Sponsored Links
Gidan Aunty Book 1Hausa Novels

Gidan Aunty Book 1 Page 6

Sponsored Links

BOOK 1📕

FREE PAGE 6

Yau ma da asuba suka tashi, bayan sun idar da sallah aikin gidan suka fara , TAHEER da TAHEERA suka debo ruwa kafin suyi wanke wanke, yau ko buga kofarsu da aka saba yi ba ayi ba, gidan tsit kamar ba kowa a ciki, suna kammala aikin nasu daki suka koma, wata tsohuwar 200 oumma ta  basu “nasan kunajin yunwa, kuje Wajan abu me kosai kuce ta baku kosai”, Godiya sukai mata tare da nufar kofar da zata sadasu da waje , a hanya suka hadu da Dije zata shiga ban daki , tana ganin su tai saurin shigewa bayi tana tsine musu, basu bi ta kansu ba dan yunwa suke ji . Basu dadeba suka dawo, ganin oumma na karatun azkhar dinta yasa basu kuma cewa komai ba har saida ta kammala . Kosan tahee ta Mika mata tare da dakko musu wani plate din robber , juye kosan sukai a ciki tare da faracin abinsu, bayan sun kammala ruwa suka sha tare da yin hamdala, sai lokacin suka fara yar hirarsu, musamman taheer da taheera , oumma na sa baki lokaci zuwa lokaci. “Oumma” cewar tahee, amsa mata oumma tayi da “uhm” ko muma kosannan zamu kwadayi ko za a siya,Jim kadan oumma tayi kamar ne tunani abinda zatace sai kuma ta kalli tahee” banki ta taki ba auta, amma kinsani ko mun fara ba barinmu zasuyi muyi ba, kinmanta abunda ya faru kwanaki”, turo baki tahee tayi jin oumma tace mata auta” wai TAHEER ne fa auta amma kullum ni kike cewa auta”, kallan up and done TAHEER yayi mata “shikenan zo mu kwada tsaho , duk Wanda ya fi tsaho a cikin mu shine babba”, dariya duk suka saki dan sun sa da biyu ya fada mata wato dan ya fita tsaho. Daga waje suna jin yadda yan gidan ke musu habaici da zagin su musamman Dije da yarta.

Da azahar ma haka suka sha kwaki da gyada cikin raha da kaunar junansu, bayan sallar isha’ine suka roki oumma zuwa dan dali, sai da oumma ta ja musu kunne sosai sannan ta barsu sukaje. Suna tafiya suna hirarsu Daidai sunxo shiga dandali tahee taji abu ya soketa, wajan ta taba Daidai inda shatin maciji ya fito a ciki dan kadan, TAHEER ne ya ankara da zanan macijin yayi sauri ya sa hannunsa a wajan, kamar kiftawar ido shatin ya bace bat. Hararar ta TAHEER yayi “me yasa ba kya kula , yanxu da wani ne yaga tanbarin macijin nan bani ba me kike tunani”, girgiza masa kai tahee tayi “bansan ya Akai ya fito ba sabida naji kamar wani abu ya tsirenii a wajan, ina tunanin akwia abunda yake faruwa a masarauta, dole muje mugani “daidai taheer ya bude baki da niyar yin magana yaji an bangajesu tahee har da faduwa kasa, kashi tayi a fusace da niyar bin bayansu amma TAHEER yayi azaman rike hannunta,” kasake ni, Raina ya baci”, kin sakinta taheer yayi sai ma wani abu me kama da na fito da ya dakko ya fara busawa , cikin kankanin lokaci tahee ta fara sauke  ajiyar zuciya. “ ki dinga sassaita fushinki , banaso ranki yana baci , anjima zamuje daula”, gyada masa kai tahee tayi suka nufi wajan dandalin. Suna shiga aka fara gulmarsu ana zaginsu , iya kuluwa tahee ta kulu ganin yadda ake nunasu ana dariya, saurin damke mata hannu TAHEER yayi tare da girgiza mata kai suka kama hanyar komawa, jin muryar bintalo sukayi tana fadin “yanxu ma haka ana tunanin ba kawun mune ubansu ba , shiyasa ma ake nuna musu hantara ,kun manta uwarsu ba yar kasar nan bace kowa dai yasan halin buzaye da bun malamai “, saurin fusge hannunta tahee tayi, da nufar inda bintalo take , saukar marin da bintalo taji a fuskar tane yasa ta wuntsulo wa , tahee bata kyaletaba, ta kara tsinka mata wani marin, duk Wanda yayi kokarin binta sai tahee ta tsinka masa mari, taheer nagefe yana kallansu , sai faman sakin murmushin Mugunta yake, ganin tahee ta shako wuyan buntalo ne yasa shi nufar inda suke , yana zuwa da niyar rabasu shima ya samu nashi rabon dukan, kwata kwata tahee idanuwanta sun kulle, kara nufar su taheer yayi da niyar rabasu yanxun ma wani raban dukan ya samu, Daidai wajan kafadun ta ya samu ya daka da karfi, ko motsi bata karaba ta zube a kasa , bintalo ma sai faman zare ido take dan ba karamun shaka tahee tayi mata ba, duk kawayen ta da suka labe suka fito sai faman zugata suke akan abunda tahee tayi mata, ba Wanda ta kula a cikinsu sai kwallar bakin ciki da take, hanyar gida ta nufa kawayenta na taka mata baya , shima TAHEER kama tahee yayi suka nufi hanyar gidan.

