Sponsored Links
Arubuce Ta Ke Hausa NovelHausa Novels

Arubuce Ta Ke 63

Sponsored Links

Page 63

Koda ta hado kayan abincin ta dawo bata sameshi a falon ba,amma taga qofar dakinsa a bude,da alama yana ciki,tadan bata fusja kadan,itafa batason haduwarsu sam,ya gama kalle mata jiki ta yaya zata iya fuskantarsa,amma dai babu yadda ta iya,haka ta taka zuwa dakin nasa roqe da tray din data shiryo komai akai.

Sanda tayi sallama ta shiga ya gama fidda kayan jikinta,daga shi sai pant na maza iya cinya,a yadda ta ganshi tayi masifar tsorata,don bata taba ganinsa koda singlet ba,hakanan tsahon rayuwarta bata taba ganin wani namiji haka ba sai a kansa,saura kadan ta zubda kayan hannunta,taja baya da sauri tana neman qofar fita amma sai ya rigata isa wajen,yasa hannu ya maida qofar ya rufe,ta bude baki ya tabbatar ihu ko kuka zata masa,sai yasa hannunsa saman bakinta ya rufe da kyau,sannan yasa daya hannun ya karbe tray din daketa tangal tangal a hannunta zai kife ya aje a qasa.

Dab da ita ya matsa,har jikinsa yana dan gogar nata,sai taji kamar numfashinta zaiyu qaura yabar gangar jikinta,manyan idanunta gaba daya sun fito waje kamar zasu fado.

Magana yakeson mata amma ta maqale masa a maqoshi,qamshinta dake tashi daga jikinta keson rikita masa lissafi,idanunta masu haske da ruwan hawaye ya cikasu suka soma fusgarsa,yayi ta maza cikin taushi da raunin murya yace

“Keep silent please….. hajiya tana ciki fa,so kike tace na miki wani abu?,zata batamin rai idan haka ya faru” ya qarashe zancan a narke kamar yaron dake tsoron duka daga mamansa.

Sake sanya idanunsa yayi sosai cikin nata,itama shi take kallo,wasu irin idanuwa da suka dinga tilasta saukar nutsuwa a jikinta,a hankali yaci gaba da aike mata da wani saqo ta cikin idanuwansa,har hawayenta suka fara bacewa,nutsuwarta ta fara daidaita,kunya ta maue gurbin tsoronta,sai ya sauke hannunsa a hankali daga kan bakinta daya gaji da motsawa yayi laqwas,yaja da baya a hankali ya dauki babbaj towel ya rufe jikinsa sannan ya doshi bandaki,doke sai yayi da gaske,ya cire tsoronsa daga ranta muddin yanason su zauna zama na auratayya mai dadi,sai ya sake kawo kusanci sosai a tsakaninsu,sai ya zama komai nata ya kusanta kansa da rayuwarta,tana da kima da darajar da yake jin dole ya sama mata gurbi a rayuwarsa,saboda ita din kamar isharar mahaifiyarsa abar soyuwarsa ce,ya zama dole ya kimantata ko don farincikin mahaifiyar tasa.

“Ka rufe qofar fa” ta fada bayan ta hadiye wani abu muryarta tana dan rawa,har ya sanya kai a toilet din sai ya fasa ya waiwayo

“Ki jira na fito daga wanka tukunna” sai ya shige.

Jikinta babu kuzari ko kadan ta sulale ta zauna a wajen,wani abu ya fara mata yawo cikin kwanyarta gangar jiki da kuma zuciyarta,a yau daya kusanta kanshi da ita bawai tsoro kadai taji ba,kunya nauyi da kuma wani irin yanayi da batasanshi ya mamayeta,saidai akwai wani irin tsoro nasa danqare a zuciyarta,hakanan yana mata mugun kwarjini mara misali.

