Sponsored Links
Gidan Aunty Book 1Hausa Novels

Gidan Aunty Book 1 Page 7

Sponsored Links

Free page 7 🦋

Not edited

Zaune Suke su biyu cikin wata katuwar masarauta me shegen kyau da daukan hankali, duk Wanda yazo wuce wa sai ya duka musu tare da gaishesu, TAHEER ne ya fito cikin wata kofa sanye da wasu kaya na alfarma masu tsananin kyau ba karamun kyau yayi a cikinsu ba , hannunsa dauke da wani siririn maciji fari tass dashi, Daidai inda tahee take ya nufa, zaune take cikin  shigar alfarma na kayan sarauta , gefe da gefe masu yi mata fiffi tane ko wananne kawunanshi akasa, tanbarin macijin dake bayanta ya fito radau dashi, murmushi ta sakar masa ganin ya karaso inda take, shima murmushin ya sakar mata tare da Mika mata kyakkyawar farin macijin, mikewa tayi sosai tare da karban macijin, a daidai kan cinyarta ta dora macijin , shima macijin lumshe idanu yayi kamar mai jin bacci, kallan taheer tayi da mamaki dauke a fuskar ta,” kyauta ne na baki yau shekara 300 daidai da haihuwarki, zai debe miki kyewa “cewar taheer, tsananin farin cikine ya bayyana a kan fuskar tahee “ oh my god , nagode SIF” , jinjina mata kai kawai yayi , har ta bude baki zata sake magana sai wasu siraran hawaye suka zubomata”ka tuna lokacin da Nonna ta bani kyautar maciji kamar haka , amma sun kashe mun shi, sun kashe mun nonna , sun kashe mun susan”, shima girgiza mata kanshi ya shiga yi”Lola Raina yana baci duk lokacin da na turo wannan bakar ranar, kamar randa suka rabamu da nonna da susan Muma baza mu kyalesu ba,ga memaw nan ki rikeshi kamar yadda kika saba da susan, shima zaki soshi sosai”, yana gama fadar haka ya bar wajan , murmushin yake ta saki tana hadiye abunda ya tsaya mata a makogaro,kallan memaw din dake kan cin yarta tayi kafun ta kira sunan shi,”memaw”, bude idanuwansa yayi masu kalar baki tare da fara yawo a jikinta yana zagayeta , hakan ba karamin nishadi yasa taba, sai faman yawo suke , saida suka gaji dan kansu sannan suka tsaya har lokacin mucijin be dena yawo a jikinta ba.TAHEE!!TAHEE!!! A firgice ta farka daga baccin da take bakin ta dauke da adduar tashi daga bacci, kallan ta oumma tayi ganin yadda ta jike da zufa duk da kasan cewar akwai dan zafi zafin da ake ,”lapiyan ki kuwa”cewar oumma , saurin girgiza mata kai tahee tayi “ mafarki kawai nayi”, shafa kanta oumma tayi “ki kwantar da hankalinki mafarki ba gaskiya bane sannan ki dunga addua “nanma gyada mata kai kawai tayi,tunda umma ta fita a dakin kuma bata motsa ba mafarkin da tai na yi mata yawo aka“ NONNA,LOLA,SIF,SUSAN,MEMAW!? Sudin su wanene!? Maciji fa !?” Macijin da ta gani a mafarkine yashiga yawo a kwakwalwarta, amma sanin cewa mafarki ba gaskiya bane yasata share zancen tare da mikewa ganin oumma na kokarin shigowa dakin.

Bayan sallar azahar kamar yadda suka saba bayan sun kammala ayyukansu, zama sukai suna hira , lokaci zuwa lokaci tahee sai ta dako ta kalli taheer har yanxu mafarkin da tayi yana mata yawo a ka , duk lokacin da tayi tunanin mafarkin sai taji wani abu kamar ya tabata, yanxu ma dago da fuskar ta tayi tana kallan taheer, hararar ta yayi ganin tun dazu sai faman binsa da kallo take kamar wata me aljanu “na canza miki ka manni ne kike faman bina da kallo fisabilillah”,cewar taheer yana hararar ta , murmushin da yafuto da dimples dinta ta saki”gani nai ka kara kyau kamar wani balarabe “ ta karasa maganar tare da kashe masa ido daya,yanxun ma wani hararar ya mata “dadin abun bake kadai ce me kyau ba, da nice mace ma kyan da zanyi sai nasaka maza kuka”, dariya duk suka saki, oumma ta girgiza kanta “Allah ya shiryeku “.

