Kila maamah na kitchen din Amma bata Nan.

Juyawa tayi ta nufi dakin maamah din ta Tararda ita tana sallah itama ta ajiye Jakarta da wayarta kan kujera ta nufi bedroom din maamah din ta shige toilet Tayo alwala ta fito tazo inda maamah din ta gama sallah tayi tata sallan.

Bayan ta idar da sallan addua tayi tana gamawa ta miqe ta dauko wayarta Dake ringing Taga sunan Haydar.

Murmurshi me kyau ta sake tana zaunawa tareda daga wayan tana ambatar sunansa Dan maamah data zuba mata idanuwan son sanin me wayar taji waye dinne.

Ta lura da yanda fuskan maamah ta sauya da Dan murmushi da farin cikin jin Haydar ne Dan haka taci gaba da wayarta da Haydar Wanda wasu maganganun ma maamah batasan me suke fada ma Dan turanci ne Da suka fara sabawa dashi yanzu sbd rayuwar can din basa iya dadewa suna magana da zallan Hausa.

Abdulhameed ma karban wayar yayi suna sake hayaniyarsu wadda idan Bada su din ba Se anty Farha yanzu Amma Babu Wanda zaaji Amatu na magana sosai dasu haka tana daga murya idan Basu ba.

Har Akai ishai Basu gama ga Saida ta Basu suka gaisa da maamah itama suna sake hayaniyarsu sukai sallama ta kashe wayar ta Nemo numbern anty Farha taji idan ta Isa gida lfy.

Wasu maganar da anty Farha ta fara yimata ne ya Sanyata Satan kallan inda maamah take gabanta na faduwa hakama tana rikicewa sbd kunya da tsoron maamah wadda ta zuba mata idanuwanta Amma batajin me anty Farha din ke fada Dan haka sallama da anty Farha din kawai Amatu tayi ta kashe wayarta batareda ta iya cigaba da sauraran abinda anty Farha din ke fada.

Maamah tashi tayi ta tada sallan ishai dinta
Itama Amatun miqewa tayi ta tayar da tata gajiya ma take Dan ji wanka take buqatan yi.

Bayan sun idar Amatu Bata Wani jik yunwa sbd sunci abinci taredasu anty Farha Dan haka batajin zata sake cin Wani abin.

Kallanta maamah tayi lokacinda take daukan banana data Gani a fridge dayake palon maamah din takai bakinta tace

“ASH ya dawo”……cak Amatun ta tsaya ayaban data Saka bakinta tana wuce maqoshinta batareda ta taunaba.

“kafin ki wuce dakinki muje muyi masa barka da dawowa ki wuce ki shige tinda fitan safe kikeyi.”

Danne yanayinta tareda boye faduwan da gabanta yayi Amatun tayi tana cigaba da cusa ayaban hannunta bakinta sbd kada maamah din tace tayi Wani abu akan auren Wanda shine abinda yake faruwa tsakaninsu yanxu.

A Dan matse ta gyada Kai tana Jin jikinta na sanyi Dan kuwa a ayanzu kaman tsaka me wuya ne take tsakanin maamah da ASH din gaba Daya.

Miqewa tayi tana fasa qara cin ayaban sbd Jin tayi cikinta ya cunkushe ba guri ma.

Fitowa sukai maamah na sanye da hijab har qasa ita Kuma Amatun kayan data dawo waliman anty Farha dasune a jikinta Riga da skirt na navy blue dry exclusive lace da mayafi Dan daidai irinta Yan mata marasa jiki.

Sama suka hawo maamah ce a gaba tasa Amatun ta biyo bayanta Dan haka a sanyaye take biye da maamah din ita da maamah dinma tabar gaisuwan zuwa gobe sayi.

Dining room suka nufa mum Aisha ma lokacin take shiga Husnah ce ta fara fitowa ta kofan palonsa fuskarta cikeda farin ciki da walwalan kasancewa da mahaifinta.

Husnah suke kalla kowa fuska a sake kafin suyi magana sai gashi ya fito Shima sanye cikin hoodie Riga da wandon rugby masu Dan kauri gaba Daya black hakama slippers dinsa dasuka bayyanarda hasken qafarsa da kaman Baya tafiya da ita black ne.

Fuskarsa idan akace Aiki yake zakai mamakin haske da hutun Daya bayyana tareda shi har wata kwantacciyar lafiyayyar gashin fuska ya Dan Tara Daya sauya kamanninsa gaba Daya zuwa Wani lafiyayyan matashin da bazaa ce ya haife saurayin ‘da Haydar ba da Husnah.

Qamshinsa kawai hancinta ya Shaqa taji jikinta ya mutu gaba Daya Amma bazata iya dagowa ta kallesaba sbd mahaifiyarta Dake gurin Dan haka numfashi me sanyi kawai ta sauke a boye.
Maamah da mum Aisha kuwa kasa iya kallansa sukai sedai gaisuwa da masa barka da dawowa.

Daga bayan Maamah ta iya Bude Baki itama cikin sanyin murya ta furta kalman

“Barka da dawowa”

Zama yayi bayan Jin saukan muryarta cikin kunnuwansa zuwa zuciyarsa data kasa hanasa kallanta duk da mahaifiyarta Dake gurin.

Fararen idanuwansa ya watsa gurinda maamah take tsaye dole maamah din ta janye sbd nauyin idanuwansa akanta tareda Jin nauyi saiga Amatun ta bayyana a bayanta tsaye.