Yana goge ruwan jikinsa yadan kalleta,ta takure waje daya,ta kuma qi yarda su hada idanu,ya saki boyayyen miskilin murmushi,yasan me yake damunta,ya matsa gaban mudubi ya fara shafa mai

“Kina sane kenan kika shigomin daki ko?,kin rama nima kin ganni babu kaya” yayi maganar yana kallonta ta cikin mudubin,kai ta daga da sauri,suna hada ido ta mudubin kuma saita maida kan nata ta fara qananun hawaye harda rantsuwa ita batasan ya cire kayansa ba,ita bata kalleshi ba,dariya kamar yayi me,wanann wautar tata da quruciyarta wani bangare ne dake sanyashi nishadi,ya gama shirinsa cikin wata armless fara qal din shirt,sai wando daya tsaya masa iya qaurinsa

“Ai shikenan……”

“Budemin to zan tafi” ta katsi numfashinsa

“To zubamin abincin naci tukunna” da sauri ta zuba masa komai ya zauna zai fara ci sai ya kalleta

“Zauna muci” kai ta gyada

“Na qoshi”

“Bakison tafiya kenan?” Kai ta kada da sauri,saita matso ta sanya hannu suka fara ci.

Suna ci yana kallon idanunta,saidai ko kadan taqi yarda ita din ta kalleshi,yadda cin abincin yayi masa dadi saboda ya saba ci dasu mimi a gida nan kuwa saishi daya…..haka abincin ma yayi masa dadi

“I can’t believe ke kikayi girkin nan” abinda take son ji dama taji ya yaba kenan,har batasan sanda ta kalleshi ba tana dan murmushi

“Allah nice nayi,yankan kubewa kawai muneera ta tayani”

“Wow…wow,,nan gaba ina da great cook kenan,na shirya cin abinci da kyau” murmushi ya subuce mata,tayi qasa da kanta,tana jin dadi sosai har cikin ranta.

Ganin ya gama cin abincin yana shirin sake zama sai tace mishi

“Kace idan ka gama zaka rakani fa”

“Oh yeah,muje to” ya furta yana sanya bedroom slippers dinshi,yana gaba tana binsa a baya.

Murda qofar kadan yayi,sai ya waiwayo yana dubanta da alamun damuwa kan fuskarsa

“Ayyah….sun riga sun kulle qofar” kallon qofar tayi sannan ta kalleshi

“Wayyo Allah na”

“Ko ayi knocking ne?” Ya fada da sigar jarrabata,taci kuwa jarrabawar da karon farko.ta qara mata kima da daraja mai dimbin yawa a idanunsa,don kai ta girgiza

“A’ah,ummu ta hana,tace ba’a tashin babba idan yana bacci,hajiya ta gaji tun dazu na gani…..amma saidai…..” Sai kuma tayi shuru tana kallonsa.

Wani qawataccen murmushi ya saki,idanunsa cikin nata yana jin kamar suna narkewa ne zuwa sassan jikinsa

“Saidai me?”

“Saidai na kwana a falo?” Kai ya girgixa

“Qwarai kuwa” ya fadi sounding seriously,sannan ya fada takawa yana nufar qofar dakinsa,da hanzari ta taka ta bishi,harda riqo masa hannu ba tare data sani ba

“Da gaske tafiya zakayi ka barni a nan?” Kai ya kada,yanata qoqarin danne dariyarsa

“Yes,da ina zaki bini?” Marairaice masa tayi,harta fara guzurin hawaye

“Please mana,kaji tausayina” badon yayi da gaske ba wannan karon dariyar saita fito

“Oh…. okay,me kikeso yanzu?”

“Ka barni na kwana a dakinka,nan din tsoro nakeji Allah” ido yq zaro kamar gaske

“Dakina kuma?”

“Eh” yadanyi shuru kamar mai tunani

“Matsalar ni gaskiya ba za’a hanani kwanciya a gadona ba,kuma idan muka kwanta gado daya ina da juye juye,zan.iya danneki ban sani ba,saidai ki tasheni idan kikaji haka saina dagaki,kin yarda?” Kai ta gyada da sauri,saboda kukan mage data fara jiyowa

“Fine,muje” tuni tayi gaba suka jera kafada dashi, dariyar kamar yayi ke haka ta dinga cinsa,yana sane yayi mata wannan hikimar,banda haka tubura zatayi masa.

