Sponsored Links
Gidan Aunty Book 1Hausa Novels

Gidan Aunty Book 1 Page 21

Sponsored Links

BOOK 1

Free page 21 🦋

Ba kowa bace ta shigo dakin face amrah dake a zabure idanuwanta duk sun kunbura, a yadda ta gansu ne yasata fashewa da kuka tare da barin dakin cikin sauri, da Sauri ya bangaje tahee da batasan meke faruwa ba sabida yadda kafarta ke mata ciwo a kasa  , har ya daga hannu da niyar tsinka mata mari sai kuma ya dungule hannu tare da rintse idanuwansa da suka kada sukai ja, kallo daya kawai yayi mata tare da ficewa a dakin ransa a bace , ko da ya fito falon be tarar da ammi ba hakan ya bashi damar fita daga part din gaba daya, ko part din ummey be karasa ba ya bar gidan .

****Da gudu amrah ta karasa part din aunty, bakowa a falon tai saurin shigewa daki, kuka ta fashe dashi sosai , kome ta gani sai tayi bal dashi, a haukace take fasa abunda taci karo dashi,”taheera “shine sunan da take nanatawa tana hawaye “wallahi sai na kashe ki,sai naga bayanki, shegiya tsinanniya ,wacece ke da zaki rungumeshi har dayi mishi kiss, wallahi sai na la’antaki bazan kara fadawa kowa bama da kaina zan kashe ki har lahira sannan na kashe banza”, bata karasa zancan nata ba aka tsitstsinka mata mari dama da hagu, a tsorace ta dago da idanuwanta a tunaninta aunty ce ta mare ta ganin ba kowa a dakin  ta fara zazzare idanuwa, mafarkan da ta dungayi jiya da daddare ne ya fado mata a zuciya ,da kyar take iya hadiye abunda ke makoshinta, taku ta fara a hankali da niyar barin dakin,talewar da kafarta tayi ne yasa ba shiri ta bige kafar take da sakin azababban kuka, wani saukan marin da ta kuma jine yasa ba shiri ta mike tsaye ga azaba da kafarta kemata kamar wacce tayi targade.”ke “ taji wata razananniyar murya ta kirata,cikin rawar murya ta soma amsawa “naa…am, dan.. Allah kuyi… hakuri innayi muku lefi…”bata karasa maganar taba taji saukar bulala a bayanta,ihu ta soma “nashiga ukuna na lalace,dan Allah kuyi hakuri na tuba bazan sake ba “, kamar wayanda ake zugawa haka suka shiga laftarta saida suka ga ta daku sannan aka daka mata tsawa cikin muryar mata ,”ke, mike tsaye”azabure amrah ta mike fuskarta duk ta baci da majina ga kukan da Tasha “rufe mana baki”aka kara daka mata tsawa, hannayenta biyu tai saurin daurawa abakin mata sai faman waige waige take ga hawayen da ke zuba a fuskarta,”rawa zaki mana yanxun nan , duk rawar da muka saki,kuka kuskura kika fadi zaki gane kuranki, kinajina”, da sauri ta shiga daga kai har ynxu hannunta na kulle a bakinta,dariya muryoyin mace da na mijin suka saka kafun lokaci daya wajan yayi shiru,”maza yi mana rawar dan biri”ana gama fada mata haka aka jefo mata ayaba kuda d’aya, da sauri ta dauki ayabar ta fara tsalle kamar yadda dan biri keyi, fuskarta duk ta baci da hawaye ga guntun gashin ta da ya barbaje sai ta dawo kamar dan birin kuwa, tanayi tana kwantawa alokaci daya kuma tana kuka, sosai taji muryoyin nan guda biyu suna dariya kafin ta karajin wani sautin,”yi mana yadda mage take kuka”, kara fashewa da kuka amrah tayi kafun ta fara “meowwww meowww meowwww moewwww” ta nayi tana share fuskarta da ta baci, sosai suka wahalar da ita, iya rawan dabbobin kam har Wanda bata sansuva tayi rawarsu,ga kafarta dake tsananin yi mata ciwo kamar wacce ta goce a kashi.