Suturar Dake jikinta ya kalla saga qasa zuwa Samanta cikin nutsuwa kafin ya tsayar da kallansa kan fuskarta data kasa dagowa ta kallesa.

Maamah,mum Aisha da Husnah kusan kowannensu maida kallansa yayi kan Amatun Babu Wanda gabansa Baya mummunan bugawa da kallan tsaf da ASH din yayiwa Amatun cikin nutsuwa a gabansu.

Ahankali maamah ta juya ko ganin gabanta sosai Batayi ta fice daga gurin Amatu ta bi bayanta cikin kasalan da Idanuwansa tana jinsu a kanta suka sakar mata.

Maamah Bata iya tsayawa dogon maganaba ta raka Amatu har kofan dakinta tai mata seda safe ta wuce Dan idan Amatun ta biyota dakinta kwana yau din zata iya mata mummunan furuci akan abinda ya faru yanzu din bayan batasan mema zatace Yana faruwaba.

Jiki mace Amatu ta shige bedroom dinta itama,

Zaunawa tayi ta sauke ajiyan zuciya a Jere tana dawowa hayyacinta yanda ya kamata kafin ta miqe ta tube kayanta ta shige toilet.

Wanka tayi da ruwan zafi sosai jikinta ya sake kafin ta fito daure da towel ta zauna gaban mirror.

Body oil kawai ta shafa da turare ta miqe ya nufi kayan baccinta ta Ciro Riga da wando marasa nauyi masu santsi ta Saka.

Gadonta ta nufa tana kokarin kashe wayarta sakon daya Saka gabanta faduwa me qarfi shigowa wayarta.

Zaman tayi bakin gadonta tana sake karanta sakwan hakanan gabanta ke faduwa da tinanin zuwan kawai.

Kallan wayarta ta sake yi tana rasa tinanin kamawa na zuwa ko yiwa sakon shiru.

Lokaci me tsayi ta dauka tana shiga tinani da rashin sanin abinyi.

Numfashi ta sauke ahankali bayan kusan awa da shigowan sakon ta miqe tsaye jikinta ba qwari ta nufi wardrobe ta Dauko hijab ta Saka tareda daukan wayanta ta fice qafa ba qwari.

Kitchen ta nufa Bata dafa tea ba fridge kawai ta Bude ta zuba fresh juice da aka hada ranar na mango ta hada komai ta jera ta dauka ta koma saman ta nufi hanyar palonsa Kai tsaye lokacin har 11 ta Dade da wucewa.

Tana Bude kofan palonsa Baya palon Dan haka ta nufi bedroom dinsa ta Bude ahankali cikin nutsuwa.

Akan dadduman sallah yake Yana sallah Dan haka table ta nufa ta ajiye kayan hannunta tana juyowa Yana sallamewa.

Idanuwansa ya zuba mata Yana mata kallon gaskia da gaskia na abinda yakeji a zuciyarsa Yana rasa Menene yake Jin din,
Menene suna ko ma’anar abinda yake ji cak a tsakiyan zuciyarsa game da ita da duk abinda ya shafeta.

Cikin sanyi da kasalan idanuwansa akanta ta dago nata idanuwan ta saukesu akansa Daman abinda yake jira kenan ko zai samu sassaucin abinda ya tsaya tsakiyar zuciyansa Amma still kallan nata kaman sake nauyin koma Menene yayi Dan haka a sanyaye Shima ya daga hannunsa Daya ya kirata ta Tako a natse tazo har gabansa.

Miqewa tsaye yayi ya kama hannunta Daya ya dago cikin sanyi yakai bakinsa yayi kissing din hannun tareda lumshe idanuwansa yanajin nutsuwa da sanyi na mamaye zuciya da ruhinsa ahankali.

Cikin sauti me sanyi da nutsuwa yakai bakinsa gap da kunnenta ya tambayeta tana tareda alwala.

Kasa dagowa tayi ta gyada masa Kai cikin sanyi.

Janyota yayi ahankali gefensa daga bayansa kadan ya tayar musu da sallah.

Nafila ce sukai wadda batasan ta Menene ba harsai da suka gama ya miqe ya zare mata hijabinta ya ajiye mata kan sofa ya janyota jikinsa ya rungume ahankali.

**Mr Jameel Dake Kiran wayoyinsa kaman zai Ari hauka a lokacin Jin yakeyi zufa da farin ciki da kuma rashin sanin mafita Yana Neman zautashi.

Cigaba yakeyi da sake Kiran wayoyinsa Amma Sam Babu Wadda ke shiga Dan haka ya kira ta Amatu itama tata a kashe Dan haka yakira Farha akan ta tura masa numbern Amatun Daya.

Tana tura masa yafara kira itama Bata dauka sbd wayarta Dake silent a lokacinda suke sallah.

Farha data kasa hakuri ta kira mr Jameel din ta tambayesa lafiya tana gama waya dashi text tayiwa Amatun Wanda ya shiga wayarta a lokacinda suka bar gurin da wayarta ke ajiye.

“Ankira Mr Jameel daga Greece Madame Abeeda ta Farka”

Shine text din data turawa Amatun tana Jin zuciyarta na Rasa itama murna zatayiwa TALBAs din kokuwa.
##MAMUH#

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at๐Ÿ‘‡
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

 

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at๐Ÿ‘‡
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button