Ta rigashi kwanciya amma idanunta biyu,yana kallonta ta ninka duvet dinsa guda daya ta raba gadon dashi,taja daya ta lulluba, murmushi yayi qasa qasa

“Zanyi maganinki yau kam” ya fadi yana maida dubansa ga takardun da yake dubawa,sai daya gama komai,sannan ya haye gadon,ya jawo wayarsa ya kunna sound na kukan mage,ya saitashi wajen kanta ya koma ya kwanta abinsa.

A hankali kukan magen ya fara ratsata daga baccin daya dauketa,dama kuma ba wani nisa can sosai baccin yayi ba,rudewa tayi gaba daya saboda jin kukan a kusa da ita sosai,batasan sanda tayi cilli da katangar data gina a tsakaninsu ba, hankali kwance yaji ta shige jikinsa hadi da qanqameshi,wanan lallausan jikin nata ma’abocin qamshi ya nutse cikin faffadan qirjinsa,sai ya saki wani tattausan murmushi,cikin sanyi ya kamota zuwa jikinsa sosai ya mata kyakkyawar runguma da har sai da zuciyarsa ta gamsu da hakan,ya dora hannunsa a gadon bayanta yana dan bubbugawa

“Shshhhhhhh…..,zata tafi fa…..yanzu” maganar tasa ta rarrabe saboda yadda ta raba tsakanin cinyoyinsa da qafafunta tana sake shige masa kamar zata koma jikinsa

“Tana qasan gadon,ka koreta uncle” cikin tsoro take fadar haka,tuni ta soma rikitashi,sai ya dora bakinsa saitin kunnenta

“It will be alright”furucin da ya sanya jikinta wani zubawa,abinda bata taba jiba tsahon rayuwarta,yanayin da yasa ta sake maqale masa da kyau,ta kuma sanya fitar numfashin sa sake jirkita,ya nutsa hannunsa gadon bayanta ya hade da ainihin fatar jikinta mai santsi a maimakon rigar dake jirkitanta,taji hakan har cikin qashi da bargonta,to amma kuma tsoro ya hanata motsawa,ji yayi kamar kada ya kashe kukan,amma yadda yaga ta tsorata dole badon yaso ba ya zura hannunsa ya kashe wayar gaba dayanta.

A hankali a hankali ya fara fitar da numfashi da gudu gudu,tun tana tunanin ba komai bane har hankalinta ya kawo kan canzawar da taji yayi,hakanan bugun zuciyarsa sosai yake shiga zuwa ga kunnuwanta dake kwance saman qirjinsa dake shimfide da lallausar gargasa,a hankali ya daga kanta tana duban fuskarsa

“Uncle…..baka da lafiya?” Murmushi ya qwace masa,gumi na saukowa ta saman goshinsa kadan kadan

“Am fine,kwanta kiyi baccinki” ya qarashe maganar yana cije labbansa,saboda yadda mararsa ta murda masa

“Gumi fa kake uncle”

“I know,na sani”

“Ka bari na taso hajiya”

“Aah”

“To akwai magani na dauko maka?”

“Kece maganin” ya fada muryarsa tana rawa,sam bata fahimci me yake nufi ba,don batasan ainihin abinda yake damunsa ba

“Ni kuma uncle?”
“Yes,but…..ki kwanta kawai nace” ya fada da dan kaushi,saboda ciwon da cikinsa ya fara,jiki a sanyaye ta zame kanta daga jikinsa zata kwanta gefe,sai yasa hannunsa ya tarota

“No,don’t leave me,stay here,i will be okay” gaba daya sai taji bata da kuzarin musawa,ba wani sauran tsoro tattare da ita,tana jin sanda ya matso da ita zuwa jikinsa sosai,sai taji tausayinsa ya kamata,tana da saurin kuka da karyewar zuciya akan mara lafiya,don haka tasa dukka tafukan hannuwanta biyu a kuncinsa hagu da dama tana masa sannu da muryarta can qasa,abun sai ya zame masa kamar fami,don haka yasa hannayensa ya cire hannun nata,ya kuma jawota jikin nasa still yana cewa

“Kiyi bacci,good night”.[3/14, 7:17 PM] +234 816 133 8078: *H U G U M A*

*_A RUBUCE TAKE_*
(K’addarata)
*Arewabooks:Huguma*

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button