A soron gidan suka samu mutane shake a wajan, ga bintalo a gefe sai faman kuka take , kowa maida kallansa yayi kan su taheer dake shigowa, “muna fukan Allah har kun dawo,kenan toh wallahi bazata sabuba me yata tayimuku da zakuyi mata irin wannan bugun, ita uwar taku da yake tasan me kukai shiyasa ta makale a daki taki fitowa “cewar dije, kallanta TAHEER yayi kamar ma besan me ya faruba “aunty dije lapiya, ko Ance miki wani abune”, duk zuba masa ido suke bintalo kuwa tun bayan shigowarsu taji kamar abu ya shigar mata ido.hararar sa wata daga cikin kawayan Dije tayi” karya za ai maka kenan “, kallan ta TAHEER yayi sosai “ni bansan akan abinda kuke magana ba , in kuma akwai wani abun ai sai ta fada muji “,kallan bintalo dije tayi” maimaita abunda yayi miki ai ba karfin mu suka fi ba, ina daga  masu kafane”,narnar bintalo tayi”inna daman ba abunda sukai mun, nice bansani ba na bangajesu suka fadi”, salati mutanan gidan suka fara , yayin da kawayen dijen suka fara binsu da kallo. Wani dan iskan murmushi TAHEER ya saki tare da nufar dakinsu da tahee duk wannan abun da ke faru oumma na daki na bacci batasan me ke faruwa va.

➰➰➰➰➰➰➰➰➰➰
Cikin wani hadaddan company motocinnan suka tsaya, daga saman company din ansa A_N_business enterprise’s, yanda aka rubuta sunan company din shi kansa abun kallo ne , komai na cikin company din da glass akayishi amma baka ganin komai da ke ciki saida su mutanan ciki su ganka. A Daidai wani parking space motocin sukai parking, zaki ne ya bode masa kofa, har yanxu lumshash shun idanuwansa a kulle suke, sai yanxu ne ya bude su a hankali, kafafuwansa ya fara zurowa kafun ya fito daga cikin motar gabaki d’aya,tunda ya shiga company’n ma’aikata ke ta faman miko gaisuwa,da hannu kawai ya ke amsawa bata re da yace komai ba Wanda sun Riga da sun saba da yanayin amsa gaisuwar sa . Daga inda zai hau lifter duk sauran bodyguard din suka tsaya ,shida zaki ne kawai a lifter din , Kai tsaye floor 4 dake last floor suka nufa,baka jin ko wace irin hayaniya a wajan komai tsit kakeji sai kamshin da sanyin ac dake tashi ta ko ina. Wata kofa zaki ya bude masa daga samanta an rubuta C.E.O TAHNOON cikin wani stylish way , ha daddan office ne ya bayyana me shegen kyau da tsaruwa iya kyau office din ya hadu kamar ba a shigarsa amma ko ina tsaf tsaf yake , daga cikin office din akwai wasu dan ubansu set din kujeru masu shegen kyau daga kan table din akwia wani dan karamin hotan samari su biyu masu dauke da harafin M&T,a kan daya daga cikin set din kujerun ya zauna, wasu briefcase zaki ya miko masa, be amsa ba illa “seat “ kawai daya ce cikin cool voice dinsa, cikin girmamawa zaki ya amsa da “ thank you boss” kafun ya samu waje ya zauna,rikitattun idanuwansa ya Dora kan zaki kafun a hankali ya furta “explain”. Gyara zaman shi sosai zaki yayi tare da soma bayani” boss duk wata sai an furar da makudan kudi daga a susun bankin company dinnan, batare da cikakken dalili ko sa hannu ba ,a cikin shekarar nan an rasa makudan kudade masu yawan gaske tacikin wani asusun banki da haryanxu ba a ganoshi ba”.sannan ya cigaba da yi Mishi bayanin abubuwan da ya shafi company din, kamar ba sai amsa ba tsahon munyi biyu kafin ya bude bakinsa” ina bukatar bayani game da futar kudinnan, sannan ta Wana bank ake fitar dasu”, jinjina masa kai zaki yayi “okay sir “ tare da nu far hanyar fita, “called zuhra” yaji saukar muryarsa, nan ma “okay “ kawai zaki yace masa. Dafe goshinsa yayi da ya fara sara masa sabida doguwar maganar da yayi, ko mintuna biyu cikakku ba ai ba akai knocking din kofar, shiru ba a amsa ba sanna ba a kara knocking ba kusan tsawan 3 minutes , kafun ya bude baki “come in”. Da Sauri aka bude kofar tare da shigowa ciki, tunda ta shigo ta zuba masa manyan ida nuwansa,be dago ba amma yaji yanda take binshi da kallo, ya tsani kallo amma duk da hakan be matsa daga inda yake ba , bata Ankara ba sai jin dakakkiyar muryarsa tayi “get out”, sosai jikin ta ya fara rawa  sam hankali da nutsuwarta ya tafi akallon irin kyawun da yayi kamar kullum kara masa kyau ake , saukar marin da taji a fuskarta ne yasa ta shiga taitayin ta cikin rawar harshe ta furta “ am sorry boss” tare da nufar hanyar fita , sai faman tsine wa zuciyarta take akan gaggawanta dan ko zatai yawo tsirara king natane ( uhmm😟).ranshi ba karamun baci yayi ba amma a zahiri bazaka taba tantance Wana yanayi yake cigaba , system din gabansa ya dauka , ya dade yana anfani da ita ka fun ya ajje ta ya lumshe ido.