âž°âž°âž°âž°âž°âž°
A gajiye ya dawo gidan bayan mutane uku da yayi wa aiki a asibiti da kansa ,sai faman lumshe ido yake , amma a zahiri bazaka taba tunanin hakan ba , zaka dau ka yanayinsa ne haka , shaf shaf yayi wanka cikin armani white colour, sosai kayan sukai masa kyau , a maimakon gyara gashin da ya saba yan tajeshi kawai yayi ya zubo masa har bayansa, sosai yayi kyau a cikin shigarsa, wayoyinsa kawai ya dauka tare da nufar part din ammi, yau kwata kwata be sata a idanunsa ba amma a zahiri fuskarsa a hade take ba ko alamun yasan wani abu me kama da murmushi. Yana shiga part din ya tarar da su kowa da Riga da Wando sai faman rawa suke, amrah ce me koya musu yadda zasuyi step din rawar,kwata kwata basusan da shigowarsa ba , hatta kamshin turarensa da sukaji basu kawo komai a ransuba, dan kusan kullum da kamshin a cikin falon ammi. Folding din hannunsa yayi a kirji yana bin ko wannansu da kallo daya bayan daya ransa ba karamun baci yayi ba musamman irin shigarsu ko dan kwali babu, be tankamusu ba duk da yadda kan nasa ke Sara masa , sexy eyes dinsa dasuka fara canza kala daga launin fari zuwa ja ya zubamusu, ihsan ce ta fito sanye da hijab a jikinta hannunta dauke da cup sai faman tiriri yake, kallan su amrah tayi tare da girgiza kanta , “kunsan dai yaya king ya hana wannan raye rayen ko, Allah Inya dawo sai na fadamasa dan bazaku jajamun ba”, hararar ta summy tayi “ sannu kasa yanxun ma zaki iyazuwa, matsoraciyar banza kamar da gasken iya zuwa zakiyi”, girgiza kai firdausi tayi “Aah sumy Wana irin taje ta fada kinsan dai wallahi yaya king ya Kamamu ba karamun wuya zamusha ba musan man dressing dinmu, kuma kusan bama sawa sai in bayanan “, siririn tsaki amrah taja “matsalata da ku kun fiya tsoro wallahi, kafun ya dawo ba mun gama ba , ai baze san munyi ba , yanxu fa zamu gama step din rawar kafin ammi ta dawo”. Dukkansu yanajin abunda suke fadi , duk abunda suke yana ganinsu kwata kwata basu hankalta dashi ba, amrah ce ta kunna musu wata wakar, ta juya kenan a cikin salon rawar idanuwanta suka sauka a kanshi, sosai ta firgita , bakinta ne ya fara rawa kwata kwata ta rasa me zatace, kallanta summy tayi “ke kuma lapiya jikinki yake rawa”, girgiza mata kai kawai amrah take tama kasa magana ganin irin kallan tsanan da yake jifanta dashi “watan cin ubankune yayi”a zahiri kuwa yana yadda yake ko a fuskarsa bazaka gane yanayinsa ba duk da tsananin gajiyar dayayi. Ganin sai faman kallan waje taya amrah take jikinta na rasa yasa duk juyawa zuwa direction din,”Innalillahi wa’inna’ilaihi rajiun, shikenan mun kade har gay yan mu gashi ammi batanan “kowa da abunda yake sakawa a zuciyarsa  , iya firgita sun firgita musamman ganin yadda launin idanunsa ya koma ,firdausi har da faduwa kasa tsabar rudewa,duk zubewa sukai akan gwiwowinsu ko waccen su sai matsar kwalla take,sosai suka rude musamman ganin irin kallan da yake bin kowannansu dashi, a hankali ya taka kafarsa tare da nufar sofa din dake left side dinsu , kwallar bakin ciki ihsan ta share dan duk su suka ja mata, ta ja musu Allah ya isa ba a dadi cikin zuciyarta, ba wacce ya kalla a cikin su sai ma wayar hannunsa da yake latsawa, cikin rawar murya me san sakin kuka ihsan tahe hannayanta “wallahi yaya zanyi bayani”, be Motsa da ga yanayin da yake ba balle su sa ran ze amsa mata, Kuka Kawai ihsan ta saki tana toshe bakinta karta kuma yin wani lefin, su amrah kuwa kowa sai faman zare ido yake fatansu Allah yasa be ji abunda suke tattaunawa. Kamar daga sama sukaji saukar maganarsa “ coffee “ da Sauri amrah ta tashi duk da acikin yanayin tsoran da take, dan iskan kallan da yayi mata ne yasa ba shiri ta koma tana zare idanu, ganin hakan yasa atsorace ihsan ta mike ganin be mata magana ba yasa ta nufar kitchen din cikin sauri, sai faman ajiyar zuciya take , duk tabi ta rikice ta rasa yadda zata hada masa coffee din , cikin sauri Sauri ta dakko wayanta dake aljihun Wandanta. Yanda ake yin coffee din tayi searching, cikin rudewa ta gama fito da abunda zata hada masa coffee din jikinta sai faman rawa yake .