********** kwance take kan lafiyanyan gadon dakin nata, hannu daya wayane a ciki yayin da Dayan hannun take rike da apple, waya take sai faman murmushi take saki ita kadai, turo kofar dakin da akai ne yasata dagowa,wacce ta ganine yasata mikewa zaune tare da kashe wayar, Momy kice kuma yau adakina, karasa shigowa wacce aka kira da momy tayi kafun ta samu waje ta zauna daga bakin gadon, “ko na komane”ta fada tana zubawa firdausi idanuwa, dan jinjina mata kai firdausi tayi tare da dage kafadun ta kadan,”akan wana dalili zan hanaki shigowa momy, naga yanxu bakya shigowane tun bayan tafiyar yaya haroon,ta bile baki kawai momy tayi kafun su canza hirar tasu zuwa wata,kallan ta firdausi tayi “amma momy ba kya tunanin waccan yarinyar da Gangan ta bige dan taga mutanan gidan suka tarai rayarta, kalli fa wai yau yaya king ne ya taba wata, ni ko hannunsa aka ce ya dora akan wata ai bazan yadda ba balantana wayancan shashashan da suke wahalar dakansu”,murmushi kawai momyn ta saki ba tare da tace komai ba dan Akan idanta amrah ta tura taheen, ganin momyn tata bata biye mata ba yasa share zancen suka fara zancan dan uwanta.

💖💖💖💖💖

Tunda ya bar gidan a guje zaki ya fara tuka Motan ganin yadda lokaci daya king din ya canza masa kamar wani zaki,a dake ya furta “my house “ya karasa maganar tasa tare lumshe idanuwansa, tafiya akai sosai me dan ta Zara daga banana island kafun suzo kofar wani hadadden building me shegen kyau, tundaga wajan gidan da glass akayi shi komai na cikin sa glass ne , cikin sauri sojojin dake bakin gate din suka wangale baban gate ganin me gayyane da kanshi ya zo, a Daidai parking lot zaki yayi parking inda sauran manyan motocin suke, yau be jira an bude mishi kofarba, yana fito wa ciki ya shiga cikin sassarfa, kofar dake kasa kawai ya bude ya shiga, sosai dakin da yashiga ya hadu, kayataccen falo ne a wajan babban gaske da yafi Wanda yashigo haduwa, Komai na cikinsa whites ne tunda ga kan labulayen dakin har kan lallausan carfet din dake shinfide fari tass dashi, ko ina nawajan tashin kamshi yake kamar ana anfani da shi kullum, kan daya daga cikin white sofa din ya zauna ko takalman kafarsa be cire ba, idanuwansa ya lumshe a hankali ,jijiyoyin kansa ne suka mike sosai , kyakkyawar farar fuskarsa tayi ja sosai, kara rintse idanuwansa yayi da karfin gaske ganin har yanxu yanajin tsayayyun breast dinta a jikinsa, sosai gashin jikinsa ya mike ,a zamube ya fara bal da duk abunda yaci karo dashi, zafi yake ji sosai a cikin Jikinsa,sosai gashin jikinsa ya kara tashi ji yake kamar tana jikin sa haryanzu, adduar ya fara cikin zuciyarsa, tsawan lokaci kafun wata nutsuwa ta fara saukar masa, sosai ya ke ajiyar zuciya ganin lokaci daya azababban zafin dake ratsashi ya tafi sai ma sanyi da yake danji a haka wani daddadan bacci ya dauke sa.

*****har yanxu tana zaune a kasa tun lokacin da ya tunku data, kafarta hannunta rike da kafar tata, shigowar da akai ne yasata saurin dago da kanta?ganin su dada ne yasata sakin ajiyar zuciya, da sauri dada ta karaso inda take “me nake gani haka , tahura ya naganki a kasa duk zafin ciwon ne”, rasa me zatace mata tayi kawai sai ta gyada mata kai alamar a’ah, murmushi ta sakar mata a hankali kafun ta gaishe ta “ina kwana dada” girgiza kai dada tashiga yi “Allah sarki tahura,lapiya ta Lou, jiya da kyar nayi bacci sabida halin da kika shiga “wani murmushin ta kara saki kafun ta gaishe dasu abeey, shima cikin kulawa ya amsa mata tare da tanbayarta ya jikinta, sosai ta dan saki dasu Bayan ta gaisa da su uncle musaddiq da suka shigo daga baya, ganin sauran yan gidan ma suna zuwa yasa duk suka koma falon ammi,sosai kafarta tayi sauki dan tana dan takawa kadan kadan , afalon suka cigaba da hira har ummey ta shigo part din yau batare da zoya Suke ba sabida makarantar da tafi,a haka kowa na gidan ya shigo sabanin amrah , wunin ranar a part din ammi sukayi shi sosai suka nuna mata kulawa musamman ummey dake gefenta.

🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧
🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧🫧

BUNKURE

Da sassafe kaka ta bawa ta tashi yau kai tsaye dakin su oumma ta nufa , bubbuga kofar dakin ta shiga yi, jin shiru ba abude ba yasata kara bubbugawa “maryama kina ji ina kiranki shine zakimun uwarshegu ko, zaki nunamun ba’kin halin naku kenan ko, bazaki fito bane kina jina”, ganin yadda take faman buga kofar dakin su oumma ne yasa mutanan gidan fara taruwa,Dije dake labe tun lokacin da kaka tabawa ta fito yasata karasowa wajan,kallan kaka tabawa tayi tana kumshe dariyar dake cint kafun ta soma magana”inna ai maryama yanxu ta zama abinda ta zama “kallanta kaka tabawa tayi kamar ya bangane ba,”oh ai inna komai a filine , jiya agaban idanunmu tafita daga gidan nan , har kokarin zagin mu tai da muka yi kokarin tsayar da ita” sosai kaka taba ta kalleta “kina nufin tana yawan dare kenan”, tabe baki Dije tayi”ai kowa nanan sheda ne inna ki tanbayesu”, nan da nan yan gidan kowa ya fara tashi gulmar,babu me fadar alkairi akan oumma su taheer ganin yadda tafita tun jiya bata dawo ba, girgiza kai kawai kaka tabawa tayi rai a bace ta bar wajan” za tazo ta sameni ne duk gidan karuwanci da take zuwa”, da dad d’aya kowa ya fara watse wa ganin hakan yasa cikin sauri Dije ta shige dakin harda taka rawa, kallan ta bintalo tayi,”ya naga sai faman washe baki kike kamar wata tababbiya”a maimakon ta tsawa tar mata akan kalaman ta sai ta kuma kyalkyalewa da dariya, nan da nan ta kwashe duk abunda ya faru ta sanar wa bintalo, itama bintalon sosai tayi farinciki ganin burinta na Auran babban mutum zai cika ,wani shegen murmushi ta saki a zuciyar ta kuwa fadi take “lallai ma Dije baki da hankali,ai wallahi kafin nayi Auran nan sai na ci duniyata da tsinke yanda na fara jin dadin abinnan da boka Yayi mun ,wallahi yanxu na fara anjima ma sai na koma wajan sa dan ya mallake mun duk Wanda yace zai takuramun, ciki kuwa har dake dan ke kika koyamun”,duk wannan maganganun nata cikin zuciyar ta take kafun lokaci daya ta saki wata yar iskar dariya da ita kadai ta san ma’anarta.

Comment and share

LITTAFIN GIDAN AUNTY NA KUDINE AKAN 300 kacal
zaku biya kudin ku ta wannan asusun 7041879581 palm pay ayshatou galadima , sai a turo shaidar biya ta wannan number 07041879581.

Saura few pages na gama sakin free pages dina .

MASU COMMENT INA GODIYA SOSAI DA SOSAI , I HEART ❤️ YOU ALL ✍️.

MSS LEE 💖✍️
‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/GOZ7a2miBjZ4vUjRXdRdrA

💖💖GIDAN AUNTY 💖💖
(a heart touching love story)

Story & written
By
Mss Lee 💖

PAID BOOK

NA KUSA KAMMALA FREE PAGES DINA

Mesan KARANTA GIDAN AUNTY DAGA FARKO ZUWA KARSHE ZAI IYA BIYAN KUDINSA TA WANNAN ASUSUN 7041879581 palm pay ayshatou galadima sai a turo shaidar biya ta wanna number

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button