Wutace keci sosai ta ko ina , da anyi kokarin kasheta karfin ta zai kara yawa, sosai wutar keci da wuta ga wasu bakin abubuwa dake yawa a wajan , gigitacciyar karar da aka sakine ya farkar Dashi daga baccin da ya fara . Launin idanuwansa harsun fara canzawa daga fari zuwa ja,gaba daya jijiyoyin wuyansa sun mike wata irin zufa ya fara , hannunsa na dama ya daga wani siririn diamond din  abun hannune ya fito me dauke da harafin M&T, gaba daya zuciyarsa ba dadi, bazai taba mantawa da bakar ranar nan ba. Zaki ne yashigo office din ganin halin da king yake ciki ba karamun shiga tashin hankali yayi ba, wata drawer yayi saurin nufa cikin gaggawa ya dakko wata allura, da kyar ya samu yayi wa king a wuyansa,kafun a hankali nunfashin sa ya fara dawowa daidai, launin idan sa da ya kada ya fara dawowa Daidai.

5:30 sukabar company kai tsaye wani part yashiga acikin part dinsa, komai nacikin part din royals ne tunda ga kan kujerun falon da ya gaji da tsaruwa , be bata lokacin ba Kai tsaye bedroom din falon ya shin shima sosia dakin ya dahu iya haduwa.

Ya dau kusan 10 minutes cikin toilet kafun ya fito sanye da white bathrobe kall dashi,jikakkiyar gashin kansa sai faman tsiyayar ruwa take. Wata kofa dake gefan Hagu ya shiga , ya dade a ciki kafin kamshin turaran sa ya kara de ko ina, a hankali yake fitowa daga cikin dakin , shigarsa ba karamin kyau tayi masa ba , yayi kyau sosai har ynxu fuskarsa a daure take .

Masallaci suka dufa shi da zaki bayn an idarne suka dawo gida kai tsaye part din ammi ya nufa, ba kowa a part din,sai yalwataccen Hasken da ya cika falon, bin ko ina na falan yayi da rikitaccen idanuwansa, ringing din da wayarsa keyi ne ya katse masa, be dauki wayar ba har sai da  ta kusa tsinkewa ,daga cikin wayar bata bari yace komai ba tace “part din granny now” , tana gama fadar hakan ta kashe wayanta.