Cikin dan karamin tray ta fito da coffee din kusan na uku kenan tanayi kafun tayi wannan din, ganin su amrah na frog jump ne yasa kafarta rawa idanuwanta harsun cika da kwalla, coffee din ta ajiye masa tana komarin fara frog jump din ne abazata taji saukar muryarsa “ Leave” , nannauyar ajiyar zuciya ta dauke da harshi saida yajita “ nagode yaya king, na….” Hannunsa kawai ya daga mata ,cikin sauri ta bar wajan cikin gudu gudu, tunda Allah ya kubutar da ita.

Sosai suke frog jump ko wacce fuskarta jaga jaga da majina , ga hawayen da suke yi, da zaran sunji kuka zai kwace musu zasuyi saurin toshe bakinsu gudun wani punishment’s din. Duk fadin falon ammi haka zuke zagayeshi ko wacce ta fita daga hayyacinta ba damar yin kuka a fili.

Yana zaune sai faman operating wayar hannunsa yake se yanxune ya dauki coffe din da aka hada masa” kurba daya yayi amsa ya ajjesa. “Yaya dan girman Allah da manzan sa kayi hakuri”firdausi ce tayi maganar hawaye sai bin fuskarta yake, lumshe gajiyayyun idanuwansa yayi, tariga ta hadasa da abunda baze iya musu akai ba, “God save you”yafada cikin zuciyarsa “Leave “, baki summy ta bude Baki da niyar yin magana amma ya dakatar dasu ta hanyar dafe kansa , sun gane me yake nufi hakan yasa a guje ko waccen su ta bar part din Daidai lokacin da ammi ke shigowa, da kallo tabisu ganin babu Wanda ya kula da ita kafun ta karasa shiga falon.

âž°âž°âž°âž°âž°âž°
Karfe uku na dare ko ina yayi shiru kasan cewar ko wana bawa yana wutawa a irin wannan lokacin, wani macijine fari tas dashi ya fito cikin wani rani tare da kwanciya bayan tahee,cikin mafarkin da take tafara lalube lalube har hannun ta ya Kai……

Manage plx🥹

đź’–THE TALENT TROUPE WRITERS đź’–

DUK KARFIN IZZATA (Star lady)

GIDAN AUNTY( mss Lee)

TAFITA ZAKKA ( maman sayyid )

JINI DAYA ( mrs bbk )

SARKI SAMEER (xeenat love )
‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/GOZ7a2miBjZ4vUjRXdRdrA

đź’–GIDAN AUNTYđź’–
( A heart touching love story)

By mss Lee đź’–

đź’–THE TALENT TROUPE WRITERS đź’–

PAID BOOK

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button