*******
Zazzaune ko wannansu yake a falon , ko wa ka gansa cikin farin ciki da annashuwa, daga gefe daya wasu yan matane su su hudu zAune a wajan sai faman hirarsu suke , daga Dayan side din ma wasu manyan mutane ne ke tattaunawa. A hankali kamshin turaransa
Da baya boyuwa ya kara de ko ina na cikin falon, lokaci d’aya falan ya dauki shiru kowa hanyar shigowa ya zuba wa ido, a hankali yake taka kafarsa har ya shigo falon , fuskarsa kwata kwata ba alamun murmushi sai ma kara kadeta da yayi, sosai farin kayan jikinsa ya futo da tsantsan kyawunsa,motsa bakinsa yayi ciki ciki da yin sallama, a tare falon suka amsa dan ba wai sallamar sukaji ba ta motsin bakinsa suka gane. Zoyace ya taho da gudu da niyar rungumeshi, kallan da yayi matane yasata Jan burki “ana asf akhi( am sorry brother )kwalla harta fara tarar mata, lumshe idanuwansa yayi tare da bude mata hannusa guda daya , a guje ta karasa wajan sa tare da rike hannunsa” welcome back akhi , I missed you the whole day”, lumshe mata ida nuwansa yayi tare da budewa kasa kasa ya amsa mata “ me too”, direct inda mahaifinsa yake ya nufa, zazzaune ko wannansu yake cikin takaitaccen magana ya gaishesu, kowa amsa masa yayi sai faman binsa da kallo suke , abeey sai faman sakin murmushi yake . Hajiya Amina ( uwar gidan uncle musaddiq) wacce ake kira da mamy ce ta soma magana “ Kai dai king kayi wuyar gani, ba a ganinka Indai ba a part din dada ba ko na ammonia”, matar uncle Saleem ce ta Dora “ Aushe duk kanwar jace “. Murmushi ammi ta sakar musu “ Kude kawai kun fada ne”, mikewa king yayi tare da nufar wani sofa dake can gefe dasu, kallan dada zoya tayi, cikin tsokana ta kira sunan ta”dada”, harara dada ta wata a mata “kinibabbiya ba kiran Allah da annabi kikai mun ba, tunda kinga ubanki ai dole kikashen murya”,langwabar da Kai zoya tayi “Haba my dada nasan akhi na beci abinci ba , he need some coffee before eating”, tsaki dada taja “ ke kika sani kuma inma zagina kikai ba na hanaki yimun magana cikin yaran nasara ba, wani wai kamfin ( coffee)ke kika sanshi”,kowa na falon yadda dada ta kira coffee din sai da yaso basu dariya amma ba damar yi harta king maganar taso bashi dariya amma sai wani hade rai da ya kara.kallan akhi dake gefe zoya tayi, saurin daga mata hannu yayi alamun ba ruwansa ,maida kallan ta tayi kan ummey , itama dauke idanuwanta tayi  daga kanta,mikewa ammi tayi nida ba a sako niba bari na bada coffee din, kulle idanuwanta zoya tayi tana dariya ,daya Daga cikin yan matan ne ta mike, kallanta ummey tayi amrah ina zuwa, cikin in ina wadda aka kira da amrah ta soma magana “dama zan taya ammi ne”jinjina mata kai ummey tayi , direct kitchen din dada ta nufa , basu dade ba suka fito daga kitchen din cikin yanga amrah ta ajje masa tray din abincin, “yaya king sannu da hutawa”, kamar wacce tayi magana da dutse yana zaune ko motsawa beyi ba ballantana tasa ran amsawa, zoya na gefensa a haka ammi ta fito da cup din coffee sai faman tiriri yake dayan kuma kayan tea ne a ciki da yaki bornviter , mika wa king coffee din tayi , lumshe mata ida nuwansa yayi , murmushi ta sakar masa kafun ta mikawa zoya tea dinta.beci abincin da aka kawo masa ba sai coffee dinsa da yake sipping a hankali yana gama sha ya mike tare da ce musu “good night “yana gama fada ya kama haryan fita . Cikin daga murya zoya ta soma magana “Laylat saeidat akhi, uhibuk( good night brother, love you)”,girgiza Kai kawai king yayi da barin part din. Sai a sannan yan matan suka tare da cigaba da hirarsu, dummy ce ta kalli amrah , Lalle amrah da raban kin kusa Shan Mari a wajan yaya king, Kinsan halinsa Sarai ba a burgeshi, cikin kasa kasa ihsan tace Garin masoya baya nisa kunsan yadda take mugun sonsa,murmushi amrah ta saki jin abinda ihsan tace “dadi na dake ihsan kin fisu fahimtar abu”ni kadai nasan yadda nake sanshi kumashidin mallakinane, dariyar mugunta firdausi ta saki , cikin kasa kasa da murya tace “mugani a kasa”, hararar ta amrah tayi dan Tasan itama san king take shiyasa basa shiri sosai , duk wannan magan ganun nasu cikin kasa kasa da murya sukai ba mejinsu, dago idanuwanta amrah tayi bata saukesu akan kowa ba sai nan auntyn ta , itama auntyn Tata daga mata hannu tayi alamun jinjina, firdausi ma maida hankalin tayi kan mahaifiyarta lokaci daya suka sakar wa juna murmushi duk wannan abun da suke ba Wanda ya lura dasu .

(Uhmmmm 🤭😟)

💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖

Duk karfin izzata (star lady)
Gidan aunty (mss Lee)
Sarki sameer( xeemat love)
Jini daya ( mss bbk)
Ya fita zakka (maman sayyid)

Comment and share

‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/GOZ7a2miBjZ4vUjRXdRdrA

💖GIDAN AUNTY💖

      ( A heart touching love story)

         By mss Lee

💖THE TALENT TROUPE WRITERS 💖

PAID BOOK

BOOK 1 📕

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button